GARKUWA Part 1 by WWW - Dlhausanovels.com - NG

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 309

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘

🦚🐍 🤴 🏻 💘

11:56 Am TUESDAY OCTOBER 20.

*GARKUWA*
PAGE 1

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na


www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na
yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng


You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__
*Littafi na ɗaya. Shafi na forko!*

Free page

*Gargaɗi! Gargaɗi!! Gargaɗi!!! Ban yardaba! ban Amince ba! ban lamunceba! A juya
min labarin LITTAFINA tako wacce sigar bana so ban bada damaba in kana buƙata akwai
number ta a jiki ki\ka nemi izinina a kiyaye domin zama lafiya yafi zama ɗan sarki!
In kunne yaji gaggan jiki ya tsira. Kuma hanyar lafiya a bita da shera yafi, wannan
littafin haƙin mallakarsa nawane Aysha Aliyu Garkuwa!.*

Bismillahirahamanirahim
Ina mai farawa da sunan Allah mai rahama mai jinƙai mai komi mai komai.
Ina gode Allah daya bani aron rai da lafiya da nitsuwa da konciyar hankali ya
bani damar fara wannan littafinawa mai suna GARKUWA. Ya Allah ina roƙonka ka tsare
min tunanina da hannuna ka tsare min al'ƙalamina daga rubuta shari da duk wani abu
da zai zamo guba ko masifa a rayuwar al'ummar Annabi, ya Allah ka bani ikon rubuta
al'khairi da abinda zai zamewa al'ummar Annabi dan al'farma Annabi da Alqur'ani mai
tsarki, ya Allah ka bani rai da lafiya dani da masu karatu ka nuna mana ƙarshen
littafin nan lafiya kamar yadda ka nuna mana forkonsa lafiya, Amin ya rabbil
izzati...

*LITTAFINA NA KUƊI NE, BIYA ƊARINKI UKU KACAL DOMIN SAMUN DAMAR KARANTASHI BA TARE
DA HAƘƘIN KOWA A KANKIBA, AKWAI SP GROUP SHI KUWA 1K PASTING NASU YAFI NA ƳAN 300
YAWA, TURO ƊARI UKU TA ASUSUNA 0005388578 JAIZ BANK AISHA ALIYU GARKUWA, SAI KI
TURO SHAIDAR BIYANKI DA WANNAN NUMBER TAWA 09097853276, ƳAN SPECIAL GROUP BANA SON
KATI, GA POS BURJIK A GARI, KUMA YAN 300 IN DAI KINADA DAMA DAN ALLAH YIMIN
TRANSFER TA AC YAFI, AMMAN IN YA ZAMA DOLE BA MATSALA TURO KATIN MTN NA ƊARI UKUN,
KANA BA HOTON KATIN ZAKIYI KI TURO MINBA, A A NUMBERS ƊIN ZAKI RUBUCE KU TURO MIN*

Dan girman Allah da Manzonsa.


masu tambayata tsoffin littatafaina ku daina bana so.
Ku nema a cikin groups zaku samu, in dai ba Hukuncin Allah ko NAKASA BA KASAWA
BACE, da GARKUWA kada ku tambayeni in kuna ƙaunar Allah, in kuwa bakya ƙaunar Allah
to tambayeni.

*YAHUNDE! Babban birnin ƙasar Cameroon.*

Cikin wani kekyawan rugar FULANI mai tarin al'barkatun duniya.


Kota wani sashi Allah yayiwa Rugar Arɗo Babayo, ni'imomi na musamman, makiyaye ne
cikakkun Fulanin ƙasar Cameroon.

Ranar wata jumma da yammaci la'asar sakaliya, makiyaya nata dawowa gida yayinda
kota ina. Shanu tumaki raƙuma awaki zabbi keta kai komo ko wanne na nufar garken
ma-mallakinshi domin ko dabba tasan uban gijiyinta,
Garken Arɗo Babayo yana ɗaya daga cikin garken da babu kamarsa a nahiyar Afirka
baki ɗaya,
Yanada MAKIYAYA a ƙala mutun arba'in.

Garin ya fara duhuwar sanire alamun yanayin sanyin damina da ake ciki ko ina yayi
kore shar ga tarin tsirrai kana ga igiyar ruwa da yayiwa rugar Babayo ƙawanya,

Wasu dattawane a zaune bisa ƙarƙashin bishiyar ceɗiya dake ƙofar gidan Arɗo babayo
Farin dottijon ne mai cikar zarra da mutun taka ke zaune a tsakiyarsu, kana sai
wasu manyan mutane dake zagaye dashi.
A gefen damanshi kuwa wani Babban mutun ne mai cikar zarra da wadatar zuciya ga
tarin alamomin mutuntaka da cikar imani da haiba, bisa dukkan alamu tattaunawa
sukeyi kan abinda ya shafi rayuwarsu.
Da sauri Arɗo Babayo ya ɗago kanshi ido ya zubawa sashin damanshi, inda ya hango
wasu ƴan saffa-saffan samari guda huɗu suna biye da ƙatuwar suntsuwar Boleru babban
cikinsu ne a gaba wanda zai kai shekaru 15 sa mai binsa wanda zai kai shekaru 13
sai mai bin masa da zai kai shekaru 11 kana sai ƙaramin cikinsu da bazai gaza shara
9 ba, gudu sukeyi sosai da iya ƙarfinsu sun tasa tsuntsuwar Boleru nan a gaba wacce
ta kasa firewa sai gudu takeyi da sawunta biyu, bisa dukkan alamu tsuntsuwar tanada
tsohon ciki mai girma.
Gudun da takeyi gudune na ceton rai.
Arɗon Babayo daya buɗe baki kenan da nufin zaiyi magana sai kuma ya juyo ya kalli
kekyawar yarinya ƴar kimanin shekaru 8 a duniya wacce take kan cinyar mutumin nan
dake gefen damanshi.
Ta miƙe da sauri cikin tsananin azama da harshen fillanci da ƙarfi tace.
("Acce mo) Ku barta". Sai kuma ta juyo ta fuskanci mutumin da take zaune kan
cinyarshi cikin kaɗuwa da firgici da alamun tsananin tausayawa tace.
("Appa a vi'a ɓe acca tokkugomo nɓe naunanmo) Appa kace su dena binta zasuji mata
ciwofa".
Murmushi Arɗo Babayo yayi tare da cewa.
"Kai Gainako ku barta zaku kamata a hankali ai".
Da sauri wanda aka kira da Gainako yace.
"Baffa Giɗaɗo ne yace mu kama mishi ita mu yanka mishi".
Da sauri suka juyo kan ƴarinyar jin wani irin ihu da tai tare da cewa.
"Ku yankata kuma, Appa kajifa wai zasu yankata, wayyo Appa kace musu kar su
yankata, gashifa tanata kuka gashi sun sa taji ciwo a hannunta yanata zunda jini".
Da mamaki suke kallon ƴarinyar sabida furucinta na wai hannunta yaji ciwo yana
zubda jini, ina tsunstsuwar Boleru ina hannu?.
Wanda ta kira da Appa ne ya jawota gabanshi tare da cewa.
"Parvina tsuntsu kuma tanada hannune?."
Da sauri ta miƙe tare da ɗaga murya tace.
"Ba tsuntsu bane Appa wlh mutunce gata nan da ciki gashi ma tana kuka tana-ta kare
cikin jikinta".
Cikin mamaki suka zubawa tsuntsuwar Boleru ido su dai Allah ya gani gaba ɗayansu
tsuntsuwa suke gani tana guduwa da kyar wanda kuma kowa ya ganta yasan tanada
tsohon cikine.
Giɗaɗo ne wanda shine ƙarami yaron ɗan shakara 9 kuka yasa tare da cewa.
"Wayyo ya Gainako kayi sauri ka kamo min ita karta gudu".
jin haka yasa ƴarinyar nan da aka kira da Parvina ta miƙe da gudu tabi bayansu tana
gudu tana kuka wanda har ga Allah daga cikin zuciyarta yake fitowa kuma ita ba
tsunstsuwar Boleru take ganiba a zahiri a fili da kuma baɗinin Allah ya nuna mata
mutum take gani kekyawar mace mai cikar sura da kamala kana ga ƙaton cikin dake
jikinta wanda haihuwa yau ko gobe.
Ihu takeyi tana binsu tana cewa.
"Dan Allah ku barta zataji ciwo Wayyo Appa kazo mu ceceta zasu kasheta."
Ihu tasa da dukkanin ƙarfinta tana yarfa hannu cikin gigita take kurma ihu lokacin
da su Gainako suka isa kan tsuntsuwar Boleru suka danne fikafikinta suka kama suka
medata baya.

Ihun da tayine yasa gaba ɗaya dattawan nan suka miƙe tsaye suka biyosu a guje dan
ihun nata ya cika illahirin rugar babu wanda zaice baiji ƙaranta ba dan saida
tsaunuka da kogin da suke gaɓarsu ya amsa da sautinda da take cewa.
"Wayyoooooooo! Appaaaaaa! zasu kasheta, sun karya mata hannu".
A gigice suka ƙaraso wurin wanda ganin yadda take a gigice yasa Appa kamata da
sauri, yayinda ita kuwa taketa son zillewa tana fiffizgewa daga hannunshi, Arɗo
Babayo kuwa tsawa ya dannawa Gainako tare da cewa.
"Kai! Kai!! Kai!!! Gainako sake tsunstsuwar nan saketa".
cikin sanyi Gainako ya sake tsunstsuwar, daga tsaye ta faɗi ƙasa hakan yasa,
Parvina sake saka ihu da ƙarfi ta fizge ta nufi kan tsuntsuwar da ita mace take
gani kuma sanadin saketa da akayi daga sama ta faɗi ƙasa a kife yasa cikinta buguwa
wanda yayi sanadin a take naƙuda ya fara murɗarta kana ga jini daya fara bin
sawunta.
Tana isa gaban tsuntsuwar tasa hannunta ta kamo hannun baiwar Allah nan da ita
kadai Allah ya bawa damar ganin a mutun ba tsunstsuwar Boleru ba, hannunta data
riƙo su kuma kab mutanen wurin gani suke fiffigen tsunstsuwar ta riƙo.
Cikin kuka take shafa kan kurciya a ganinsu yayinda ita kuwa hawayen fuskar matar
da take ganin take sharewa cikin muryar kuka tace.
"Sannu sunji miki ciwoko, kice musu ke ba tsunstsuwa bace ki gaya musu ke mutunce
kamarsu ki gaya musu kema bani adam ce karsu yankaki".
Kuka ta kuma fashewa dashi ganin matar nan bata magana sai dai hannunta data riƙo
ɗin ta ganshi tamkar robo wato alamun hannun a karye yake, cikin sauri ta sake
hannun tare da cewa.
"Appa mu tafi da ita mu kaita wurin masu gyaran ƙashi".
To al'amarin parvina fa ya fara zarta zaton mai zato ya fara shallake tunanin mai
tunani abin ya girmi shekarun Dattijannan.
Shi kuwa Giɗaɗo kuka ya fashe dashi tare da nufarta yana mai cewa.
"Ki bani tsunstsuwata ai tawace nine nayi ta renonta kullum tare muke cin abinci
tare komai duk abinda naci sai na barmata dan tayi ƙatuwa, kuma yanzu kice baza a
yanka min itaba".
faɗawa tayi jikin matar wanda su a ganinsu ruggume tsuntsuwar tayi ita kuwa parvina
cikin kuka ta juyo ta kalli Giɗaɗo tare da cewa.
"Kai mayene ko? To Wlh bazan baku itaba in dai ina raye a duniya bazan bari a cutar
da itaba, babu wanda zai kasheta a gabana sai dai in bana raye ku bar ce mata
tsuntsuwa wallahi tallahi mutunce kamar kowa".
Kiran sallan magriba da akayine yasa ɗaya daga cikin dottijon mai suna Yayari yace.
"Arɗon Babayo lokacin salla yayi".
Sai ya kuma kalli Giɗaɗo da Gainako da Seyoji da Ja'eh yace.
"Maza kuje kuyi al'wala kuzo muyi salla, kai Giɗaɗo ka bar mata tsuntsuwar kurciyar
kaji ko gobe da safe zabbi za'a yanka muku ku gasa kuci".
Cikin kuka Giɗaɗo yace.
"Wallahi Ni dai ta bani tsunstsuwata, bana son zabuwar ni ko ɗawisu zaku yanka min
bana so kurciyata nake so a bani abuna".
(Giɗaɗo sabo da kaza baya hana a yankata kenan)
Cikin tsawa Arɗo Babayo yace.
"Kai tafi daga nan ba kaine babba ba kaci girma ka bar mata tsuntsuwar kaji ko
Giɗaɗona".
Tura baki yayi yabi bayan yayun nashi yana cewa.
"Ni a dena cemin Giɗaɗo ai dani Giɗaɗone da komai nakeso zaku bani".

Basubi ta kanshi ba duk suka meda hankalinsu kan Parvina da tsuntsuwar dan ganin
ƙasan tsuntsuwar Bolerun yana zubda jini, wannan abun ya sasu cikin nazari to,
amman sai mgnar Parvina ta katse musu nazarin da cewa.
"Allah sarki gashi sunji mata ciwo har sun fidda mata jini".
Jin haka yasa suka sa a ransu yess jinin ne daya fita sanadin jin ciwo,
cikin kula Arɗo Babayo ya matso parvina da taketa shafa kan tsuntsuwar da suke
gani a idanunsu a hankali ya kamo hannunta cikin lallashi yace.
"Parvina muje cikin gida ko, kinga dare yayi kiyi salla kici abinci, tsuntsuwar
taki kuma ki saketa zata fire ta hau makwancinta".
Da sauri ta fara jujjuya mishi kai hawaye na zuba tace.
"Baffa Arɗo ta fire kuma? Bata da fiffigefa mutunce fa,tare zamu kwana da ita
wallahi ba tsunstsuwar bace, mutunce ku daina ce mata tsuntsuwa, karmu barta ta
kwana a woje".
Sai ta kuma kama fiffigen tsunstsuwar tace.
"Ga hannunta nan sun karya mata".
Sai ta kuma kama ƙafafun tsuntsuwar tace.
"Baffa Arɗo kaga ga sawunta ga idonta tanata zubda hawaye ga cikinta ga kunnenta ga
bakinta ga gashin kanta har bayanta".
Kallon-kallon suka tsaya sunayiwa junansu,
domin kafiyar parvina kan cewa Wannan tsuntsuwar Boleru mutun ce bani Adam ce ya
fara basu tsoro to ko dai ƴarinyar tayi gamone? Koko tsuntsuwar iskace?.
cikin tsoron daya fara rufe Appa baki na rawa ya kamo hannun ɗiyar tashi da yake
masifar so tamkar ƙoƙon ranshi cikin kaɗuwa da muryar fillanci kasan cewar sam
fulanin ƙasar Cameroon basa jin hausa koda kawo min wuƙa in kashekane shiyasa cikin
fillanci yace.
"(Parvina tsonɗu on fa na ɗum innu adamajo, ko waɗi a vi'ata neɗɗo on) parvina
tsuntsuwace fa ba mutun bace meyasa kicewa mutunce?".
Kuka ta kuma fashewa dashi harda shessheƙan gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi ganin
yadda jikin matar ke karkarwa. Ruggume tsuntsuwar kurciyar tayi a ganinsu yayinda
ita kuwa cikekkiyar kamilar mace take gani hannunta matar ta kama ta juya ta nufi
cikin gidansu dansu da Gainako suka shiga tana kukan shur-shur da hawayenta.

Zurui sukayi suka rakata da ido har ta ɓacewa ganinsu.

A mashigar gidan sukayi kiciɓis dasu Giɗaɗo da sauri ta koma gefe.


Shi kuwa Giɗaɗo wani irin dundu ya kima mata a tsakiyar bayanta tare watsa mata
harare cikin fillanci yace.
"Hegiya muguwa wallahi sai na yanka tsuntsuwata muna fuka". da sauri tasa jikinta
ta kare tsuntsuwar, tare dayin sauri tayi cikin gida.
Seyoji ta samu tsaye gefen mamansu yana bata labarin tsuntsuwar da duk gidansu babu
wanda bai san Giɗaɗo da itaba dan yanzu kimanin watanni takwas kenan kullum babu
dare babu rana a nan gidan nasu tsuntsuwar take rayuwa kullum in Giɗaɗo yaci abinci
ya rage inta kuma sai tazo tayi ta tsastsaga har sai tacinye duk abincin daya bari
kana ya ajiye mata madarar shanu nanma tazo tasha,
idan tasha ta ƙoshine sai ta juya da tafiya take barin cikin gidan ta koma bakin
kogi.

Da sauri Mamansu Giɗaɗo ta kalli Parvina tare da cewa.


"Parvina na zo nan zo keda tsuntsuwar ki kada ki damu babu mai yankata".
Da sauri ta iso gaban matar tare da cewa.
"Inna ki hanasu yankata Allah kuwa ba tsunstsuwa bace mutunce".
Cikin kula matar tace.
"To parvina kada ki damu babu mai yankata daga yau ta zama taki, yanzu ajiyeta kije
kiyi al'wala kizo kiyi sallah".
Da sauri tace.
"To".
A jiye matar tayi bisa taburmar dake tsakiyar gidan, kana taje tayi al'wala tazo ta
shimfiɗa sallaya a gefenta, itama Inna gefenta ta shimfiɗa suka sa baiwar Allah'n
nan a tsakiya...

Kamar da wasa da abin ya girmama domin koda sukayi salla isha'i fir parvina taƙi ta
rabu da tsuntsuwar nan.
Su kuwa su Arɗo Babayo sun mance batun tsuntsuwar ma, tunda sukayi sallan isha
sukaci abinci.
Suketa lissafin kan dabobbinsu kama daga kan Raƙuma, Dawakai, shanu, tumaki,
raguna, awaki, ɗawisu, tolo-tolo, zabbi, tattabaru, saida suka waresu baki ɗaya dan
sanin adadin zakkar da zasu fitar sannan suka gama fayace na zakkar kowanne daga
ciki da shariya ta umarci a bada zakkanshi.

Hira sukaci gaba dayi kan abinda ya shafi kiwon nasu.

A can cikin gida kuwa, tunda Inna ta gama yiwa su Arɗo Babayo gashin zabbi ta haɗa
da madarar shanu aka kai musu taketa fama da Parvina kan yadda ta tasa tsuntsuwar
nan a gaba tana mata magiya kan tasa hannunta taci abinci,
ganin bazata iya ci da hannun nata bane yasa iya tasa hannun tana bata abinci har
baki tana amsa tanaci yayinda hawaye keta kwaranya a fuskarta babu ƙaƙƙautawa.

Koda taci ya isheta sai ta mirgina alamun zata konta.


Ganin hakan yasa parvina kallon inna cikin sanyinta da nitsuwarta tace.
"Inna tare zamu kwana da ita".
Kai inna ta jinjina mata kana ta miƙe tace muje cikin ɗakin kinga gari yayi sanyi
Giɗaɗo da kike tsoron kada kiyi bacci yazo ya ɗauke tsuntsuwar ma yayi bacci".
Kai ta gyaɗa kana ta miƙe suka shiga cikin ɗakin,
bisa katifar gado huts ɗinnan ta zauna tare da tsuntsuwar a gefenta, yayinda ga
hasken wutan da aka kunna janareta ya gauraye ko ina na gidan da kuma ɗakin.

Inna kuwa kan gadonta take,


suna ɗan hira,
yayinda sam hankali parvina kan tsuntsuwar nan yake.
Tashi zaune tayi lokacin da taga gaba ɗaya jikin matar nan yana ta karkarwan ga
hannunta dasu Gainako suka karya ya kumbura simtin, hannunta mai lafiyan kuma ta
ɗaurashi kan tirtsetsen cikinta, gaba ɗaya jikinta zufane keta tsastsafowa tako
ina,
cikin tausayawa parvina tace.
"Sannu hannunkin ke ciwo ko? Kiyi haƙuri gobe da safe zamu kaiki gidan mai magani".
Inna ce ta zubawa Parvina ido cikin yanayin tsoro tace.
"(Parvina ɗun sonɗufa) Parvina tsuntsuwace fa. ki dena magana da ita ba jinki
takeyi ba".
Da sauri ta jujjuya kanta hawaye na zubo mata tace.
"Inna Wallahi tallahi mutunce ku dena ce mata tsuntsuwa inna ki ganifa bata da lfy,
jikinta duk rawa yakeyi".
Kai Inna ta gyaɗa kana tace.
"To na yarda yanzu dai ki kwanta kiyi bacci sai gobe da safe zamu kaita gidan mai
gyaran karaya da targade".
Jin hakane yasa ta konta tare da lumshe idonta. Sai bacci ya fara saceta sai kuma
tayi firgigit ta farka,
ta kuma tada Inna sabida, suntsuwar nan ta kasa nutsuwa, yayinda ita kuwa Parvina
take ganin baiwar Allah'n cikin mawuyacin halinda ya rintane yasa bata gane cewa
matarnan naƙuda takeyi ba.

A haka suka kwana, har garin Allah ya waye basuyi bacciba, sabida ita kanta inna
yanzu tsoron tsuntsuwar ta fara haka kuma take tsoron parvina, ita kuwa baiwar
Allah'n nan zafin ciwon naƙudane ya hanata bacci ita kuwa parvina tausayin matar da
mutanen garin da gidan ke cewa tsuntsuwar Boleru ne ya hanata bacci.

Asuban fari suka tayi sukayi salla,


daga nan suka fito tsakiyar gida, kai tsaye sashin Arɗo Babayo suka nufa ita da
Inna,
shiru sashin nashi alamun basu dawo masallaci ba, cikin alhini da tsoro Inna ta
kalli Parvina cikin daburtacciyar murya tace.
"Ajiye tsuntsuwar nan haka kina rike da ita kamar kin samu uwarki maza ajiyeta".
Cikin zubda hawaye ta tsuguna ta ajiye tsuntsuwar kan buzun Arɗo Babayo,
Wanda dai-dai lokacin ne kuma Arɗo Babayo da Appa, Gainako, Seyoji, Buba, Giɗaɗo,
Ja'eh suka shigo kamar yadda suka saba.
Cikin mamaki suka zubawa tsuntsuwar Kurciyar nan ido ganin yadda taketa birgima a
kan buzun tana wasu irin cure-cure tamkar ranta zai bar jikinta.
Ita kuwa Parvina kuka ta farayi bil haƙƙi da gskya tanayi tana yarfa hannu,
Buba ne yayi maza ya nufi kan tsuntsuwar kurciyar tare da cewa.
"Haukan banza a kan buzun salan Arɗo zaku ajiye tsuntsuwar.
Ihu mai ƙarfi parvina tasa ganin Buba ya ɗaga kafarshi da ƙarfin bala'i zai kaiwa
tsuntsuwar harbi da naushin ƙafarsa,
Kamar a mafarki kamar gilmawar walƙiya tamkar daga sama.
Sukaga tsuntsuwar Kurciyar nan tayi wani irin ɗagowa ta karkaɗa fikafikinta cikin
ƙudurar Ubangiji da hikimarsa da buwayarsa sai gata-ta d...!
Salon na dabanne labarine mai cike da sarƙaƙiya, biya 300 ko 1k ki karance
badaƙalar cikin salama.

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 2

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*LITTAFINA na kuɗine, akwai na 300 wanda a wata ɗaya za'a gama Part 1, akwai kuma
na 1k wanda a mako biyu kacal za'a gama Part 1 da izinin Allah. Yimin TRANSFER ɗin
darinki uku ko 1ooo ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu
Garkuwa. Sai ki turo shaidar BIYANKI ta number 09097853276 Ayyah ƴan SP Group
banda kati, in baki da ac bada a POS. Kuna ƴan 300 in dai da hali turamin ta ac
yafi, in babu kuma to turo katin mtn na ɗari uku ta layin 09097853276. Na roƙeki da
Allah da Manzonsa da darajar iyayenki in dai kin san niyarki ki saya ki fiddamin
littafina, dan daraja da girman Allah da tsarkin al'ƙur'ani kada ki saya Please
kuwa darajar iyayenki kada ki saya, ba don niba sai ɗan Allah da manzonsa da iyayen
da suka haifeki/ka*

~AKWAI KAYAN GYARA HAƊIN AMARE DA MASU JEGO, DA MASU SABUNTA AMARCI, IN KINASO KI
TUNTUƁI WANNAN NUMBER 09097853276~

Ta juye ta dawo mutun *bani Adam* mace fara ƙal mai tsananin kyau da cikar sura da
haiba.

Wani irin zabura sukayi cikin tsananin tsoro da firgici da tashin hankali suka
zaburi gaba ɗayansu, Giɗaɗo kuwa da azaban ƙarfi ya afka jikin Arɗo Babayo,
Inna kuwa gaba ɗaya jikinta rawa da karkarwa yakeyi tamkar mazari wata iriyar
fitinenneyar zufa mai azabar ƙarfice taketa tsastsafo mata tako wani sashi na
jikinta.
Seyoji, Gainako, da Ja'eh, gaba ɗaya jikinsu karkarwa yakeyi tamkar mazari.
Giɗaɗo kuwa wani irin juyawa yayi a firgice ya yunƙura zai gudu, Arɗo Babayo ne
yayi hamzarin kamo hannunshi ya rikeshi gam.

Zabura sukayi.
Gaba ɗayansu sabida wata iriyar fitinenneyar iska mai azabebben sanyi daya fara
kaɗawa yana rausaya ganyayyaki da dukkan tsirran dake yakin surururururu haka iskar
ke kaɗawa a hankali tana ratsa jikinsu.

"Innalillahi wa innalillahi rajiun. Hasbunallahiwani'imanwakil".


Shine abinda suketa maimaitawa gaba ɗayansu cikin tsananin kaɗuwa, ruɗani, firgici,
tashin hankali da tarin tsoro, da nitsuwar ganin ikon Allah.
Iskar dake karkaɗawa ce tasa gaba ɗaya suka hautsine.
Parvina kuwa da sauri ta faɗa jikin baiwar Allah'n tare da ruggumeta.
Baki na rawa ta fara addu'a.
"Allahumma inni as'aluka khairaha wa'azubika min sharri ha".
Da ƙarfi take fidda sautinta tana maimaita addu'ar.
Wanda sanadin haka suma kab suka fara bin bakinta.

Allah cikin ikonsa da ƙudurarsa sai ga iskar nan ta fara lafawa a hankali.

Cikin al'ajibi da tsoron ƙudurar Allah suka ware idanunsu baki ɗaya a kan baiwar
Allah'n nan, da
shigar suturar dake jikinta ne yayi masifar sasu ruɗani.
Cikin dakiya da ƙarfin zuciya Arɗo Babayo ya kalli Buba a hankali yace.
"Buba ɗauki su Giɗaɗo ku tafi garke kuje kuyi tatsa".
Kai ya gyaɗa mishi domin baki da jarumar Buba sun tafi,
Dan a iya tsawon tarihin rayuwarsa ko a films ko a books story bai taba ji da
katari da makamancin abinda ya yagini a zahiriyaba, tsuntsuwar Kurciyar ta zama
mutun mace a gabanshi ba labari aka bashiba ra'anul ayni.
Cikin yanayin tarin kaɗuwa da rawan jiki yasa hannu ya jawo hannun Giɗaɗo daya kifa
kanshi jikin babanshi.
Cikin fillanci yace.
"Zo Giɗaɗo zomu tafi".
Da sauri ya miƙa hannunshi ya kama na Buba kana suka juya suka fita.

Appa kuwa kanshi ya kauda daga kallon wannan kekyawar halittar dake gabanshi a
cikin ransa yace.
"Anya kuwa, wannan mutunce ba iskaba".
Inna kuwa gefe ta ɗan matsa cikin rawan murya na tsoro da hausar da sai ka dage
zaka gane me take cewa tace.
"Ra ga Allah bewar Allah mutun ko al'jan?".
Ido suka tsurawa matar a zatonsu ko zata basu amsa.
Sai dai ganin yanayin da take cikine ya sasu cire tsammanin samun amsarta.

Domin gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, tamkar mazari.


Kana sai zufa dake tsastsafo mata tako wani hudan gashin jikinta,
ta rumtse idanunta da azaban ƙarfi, tasa haƙoranta ta datse lip ɗinta na ƙasa,
duk mace data taɓa haihuwa in ta ganta tasan naƙudace ke azazzabarta.

Tausayin ta ne ya cika zuƙa tansu baki ɗaya.

Arɗo Babayo ne yayi ɗan gyaran murya tare da kauda kanshi daga kallonta sabida
kwarjininta yafi ƙarfin ƙwayar idanunsu cikin sanyi murya yace.
"Allahu wahidun ƙahhar, Mutunce ba al'jana bace, Allah shi ya barwa kansa sanin
dalilin kasan ce warta a cikin tsuffofin tsuntsaye, amman kam tabbas al'amarine mai
tarin girma da sarƙaƙiya, Tine taimaka mata, da zuciya ɗaya ina ji a jikina ba mai
cutarwa bace. Kuma akwai tabbaci da kekyawan zaton musulmace".

Ido ta zubawa mijin nata da yake bata ƙarfin guiwa.


Appa ne ya kalleta tare da gyaɗa mata kai, alamun eh ta taimaketa,
Ita kuwa Parvina cikin tausayawa da zubda hawaye tace.
"Appa kalli hannunta ya kumbura gashi jikinta zafi Appa a taimaka mata".
Hannu ya miƙo ya kama Parvina cikin tausayawa yace.
"Zo nan Parvina za'a taimaka mata kinga bata da lfy tashi a jikinta,
kinga ki dena danne mata hannun da cikinta".
kai ta gyaɗa kana ta kalli matar cikin sanyi tace.
"Sannu!". Bata basu amsa bata kulasu bata kuma hafimtar komai daga garesu,
haka yasa su Arɗo Babayo juyawa suka fita, ita kuwa Inna matsowa gareta tayi cikin
tarin ƙarfin guiwa irin na fulani. Fulaninma irinsu na daji ba irin wasunku na
birniba.
cikin sanyi tace.
"Taso muje daga ciki".
ido ta zubawa Inna cikin yanayin wahalar da takeji,
hannu Inna tasa ta kamo hannunta mai lafiyar, ta miƙar da ita tsaye.
Allah da ikonshi, sai gata a tsaye cas.
Haka yasa Inna ta jata suka koma cikin gida, cikin ɗakinta ta kaita,
a bakin katifar da suka kwana ta ajiyeta,
da sauri ta koma woje wuta ta hura ta ɗaura ruwan zafi.

Kana ta dawo ciki.


Cikin mamaki take kallonta ganin taja ta jingina da jikin gini kana, ta rumtse
idanunta ga hawaye nata kwaranya daga idanunta.
Gefenta ta zauna ta zuba mata ido.
Jin an zauna gefen tanne yasa ta buɗe kekyawan idanunta, cikin kula Inna tace.
"Sannu baiwar Allah, kamar naƙuda kikeji ko?".
Kai ta gyaɗa mata alamar eh naƙudar takeji,
murmushi inna tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah naji sanyi na ƙara gamsuwa ke mutunce, kuma kina gane me nake faɗa a
yanzu, to amman kiyi magana mana".
Kanta ta jujjuya mata alamun.
"Bazan iyaba".
Jin muryarsu Arɗo Babayo ne yasa inna tayi maza ta fito,
Ganin Arɗo Babayo da Appa da kuma Malam Liman da sarkin bakansu wanda yake rugar
makotansu ne yasata saurin fitowa tare da cewa.
"Sannun ku da zuwa Malam Liman, Baka barka da zuwa".
Taburma ta shimfaɗa musu, jin muryar Malam Liman ne na cewa.
"A a bar taburmarnan ina baƙuwar tamu?".
"Tana cikin ɗaki, da alamun tana fama da yanayin naƙuda ne".
Inna ta faɗa cikin alhini.

Sarkin bakanne yayi ɗan gyaran murya kana yace.


"Ina son ganinta".
Arɗo Babayo ne yace.
"To bisimilla, shigo daga ciki".
Ɗakin suka nufa Inna na gaba Arɗo Babayo na biye da ita a baya, kana Appa da Malam
Liman da Sarkin Baka suka rufa musu baya.

Suna shiga suka sameta zaune ta haɗe jikinta wuri ɗaya,


jin motsin shigowar mutanene yasa ta ɗago kanta,
da sauri ta kauda idanunta.
Shi kuwa SARKIN Bakan, kanshi ya rinƙa jinjina wa cikin al'hini yake cewa.
"Mutun ce ba al'janba, baiwar Allah an tozarta rayuwarki."
Sai kuma ya kalli Arɗo Babayo cikin sauri yace.
"Maza a bani madarar shanu mai ɗumi wanda aka tatsa yanzu".

To Arɗo Babayo yace tare da juyawa ya fita, a harabar gida yayi arba da Gainako da
yake shigowa da kwaryar nono,
da sauri ya iso, kana yasa ƙaramar kwarya ya kamfati madarar shanun daketa tururi
sannan ya juya ya koma cikin ɗakin.

Yana zuwa ya miƙawa sarkin Bakan,


yana amsar ƙoryar,
ya ajiyeta a gabanshi jakar fatar ruƙimi da yakesa magungunanshi a cikine ya sauƙe
daga kafaɗarshi, kana a hankali ya fara harhaɗa magunguna a cikin madarar,
saida yasa komai sannan ya kalli Inna yace.
"A bani zuma da zam-zam".
Da sauri tace.
"To". Kana ta miƙo ta ɗauko mishi, koda ta kawo da sauri yasa zumar da zam-zam ɗin
ya gaureyasu,'.
Kana ya bawa Malam Liman da Arɗo Babayo sukayi mata tofin ayatul shifa, a ciki,
kana ya amshi kwaryar.
Inna ya miƙawa kwaryar yace.
"Gashi bata tasha".
Amsa tayi kana ta matso kusa da matar a hankali tasa mata bakin kwaryar a bakinta.
Tare da cewa. "Bismillah ki Sha".
A hankali ta buɗe bakinta, ta fara shan madarar shanun nan da magungunan, masu haɗe
da zam-zam da zuma da kuma rahamar ayatul shifa.
Saida ta sha mai yawa sannan ta kauda kanta.

Ae fa a take saiga naƙuda ta tashi gadan-gadan. Ganin haka yasa su Arɗo kab suka
fito woje ya rage daga ita sai Inna.

Ganin haka yasa Malam Liman tura Ori da yanzu ya shigo yaje ya kira matarsa ta
taimakawa inna su amshi haihuwar.

Ba jimawa kuwa Iya laure tazo, kai tsaye cikin ɗakin ta wuce.

Cikin ikon Allah a take a sauƙaƙe Allah ya sauƙeta lfya, ta haifi yarta mace ƴar
ƙanƙanuwa.

Bayan sun yanke cibiya sun gyara,


komai na wurin.
Kana Inna ta taimaka mata tayi wonka,
ita kuwa iya laure wonka tayiwa jaririyar ta haɗeta cikin zanin Inna ta bawa
Parvina daketa tsalle.

Koda suka fito daga wonka,


konciya tayi a kan katifar, kana iya laure ta kontar mata da ƴar a gabanta.

Ajiyan zuciya ta sauƙe mai ƙarfi kana a hankali ta lumshe idonta, tana son ta tuno
wani abu na rayuwarta ta baya amman ina ta kasa tunowa,
Abu ɗaya takeji bata manceba sunan Allah wanda tunda ta dawo mutun taketa maimaita
kiranshi a zuciyarta dan taji bakinta bazata iya magana ba, amman a ranta tanaji
tana bitar karatun al'ƙur'ani mai girma da tarin addu'o'in kamar yadda takeyi tun
tana a tsunstsuwar ma.

Ganin tayi shiru ne kamar maiyin bacci yasa inna da iya laure suka fito woje.
Sashin Arɗo Babayo suka nufa,
suna shiga sukayiwa juna barkar haihuwarta lfy.
Shiru sukayi baki ɗayansu bayan duk sun zauna kamar yadda Sarkin Baka ya umarcesu,
gyaran murya yayi kana a hankali ya fara magana.
"To da forko dai sai dai muce. Alhamdulillah, mun godewa da yasa sanadinmu wata
baiwar Allah zata samu waraka daga mugun cuta na magauta maƙiya azzalumai marasa
tsoron Allah".
Kai suka jinjina alamun gamsuwa, shi kuwa tonkoshe ƙafa yayi kana yaci gaba da
cewa.
"Kamar yadda kuka gani a yanzu mutunce bani adam ce ba tsunstsuwa bace kamar yadda
kuka gani da zata a baya, aikin sihirine kawai ya maidata haka.
Amman Alhamdulillah tunda gashi yanzu Allah yayi ikonshi ya karya abun da akayi
mata ya kuma sauketa lfy dama shi asiri tasirinshi kaɗanne ga wanda yayi imani da
Allah kuma dole gsky zatayi halinta watan-watarana".
Arɗo Babayo ne yace.
"Allah mai iko, mutun a maidashi tsuntsuwar Boleru kai abinnan da al'ajabi".
Kai ya gyaɗa mishi tare da cewa.
"Ɗan Adam kenan mai wuyar gane hali babu mai sanin halin mutum sai Allah, domin shi
ɗan adam dare".
Sai ya kuma kalli Inna tare da cewa.
"Yanzu tayi magana ne?".
Da sauri Inna tace.
"A a batayi mgna ba sai dai in anyi magana tanaji kuma tana ganewa".
Kai ya rausayar tare da cewa.
"Zatayi magana in sha Allah, yanzu aci gaba da kula da ita yadda ya dace zan bata
magunguna kuma,
sannan kada kuji tsoronta ko kaɗan in sha Allah ba mai cutarwa bace".
Malam Liman ne ya gyara babbar rigarshi tare da cewa.
"To wannan baiwar Allah'n ko daga ina ta fito? Ko ta yaya zamu gano yan uwanta
danginta ahlinta ko wani nata a duniya?".
Sarkin bakanne yayi ɗan gyaran murya kana yace.
"In sha Allah ita in ta dawo haiyacinta, zatayi mana bayanin komai zata faɗa mana
sunanta sunan garinsu sunan iyayenta sunan mijinta da anguwarsu sai mu mikata
garesu".
Appa ne ya ɗanyi ajiyan zuciya tare da cewa.
"Allah ya bata lfy ya kuma dawo da ita cikin haiyacinta, kuma in sha Allah duk wani
abu daya kamata ayimata a duniya zan mata har sai munga ta samu' lafiya ta koma ga
iyayenta".

Da haka sukayi ta tattauna duk abinda ya dace ayi mata.


Anan kuma sarkin baka yaje da kanshi ya ɗaure mata karayar hannunta yayinda Parvina
kuwa ke like da ita...!

Haka Inna da iya laure sukayi ta kula da ita a cikin wannan satin sunan...!

************

...Bayan shekaru Goma sha biyu...

Cikin Ƙasar Kautal A Jihar Ɓadamaya state.

A wani yanki na Ɓadamaya state, cikin Shikan local Government area a wata rugar
FULANI mai suna.
*RUGAR BANI*

Garin Shikan wani yankine daga yankunan Ɓadamaya yankine mai tarin ƙabilu ma
banbanta addinai da al'adu wanda duk yankun Ɓadamaya shida Bimu sune sukafi tarin
ƙabilun sai dai babbancin mafiya yawan kabilun Bimu musulmaine saɓanin mafiya yawan
ƙabilun Shikan kafurine maƙiya Allah da Manzonsa.

Shikan shine sashin da yafi tara ƙabilu mafiya yawa, masu baƙaƙen zuciya ƙabulun da
hasken addini bai cimmusuba.
Ƙabila mafi rinjaye a yankin Shikan itace ƙabilar ɓachama. Mafi akasari Ɓachamawa
mutanene kafurai ne marasa ɗigon imani a zuƙatansu marasa son zaman lfya, mugunta
da kisa shine abinda ke sasu farin ciki, abinda kawo ya sanine duk sanda akaji
jihar Ɓadamaya cikin wani tashin hankali to daga ƙabilar ɓachama ne.

Duda yawan ƙabilu na garin Shikan hakan baisa fulani sun sakar musu garinba, domin
tushen garin na fulanine, sabida kowa yasan makiyayi basa nesa da wurin damshi da
ruwa, domin rayar da ababen kiwonsu.
Haka yasa akwai musulmai Hausawanmu da tarin yawa cikin garin Shikan, wanda duk
rintsi da wahala sunƙi barin garin, koda yake hakan baya rasa nasaba da irin
al'barkatu da ni'imomin da Allah yayiwa garin.

Daga gefen. Garin Shikan akwai babban kogin da yakeda ruwa biyu wanda ko wucewa
zakayi ta kan babban gadan da titin da zai kaika cikin Ɓadamaya zaka hangi ruwane
kala biyu a kogi ɗaya basu kuma taɓa haɗewa wuri ɗaya ba da izinin ubangiji.

Gefen kogin ta dama wata babbar *Rugar fulani mai suna Rugar Bani* ce mai tarin
tarihi, rugace mai girma wacce Ubangiji ya ƙawatata da ababen buƙatar yau da
kullum, wannan Ruga itace yanki mafi sanyi a yanki Ɓadamaya state rugace damu
fulani muke ce musu *JOTTAN MA'EN* Bi ma'ana fuli mazauna wuri ɗaya, ba ire-iren
fulani makiyaya masu tafiye-tafiye bin rugageba, fulanin Rugar Bani fulanine
makiyaya masu tarin dabobi masu tarin yawa, Rugar Bani Rugace da aƙalla fulaninmu
sunyi sama da shekaru dari da ashirin awannan Rugar, shiyasa harda gini zamani da
kyawawan gidaje fulanin sukayi, yayinda kuma akwai bokkokinma a cikin Rugar tasu
wanda kuma suka sayi filin da kuɗinsu zufansu a hannun sarkin Shikan na wancan
zamanin ya sayar musu yankin wurin gaba ɗaya sun biya kuɗinsu ya kuma basu takardu
su, suna zaune a nan suna noma suna kiwo.
Rugar Bani na zagaye da ƙauyukan ƙabilun Ɓachamawa da tarin yawa, wanda nan
gefensu ƙauyen Bonon yake wanda nanne dodon tsafin ƙabilar ɓachamawan take wanda
sunan dodon tsafin nasune suka sawa suna ƙauyen suna Bonon. Kauyen Bonon shine
zuciya da karfin kafuran nan, sunyi imani dashi, fiye da zaton mai zato, koda laifi
wani yayi bonon ake kaiwa ƙara kuma muddin bonon ya tsinewa mai laifinsun to zai
lalace ya ɗai-ɗaice dashi da zuriyarsa baki ɗaya, da yake sunyi imani da hakan kuma
yana faruwa suna gani shiyasa bonon yake tamkar zuƙatansu, kamar dai yadda in jikin
ɗan adam idan zuciya ta ɓaci gagganji na ɓaci to haka bonon take a wurinsu...
Wannan kenan

Rugar fulanin Bani yafi ko wani yanki na Ɓadamaya sanyi mai ɗan karen daɗi.
Koda yake hakan ya samune sanadin ƙawanya da wani babban dutse mai fesar da
numfashin sanyi yayi musu, wanda ya kasance musu tamkar rufar garin.
Gefen hagun Rugar Bani kuwa wani babban fadama ne mai cike da lamɓu mai ɗauke da
ababen more rayuwa wanda ya kasance mallakinmu Fulanin Rugar Bani, lambun yana da
duk wasu kayan marmari kamarsu.
Lemu, mangoro, gwaiba, ayaba, dabino,kwakwa, kashu, kankana, abarba, da jefi-jefin
tuppa da inabi.
Wanda wannan fili yake mallakin Fulanin Rugar Bini'nne, kana bayan filin kuma akwai
wani rafin da ya kasance masarrafin noman shinkafawa ne wanda suke yinshi noman
rani da damina, kuma shina mallakin Fulanin Rugar Bani ne, wanda komawa yasan iya
filinshi,

Daga gaban Rugar Bani kuwa kogin Shikan ne malale a gabansu iya ganin mai hange da
ido biyu gefen hagunsu kuwa nan garken shanunsu ke shimfiɗe bila adadin.

Rayuwar Fulanin wannan Rugar rayuwace mai cike da aminci da amana da hakuri da
kauda kai duk da tarin zalunci da kafurai ƙabulun Ɓachamawa keyi musu.

"Kamar yadda duk kowa ya sani duk duniya anyi ittifaƙin ba fulatani ko ba fulatana
basa neman tsokana ko tada husuma bare tada zaune tsaye. Akan cutar da bafulatani
yayi kamar bai san an cutar dashi ba ko bai ganeba, wannan dalilin yasa duk ƙabilun
ƙasar Afirka sukeyiwa ƙabilarmu kallon wawaye ne ko basu san abinda sukeyiba ko
sokayene, masu ƙarancin wayewa Gidadawa.
Mu kuwa a namu sashin fulani mun kasance masu kauda ido kan cutarwar forko data
biyu, sai dai a haƙiƙinin gsky bama lamunta ko jurar cutarwa ta uku! Domin rama
cuta ga macuci ibadace. Kuma Ba'a sarar mumini a rami ɗaya sau uku".
Wannan shine jawabin da wani farin dottijon bafulatanin dake zaune tsakiyar
al'ummar wannan rugar bayan sun dawo daga jana'izar mutun ɗaya da ƙabilun ɓachama
suka kashe musu cikin sunkuru, a daren jiya wanda ya kasance ɗane ga Arɗon Yabani
shugaban Rugar tasu kenan.
Hannu yasa ya share zafafan hawayenshi dake kwaranya daga ida nunshi cikin ɗaga
sauti yaci gaba da cewa.
"Fulani basa ɗaukar mataki domin yaƙi ko zalumci sai dai dan kare kawunansu. Kuma
kun sani duniya duk ta sani FULANI BA ƳAN TA'ADDA BANE! Ba ƴan bindiga daɗi bane,
makiyayene masu ƙare rayuwarsu dan samawa mazauna cikin birane jin daɗin rayuwa,
muyi kiwo mu kai musu suci naman susha madarar shanu kana muyi noma mu ciyar dasu.
Meyasa su mutanen birane basa ɗaukar matsalarmu tasu matsalar ana kashemu tamkar
kiyashi kuma babu masu kulawa".
Tsagaitawa ya ɗanyi tare da shashsheƙa cikin bada umarni a matsayinsa na shugaban
Rugar uban wanda aka kashe kuma yace.
"Na roƙeku da Allah kada wanda ya ɗauki makami domin ramuwa duk da munga yankan
rago akayiwa Hashimu amman bamu san wayeba kuma bamu da hujja, dan haka kada wanda
yace zai ɗauki makami.
Muyi rubutu mu aikawa maimartaba sarkin Ɓadamaya, domin Al'ƙalami yafi tokobi, mu
kai kukanmu gareshi, tunda shi sarkin wannan yanki na Shikan mun kai mishi kukanmu
a karo na barka tai bai kulaba, kuyi hakuri mu miƙa lamarinmu ga sarakuna mu, inada
yaƙinin zasuyi mana adalci".
Shiru mutanen da aƙala sun kai ɗari da ashirin sukayi.
Yayinda kowa ya keta zubda hawaye.
Sai ɗaya daga cikine da ya kasance baƙin jakada Ɓachama ruwa biyu uwarshi ƙabilar
ɓachama, wacce ubanshi bakura babarbaren borno wanda shike saida kanwa a rugartasu
ya auro Uwar Ba'ana. yana naɗa komai a wayarshi,
domin miƙawa shugaban mayaƙan ƙabilar ɓachama, komai ya gani, domin shi ɗin ya
kasance, makashinsu ne kuma taburmarsu ne, domin dama bahaushe yace sai da ɗan gari
akanci gari da yaƙi!...

A cikin babban birnin Ɓadamaya kuwa. *Land of beauty* Garin Modibbo Joɗa,
Mai tutar fulɓe garinda duk arawacin ƙasar Kautal mune kaɗai muka rage da tutar
Shehu Usmanu Ɗan Fodiyo.
Wanda ya dasashi ya kafashi da hannunshi masarautar fulbe mai ƙarfi Masarautar
Joɗa...

Cikin birnin matsarautar Joɗa.

A cikin babban birnin Ɓadamaya.


Wasu irin tsala-tsalan motocine wanda a ƙalla sun kai Goma suke jere suna fitowa
daga harabar shaharerriyar makarantar Jami'a ta dake cikin babban birnin Ɓadamaya
wato J.U.B Joɗa University Ɓadamaya

Yayinda suke tafiya a jere a jere cikin tsananin gudu tamkar zasu tashi sama kana
ga jiniya daya karaɗe illahirin sashin wurin wanda dole yaja hankali duk wanda ke
wurin gudu sukeyi tamkar zasu tashi sama da titin.
Motoci huɗune a gaba, wanda suka kasance masu kyau.
Sai wata Rolls Royce, mai kuɗi kimanin naira million 4, 959,630. Motace mai
tsananin sheƙi da azabar kyau motar sabuwace dal, sai sheƙi da ɗaukar ido takeyi
komai na motar farine ƙal sai glass ɗinta daya kasance tin tek mai duhu.
Wani kekyawan matashine mai cikar haiba da kamala da kima, uwa uba kwarjininsa mai
cika idon mutane, farine ƙal wanda da ka ganshi kasan tabbas bafulatani ne, kuma
zaka gane ya haɗa jini da larabawa.
Wata iriyar shigace a jikinsa shiga mai ƙara daraja da kamala farin yadin Super
Nour a jikinsa wanda a ƙalla zai kai tamanin ɗ kuɗinshi, ya ɗaura baƙar al'kebbarsa
ta jinin larabawan saudia Al'kebbar baƙace mai faɗi, kana yasa farin hirami a
kanshi da zagayen baƙin saman hiramin.
Fuskarshi nan ta fito ras sajenshi mai tsananin kyau yayi lib a fuskarshi sai sheƙi
yakeyi, kana gashin girarsa ya komta lib a saman siraran idanunshi masu kyau da
ɗaukar ido, wani irin tsabtaceccen gemune da bazai wuce kamu ɗaya ba ne yayi lib a
haɓarsa.
Zaune yake cikin motar ya jingina bayanshi da sit ɗin, ya lumshe fararen idanunshi,
A hankali yake motsa tattausan jajayen laɓɓansa yana tasbihi.
"Subahanallahi wal'hamdulillah wa la'ilahaillah Allah Akbar, Astagafillaha wa'atubu
ilaik".
Yanaji a jikinshi kudun da akeyi yayi yawa, to amman dolene ayi irin wannan gudun
domin lokaci na gab da ƙurewa, dan sosai sallan jumma'ar ya gabato, yasan yanzu
masallacin ya fara cika, wannan dalilin yasa bai hana drevernshi gudunba, kuma bai
hana fadawanshi sakin jiniyarba, dan ta hanyar jiniyarce zaisa a basu hanya su samu
su isa kan lokacin daya dace.
Bawai ya bari ayi jiniyar da gudun dan nuna isa da ɗagawa bane, sai dan son isa
masallacin Masarautar Joɗa da yake limanci kuma yake gabatar da Hudubar jummar
matuƙar yana ƙasar tiyatar da yayiwa watace ya sa lokaci yaso ƙure mishi.
Motoci, biyar kuma na bayanshi wanda uku daga ciki na ɗaliban J U B da ya fitone,
wanda yana aiki cikin Hospital ɗin makarantar, bayan kuma asibitinshi da kuma
Genaral Hospital Ɓadawaya da yake zuwa sau ɗaya cikin ko wanne sati.
motoci biyun bayanshin kuma, Jalal ne da abokanshi.
Shiyasa motocin suka taho a jere-a jere dan shi bai fiye yarda ya fita da mota sama
da biyarba, suma ba kullum ba, wani lokacinma yakan fita shi ɗaya.

A haka dai har suka fara ratsowa cikin Ɓadamaya, a dai-dai mashigar laleko ne,
Cunkoson ababen hawan ya yawaita, yayinda suka danno kai wurin yasa da yawa suka
fara komawa gefen titi suna kauce musu dan basu hanya dan jiniyar dake musu nunin
akwai uzurin gaggawa ga kuma fadawa a motocin.

Wani mai keke Napep ne ya gangara gefen titi har kusa da wani mai saida su Oranges
Banana da dai sauransu.
Dogon tsaki mai Napep ɗin yaja tare da cewa.
"Wannan ai mulkin mallaka ne da izza duk an tsaidamu sabida wani can zai wuce ai
duk nan muma saurin mukeyi munada babban uzuri, saurin da duk mutanen wurin nan
keyi duk an katse mana hamzarinmu na son isa masallaci kan lokaci muji huɗubar
jumman wannan rana".
Mazan dake cike a bayan napep ɗin ne suka haɗa baki wurin cewa.
"Wallahi kuwa, gashi motocin nasu nada yawa.
zasu sa mu rasa jin hudubar wannan fasihin Malamin".
Wani mai motane dayake gefensu ya amshi zancen da cewa.
"Kuma gaba ɗaya mutanen nan wurin masalacin zasu tafi, sabida duk mai son jin
huɗuba mai ratsa jiki da zuciya baya ƙaunar ko furuci ɗaya na wannan malamin ya
wuce shi domin Allah ya rigada ya mishi baiwar lafazi mai shiga zuciya".

Wanda ke gefensu ne ya amshi zancen da cewa.


"Gaskiya ne wannan sabida shi Allah yayi mushi baiwar lafazi da iya tabsiri mai
nusar da gafalelle".
Mai saida kayan yayan itatuwan dake gefen sunne yayi ɗan murmushi kana ya miƙawa
ƴan matan daketa kallon motocin da ido, lemun da suka saya ya miƙa musu.
Kana ya kalli dan-dan zo matasa daketa wuce da kafa,
mutanen daketa maganar Malamin ya kalla tare da cewa.
"Eh kam gsky duk malaman ƙasar nan babu yashi a lafazi, cikin second ɗaya zai yi
maka lafazin da zai gamsar da kai tsawon shekaru Talatin,
koda yake hakan baya rasa nasaba da tsatson mahaifiyarshi, da ta kasance balarabiya
kuma alarabawanma a cikin ƙabilar da tafi dukkan ƙabilun duniya a baiwar lafazi da
iya sarrafa harshe".
Cikin mamaki suka kalleshi,
Alhajin dake cikin zazzafar motar shin nanne yace.
"Haba sai haka mana ashe Balarabe ne wani yanki na tsatsonshi Allah yayi mishi
rahamomi masu tarin yawa.
Gashi wannan zai hanamu muje muji Kuɗubar".
Murmushi mai Appul ɗin yayi tare da kallon gefen baya yadda ya hango dandazon
motoci da keke Napep dama masu tafiya da sawu ma.
Wasu na meda motocinsu gefe sukayi suna fitowa da sallayoyinsu a hannu suna takowa
da ƙafa,
kanshi ya ɗan rausayar ya kalli mutanen dake gaban nashi tare da cewa.
"Kasan su wayene a cikin motocin nan da kuketa zagin kuwa?".
Da sauri suka jujjuya kai tare da cewa.
"A a waye ne?".
Tsala-tsalan motocin ya zubawa idanu zazzafar farar mota kirar Rolls Royce ɗince
ya zubawa ido a hankali ya maida kallonshi garesu tare da cewa.
"Shine Sheykh J....!
Uhummmm wasa farin girgi.

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 3

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*FREE PAGE*

*LITTAFINA NA KUƊI NE. TURO 300 DOMIN samun damar KARANTASHI. Ko ki turo 1k domin
shiga SP Group, inda zaku samu posting fiye da na 300. Ayyah Ƴan SPG bana son
katin, turo dubu ɗayan ta asusuna na, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai
ki turo shaidar biyanki ta layina na 09097853276. Kuma masu 300 in dai kinada damar
turawa ta ac tura,in kuma baki da dama to turo katin mtn na ɗari ukun ta layina na
09097853276, ba hoton katin zaki turoba, numbers ɗin zaki kofa ki turon*

```ALHAMDULILLAH MASU NEMAN TSOFFIN LITTATAFAINA, NA SAMESU GABA ƊAYA, SAI RIGAR
KOWA NE BAN SAMUBA. IN KINASO KIZO DA KATIN MTN NA ƊARI UKU kacal IN BAKI DUK
LITTAFIN ƊAYA DA KIKESO, A CINSU.ƳAR FULANI, MU'WASMITI, NAMIJI BAYA KAƊAN, A
TAUSAYAWA JUNA, BANDIRAWO, RUBUTACCEN AL'AMARI, HUKUNCIN ALLAH, NAKASA BA KASAWA
BACE, DA KUMA GARKUWA.```

"Sheykh Jabir Habibullah Nuruddeen Bubayero Joɗa ne.


Doctor Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero kenan. Ina nufin GARKUWAN FULANI".
Da mamaki a fuskokin su sukace.
"Astagafirullaha. Bawan Allah ashe sauri yake ya rigamu kada muje muyi ta jira".
Kai mutumin ya jinjina musu tare da nuna motoci biyu wanda Jalal da abokanshi ke
ciki, wanda kiɗan dake tashi cikin motocin ya cika ko ina, a hankali yace.
"Wannan kuma Jalaluddin kenan ƙanin Sheykh Jabir Habibullah Nuruddeen Bubayero".
Dai-dai lokacin kuma motocin su Jalal keta gilmawa suna bin bayan nasu Sheykh da
azaban gudu har kamar zasubi ta kan motocin gaban nasu, cikin mamaki mutanen sukace
"Ikon Allah to wannan saurin duka na menene? shi kuma".
Kai ya jinjina musu lokacin da yake rurrufe kayayyakin shi dan shima shirin tafiya
masallacin yakeyi cikin yin ƙasa da murya yace.
"Kuyi a hankali kada ya jimu domin takadirinin yarone, saurin da yakeyi kuma, yasan
muddin Sheykh bai gansu a masallaci ba ranshi zai ɓaci".
Cikin nisawa mai Napep ɗin yace.
"Kai masu saida kaya a titi iyayen gulma, dasa ido to kai ina kasan su haka?".
Da
Murmushi mai lemun ya ɗanyi tare da cewa.
"Wallahi sam ba gulma bace, akwai ƙaninshi Jamil abokin tagwaicin Jalal ɗin mutumi
nane yakan tsaya a nan in zai shiga gari, kuma yanada ɗan karen surutu da fara'a
shiyasa na sansu, akwai randa yana tsaye a nan yaga Jalal ɗin ya wuce a guje shine
yayi dariya yace.
"Hege mai komaɗeɗɗiyar fuska bosawa Sheykh ne ke nemanshi shine yake gudu kamar zai
tashi sama".
to nan ya ɗan bani labarinshi. Kuma Sheykh ɗin da kanshi akwai shekarar da yayi
azumi a garin nan yakan sayi kaya wurina, wani lokacin
Shiru sukayi tare da zubawa motocin idanu.
ganin sunata gilmawa, saida suka wuce gaba ɗayansu.
Sannan sauran al'ummar gari suka fara biyo bayansu.
Mafi akasari ababen hawan dama mutanen dake tafiya a ƙafa kab masallacin Masarautar
Joɗa ba fadan jihar suka nufa wanda tuni Sheykh ya isa har yanata gabatar da
Hudubar jummar sa mai taken, mu tsaida salla a lokacin ta.

A can cikin masallacin Masarautar Joɗa kuwa tuni al'ummar Annabi sun cika sunyi
maƙil tako wacce kusurwa jama'a ne saffan-saffan suke shigowa,
yayinda cikin masallaci yayi maƙil har harabar masallacin ma ya cika tab da muminai
salihan bayin Allah.

Kusan a guje wasu ke shigowa sabida lokaci na gab da ƙure musu domin bisa dukkan
alamu an kusa ƙare Huɗubar.

Duk da tarin mutane manya da yara, amman sabida ladabi irin na addinin musulunci
addinin mafi karamci da tsari, shiyasa baka jin motsi ko sautin kowa.
Sai wata iriyar zazzaƙar murya mai tsanani daɗin ji da sauraro da iya sarrafa
harshe, cikin nitsuwa da iya laffazi muryar Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen
Bubayero ke tashi yayinda yake ratsa zuciya da jiki da Kunnuwan dukkan muminin dake
sashin da sautin muryarsa ke kaiwa.

A can cikin masallacin yake a fili na musamman wurin da aka ware domin Limami,
Yana tsayene bisa sawunshi ya fuskanci tarin bani Adam dake cike maƙil a wurin.

Kekyawan matashine mai tarin kwarjinin da haiba mai firgita magautanshi,


Sanye yake cikin shiga ta al'farma shigar dake nuna nasabarsa ta wanne sashi,
Wani datsetstsen yadin Getzner ne fari ƙal-ƙal wanda yasa riga da wondo,
Kana sai wata hamshaƙiyar al'kebba dake nuni da nasabarsa mai tarin ilimin addini
da kuma alaƙantuwa da jinin sarauta,
Wani irin rawani ne ke murze a kanshi wanda jelanshi ke kwance a gadon bayanshi.

Farar fuskarsa dake zagaye da tattausan saje baƙi ƙirin mai fitinenne sheƙi da
ɗaukar ido,
Ne yayi matuƙar kara mishi ƙwarjini sai tsabtataccen gemunshi da bazai gaza kamu
ɗaya ba.

Cikin rahama da nimar da ubangiji yayiwa laraba ta baiwar iya sarrafa harshe da
tausasan laffuza, yake gabatar da Hudubar jummar da yakeyi.
Wanda yana bayayi ne da jan hankali kan girma da darajar salla da tsaida ita a kan
lokacin ta.

Shiru mutane nen ya ƙara tsananta ne a lokacin daya fara tsorotarwa a kan illloli
da masifun dake bibiyar mai wasa da salla.

Shiru masallacin da farfajiyar sukayi baki ɗayanshi sai sautin A/C da kuma sauƙar
numfarfashi mutane da shessheƙan kukan da wasu salihan bayin Allah sukeyi sabida
yadda wa'azin ke ratsa jiki da zuciyar mai imani.

A hankali yasa hannunshin ya gyara zaman al'kebbar jikinshi tare da gyara abin
sautin maganar dake saƙale a wuyan al'kyabbar jikinshi.
A hankali ya lumshe idanunshi kana yayi ƙasa da kanshi cikin yanayin nitsuwarsa ya
buɗe jajayen laɓɓansa cikin zazzaƙan sautin muryarsa yaci gaba da cewa.
"Ya ƴan uwana musulmai muji tsoron Allah mu tsaida salla, domin itace forkon, abin
bincika a cikin aiyukanmu.
Kada muyi wasa da salla a cikin dukkan halin da muke ciki.
Domin hukuncin mai wasa da salla hukuncine mai girgiza zuciyar dukkan mai mutuwa".
Kanshi ya ƙara rusunarwa sabida tarin manyan mutane daddatawa dake gabanshi waɗanda
da yawa sunyi jika dashi wasu kuwa sun haifeshi, cikin tausasa lafazi yaci gaba da
cewa.
"Hukumcin mai wasa da salla lokuta biyar ɗin nan.
Duk mai wasa da salla, za'a ɗebe al'barka a rayuwarsa.
Ƴa yan uwana mene amfanin rayuwar da babu al'barkan Allah a cikinta, babu.
Kana duk mai wasa da salla za'a ɗauke kamala ta mutanen kirki a fuskarsa, ya zamana
baka da kamala da daraja a idanun al'ummar duniya.
Sannan muddin baka tsaida sallaba dukkan wani aikin da zaka aikata Allah bazai baka
ladaba.
Kana dukkan addu'o'in da zakayi baza'a ɗaukakasu zuwa samaba.
Kana bazaka kasance daga cikin addu'o'ina salihan bayiba matuƙar kana wasa da
salla".
Sassauta muryarsa yayi cikin yanayinshi na tarin kamala ya ɗan nago kanshi wanda
dai-dai lokacin kuma ya hango ƙaninsa Jalal yana shigowa cikin harabar masallacin.
Kanshi ya kauda kana yaci gaba da cewa.
"Akwai uƙuba uku lokacin mutuwar dukkan mai wasa da salla.
Na ɗaya duk mai wasa da sallah zai mutu a matsayin matsiyaci gafalelle.
Na biyu
Zai mutu yana jin yunwa.
Kana na uku
Dukkan mai wasa da salla zai mutu yana tsananin jin ƙishi.
Ƙishinda koda za'a bashi ruwan ƙoraman duniyar nan baki ɗaya bazai gusar masa da
wannan ƙishinba.
Kana duk mai wasa da salla akwai uƙuba uku dake jiransa a ƙabarinsa.
Za'a ƙuntata masa ƙabarinsa ya tsuƙe ya matse har sai ta kai matsayin da
haƙarƙarinsa na dama ya haɗe dana hagu.
sannan kuma. Za'a saka masa garwashin wuta a cikin ƙabarinsa yayi ta juyawa a
cikinsa ba dare ba rana.
Na uku. Za'a saka masa wata macijiya mai suna Shuja ul Qara,u wacce ta kasance ne
ɗaya daga cikin macizan wuta.
Ida nunta na wutane. Farshenta kuma na baƙin ƙarfene.
Tsawon ko wani farcenta ɗaya tsawon tafiyar wuni ɗaya ne.
Zatayiwa mamaci magana, da muryarta mai tsawa da amo mai firgitarwa, zatacewa
mamaci mai wasa da salla yayin rayuwarsa cewa.
(Ubangijina ya umarceni inyi ta saranka tun lokacin sallan asuba har zuwa azahar,
daga azahar har suwa la'asar daga la'asar har zuwa magriba daga mangriba har zuwa
isha'i daga sallan isha'i har zuwa wayen gari asuba.
Duk sara ɗaya da zaiyima mai wasa da salla har ya mutu bai canzaba zai nitse cikin
ƙasa anayi mishi azaba, bazai gusheba anai mishi azaba har tashin al'ƙiyama.
Allah ya tsaremu.
Uƙuba uku lokacin fitowarsa daga ƙabarinsa itace.
Na ɗaya hisabi mai tsanani.
Na biyu. Fushin Ubangiji.
Na uku. Shiga wuta. Allah ya tsaremu ya bamu ikon kiyaye salla da tsaidashi a kan
lokacinsa, yaku taron matasa kune shagala tafi auranku, mu dage mu tsare salla duk
rintsi".
Ya ƙarishe maganar cikin rauni da kushu'i.

Gaba ɗaya kowa jikinsa yayi la'asar musamman matasa masu wasa da salla,
Jin ya juya yayi gyaran murya ne.
Yasa gaba ɗaya kowa ya mike ya fuskanci gabas masamar lada.

Cikin nitsuwa da tattausan harshe yake rare karatun al'ƙur'ani mai girma.
Lokacin da yake limancin sallan jumma'ar da a ƙalla yana samu halartan mutun sama
da Dubu biyu.

Bayan anyi salla raka'a biyu kamar yadda yazo a nafsi, akayi addu'a aka shafa
kana, mutane suka fara firfita daki-daki.

Bayan 30 minute shal cikin masallacin.


Dan gaba ɗaya kowa ya nufi wurin lamuran yau da kullum ɗinshi sai mutanen da ba'a
rasaba wanda su sai dare zasu bar cikin masallacin.

Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa, ne tafe a hankali cikin irin takunsu na sarakai,
Yayinda Jikinsa mafi soyuwa a garesa ke gefen damanshi,
fadawane ke biye dasu a baya, sun zagayesu,
Sai kuma bayansu can kuma Ayarin fadawan Jalal da Jamil ne wanda suke tagwaye
ƙannen Sheykh Jabeer.
shi kuwa Malam Jabeer taku yakeyi a hankali cikin rashin nuna ɗagawa a kan doron
ƙasa, tafiyar yake tamkar yana tausayawa ƙasar yayinda mutane kuwa ke kallon hakan
a matsayin ƙasaitace da jinin sarauta dake yawo a sasan jikinshi.

Suna tafene a tare yayinda bakin Sheykh Jabeer ke motsawa a hankali hankali, wanda
sai ka lura kake gane, tasbihi yakeyi a zuciyarshi wanda hakan ya zame mishi abin
ci da sha a rayuwarshi.
"Astagafirullaha wa'atubu ilaik, Astagafirullaha! Astagafirullaha!! Subahanallahi!
Walhamdilillah wa lailaha'illalahu Allaahu akbar. Astagafirullaha".
Waɗannan sune kalamen da basa rabuwa da bakinsa, dama wasu masu tarin yawa.

Ta ƙofar dake shiga masarautar daga jikin masallacin sukabi.

Masarautar Joɗa babbar masarautace mai tarin girma tarihi.

Ginin Masarautar ginine mai masifar kyau da ɗaukan hankali.

Kana shiga daga asalin babban gate ɗin fadar, zaka samu wata shimfiɗeɗɗiyar hanya
mai girma irin mai guda biyun nan, gefe da gefen hanyar duk wasu irin dogin
fulawowi na mijin kwanda ne masu tsawo da kyan gani,
sai kuma tsakanin titunan, shima jerin dogayen bishiyoyin ne.

Tafiya mai ɗan tsawo, zakayi kafin, ka isa wani babban Round about mai masifar
kyau, wanda cikinsa ke ɗauke da babban kwarya a ƙasa, sai kuma ƙananan kware, guda
uku, sai kuma ginin mutum-mutumi na kekyawar saniya fara mai ɗigo-ɗigon baƙi, wanda
mace ke tsugune a gefe kamar tana tatsan nono sai kuma ɗan saurayi matashi na riƙe
da sanda ya coge da ƙafa ɗaya.

Sai kuma korayen ciyawi masu masifar kyau da sanyi wanda akayi alamun manomi na
ciki.

Daga nan ne hanyoyin cikin masarautar suka rabu huɗu, ɗaya yayi gefen dama ɗaya
yayi gefen hagu ɗaya yayi gabas ɗaya yayi yamma wanda ta nanne ake shigowa.

In ka miƙe ta yamma daret itace titin da zai sadaka da asalin sashin Sarki
Nuruddeen Bubayero Joɗa wanda nan sashin matanshi da hadimanshi yake da sashinshi
dama faɗar duk nan take.
In kayi gefen dama kuwa wasu irin tsala-tsalan gine gine-gine masu tsananin kyau
da ɗaukar hankalin wanda suna nan part-part ne masu girma da tsaruwa, an ƙawata
tsakiyarsu da wani sassanyan Garden mai girman gaske.

Inda part ɗin sun kai goma, mafi kusa da sashin mai martaba sarkin Nuruddeen Aliyu
Bubayero, shine sashin GARKUWAN FULANI, wato Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen
Bubayero.
Sai kuma na gefen daman Sheykh Jabeer shi kuma na Jafar Habibullah Nuruddeen
Bubayero ne, da matarsa Juwairiyya.
Sai na gefen hagunshi kuma na Jalal, ne na kusa da Jalal da kuma na Jamil ne sai
dai Jamil yafi zama a sashin Jalal duk da korarshi da yakeyi wasu lokutan kuma
lokacin kuma yana sashin Sheykh.
Sai sashin baya kuma sashin Affan.

Daga gefen hagun Masarautar kuwa wasu tamfatsa-tamfatsan plat ne masu girma har
guda huɗu, sai kuma wani babban bene dake tsakiyarsu mai tarin girma wanda nanne
sashin babban ɗan sarki Habibullah da matanshi.

Sai ta gefenshi can kuma wasu manyan part- part ne kimanin guda biyar wanda duk
ƙanne shi ne da iyalansu da ƙananan yaransu a ciki.
Yayinda duk manyan yaransu kuwa kowa nada part ɗin shi a gefen da part ɗin Sheykh
yake a ƙalla dai Part ɗin cikin masarautar Joɗa sun kai hamsin da biyar.

Can wurin mashigar kuma wasu ƴan saffan-saffan part-part ne wanda bisa dukkan alamu
duka na bayine da hadimai da matansu.

Tsayuwa fasalta cikin ko wanne sashi na masarautar bazai yiwuba, sai a hankali.

Sai dai ko wanne part yanada Garden mai ɗan girma, wannane yasa gaba ɗaya
masarautar ke zagaye da korayen fulawowi da bishiyoyi masu kyau.
Fentin masarautar gaba ɗaya iri ɗaya ne, Sky blue and white, mai ɗan karen kyau, a
mahaɗar sashukan kuwa wani irin tamfatsetsen sweeminpool mai girma wanda ruwansa
ke sky blue.
Can bayan sashin Mai martaba da Sheykh kuwa wani ƙaton filine mai cike da dawakai,
da sashin mai rainonsu, gefe ɗaya kuma raƙuma da shanaye ne da makiyaya su, kana ga
tumaki, a gefen Sheykh Jabeer ne kuwa akayi wani ɗan madai-daicin gidan zu ta bayan
ɗakunan shi wanda yake da tarin tsuntsaye kamarsu, Ɗawisu, jimina, mikiya, agwagin
ruwa, tolo-tolo, tattabaru, kana sai Aku. Da sauran tsuntsaye carki, kurciya,
hasbiya, caccagi da-dai sauransu, shiyasa sashinsa ya kasance namusamman, don
Garden Park ɗin ciki yafi na sauran part ɗin duka girma da kyau, sabida shine
asalin Garden ɗin tarihin masarautar Joɗa.
Daga nan mashigar masarautar kuwa akwai wani babban filin sukuwa mai girma.

Daga masallacin Masarautar kuwa akwai miƙeƙƙiyar hanya har cikin masarautar wanda
za'a iso gab da fada sannan kowa zai samu hanyar sashinsa.

A tsakiyar cikin masarautar ma kuwa akwai wani masallaci mai girma.

Wannan kenan sai a hankali zaku san mutanen masarautar da sunayensu halayensu dama
nasabarsa da danƙantarsu da manufarsu.

A hankali Sarki Nuruddeen da Sheykh Jabeer suke takawa.


Suna shiga cikin gidan waɗannan fadawan suka tsaya a bakin Gate ɗin.

Kana wanda suka samu a wurin suka miƙe da azama wani dogon carpet mai azabar kyau
da taushi, ɗaya daga cikin fadawan ya zo ya ajiye gabansu kana ya rinƙa yin baya-
baya yana worwore musu carpet ɗin.
A hankali Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa yasa hannunshi ya kamo hannun kekyawan
matashin jikan nashi da kab cikin jikokinshi ya fita da ban, hannunshi yake murzawa
cikin nasa hannun a hankali a hankali.
kana suna tafiya a hankali, cikin takun sarauta,
Gefen mai martaba Nuruddee bayine da dogarai a ƙallah sun kai Ashirin da biyar,
gefen Sheyk Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero kuwa,
Ƴan saffan-saffan fadawane da basu kaishi shekaruba, a ƙalla sun kai goma.
Wanda wannan tsarinsa ne yace bazai iya ganin sa'an mahaifinshi ba ko sa'an Ya
Jafar ɗinshi ba suna mishi bauta Babban Yayansu Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero
suke kira Yah Jafar.
Kanshi ya ɗan murza ya juya a hankali da gefen ido ya kalli Kakan nashi dake magana
cikin yin ƙasa da murya dan ko sarkin dogaren dake gefenshi baiji me yake cewa ba.
"Sheykh yaushe ne tafiyar taku?".
Siraran kyawan Idonshi ya lumshi a hankali ya kuma buɗesu tare da rausayar da
kanshi.
Maimartaba bai damu da jiran amsar tasaba yaci gaba da cewa.
"Munyi Magana da Aminina Sarki Jalaluddin yace min Kakarka UmmuKulsum tace tafiyar
taku ta ƙara toko?".
Shiru ya ɗanyi har saida sukayi taku uku zuwa biyar kana ya gyaɗa mishi kanshi kai
a hankali irin gyaɗa kai na kamala".
Dai-dai lokacin kuma suka iso dab ƙofar mashigar sashin Maimartaba, wanda dama duk
ran jumma'a daga shabiyu yake tashi zaman fada,
sanin hutawa yake a irin wannan lokacin ne ya sashi ɗan sake hannun Sheykh Jabeer
tare da cewa.
"Sirranta komai a rai yanada wuya, amman kai baya maka wuya, ya zama kamar jininki,
akwai tauraro na musamman a goshinka, wanda nake fatan watan wata rana ya haska
zuƙatan ahlinka dama talakawan da zaka mulka".

Jin kakan nashi ya sake hannunshi da kalaman da yake jero mishine yasa ya ɗan
kalleshi a hankali ya kuma sunkuyar da kanshi.
Sai ya kuma ɗan kalli Sarkin tare dayin mgna.
"Mulki yana da nauyi mai girmi Ni kuwa baya cikin tsarin jadawalin ababen buƙata ko
sha'awa a rayuwata,".
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
"Ba sai lallai abinda mutun keso ke samu ba, bakuma dole ka rasa abinda baka soba".
Ganin kakan nashi yaci gaba da tafiya ne yasa shima ya yaci gaba da tafiya.

Inda fadawanshi ke biye dashi a baya.

Yayinda fadawan Maimartaba kuwa suka tsaya a bakin sashin sa.

Sunyi tafiya mai nisa kaɗan kafin suka ratso ta gaban sashinsu mai azabar girma da
kyau sashine mai ɗauke da part-part masu tarin yawa da girma wanda tsakanin ko
wannensu da ƴar tazara sosaima.

A hankali ya ɗago hannunshi daga cikin babbar rigarsa da zazzafar al'kebbarsa ta


rufe,
ɗan ɗaga musu hannunshi yayi alamun su tsaya daga nan.
Cikin abinda bai gaza 18 second ba duk suka rusuna ba tare da sun ƙara koda taku
ɗaɗɗaya ba, kusan a tare suke cewa.
"Takarwarka lafiya ɗan Baban yaya Habibullah jikin Sarki Nuruddeen, jika ga sarki
musulmai Jalaluddin".
A hankali ya kuma ɗaga musu hannunshi alamun ya isa haka, dan shi dai Allah ya sani
har ranshi baya jin daɗi da son wannan kirare-kiraren dan yayi imani da Allah zasu
iya sawa ɗan adam ɗagawa da jin kanshi shi wani abune, zasu iya sa mutun yaji kansa
a matsayin wani sarki mai iko bayan kuma babu wani Sarki sai Allah.

Yana tsoron ɗagawa ta samu mazauni a zuciyarshi, sam baya son wannan kirare-kiraren
na zamanin jahiliyya ina dalili kana mutum ɗan Adam mai daraja azo ana wani ce maka
toron giwa ko tozon raƙumi ko dokin ƙarfe yaya Allah ya karramaka yayika ɗan Adam
ka bari na ƙasa da kai suna suffantaka da dabbobi.
A hankali yace.
"Ya isa, duk kuje kowa yayi uzurin gabansa in inada buƙatar ku zan nemeku".
Shiru sukayi tare da baje manyan rigunansu suka zauna a inda ya dakatar da suɗin.
Kana sukace.
"An gama".
Shi kuwa a hankali yake taku cikin shigarsa da tafi kama data limamen harami.
A hankali yake taku, har ya iso bakin ƙofar shiga side ɗinsa inda a nan dogari mai
tsare mashigar sashinsa sarkin ƙofarsa ke tsaye.
Tuni Sarkin ƙofa ya miƙe yasa hannu zai buɗe mishi ƙofar kenan sai ya kuma ɗan
rusunar da kanshi,
Ganin Jamil ya rigashi kai hannunshi ya buɗe ƙofar cikin salonsa na raha ya nunawa
Hamman nashi ƙofar tare da cewa.
"Sheykh Dr Malam Hamma Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero Joɗa GARKUWA barka da
yamma".
Kanshi ya kauda daga kallon ƙanni nashi, sannan ya kutsa kai ciki,
da sauri shima Jamil ya mara mishi baya,
Cikin wani haɗeɗɗen corridor mai fitinenne ƙamshi da azabebben sanyi suke tafiya a
hankali.

Tafiya kaɗan sukayi sai gasu cikin wani tamfatsen falo na al'farma da more rayuwa,
ɗaya daga cikin lumtsuma-lumtsuman kujerun kilisai na manyan sarakunan dake falon
ya zauna a hankali.

Ido ya ɗago ya watsa ƙanin nashi su, cikin sauri Jamil yayi ƙasa da kanshi tare da
cewa.
"Na tuba Hamma kayi magana ina tsoron hukunci da idanunka gwara kamin duka kon ka
haɗani da wannan saggamemen na bakin ƙofar kan nan ya dakani kawai in huta".
Kanshi ya kawar Cikin harshen larabci yace.
"Ban gankaba a masallaci".
Da sauri ya durƙuso gaban Hamman nashi cikin yin wuƙi-wuƙi da idanu cikin sanyi
yace.
"Ana Aspet ya Akhi, a matsallacin ƙofar gidansu, Khadija nai sallan jumma'ar".
Kanshi ya gyaɗa kana ya kauda kanshi ya fuskanci wani katon majigi dake liƙe a
jikin ginin yana fuskarta kujerar da yake zaune a kai.
Majigine dake ɗauke da full Qura'an, a hankali yake karatun cikin sassanyan murya.
Ganin hakane yasa Jamil ɗan rusuna duk da yasan ba amsa zai samuba cikin sanyi
yace.
"Hajia Mama tana son ganinka".
Kanshi kawai ya gyaɗa yaci gaba da karatun shi.
Ganin hakan yasa Jamil ya juya ya fita. Shikuwa Sheykh yaci gaba da karatunshi,
kusan awa ɗaya kana ya shiga Bedroom.

Shine bai fitoba sai lokacin da sallan la'asar ta gabato, jin an kira sallane, yasa
ya shiga ya sabunta al'wala kana ya fito ba kowa a wurin sun watse kemar yadda ya
umsrcesu.
Sai can bakin mafita ya samu mutun huɗu, yana tafe fadawanshi na biye dashi wanda
suma sunyi al'walan.

Jamil kuwa daga sashin Hajia Mama ya fito da nufin zaije side ɗinsu yayi al'wala.

A harabar gidan yayi kiciɓis da abokin tagwaicinsa wato Jalal, cikin sanyi ya kalli
yadda Jalal ke zagaye da fadawa yana tafiya da yanayinsa da muddin zaka yanke mishi
hukunci da ganin zahiri zakace cikekken ɗan iskane, sai dai a baɗinin ba haka abin
yakeba.

Kekyawa ne shima dan shi yana ɗibin kamanni da Hamma Jabeer ɗin nasu sosai saɓanin
Jamil da yafi kama da Babban yayansu, Barrister Jafar Habibullah Nuruddeen
Bubayero.

Tafiya yake cikin shigar tsamari zamani, wondon a saɓule har kana iya hango boxes
ɗinshi, kana ga wani irin kafirin aski da yayi mai ɗaukar hankali.
sam a rayuwarsa shi baya ta'ammali da manyan kaya,
Baya tsoro ko shayin ko shakkar kowa a duniya sai Hammansun kaɗai.
tafe yake bayinshi na biye dashi a baya, da wasu kolabe a hannunsu, cikin tsare
fuska Jamil yace.
"Kai ku tsaya, kolaben menene wannan a hannunku?".
Juyowa yayi a zafafe cikin halin faɗa yace.
"Kwalaben Giyane ko kanada maganne Akukkuturu?."
Da azaban ƙarfi da tsoro Jamil ya zazzaro ido cikin ɗaga murya yace.
"Kwala ben giya a gidannan Jalal kasan abinda kake cewa kuwa? Kwalaben giya a
Masarautar Joɗa".
Ya juyo da masifa kenan yayi arba da Hamman nasu,
shiru yayi tare da yin ƙasa da kanshi, jiki a mace.

Shi kuwa Sheykh Jabeer idanu ya zuba mishi na wasu yan daƙiƙu kana ya juya ya nufi
hanyar da zata sadashi da ƙofar tafiya masallacin Masarautar tasu ba tare fitar nan
bisa dressing mirror suka ajiyesu kana suka juya suka fita.

Shi kuwa al'wala yayi ya nufi masallacin.

Ƙarfe tara dai-dai na dare. Sheykh Jabeer, ne zaune a bisa wani tattausan carpet
mai azabar taushi,
Wata Hamshaƙiyar Gimbiyace mai cikan iko da muƙami, mulki, iko, cikin wani irin
kallo mai cike da kulawa tasa hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin nonon inabi dake
cikin wani kekyawan tray dake gabanta miƙa mishi tayi tare da cewa
"Jabeer Yaushene tafiyar taku?."
Tankwashe kanshi yayi bisa kafaɗunshi kana a hankali ya ɗan kalleta tare da motsa
laɓɓanshi a hankali yace.
"jibi".
ya faɗi mgnar a gajarce, gyara kishingiɗarta tayi bisa kilisan tum-tum dake
gefenta,
Cikin kulawa tace.
"Da Umaymah zakuje ne?".
Kanshi ya jujjuya mata alamun a a.
Kanta ta rausayar cikin ƙasaita tace.
"Naga kamar bacci kakeji Saida safe".
Kanshi ya gyaɗa kana cikin girmamawa yace.
"Allah ya bamu al'khairi".
Amin tace, shi kuwa daga nan ya fita ya tafi.

Koda ya koma sashinsa. A falo bakin ƙofar ya samu Jakadiya, tana ganinshi ta ɗan
rusuna duk da tasan yana hanata hakan a hankali tace.
"Akarmakallahu, Umaymah ce take biɗar mgna da kai, ta kirayi layinka ba'a ɗagawa,
shine tace in kawo maka wayar".
Kanshi ya ɗan sunkiyar a hankali yace.
"Ummi kice mata tayi hakuri saida safe".
Cikin mamaki jakadiya tace.
"Lafiya dai ko Sheykh?".
Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh lfy.
"To ba laifi zan gaya mata".
Daga nan ta juya ta koma sashinta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, daga bakin ƙofa ya dakatar da bayinshi.


Kana cikin nitsuwa ya kallesu tare da cewa.
"Sarkin ƙofar ka janye bayin dake bina da bin Jalal da Jamil, kaima ka koma can
sashunku, ba'a buƙatar bibikon nan, in inada buƙatar ku Ummi zata sanar muku."
Ciki girmamawa sukace.
"To Sheykh". daga nan ya juya ya nufi ciki.
Su kuma suka juya.

Koda ya shiga ɗakinshi kai tsaye bathroom ya wuce wonka yayi tare da al'wala a
cikin bathroom nashi da yafi makoncin wani kyau.
Komai na bathroom ɗin glass ne mai ruwan garai-garai, bathroom ɗin katone, mai
ɗauko da babban drower'n glass wanda yake cike da ƙananun kayan sirrin jikinshi
kamarsu vets boxes and pants kana towels da rigunan wonka da jalabiyoyinshi masu
masifar kyau da tsada da taushi da yawa, sai kuma 3 qtr da kuma turaruka dasu brosh
da su makilin da dai sauran kayan buƙata na aske pravet part. Ko ina na kusurwan
ban ɗakin da madubai.

Bayan ya fitone, yayi shirin baccinsa cikin wani tattausan jallabiya mai masifar
kyau da tsada,
A bakin gadonshi na sarakuna ya zauna,
idonshi ya zubawa woyoyinshi dake kan bedside drower' Woyoyin sun kai biyar,
a hankali yasa hannunshin ya ɗauki ɗaya daga cikinsu data kawo haske, alamun ana
kiranshi,
Karawa yayi a kunnenshi tare da yin shiru.
A can ɗaya sashin kuma kekyawar tsohuwar balarabiyace keta mishi faɗan ina ya shiga
tana kiranshi bai amsawa.
A hankali ya lumshe idanunshi tare da mirginawa ya konta tattausan gadonsa da
shimfiɗar sa, wanda Jamil ke gyara mishi a koda yaushe, cikin harshen larabci yace.
"Sitti raja'an!".
shiru sukayi baki ɗayansu, can kuma sai yaci gaba da magana cikin larabcin,
sawon 32 second yana maga kafin ya katse kiran,
kana yayi laduban konciya bacci ya konta.

Washe gari da safe da misalin karfe sha ɗaya na rana.


Dawawonshi kenan daga fada,
Yana shiga falonshi asalin falon dake gab da makoncinsa kiran Umaymah na shiga
wayarsa.
Ganin video call ne ya sashi, amsa kiran kana ya ajiye wayar kan Glass Stull dake
gaban kujerar da yake zaune.

Fuskar wata kekyawar Matace ya bayyana a fuskar wayar tashi, cikin sanyi ta zuba
mishi idanu ganin yadda ya tonƙoshe wuyanshi bisa kafaɗunshi a hankali tace.
"Jazlaan". Kanshi ya ɗan mirgina cikin wani yanayi ya jujjuya mata kai a hankali
yace.
"Jazlaan, Umaymah sai yaushe zan zama Jazlaan? Sai yaushe, Jazlaan zai wadaci
rayuwarmu?".
Murmushi mai ciwo a zuciya tayi tare da cewa.
"In sha Allah nan kusa".
A hankali ya lumshe idanunshi cikin sanyi yace.
"Umaymah, kizo kafin mu tafi, ina so mu haɗu".
Cikin tarin kulawa da tsananin ƙauna tace.
"Menene matsalarka?".
A hankali yace.
"Ya Jafar...!

Littafin na kuɗine.

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘
*GARKUWA*

PAGE 4

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GAREKU MUTANEN NIGER, +22799460151 kuyi haƙuri an samu akasin number da nada bada,
wayarta ta lalace. Yanzu ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 300 ko 1k idan kun
turata mata, saita turo min number ki/ka sai in saki/ka a group ɗin da kika
biyawa🤝🏻. Gareku mutanen ƙasata ga number ta 09097853278, turo katin mtn na ɗari
uku kacal, ko kimin TRANSFER ɗin darinki uku ko 1k ɗan samun SP Group. In kin biya
sai kiyi screenshort ki turo min shaidar biyan kuɗin littafin GARKUWA ta wannan
number dai 09097853276*

Cikin nitsuwar da ya kasance halittarsa, ya ɗan ranƙwafar da kai yayinda fuskarshi


ta ɗan sauya yanayi murya can ƙasa yace.
"Ya Jafar! Yana buƙatar kulawata, baya son nayi nesa dashi, Umaymah Jalal da Jamil
basu da hankali yaran basu da nitsuwa Umaymah basu san ciwon kansuba Affan kuma
baya nan".
A hankali wacce ya kira da Umaymah ta gyara zama cikin tarin kula da bege da
tausayi da ƙaunar Jazlaan ɗin nata cikin tausasan laffazi tace.
"Daɗewa zakuyi ne Jazlaan?".
Hannunshin yasa yana ɗan shafa sumar kanshi cikin rumtse ido murya can ƙasa yace.
"Sitti tace zamu daɗe a can, kuma Maimartaba ta gayawa kai tsaye, shi kuma ya
faɗawa Abba kai tsaye umarni suka bani".
Kai ta ɗan rausayar tare da cewa.
"Ba komai Jazlaan in sha Allah babu abinda zai samu Jafar, in kaje kayi ta mishi
addu'o'in kamar yadda ka saba, in sha Allah yana cikin kulawa da kariyar Allah".
Kanshi ya ɗan gyaɗa mata,
Domin bai fiye yawan maganaba in ba amɓaton Allah ba, dan ma ta kasance cikin mutun
biyar ns duniya da yake iya yin doguwar magana dasu, musamman Maimartaba da mafi
akasari faɗa ke haɗasu, sai ita sai kuma Umminshi Jakadiyarsu kenan wacce tun yana
jariri itace uwar rainonshi sai Sitti da Jadda".
shiru ta ɗanyi tana kallon yadda ya lumshe ido tamkar bazaiyi magana ba,
bata dai katse kiranba har tsawon 3 minutes kafin ya ɗan motsa laɓɓansa ba tare
daya buɗe kwayar kekyawan idanunshi yace.
"Umaymahhhh".
yadda ya kira sunanra ya tabbatar mata halin da zuciyarshi ke ciki, tafi kowa na
duniya sanin matsalarki Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero.
Cikin kulawa tace.
"Na'am Jazlaan".
tashi yayi zaune a hankali ya fuskanci wayar tasa da kyau, hannunshi ya haɗe wuri
ɗaya tare da cewa.
"Umaymahhhh Jalal".
Cikin kulawar da ƙanwar uwa shaƙiƙiya kan iya bawa ƴaƴan ƴar uwarta, da tarin son
da takeyiwa ƴaƴan ƴar uwarta Tata, musamman shi Sheykh, a hankali tace.
"Me Jalal yayi".
Kanshi ya ɗan ranƙofar tare da cewa.
"Umaymahhhh Jalal bayaji, ya fiye gagara, da son jawowa Ahlinmu abin faɗa.
Ɗazuma kwalaɓen giya fa ya shigo dasu cikin masarautar da ta kasance tsarkakkeya.
Ga Jamil kuma babu nitsuwa tattaredashi, duk inda yaga mace, jikinshi na rawa
yakebi ya zama kamar ɗan akuya, Umaymah in nayi nisa da gida, zasuyi abinda zai
sasu a matsalar rayuwa".
Wani dogon ajiyan zuciya Umaymah ta sauƙe a hankali tace.
"Kada ka damu, in sha Allah babu abinda zasuyi da izinin Ubangiji rayuwarsu bazata
lalaceba kodan addu'o'in da kakeyi musu, da irin tarbiyar da kake basu".
Kanshi ya gyaɗa tare da taune lips ɗinshi na ƙasa yayinda lokacin ɗaya kwayar
idanunshi sukayi wani irin kala su ba jaba sunba fariba.
Cikin rauni miskilar muryarshi yace.
"Na sanifa Umaymah babu abinda sukeyi, nasan Jalal ba mashayin giya bane baya shan
komai, amman ya rigada duniya tanayi mishi kallon mashayi, tantiri kana taƙadirin
yaro.
Haka nan nasan Jamil ma ba mazinaci bane Umaymah amman a idanun mutanen duniya shi
tamkar ɗan akuya suke ganinshi,
Kamar yadda Ya Jafar yake ba majanuni bane amman mutanen duniya kallon majanun suke
mishi".
Kanshi ya sunkuyar cikin sakekkiyar murya yace.
"Duk an liƙa musu munanan tabo, a cikin rayuwarsu, Umaymah, ni ma ɗin bazan tsiraba
tabbas nasan nima akwai wani tabon da ake kallona dashi, nasan nima bazan tsiraba".
Da sauri Umaymah ta sunkuyar da kanta ƙasa wasu zafafan hawaye masu azabar zafi da
ƙuna a zuciya suka fara kwaranyowa a idanunta, wani zazzafan shessheƙan kuka ya
kwabce mata.
Jin shessheƙan kukan natane yasa Sheykh Jabeer ya ɗan ɗago kanshi cikin jarumta da
ƙarfin hali yayi wani murmushi mai ciwo a rai.
A hankali yace.
"Kuka kuma Umaymah, inada yaƙinin ƙarfin zuciyarkine da yasani sanar dake matsalar
ƴaƴan ƴar uwarki, tunda ita bazata iya yin komai a kaiba".
Cikin shessheƙan kukan tace.
"Ba komai Jazlaan in sha Allah babu komai face al'khairi a cikin rayuwarku, insha
Allah babu wani tabon da mutane ke ganinka dashi.
Yanzu yaushe zaka wuce Leddi julɓe?".
Cikin miskilar murya mafi karamci yace.
"Yau da dare zan wuce, gobe da asuba zamu wuce Saudiyya Sittin ta matsa tana so
taje taga ahlinta".
Kai ta ɗan gyaɗa kana tace.
"Ibrahim ma yace ya kusa dawowa".
Kanshi ya ɗan rausayar kana yace.
"Eh munyi mgna dashi ɗazu".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli sauran woyoyinsh dake bisa Stull ɗin dake gefenshi,
Kiran shugan ɗaliban J.S.U Ɓadamaya ne ke shiga,
bai kula kiranba yaci gaba da magana da Umaymahnshi, har saida yaga ta samu nitsuwa
kafin ya barta.

Tashi yayi a hankali yake taku cikin kamala da nitsuwa irinta manyan limamai a
hankali yake manna farar tattausar fatar ƙafarshi da in ya taka sai kaga kamar jini
zai tsallo.
Yana shiga cikin ɗakin nashi, al'kyabbarsa ya cire tare da buɗe wani sashi na
durowarsa ya sanƙala a masanƙalinta.
Da tattausan farar jallabiyar dake ƙasanta ya shiga bedroom da ita,
Wannan lokacin wonkansa ne, babu abin da zai katse mishi uzurin domin ya kasance
mutun mai mutunta lokacin rayuwarsa ko wani lokacin da abinda yakeyi.

Wonka yayi cikin tamfatsen bathroom ɗin nashi.


Yana fitowa, ya wuce gaban dreesing mirror, kimtsawa yayi a gaggauce dan lokacin
tafiya aikinshi ya karato.

Koda ya gama kimtsawa cikin wasu tattausan manyan kaya riga da wondone da kuma
babbar gariyarsa, kayan sun kasance farare ƙal-ƙal ne, sai zazzafan aikin kufta da
akayi mishi mai blue color, kana sai hular zanna bukar daya murza bisa kanshi da
yake wadace da tattausan suma baƙiƙƙirin mai sulɓi da sheƙi,
hular itama farace sai ratsin blue, hakama takalman sawunshi da suka kasance irin
na sarakuna ne,
Agogon Daimond dake hannunshi shima yanada yanayin ɗigon blue mai garai-garai,
Sai kuma ya sunkuyo ya ɗauƙi biyu daga cikin woyoyinshi yasasu a al'jihun babbar
rigar tasa,
jakar system ɗinshi ya ɗauka da hannunsa na dama, kana hannunshi na hagu kuma
sajenshi yake shafawa a hankali har zuwa kan madai-madaicin tsabtaceccen gemunshi
mai ɗan karen kyau da burgewa.

A haka ya fito daga cikin ɗakin nashi.


Yana fitowa cikin tamfatsen falon nashi da ya kasance yanada iyaka da bayi da
hadimai duk iya karsu can bakin ƙofar babban falo bai yarda da wai bayi su shigo
suyi mishi hidima har cikiba,
Jamil shike kula da tsabtan sashin sirrin ɗan uwan nashi.
Ido ya lumshe jin wani irin sassanyan ƙwamshi da sanyi mai ratsa zuciya daya
ziyarci jiki da zuciyarshi.

A hankali yake taku, har zuwa dinnin area, a hankali ya ɗan juyo, jin an jamishi
kujerar.
Jamil kenan.
Zama yayi bisa kujerar, kana, ya miƙawa Jamil jakar system ɗin nashi.
Amsa yayi ya rataya a kafaɗarshi,
sannan ya matso gab kusa da ɗan uwan nashi,
baƙin Tea ya haɗa mishi da zuma sai bredy wanda shima da zuma a jikinshi ,
wanda yasan iya abinda zai ci ya sha kenan duk da tarin. Abinci da hadiman Aunty
Juwairiyya, suke kawowa dominshi ga kuma na Hadiman Hajia Mama, wanda duk Umminshi
Jakadiyace ke kawosu, domin ita tana shiga har cikin falonshi ɗakin konciyarshi ne
dai bata shiga, amman falo ukun nan duk tana shigarsu da kitchin da sauran ɗakunan
sashin.
Suna zama babu jimawa, wayar Jamil ta fara tsuwa, da sauri ya ɗauka tare da karawa
a kunne,
sai kuma yayi zuru-zuru da idanu ganin yadda Hammanshi ya tsareshi da fitinannun
idanunshi masu sa hanjin cikinsu kaɗawa, cikin yin ƙasa da murya yace.
"My love Sheykh yana kusa".
Ya ƙarishe mgnar da murmushi a fuskarshi, shi kuwa Sheykh kauda idonshi yayi yaci
gaba da zuƙan tea ɗin a hankali a hankali.
Shi kuwa Jamil cin abinci yai haninƙan kana.
Shi kuwa Sheykh ido kawai yake zubawa ƙanin nashi bai tashiba har saida yaga ɗan
uwan nashi ya gama cin abincin.

Sannan suka jero suka fito falo,


A can bakin ƙofar shigowa babban falon suka samu sarkin ƙofa da kuma hadimai na
jere a wurin suna hangosu duk suka rusuna har ƙasa har suna haɗa baki wurin cewa.
"Takawarka lfy ɗan Babban Yaya jikan mai martaba sarkin Nuruddeen jika ga mai
Alfarma Sarkin Musulmai Jalaluddin.
Malam ɗan Malam Habibullah jinin Limamen Saudia malamai magada annabawa, jika ga
ƙabilar da tafi ko wacce ƙabilar duniya d...".
Hannun shi biyu ya ɗaga musu alamar amsawa gaisuwar da sukayi mishi, da kuma
dakatar dasu da kirarin da sukeyin.
Kana yaci gaba da taku Jamil na biye dashi a baya, Sarkin ƙofane yayi saurin
rusunawa tare da cewa.
"Hajia Mama ta turo jakadiya a sanar maka cewa tana buƙatar ganinka".
Kanshi ya gyaɗa kana yaci gaba da tafiya,

Gefen dama ya nufa, inda wani tamfatsetsen part mai tarin girma yake, a hankali
hadiman dake tsaron wannan ƙofar suka fara rusunawa tare da bashi hanya da
gaidashi.
Tafe suke har cikin part ɗin, wani babban falo suka fara ratsawa kana suka wuce
zuwa cikin wani corridor sai gasu a wani fitinenne falo mai wadatar tsabta da
ƙamshi.

Wasu ƴan yarane guda biyu duka mata,


Suna ganinsu suka ruga a guje jikin Sheykh Jabeer suka faɗa tare da cewa.
"Sabahul khair Uncle MJ".
Sunkuyowa yayi ya ɗan shafa kansu tare da cewa.
"Sabahul noor ya Habittey".
murmushi sukayi kana suka sakeshi suka isa gaban Jamil sunkuyowa yayi ya ɗauki
ƙaramar bayan sun gaidashi ne babbar ta juya da gudu tana cewa.
"Ummi ga Uncle MJ".
tsayawa tayi tare da kamo hannun wata kekyawar mace matashiya yar duma-duma, tayi
shiga irin ta larabawa, kamo hanunta tayi suka fito falon.

Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.


"Barka da safiya GARKUWAN FULANI, GARKUWAN ahlin Sitti".
Fuska ya ɗan sake still bawai yayi murmushi bane, a hankali yace.
"Barka da safiya".

"Barka dai Sheykh Dr Garkuwa".

Babbar rigarshi ya ɗan gyara tare da cewa.


"Ya jikin Ya Jafar?".
Kai ta ɗan ranƙwafar tare da yin rau-rau da idanunta murya na rawa tace.
"Jiya kwana yayi baiyi bacciba, Sheykh, hankalina yana tashi, sabida duk randa
baiyi bacciba, to kwana yake karatu yanayi yana kuka, kukan da yakeyi ɗin ne yake
sashi zazzaɓi da ciwon kai, gashi ba cikin zuciyarsa yake karatunba ya wuni karatu
a baiyane ya kwana karatu a baiyane babu bacci".
Kanshi ya ɗan jujjuya tare da nufar kofar wani ɗaki.
Jamil da Juwairiyya na biye dashi a baya.

Suna shiga cikin ɗakin, da sauri Sheykh ya karisa gaban wani kekyawan mutun fari
ƙal mai tarin tsabta wanda yake tsananin kama da Jamil duk da duk suna kama da juna
amman Jalaluddin yafi kama da Jabeer, Jamil kuma yafi kama da Jafar.
Zaune yake bisa sallaya, ya jingina kanshi da jikin gado, karatun al'ƙur'ani yakeyi
cikin nitsuwa da da cikar tajwid, babu ɓata ko na ɗigo, yana karatun ne hawaye na
kwaranya daga kwayar idanunshi,
A hankali Sheykh Jabir yasa Hannu ya kamo hannun ɗan uwan nashi,
A hankali Ya Jafar ya buɗe idanunshi ganin mutumin da shi kaɗai ke sashi yin abu
yayi ko ya hanashi ya hanune ya sashi gyara zama still yana karatu.
A tausashe Sheykh Jabir ya ɗan ranƙwafar da kanshi cikin salon tausayawa da muryar
larabawa yace.
"Sadakallahul Azeeeeeem".
Jin hakane yasa wannan bawan Allah'n ya ɗago tafin hannunshi addu'o'in ya, fara
karantawa kusan tsawon 3 minute sannan suka shafa a tare,
Cikin wani zafi da ƙuna Sheykh Jabeer ya taune lips ɗin shi na ƙasa hannunshin yasa
ya kamo na Ya Jafar ɗin,
ba musu ya miƙar dashi,
kan gadonshi ya zaunar dashi,
A hankali ya juyo ya kalli Juwairiyya cikin sanyi yace.
"Yaci abinci kuwa?".
A hankali tace,
"Tunda asuba daya dawo masallaci na bashi yaci abinci, kuma yanzuma na bashi ya ɗan
ci".
Kanshi ya rausayar kana yace.
"Maganin shi fa kin bashi".
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Eh na bashi maganin yasha".
Jin hakane yasa Sheykh ya kamo hannun kekyawan Yayan nashi ya kontar dashi bisa
gadon blanket yaja ya rufe mishi rabin jikinshi a hankali yace.
"Ya Jafar kayi bacci, kaji jikinka zafi".
Shiru bai kulashiba sai dai, ya lumshe idonshi.

A hankali ya juyo ya kalli Matar ɗan uwan nashi kuma ƴar kawunsu yayan Mamansu
yace.
"Juwairiyya Nagode".
Hawayen dake zubo mata ta sharce tare da kamo yaranta ta ruggumesu,
Jamil kuwa tuni yaketa zubda hawaye.
Cikin rawan murya Juwairiyya tace.
"Sheykh ka dena gode min nimafa Ya Jafar ɗan uwanane kuma mijinane, uban ƴaƴana, to
in ban kula dashiba da waye zan kula a duniya?."
Kanshi ya kauda kana ya juya ya nufi hanyar fita a ranshi yanajin ko sai yaushe
manyan burukan rayuwar da fatanshi da addu'o'in shi zasu ƙarɓu yana ganin daraja da
girman Juwairiyya domin tayi musu tsantsar halacci ta zauna da ɗan uwanshi a
matsayin majanuni, a haka suke tafiya yana zancen zuciya.
Jamil na biye dashi a baya.

A haka suka fito, suna tafe hadimansu na biye dasu a baya.


A hankali ya ɗan juyo ya kalli Jamil da yasan yanada rauni dan Jamil yanada
tausayin ɗan uwanshi duk da yanada shekiyanci amman yanada rauni a kansu abu kaɗan
ke sashi kuka,
Sashin dake tsakanin sashin su Jamil dana Ya Jafar suka wuce wanda nanne sashin
Sheykh, sashin su Jamil ɗin suka shiga.
Kai tsaye suka wuce har cikin bedroom.
Tsaye suka sameshi yana taje suman kanshi mai yawa ga wondo iya ƙugu duk rabin
boxes ɗinshi a woje ga wondon da rabin jiki duk woje waishi kirezi ko? da alamun
fita zaiyi.
"Meya hanaka zuwa masallacin jumma'a da wuri jiya?
Waɗannan kolaben barasar na waye ne?".
Sheykh ne ya jero mishi tambaya biyu a lokaci guda,
A hankali Jalal ya juyo cikin shakku da shayi da kwarjin Hamma nasu ke sasu ji
yace.
"Mamace ta aikeni, jiya shiyasa na dawo a ƙurerren lokaci.
Kolaben barasar kuma nasu Ashid ne, na kwace ne lokacin da suka saya, dan karsu
sha".
Kanshi ya gyaɗa dan ya gamsu ya kuma yarda dan yasan duk rintsi ƙanennshi basa
mishi ƙarya.
Cikin faɗa yace.
"Ka kula da salla, ka tsaida ita kan lokacinta, kasan irin abokan da zakayi yawo
dasu, ka tabbatar kaikeyi nasara akan juya halaiyarsu daga mummuna i zuwa kekkyawa.
Shiyasa ban hanaka mu'amala da suba, domin manzon Allah yace.
"Mutun ɗaya ya shiryu ta dalilinka, tarin ladan yafi a baka tarin jajayen raƙumi.
Kada ka bari suyi nasarar juya rayuwarka daga kekkyawan i zuwa mummunan.

Kanshi ya gyaɗa cikin ladabi yace.


"In sha Allah".
Daga nan suka juya baki ɗayansu,
Kai tsaye sashin Hajia Mama suka wuce.
Inda hadimanta sukayi musu iso,
Har cikin bedroom ɗinta suka shiga,
A bakin gado suka sameta, zaune, yayinda baiyawarta Mansura keyi mata tausa.
Murmushi tayi tare da kallonsu yadda suke a jere, koda maƙiyinsu ne sai sun
burgeshi sun bashi sha'awa yayi fatan inama da ƴaƴansa ne.
Kan dantsatsetsen shimfiɗar kilisa mai kyau da zanen tsuntsuwar ɗawisu, suka zauna,
Cikin kula tace.
"GARKUWAN FULANI, Jamil, Jalal, Allah yayi muku al'barka".
Amin Amin, Sheykh da Jamil suka amsa,
Jalal kuwa shiru yayi,
Ita kuwa Hajia Mama murmushi tayi tare da cewa.
"Babanmu mai Al'farma Sarkin Musulmai Jalaluddin meya farune naga fuskarka a
haɗe?".
Kanshi ya girgiza alamar.
"Babu".
Shi kuwa Sheykh ido kawai ya zuba kan wayarshi,
Jamil ne ya ɗan gyara zama, tare da cewa.
"Mama Abba fa".
Kai ta ɗan jinjina tare da cewa.
"Abinda yasani nemanku kenan, Abbanku ya tafi Abuja jiya da dare, yanzu kuma
Gimbiya Samira zatabi bayanshi".
Shiru Sheykh yayi a ranshi yake jinjina al'amarin mahaifinsu.
Babusu a cikin dukkan sabgogin rayuwarsa komai nashi saidai suji a bakin Hajia Mama
ko kuma a jaridu ko gidajen Radio ceɗi meɗinshi da amaryarshi Gimbiya Samira ƴar
sarkin Nokan ce ita kuwa mijinta shine rayuwarta babu ruwanta da sabgar kowa.
Sam Abba bai shaƙu dasuba da wuya ka ganshi zaune dasu yana hira dasu kamar uba da
ƴaƴan shi.
Saɓanin Maimartaba ko meye zaiyi Sheykh zai sani shine mutumin da yake shawara
dashi akan duk abinda ya shafi addini.
Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa.
"Allah ya dawo dashi lfy".
Amin Amin sukace baki ɗayansu,
Cikin kula yace.
"Hajia Mama Affan fa sai yaushe zai dawo?."

"Next month?". Ta bashi amsa a gajarce.

A gogon hannunshi ya ɗan kalla kana a hankali ya miƙe tare da cewa.


"Zan wuce Hospital shugaban ɗaliban makarantar ya kirani cewa sunada mara lafiyar
da take buƙatar kulawar gaggawa".

Kai ta ɗan rausayar tare da cewa.


"A dawo lfy".
Amin Amin sukace kana suka fita suka tafi.

Daga nan kai tsaye FADA suka nufa.


Inda sarkin fada yayi musu iso zuwa ga Maimartaba kakansu.

Suna shiga suka samu fada na cike da dattawa karsu Waziri, Matawalle, Galadima,
Wambai, Ɗan isa, ɗanm' buram, sairkin Dogarai sarkin Gida, da kuma Duba gari,
kana, sai kuma hadiman dake tsaye bayan sarki sunayi mishi fifitar sarauta da
maficin fiffigen Ɗawisu.

Farin dattijo bafulatani, mai cikar haiba.


Yana cikin manyan kaya na sarakai, wanda al'kyabbarsa kaɗai ta kai kuɗin mallakar
wani gidan,
A gabanshi suka zauna gaba ɗayansu uku,
A hankali Sheykh yasa tafin hannunshi kan rumfar sawun kakan nashi da suke kan wani
tim-tim mai girma da masifar taushi.
taɓa sawun kakan nashi yayi tare da cewa.
"Barka da hantsi Maimartaba, ya sawun naka?".
Duk maganar nan da yayita a hankali yake yinta ko Jamil da Jalal dake gefenshi
basujiba.
Shi kuwa Maimartaba hannunshi ya ɗaura kan tsakiyar kan Sheykh wanda tun kafin ya
zauna ya tura hulanshi ya koma baya, dafa tsakiyar kanshi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ya kalli Jamil da Jalal da suke gaidashi,
dan su sai yanzu suka haɗu dashi tunda gari ya waye,
Tsaɓanin Sheykh da kullum tare suke dawowa masallaci sallan asuba daga nan kuma
ɗakin hutunshi suke shiga kakarsu mace ta kawo musu abin taɓawa.

Bayan sun gaggaisa ne da mutanen fada, suka fita suka tafi.

Sashin kakarsu Gimbiya Aminatu suka nufa.


Basu da hijabi da sashin kakar tasu shiyasa kai tsaye suka shiga a falo, suka
sameta,
Da alamun yanzu ta fitito Dan ga al'kyebba a jikinta ga kuma hadimanta a zagaye da
ita.

Cikin tarin so da ƙaunar Jazlaan ɗin nata take kallon su,


Murmushi tayi tare da cewa.
"Miskili kafi mahaukaci ban haushi, kai dai kaji abinda malam zaice kada kace zaka
binciki aikin malam".

Shiru Jamil da Jalal sukayi, shi kuwa Sheykh ido ya zuba mata.
Ita kuwa rausayar da kai tayi tare da cewa.
"Eh mana kaji abin da malam yace kada ka duba aikinshi, dazu na gama jin wani
wa'azin ka da kayi kan falala da ni'imomin dake cikin aure, kana bayani duk
maluntar mutun darajarsa bata cikaba in bashi da aure.
Sai najima wa'azin kamar da kanka kakeyi.
Meyasa ne Jabeer kayi niyar yin aure mana ka cikata nasabarka da kamalarka da
martaba da darajar ka data masarautar Joɗa".
Jalal ne ya miƙe tare da cewa.
"Ke in anzo gaisheki sai ƙaƙale-ƙaƙalen zance tsiya kika iya ni na tafi dan inada
aikin yi".
Haratanshi tayi tare da cewa.
"Tafi daga nan mai ƙugu kamar buzuzu hegiyar masifa".
Hararanta yayi kana ya juya ya fita.
Ita kuwa Gimbiya Aminatu.
Jamil ta kalla wanda shima ya miƙe yabi bayan Jalal.

Shi kuwa Sheykh numfashin ya fesar tare da cewa.


"Maganinki ya kare koda saura?."
Da sauri tace.
"Yauwa magani ya ƙare a kawo min wani".
To yace kana ya mike ya fita.

Daga bakin harabar sashin kakar tasu,


Fadawanshi ke biye dashi a baya har parking lot ɗinsu mai ɗan karen girma da kyau,
duk zagaye suke da fulawowi masu kyau.
Wasu tsala-tsalan motocine da a ƙalla sun kai su takwas sai sheƙi sukeyi.

Da sauri Ado drevernshi ya buɗe mushi ƙofar wata mota mai ɗan karen kyau wacce bada
ita ya fita jiyaba, dan ita sai ranakun jumma'a-jumma'a yake hawanta,
wannan ta yau mai kalar ruwan tokace sai sheƙi takeyi,
yana shiga sauran fadawanshi suka yi yunƙurin shiga motocin dake jere a wurin a
gefen wurin wanda dasu akeyi mishi rakiya.

Da sauri ya ɗaga musu hannu, cikin in in narsa da in yana saurin mgna yake fitowa
yace.
"Kkku ba bari ba'a bukatar rakiya".
Da sauri suka ɗan rusuna tare da haɗa baki wurin cewa.
"Aje lafiya a dawo lfy Allah ya kiyaye gabanka da bayanka Sheykh".
Amin Amin yace a taƙaice kana ya shiga motar, sarkin ƙofa ya rufe mishi marfin
sannan Ado yaja suka tafi.

Suna fita kai tsaye Babbar jami'ar dake cikin babban birnin Ɓadamaya suka nufa.
A can cikin makarantar kuwa,
Kasan cewar duk ɗaliban jami'ar sun san babban Doctor zai shigo yasa gaba ɗaya
harabar asibitin dake cikin jama'ar cika da taron tsala-tsalan ƴan mata ƴaƴan
manya, duk mai matsalar lfy tana fatan ya dubata sabida ƙwarewarsa.

A hankali wasu ƴan mata biyu suke taku a farfajiyar shiga asibitin, bisa alamu duka
ɗayar bata da lfy dan ɗayar na rike da hannunta, kuma a hankali suke tafiya.

Cikin tausayawa ɗayar ta kalli wacce ta riƙewa hannun a hankali tace.


"Garkuwa ki daure kiyi sauri mu isa, wallahi zamu samu layi da yawa, kuma wannan
Sheykh ɗin kasaitarsa nada tarin yawa, yanada doka da ƙa'idoji da tsari, yanada
tsauri kan tsare kima da darajar addininshi, daga shigar jikinki in kinyi kuskure
kaɗan na shigar kima wallahi bazai dubaki ba.
Shiyasa ahlul kitabi dake cikin makarantar nan suke masifar shakkarsa,
kinga gashi azahar ta kusa, kuma wallahi ko sarkin garin nanne yazo ya dubashi in
dai lokacin salla yayi to tashi zaiyi ya fita ya barshi, gashi shiru-shiru da ido
yake hukunta mutun".

A hankali wacce aka kira da GARKUWA tasa hannu ta gyara niƙab ɗin dake fuskantar,
wacce ta dace da wata kekyawar arabian gawn dake jikinta
wanda dama shigartace haka kullum sabida gudun kada wani ya ganta ya tsaida ita dan
tasan duk namiji daya nuna yana sonta har lahira ake kasheshi wanda kuma duk
Rugarsu akeda yaƙinin Ba'ana ne dan mutunne mai masifar baƙin kishi, yasha sanar
mata a kanta zai kashe kowa ba damuwarsa bane da fari duk wanda ya nuna yana sonta
da bulalin shaɗi yake korarshi, to yanzu duk wanda yace yana sonta sai dai a wayi
gari ya rasu.
Cikin sanyin muryar dake nuna azabar da takeji, murya na rawa tace.
"Rafi'a, bazan iyaba marata ciwo kamar zata ɓalle, ki sakeni kije ki amsar mana
foldana kafin in ƙaraso".
Jin haka yasa Rafi'a cewa.
"Zaki iya tahowa ke ɗaya?".
Kanta ta gyaɗa mata a hankali.
Hakan yasa cikin sanyi ta saketa kana ta wuce cikin Hospital ɗin da sauri.

Dai-dai lokacin kuma motar Dr Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero ta kutso kanta
cikin farfajiyar.
Bayan Ado ya dai-dai ta parking ne a cikin rumfar adana motor da aka rubuta Dr
Jabeer a samanta.
Ado ne ya fito da sauri ya buɗewa, Sheykh marfin motar, a hankali ya zuro
ƙafafunshi ya fito.
Cikin nitsuwa ya fara taku yana ratsowa cikin farfajiyar Hospital ɗin.
Kasan cewar ta gabas ya fito Aysha kuwa ta yamma ta fito sai ya zama suna fuskantar
juna.
Yayinda sai sun haɗu wuri ɗaya zasuyi kwana sun fuskanci kudu inda nanne mashigar
cikin asibitin.

A hankali suke takowa suna fuskantar juna.


Sosai ya zuba mata ido sabida ya lura gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi alamun
tsananin ciwo takeji gashi a hankali take taku.
Ita kuwa Aysha, tafiya takeyi da kyer sabida azaban ciwo da mararta keyi.
Kanta a sunkuye take tafiya, hakan yasa bata san da mutunba a gabanta.

Da sauri Sheykh ya tsaya sabida wani irin bugawa da ƙirjinsa ya fara. Ganin ta
tunkaroshi gadan-gadan, kuma daga yanayin tafiyarta tamkar zata faɗi ƙasa.
Ganin tayi wani irin sunkuyawa tasa hannunta duka biyu ta damƙe mararta da takeji
tamkar caccakarsa akeyi da allura.
Gefe ya ɗan tsaya yana kallon ikon Allah, ita kuwa GARKUWA rumtse idanunta tayi da
karfi, wata fitinenniyar zuface ke tsastsafowa tako ina,
a hankali ta fara buɗe idanunta jin kartan da mararta keyi ɗin yana ɗan lafawa,
a hankali ta zubawa kyawawan sawunshi idanu, cikin sauri ta ɗago kanta, ganinta
tsaye gab kusa da namijin da bata saniba ne yasata ja da baya da sauri tare da
miƙe tsawonta cikin firgici murya na ɗan rawa tace.
"I'm very sorry".
Bai kulata ba, sai kauda kanshi da yayi gefe.
Ita kuwa Garkuwa cikin sanyi tace.
"Dan Allah kayi haƙuri".
Kai ya ɗan gyaɗa mata alamar Uhumm.
Ita kuwa cikin sanyi tace.
"Uhumm kaima Doctor Sheykh ɗin kazo ganin ne?".
Da mamaki ya ɗan kalleta da gefen idonshi, sai kuma ya ɗan juyo kanshi kaɗan jin
muryarta a sanyaye taci gaba da cewa.
"Muyi sauri mu shiga ance yanada shegiyar ƙasaita da isa, wai ko sarkine yake
dubawa in dai lokacin salla yayi tashi yakeyi ya fita".
Cikin tarin mmki ya ɗan waro kyawan idanunshi tare da cewa.
"Umh".
Ita kuwa Garkuwa, hannu tasa ta matse mararta tare da cewa.
"Muyi sauri mu shiga, kaga kuwa kayi sa'a kayi shigar mutunci dan ance shi baya son
ganin musulmi da lalatacciyar shiga, ancema in mace tayi shigar banza baya dubata,
kaji shishshigin mutunfa ko meye ruwansa da rayuwar wasu ai kowa yayi mai kyau dan
kansa ko?".
Rolling Ball eyes nashi yayi tare da gyaɗa mata kanshi.
Kana ya tsuke fuska yaci gaba da tafiya.
Ita kuwa Garkuwa cikin yin ƙasa da murya tace.
"Uhum shidama akace shine shugaban tuzuran ƙasar nan, yana zaune baiyi aureba, ai
zama ba aurema ba kyau tunda dai yanada damar yi ko?".
Ɗan tsagaita takunshi yayi tare da cewa.
"Hummh".
A hankali ta bishi a baya cikin yanayin muryar mara lfy tace.
"Dan Allah ka tsaya in rigaka shiga kar yace sai ya dubaka kafin ya dubani".
Dai-dai lokacin kuma suka kutsa kansu cikin asibitin.
Da sauri Garkuwa ta zazzaro idanunta baki ɗaya, tare da dafe ƙirjinta ganin gaba
ɗaya Nurses ɗin dake ƙoƙarin fitowa sunyi maza suka koma baya, tare da rusunawa
suka haɗa baki wurin cewa.
"Barka da hantsi Sheykh".
Kai kawai ya gyaɗa musu yaci gaba da tafiya, har ya shiga cikin wani ɗan corridor
ya shiga wanda zai sadashi da tamfatsetsen Office dinshi ba tare daya ratsa ta
cikin Reception ɗin su ba.

Ita kuwa Garkuwa gaba ɗaya tsorone ya rufeta,


Gefen Rafi'a taje ta zauna wanda a take kuma mararta taci gaba da murɗawa da
kartawa.

Da ƙarfi ta damƙi hannun Rafi'a.


Cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Sannu, in sha Allah bazamu jimaba za'a kiraki, dan na nemi al'farman sauran sun
yarda Khadija Nasir Shugaba ce aka shigar, ƴar gwamnan, ba lfy".
Kai kawai ta iya gyaɗa mata, sai taune lips ɗinta da takeyi.

Shi kuwa Sheykh yana shiga Office dinshi, ya fara aikin daya kawoshi cikin ikon
Allah kuwa Khadija ta samu sauƙi tunda ya dubata aka bata magunguna.

Mutun biyar ya duba, na shida kuwa, Aysha ce.

Koda aka kira sunanta jiki a mace ta miƙe ta nufi inda take ganin ana shiga.
Nurse namiji na gabanta.
A haka suka shiga,
Ajiyan zuciya taja a hankali sabida tsaruwa da kyau da tsabta da ɗan karen ƙamshin
da ya ziyarci hancinta, su sukasa ta son bin Office ɗin da kallo amman ina ciwo
bazai bartaba.

A hankali ta iso gaban table ɗin baƙin Glass dake gabanshi.


Ɗaya daga cikin kujerun biyu dake gaban table ɗin ta zauna.
Ƙasa tayi da kanta cikin tarin ciwo da fargaba.
Shiru tayi zaune bisa kujerar tayi ƙasa da kanta.
Shikuwa Sheykh ko kanshi bai ɗago ya kalli inda takeba wanda wannan al'adarsace da
wuya ya kalli mutun, mafiya yawan lokuta yafi kallon mutun ta cikin gilashi table
ɗinshi,
shiru Office ɗin sai sautin A/C da yake busawa, shima kanshi Nos ɗin sai ya gaza
abin cewa,
Ita kuwa Aysha pat-pat haka zuciyarta ke duka, gashi tana jiyo mararta na fara
kartawa.
Kusan tsawon 1 minute suna a haka, cikin dakiya da rauni ta ɗan nago kanta ta
kalleshi,
Ga mamakinta sai taga asalima hankalinshi baya kanta, yana dai murza yatsunshi da
alamun tasbihi yakeyi.
Shi kuwa Sheykh duk abinda takeyi yana ganinta ta kan glass ɗin,
Cikin sanyin murya tace.
"(Jam ɓanɗuna). Ina kwana".
Shiru bai kulataba har sawon wasu daƙiƙun har ta fara zaton ko bai jita bane.
Da sauri ta ɗago kanta jin yayi mata magana, cikin wata sahihiyar murya a takaice
yace.
"Suna?".
Cikin fargaba ta tace.
"AYSHA ALIYU GARKUWA....!

*Uhummm wani kayan sai amale, wani littafin yafi ƙarfin a baka lbri ka iya haƙura
baka karantaba. GARKUWA YA WUCE ZATON MAI ZATO*

By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 5

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*LITTAFIN GARKUWA na kuɗine ga masu buƙatar biyan kuɗin samun damar karantawa
al'ummar Niger da kewaye ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 biya ɗari uku, ko
dubunki ɗaya kacal un saki a group. Gareku mutanena mutanen ƙasata in kina buƙatar
GARKUWA ga hankaɗo min ɗari uku kacal! ko dubu ɗaya rak! Ta asusuna na Jaiz bank,
0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyan ki ta
number ta 09097853276. Mutanen Ayyah SP Group bana son KATI. Kuma al'ummar 300 in
ba dole ba yaseen bana son KATI, to amman in babu yadda zakiyi, nasan akwai irina
ƴan ƙauye, ba POS. Kuma kuna son karantawa, to hankaɗo katin mtn ɗinki na darinki
uku kisha karatu. Allah ya nuna mana ƙarshensa lfy kamar yadda ya nuna mana
forkonsa lfy. ALLAH ya bamu haƙurin zama da juna*

```Fans 1&2 sarakan surutu, Ina gaidaku ina ji daku har cikin ƙoƙon raina. SP
Group, inai muku jinjina dubu-dubu.Fans 3
Allah ya rayamu ku cika maƙil. Group ɗin kurame kuma ina sane duku ina kuma jin
daɗin nitsuwarku ba surutu. i love all my fan's irin lodi-lodin nan mafa```

```Gyaran amare uwar gidaye masu jego da masu tada komaɗa da sabunta dararen satin
forko na amarci. Ku garzayo gani gareku da tsaraba kamarsu, tsumin Tsartai, sa buzu
kuwa, garin babambaɗe, garin maɗi mai maɗemaɗin ni'imomi, bunbar ke ɗaya, gumbar
Mali mai taken kolli mai sheƙi sai dai gsky ita tanada tsada, gumbar Uku
csrmazaƙoi, gumbar haɗin inabi dabino kwakwa riɗi.
Akwai haɗin ilan waddi, duk ba fula tani in yaji ilan waddi uhumm, akwai garin
Belɗam yel, akwai tsumin ta baje, akwai kwanon ƙasaitacciyar mace, akwai kirɓeɓɓen
tsumin domin mutanen nesa, akwai mgnin sanyi Infection, akwai butar sirri mai.
abubuwan dai da yawa, gani ya kori ji, in kina buƙata kiyi min mgn ta wannan number
09097853276 kada ki kira dan ban fiye daga kiraba, gwara kimin mgn ta whatsapp in
kinga bana kusa Turo min text message ta in-box```

A hankali ya ɗan ɗago ƙwayan idanunshi ya kalleta.


Kanta a sunkuye hannunta biyu duka na kan mararta cikin wani, irin yanayi take
wanda yake nuni da tana cikin wahala.
A hankali ya maimaita sunan cikin zuciyarshi.
"AYSHA ALIYU GARKUWA! To GARKUWAN ina? GARKUWAN meye?."
A fili kuma kauda idonshi yayi daga kanta ya maida idanunshi kan tarin foldan dake
gabanshi, wanda sunanta ke rubuce akan na samanshi yaja da yatsu biyu.

Shafin forko ya buɗe a folder kana, yasa hannu cikin wani ɗan abu mai kama da kofi
wanda yake cike da biro masu kyau da tsadar gaske.

Tsiraran idanunshi ya lumshe sabida wani irin bugu da yakeji zuciyarshi nayi tun
sanda ya hango yarinyar har zuwa yanzun nan da take gabanshi a zaune.
Rubuce-rubuce yayi a ciki irin nasu na Doctors masu kama da tafiyar wahainiya.
Kanshi ya kuma ɗagowa ya kalleta a fizge da gefen idonshi,
sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa.
"Meke damunki?".
Cikin shessheƙan wahala da son danne kukan da ke son kabce mata tace.
"Marata, da bayana".
Kai ya ɗan jujjuya tare da kallon shekarunta dake rubuce a cikin folder din,
Yar shekara ashirin kuma da ƙorafin ciwon baya, cikin dakekken sauti yace.
"Yaushe ya fara miki ciwo?".
Hannu tasa ta cikin niƙabin da yayiwa fuskarta ƙawanya ta share hwayenta a hankali
tace.
"Shekara uku da suka wuce".

"Meyasa bakije asibitiba tun lokacin?". Ya tambayeta a daƙile.

"Ina zuwa asibiti duk sanda ya tashi".

"Kamar yaushe da yaushe yake tashi?". Ya jefo mata tambayar kamar yadda zuciyarshi
ke harbawa da ƙarfin tsiya da kuma sauri-sauri,
Kai ta sunkuyar tare da cewa.
"Duk ƙarshen wata daga 21 zuwa 25". Shiru yayi kamar bai jitaba sai wasu rubuce-
rubucen ya kumayi.
Saida ya gama sannan ya tura mata folder ɗin gabanta.
Jikinta na rawa tasa hannu ta ɗauki folder ɗin, ta yunƙura zata tashine, ya basu
damar samun kusanci da juna,
da sauri ya rumtse idanunshi sabida wani irin azabebben bugu da zuciyarshi keyi
tamkar zaiyi tsalle ya faɗo woje,
cikin zuciyarshi yake maimaita.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun."
A hankali ya buɗe kyawar kyawan idanunshi jin bugun zuciyarshin ya fara yin ƙasa-
ƙasa, ido ya zubawa mata ganin ta juya tana tafiya,
wani abin al'ajabin a gareshi shine duk taku ɗaya da zatayi tana nesanta dashi sai
yaji zuciyarshi na tsinkewa yana bada wani mugun bugun ras-ras, yayinda bugun
tsinkewanta kuwa yaketa dai-dai-ta,
Cikin mamaki ya sunkiyar da kanshi yana kallon yadda takeyin taku, tana riƙe da
mararta, taje gab bakin fofar fitane,
Taji wani irin murɗa da kartan da mararta ya farane yasa ta sakin wani sauti mai
cike da wuya.
"Wayyoooooooo Allah na, Wayyo Ummeyna cikina".
Da sauri nurse ɗin nan yayi kanta tare da cewa.
"Isah Allah rena joɗu".
Ya ƙarishe mgnar da nuna mata kujerun farin ƙarfe dake gab da bakin ƙofar.
Bata da zaɓin daya wuce ta zauna ɗin, domin gaba ɗaya ƙafafuwan ta rawa sukeyi
alamun bazasu iya ɗaukar nauyinta ba ga duhun daya rufe mata ido.
Sunkuyowa Nos ɗin yayi ya amshi folder kana yace.
"Zauna bari inje Pharmacy in amso miki magungunan da alluran sai ayi miki".
Kai kawai ta iya gyaɗa mishi tare da bashi.

Har ya fita sai kuma ya dawo yace.


"Ok sir". Jin Sheykh Jabeer yace mishi ya turo ta gaba
Da sauri ya fita.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, tasbihinshi yaketayi da yankan yatsunshi yake ƙidayar,
sabida, suma yatsun su kasance cikin bautar Allah shiyasa yake ƙidayar amman ba don
wai yasan adadin salati da hailala da istigifarin da yakeyiba, wannan ubangijine
kawai masanin adadinsu.

Bayan fitar Nos ɗin da kamar 1 minute wata,


Kekyawar budurwa ta shigo, cikin yauƙi da ƙasaita, sai wani irin masifeffen ƙamshin
da take zubawa.

Ƙarasowa tayi gaban table ɗin nashi ta zauna,


cikin yauƙi da korkosa tace.
"Barka da rana Al' Sheykh".
Ko inda take bai ɗaga ido ya kallaba, ya lura ya gane akwai wani abu tattere da
yarinyar, dan mafi akasarin ranaku sai tazo, wai bata da lfy, kuma takan zo da
ciwuka mabanbanta ne.
Sanin ba musulma bace yasashi ƙara tsuke fuskarsa tamkar zatayi aman wuta, a zafafe
yace.
"Name". Cikin yauƙi da son isar da aikin da aka bata tasa hannu ta jawo foldan ta
dake sama tura mishi gabanshi tayi,
Cikin harshen hausa da tasan bai fiye son English language ba a rayuwarshi a
hankali tace.
"Breast ɗina kemin ciwo, har bana iya sa bra."
Sai kuma tayi ƙasa da mayafinta dake jikinta, hannu tasa kan zip ɗin gaban rigarta
tana ƙoƙarin zugeshi ƙasa tare da cewa.
"Kalli Nipples ɗin sun....
Cikin tsananin firgita da tsoro, ta miƙe da azaban ƙarfi, jin yadda yasa hannunshi
ya bugi table ɗin da azaban ƙarfi wani irin gigitaccen tsawa mai firgitarwa ya daka
mata tare da cewa.
"Tashi, daga gabana".
Karkar jikinta ke tsuma sabida kwarjinshi da tsoronshi sun daki zuciyarta da take
cike da fajirci dama dan bata kallon fuskarshi ne ta iya faɗin waɗannan kalaman ma.
Dai-dai lokacin kuma, Nos ɗin nan ya shigo,
ganin yadda AYSHA ta gigice taketa karkarwa, alamun tana son ta miƙe kuma ta kasa
tashi.

Shi kuwa Sheykh foldan ɗin Rabeca ya jawo wani rubutu yayi saman foldan ɗin kana ya
tura matashi gabanta cikin zafi da tsauri ya nunata mata hanyar fita tare da cewa.
"Fice min daga Office daga yau in kina buƙatar ganin Dr kije gun Dr Ute, shi
zakiyiwa duk sakarcinku na al'jihun baya. Ba niba, sannan daga nan ki wuce Zaria
kije asibitin Shika domin ina zaton breast cancer kike dashi".
Da sauri tasa hannu ta ɗauki foldan ɗin, gaba ɗaya jikinta na rawa, juyawa tayi ta
fice tare da yin magana can ƙasa yadda bazai jitaba tace.
"Allah ya sauwaƙa Ni bani da breast cancer, mugun bakin kawai."

Shi kuwa Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar lumshe idonshi yayi
a ranshi yake haɗa kalaman da yaci karo dasu a safiyar yau.
Kakarshi tace mishi, aji mgnar Malam kada a duba aikinshi, ta jaddada mishi, wai
yayi aure, kana wannan mayyar yarinyar da in tana kusa dashi zuciyarshi ke barazar
fashewa, kuma tace mishi wai shine shugaban tuzuran ƙasar nan baki ɗaya.
Tabbas wannan shaidace na abinda ake faɗa a cikin gari a kansa kenan, yaji ya sani
Sitti ma da take son suje saudia wai so take ya zaɓi matar aure a can, ga wannan
kafurar da ya san turota akeyi ta tallata mishi kanta, don a samu cinikin jarida ya
hauhawa ta hanyar buga kanun labarai cewa, Sheykh mazinacine ko kuma mata yakebi
shine ya hanasa aure.
Jingina kanshi yayi da kujerar tare da mgn a zuciyarsa.
"Ya ilahi ya mujibadda'awati".
Ta yayane ta inane wa zai gayawa cewa,
shifa yanada banbanci da sauran maza, ba kamar kowa yake ba, taya zai gaya musu ko
zai samu a daina binshi da kalmar yayi aure, me zaiyi da mace ta yaya zai fahimtar
dasu su barshi ya huta.

Wannan shine nazarin da yakeyi cikin zuciyarshi,

Ita kuwa Aysha ido ta tsurawa, ƙasan kujerar da yake zaune a kai tana kallon wani
al'amari mai cike da ruɗarwa.
Ido ta rumtse sabida bazata iya jurar ganin wannan abun ba.

A hankali Nos ɗin nan ya matso gabanshi, magungunan da alluran daya amso ya miƙa
mishi su.

Cikin sanyi yace.


"Sir ga magungunan".
Kanshi ya ɗan tankwarar tare da cewa.
"Kira Dr Ruƙayya tazo ta mata alluran".
A hankali yace.
"Sir na duba duk sun tashi, sabida babu kowa. A Reception ɗin, mune kadai muka
rage".
Kanshi ya jinjina, don shima yanzu zai tafi, sabida akwai gidajen likitocin a nan
kusa koda shi ya tafi Dr Ruƙayya da Dr Ute suna nan cikin makarantar.
Ta gefen idonshi ya ɗan kalli Aysha daketa fama da ciwo,
Ganin Nos ɗin na haɗa allurar ne yasashi, fara tattara woyoyinsh dake bisa table
ɗin.

Shi kuwa nos ɗin. Yana gama haɗa alluran ya nufi inda take, tare da cewa.
"Gyara in miki alluran".
Cikin sanyi tace.
"To". Yana isowa gabanta yace.
"Dole ai sai kin tashi tsaye, kinga doguwar rigace a jikinki kuma sai kin naɗeta".
Ido ta ɗan zuba mishi ta cikin niƙabin tare da jujjuya kai a hankali tace.
"Um ummm".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"Tashi mana sauri mukeyi lokacin sallah ya ƙara to".
Shi dai Sheykh ido ya zubawa bayan Nos ɗin yayinda ita kuwa yake kallon gefenta,
cikin bada umarni yace.
"Kuzo".
Da sauri Nos ɗin ya juyo ya nufoshi,
hannu yasa ya amshi allurar,
kana ya ɗan kalleta a fakaice yace.
"Zo nan".
A hankali ta taso cikin sanyi takeyin taku tana matsoshi.
A take kuma bugun zuciyarshin ya fara hauhawa yana komawa matakin sama.
Taku biyu tayi ana uku yaji ƙirjinshi ya bar tsinkewar da yaketa yi ɗin, sai kuma
bugun da yakeyi da sauri-saurin ne yaketa tsananta.

Taku takwas tayi ta iso tsakiyar Office ɗin, ido ya fara jujjuyawa kan table nashi
yana mai jin wani masifeffen bugun zuciyarshin dayasashi hatsala cikin ɗan ɗaga
murya yace.
"Ke da Allah kiyi sauri".
Jin hakane yasa ta kara saurinta, ai kuwa da sauri ya dafe ƙirjinshi lokacin da ta
iso gab dashi, cikin ranshi ya kuma cewa.
"Hasbunallahiwani'imanwakil".
A zahiri kuwa, da kai ya nuna mata ta kuma matsowa, ba musu ta matso,
yatsarshi ya jujjuya mata alamun ta juya mishi baya,
still babu musu ta juya, a hankali ya murza kujerar da yake kanta, ya juyo ya
fuskanci bayanta, dai-dai saman mazaunanta ta sama ta ɗan gefe kaɗan, ya saita,
tsinin bakin allurar, cikin iyawa da gwarewa dan salonshi ne baya taɓa yarda ya
kalli fatar jikin wanda zaiyiwa alluran ta saman tufafinka yake zira allurar, shiru
tayi tana jin yadda, allurar ya ratsa dogon rigar jikinta ya bada sautin tub alamun
ya huda rugar, a hankali ta kuma jin ya huda, dogon wondon jikinta tub, sai kuma
taji ya sauƙa kan pantien jikinta, daga nan taji ya ɗisa bakin allurar kan fatarta,
rumtse idanunta tayi da azaban ƙarfi sabida, wani zafi da taji yana ratsata, bawai
tana tsoron Allurar bane, sai dai hannunshi yanada masifar zafine,
kana shina ruwan alluran irin mai, mai-mai ɗinanne kuma duk cikin allurai yafi
zafi.
Da ƙarfi tace.
"Wach Allah na zafi-zaffi."
Wani irin azaba taji lokacin daya fara cusa mata ruwan allurar a jikinta, babu zato
babu sammani yaji tasa hannu damanta ta cabki hannunshi dake mata alluran hannunta
na hagu kuwa yarfashi take tare dasa kuka da sauti tace.
"Wayyo Allah na, ka bari bana so zare Allurar nan zafi nakeji".
Ta ƙarishe magar da zurma sakalin ihu".
Bugawa da zuciyarshi keyi yana bada sautin dib dab dib dab dib dan shine ya kusan
hallakashi lokacin data riko hannunshi, da sauri ya tura mata ruwan kana ya zare
Allurar da ƙarfi.
Sannan ya miƙe tsaye, sabida muddin yana kusa da ita babu makawa wata ƙil
zuciyarshi zata faso ƙirjinshi ta fito woje.
Wani dogon tsaki yaja tare da juyawa ya bi gefen Nos ɗin ya fice.

Itama da sauri tabi bayanshi bayan tasa hannu ta amshi ledan magungunan.

Shi kuwa da sauri yake tafiya sabid iya yedda yake nesanta da ita iya yadda
kirjinshi ke dai-dai ta bugawa, sai kuma tsinƙewa da zuciyarshi keyi babu
ƙaƙƙautawa.
Ita kuwa AYSHA da sauri ta nufi sashin makwancin ɗaliban Hostel dake cikin
makarantar sabida ta fara jiyo alamun bakonta ya iso.

Baba Ado kuwa drevernshi yana hangoshi ya tashi ya buɗe mishi marfin motar, yana
zuwa, ya shiga, maida kofar Baba Ado yayi ya rufe sannan ya shiga yaja motar suka
fice daga harabar asibitin.

Ita kuwa Aysha tana shiga Side ɗinsu ita da Rafi'a, ta samu Rafi'a bata falo da
alamun tana kitchen nasu, dan tajiyo ƙamshi alamun tana ɗan dafa musu abinda zasuci
ne.
Kai tsaye bathroom ta wuce, tabbas kuwa baƙon ya iso, dan haka ta nitsu ta gyara
jikinta, bayan ta gama ne ta miƙe a hankali ta kwance niƙabin tare da fara zare
dukkan kayan jikinta dan yin wonka,
Aysha farar ba fullatanace irin farare ƙal-ƙal ɗin nance, gashin kanta kuwa mai
tarin yawa da tsawone baƙine sit mai sheƙi, yanada cika,
jikinta ɗan fiyau, sai dai tanada welcome and bey bey masu girma da cika, cikinta
kamar babu hanji a ciki ɗan fiyau dashi, breast ɗinta tirtsa-tirtsane masu cika
tab-tab kuma irin mai gindin tasa ɗinnan wanda da alamun ba masu zubewa bane, domin
suna nan cas dasu, kamar zasu tsone idon mai gani, tanada tsukekken ƙugu da
kyawawan mazaunai, sawonta dai-dai musali baza'ace mata doguwa ba sam, kuma baza'a
ce mata gajera sosaiba in tana kusa da dogo dai za'a iya kiranta da gajera.

Fuskarta kekyawa ce irin kyan da babu namijin da zai gani ya cire ido, hancinta
dogo har kan ɗan ƙaramin bakinta mai jajayen tausasan laɓɓa idonta manyane sai dai
ba ƙattiba, zirin idonta wurinda akesa kolli jane mai kyau, shiyasa yake ƙara
baiyana farin idonta bakin ciki kuwa bakine sitik sai dai ɗan ƙaramin ɗigon cikin
bakin shi kuma ruwan ƙasane wanda yakeda sirri namu samman.
Gashin idonta zara-zarane, gashin girarta kuwa irin mai W ɗin nanne kamar na Kajol,
bi ma'ana yana haɗe bisa karan hancinta,
Tanada fararen haƙora masu kyau suna jere reras dasu tanada dimple ɗinta mai ɗan
karen kyau. Idanunta kuma ko yaushe kamar maijin bacci suke.

Wonka tayi kana tayi al'wala dan ko bata salla bata zama babu al'wala.

Tana fitowa ta kimtsa jikinta kana ta zura tattausan doguwar riga.

Tana kokarin fitowa falo Rafi'a na ƙoƙarin shigowa da sauri Rafi'a ta zaro ido tare
da cewa.
"Yaushe kika dawo?".
Hararanta ta ɗanyi tare da cewa.
"Ba dai kin gudo kin dawo kin barni ni ɗaya ba".
Cikin tausayawa Rafi'a tace.
"La wlh yanzu nake ƙoƙarin komawa, na dawone in ɗan dafa mana abinda zamuci in mun
dawo, sabida naga rabonki da abinci tun jiya, shiyasa kina shiga Office ɗin Dr na
dawo".
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana tace.
"Na dawo a guje fa, wannan Sheykh ɗin hannunsa zafi kamar allurar mashi yakewa
mutun".
Zaro ido na mamaki Rafi'a tayi tare da cewa.
"Shida kanshi ya miki?".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Eh".
Cikin taɓe baki tace.
"Lallai yau kin tashi da ƙafar dama, gashi kuwa naga har kin worke".
Wucewa sukayi zuwa tsakiyar falon, cikin sauƙe numfashin Aysha tace.
"Ba doleba yadda yake tura ruwan alluranshi nan kamar mai tura mai a mota, kuma ina
dawowa nasha mgni, sannan abin ya iso, kinsan dama wuyar kafin ya isone".
Dariya Rafi'a tayi tare da cewa.
"Kinji allurar manyan likitocin da duniya keji dasu dai".
Uhum kawai tace sannan suka fara cin abinci, sunaci suna hira.

Cikin hirar tasu ne Rafi'a tace.


"Anjima da yammafa jirginmu zai tashi".
Da sauri Aysha tace.
"Haba dai Rafi'a dan Allah ki bar zuwa hutunnan mana ki bari mu zauna, wallahi in
kin tafi nima dole in tafi kuma ke kin san matsalar da nake da ita a gida ko Mamey
ma da mukayi waya dazu cemin tayi kar in koma hutu Rugarmu, in zauna a makaranta".
Cikin sanyi Rafi'a tace,
"Wallahi nayi kewar gidane Aysha, shekara guda kenan banje gidaba fa".
Cikin sanyi Aysha tace.
"Haka ne kam ba, matsala, ai hutun sati ukune, kina tafiya yau nima gobe zan shirya
zan koma Rugarmu".
a haka sukaci gaba da hira suna cin abinci.

Ƙarfe huɗu dai-dai na yamma jirginsu Rafi'a ya tashi daga Ɓadamaya international
airport, zuwa Farazan state.

Ita kuwa Aysha taci gaba da shirinta ba tare da ta gaya mutanen gida cewa zata dawo
ba.
Kaya kaɗan ta ɗiba dan tanada kaya a gida, system ɗinta da wayarta da kuma kaya
kala biyu kawai ta ɗauka, sai yan ƙananun abubuwan, ta da tayi nufin sai gobe zata
koma.
Amman ina tafiyar Rafi'a yasa taji bazata iya zaman kaɗaicinba, dan haka huɗu da
rabi, ɗaya daga cikin motocin dake maida ɗalibanda in gidajensu na kusane ya ɗauke
ta.

Kai tsaye garin Shikan suka nufa.


Tafiyar ba wata mai nisa bace daga cikin birnin Joɗa zuwa Shikan, cikin mitina
kaɗan suka isa,
Ƙarfe biyara da miti biyar suka isa.
Cikin Shikan a nan tasa drever ya tsaya ta sayi Junainah sweet.

Biyar da mintuna goma dai-dai suka isa kwanar mashigar Rukarsu Rugar Bani.

Cikin tsoron kada Ba'ana yaga wani yazo ya sauketa ya masa rashin mutunci, tace.
Ya sauketa a nan ba musu ya sauketa dan ai inda sabo ya saba.

Tana fita taja jakarta, ta rataya kana ta gyara tarhan da tayiwa kanta.
Shi kuma ya juya ya tafi.

A hankali ta zubawa yankin garin nasu ido, ko ina yayi kore shar, yabanya da
ni'imar damina ta wadaci ko ina, wata iriyar sassanyar iska mai daɗin ke ratsa mata
jiki da zuciya.

Ajiyan zuciya ta sauƙe a hankali tare da lumshe idanunta kana ta buɗe hannayenta
cikin begen gida tace.
"Rayuwar ƙauye mu akwai daɗeeee".
Ido ta buɗe tana kallon tako ina makiyayen rugarsune suketa dawowa daga kiwo,
Dabbobi saffan-saffan sunata dawowa,
garin yayi lum ga wani hadari mai ƙarfi daya keto, daga ƙasan dutsen da yayiwa
Kyauyen ko ince Rugar Bani ƙawanya, a hankali take taku tana bin kan faffaɗan
hanyan da makiyayan sukayishi bi ma'ana burtali kenan.

Taku take yayinda gefen hagunta wutsiyar kogin Shikan ne konce iya ganinta,
gefen dama kuwa Garden ɗinsune mai girma wanda yasa sanyin wurin yake yawaita,
sauri ta ɗan farayi sabida akwai ƴar tazara kana kuma gashi magriba ta karato.
Tana cikin tafiya tana rataye da jakarta, kamar daga sama taga wulgawar inuwan
mutun, cikin sauri ta zaro idonta ta kalli gefen hagu da damanta,
Ba kowa ganin hakane yasa taci gaba da tafiyarta cikin dakiya, taku uku tayi ana
huɗu taji ansa hannu an amshi jakarta, da sauri ta juyo ta kalli gefen da aka amshi
jakar.
Babu kowa a wurin kuma ga jakarta a rataye ita ɗaya tana binta suna tafiya a jere.
Cikin wani irin fargaba tsaro kaɗuwa da tsananin firgita ta....!

By
*GARKUWAR FULANI*[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇
🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 6

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*FREE PAGE*

*Kada dai ku manta har yanzu Free page kuke samu, wanda zamu datseshi cikin ko
wanne lokacin, hamzarta ku biya darinki uku kacal ko 1k ga mai dama da niya, domin
samun cikekken labarin daki-daki cikin salama. Turo kuɗin ta asusuna na Jaiz.
0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidan biyanki ta layina
09097853276. In ya zama larura ba halin turawa ta ac turo katin mtn na ɗari uku, ko
na 1k ɗin domin ci gaban lbrin GARKUWA. Sayan na gari maida kuɗi gida. Ina mai yi
muku fatan al'khairi masoyana makaranta, ina sonku domin Allah ina fatan kyautata
alaƙa ta da kowa sabida nasan ko ina raye watarana zan zama tarihi a duniyar
marubuta, sabida yauda gobe ta wuce watsa, in ba mutuwa akwai tsufa. Kana dole
watan wata rana gwanayen zasu zama tsoffin hannu kana yan koyo na yanzu su zama
gwanayen, domin da babu yan koyo tabbas da gwanayen sun ƙare, inada fata da burin
ganin al'ƙaluman Adabi sun inƙanta baki ɗayansu ba nawa kaɗaiba, tsarkake rubutu
ki/ka domin kece madubin wata marubuciya da zata iya tasowa nan gaba.Ina mai muku
fatan al'khairi🙏🏻🤝🏻😘 🥰😘 makaranta da marubuta*

Cikin firgita da tsoron tace.


"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil, lailaha'illalahu
Muhammadurasulillahi sallahu'alaihi wasallam Auzubikalimatillahi ta'ammati min
sharrin ma khalaƙa Allahum...".
Da sauri ta koma da baya ba tare da karisa addu'ar ƙarshen data faro ɗinba. Ganin
Ba'ana ne tsaye a gabanta cikin wata iriyar dariya yace.
"Ke ki nitsu masoyinki ne ke gadinki, gsky *Mata* dole in rage miki wannan tsoron,
domin matar Ba'ana bazata kasance matsoraciya ba, dole in ƙara tsumaki in dafaki da
kyau, ta yadda idanunki zasu buɗe da kyau".
Cikin karkarwar da bai bar jikintaba tace.
"Bana so. Ni ka barnin da tsorona, nifa macece ba namiji irinka ba, kaine ke shiga
daji da tsaunuka kake buƙatar wani abu ya kare ka".
Da sauri Ba'ana farin kekyawan babarbare ya matso gareta cikin shigar fulanin da ya
zame mushi sutura yace.
"Mata ke bakya buƙatar kariyar ne?."
Da sauri ta gyaɗa mishi kai tare da cewa.
"Ni na yarda cewa addu'a'u saiful muminin ne, kuma shi na riƙe, so bana buƙatar
waɗannan asirce asircen".
Murmushi yayi tare da murza ƙafarshi ta hagu sai gashi ya zama kamar inuwa ba mutun
ya ɓacewa ganinta ɓat.
Da sauri ta rufe idanunta tare da cewa.
"Bana so ina tsoro ka dena caccanza kamanni a gabana".
Da sauri tayi baya ganinshi gab da ita,
Dariyar ƙeta yayi tare da cewa.
"Baga irinta nanba, idonki baya iya ganin komai, dole zan ƙara haɗaki irin haɗin da
zaki ke banbance mai layar ɓata data zana da jingina bongo da dama duk mutun mai
juyewa i zuwa wata halittar".
Ya karishe mgnar yana nuna mata hanya alamun su tafi.
A hankali suka jera suna tafiya a tare.

Allah ya sani Ba'ana yana masifar son Shatu tun tana ƴar ƙaramar yarinya, yana
sonto irin sonda ko ƙudane in ya sauƙa kanta in dai namiji ne to zai kasheshi,
ganinta kusa dashi kawai yana sashi jin daɗi, duk muguntarsa baya yi mata, duk
duniya babu wanda Ba'ana ya yarda da shi bare yasan sirrin makarin sihirurrukan
dake jikinshi. Ba'ana mutunne da yake tamkar al'janu sabida yawan ta'ammali da
sihiri kai harma da tsafi, Ba'ana riƙeƙƙen tantirin ɓarawone wanda ya buwayi Fulani
al'ummar Afirka gaba ɗayanta, da sace-sacen dabbobinshi, muddin ya ƙella ido yaga
garken shanunka yayi mishi, to tazarar kilo mita talatin da biyar yake tsayuwa da
garken, yayi FITO ɗaya tak, wallahi duk sihirin kafiyar garkenka zai kunce kuma duk
inda yayi shanayenka zasu bishi a baya da kuma wannan tazarar, da zaran kasa Hukuma
cikin zancen kuma yana burza layar ɓatanshi dashi da dabbobin duk zasu ɓace.

Duk garken da yaga yayi mishi to sai ya kwashesu tsan da wannan ya tara dukiyar
dabbobin da shi kanshi baisan adadinshiba babu ƙasar da bashi da makiyayanshi kamar
su.
Chadi, Nijer, Cameroon, Ghana, Gabon, Maroco, Senigal, da dai sauran kasashen
makusantanmu kuma masu dabbobi, hikimar da yakeyi, muddin ya saci shanayen ƙasar
Niger to sai ya cillasu ƙasar Senegal, in kuma makiyayanshi na ƙasar Sanigal sukayi
sata to sai ya turo shanayen ƙasar Gabon, haka dai yake banbance mazauninsu.

Sai dai garin zamansa ɗaya ne Rugar Bani, inda nan aka haifeshi mahaifinshi Bukar
wanda babarbaren Norba ne saye da sayar da kanwane ya ajiyeshi cikin rugar FULANI
shiyasa ya zama dilan saida kanwa, sabida dole duk bafulatani makiyayi yana
ta'ammali da kanwa dan ana zubawa dabobbi susha a ruwa ko asa musu a dusa ko harawa
yana musu mgni.

Ba'ana ya shiga cikin Fulani ya saje dasu.


Yayinda hakan ya bashi damar da duk duniya ake ɗaukarshi matsayin bafulatani, koda
yake hakan baya rasa nasaba, da kallon da mutanen duniya sukewa duk mutumin da
akaga shanu, tumaki a gabanshi tofa ko wacce gabilace shi, ya zama bafulatani,
wanda kuma sam ba haka abin yakeba.

Mahaifiyar Ba'ana ɗaya daga cikin ƙabilar ɓachama ce,


wacce Bukar ya aura tana a matsayinta na anniya, koda kuwa suka haihu ɗan su. Bukar
ya rinjaye ta Ba'ana ya kasance musulmi, sai daifa a baɗini baƙar zuciyarsa da
aiyikansa na kafuraine, sata kuwa a wurin babarsa ya gada.

Ba'ana kekyawan mutun ne ajin forko wanda ya gaji wannan kyan ne a kakarshi
mahaifiyar babanshi wacce take shuwa Arabce, koda maƙiyinshi yasan tabbas Ba'ana
kekyawane.
A duniya kab Shatu ce tasan sirrinshi ciki da woje,
sai daifa bata san yana sataba, amman duk wani abu na asiri da yadda za'a karya
asirin da kuma yadda yake juyewa duk ta sani.
To hakanne yasa sam bata fatan ya zama miji a gareta bare uban ƴaƴanta, sai dai
babu yadda ta iya. Domin ya mata babbar rana a rayuwarta ya mata taimakon da yasa
aka ɗaukar mishi al'ƙawarin aurenta.
Gashi kuma duk wanda yace yana sonta karshenshi mutuwa, kuma yana gaya mata cewa
duk wanda yace zai rabashi da ita zai kasheshi Wannan yasa kullum addu'ar shirya
take mishi da fatan Allah ya rabata dashi lfy innshi ba mai shiryuwa bane.

Tafiya sukeyi cikin nitsuwa a hankali, murmushi yaketayi cikin so da ƙaunarta yace.
"Mata ya akayi na ganki da ƙaramar jaka?".
Kai ta ɗan gyaɗa mishi tana kallon kekyawar fuskarshi, cikin murmushi yace.
"Kece kika ajiyeni a kasar Kautal a Rugar Bani, kina ƙare karatunki zamuyi aurenmu
in ɗaukeki mubar ƙasar, kawai dolece tasa na hakura da batun aurenmu kiyi karatu,
dan naga kina son karatun kuma nasan zaki karantar mana da yaranmu, kuma ina son ki
zama babbar lawyer mai zaman kanta, sai ki zama lawyer na koda watan-wata rana,
rana zata ɓacin min".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kamar yaune zan kare karatun, Ya Ba'ana".
Kanshi ya rausayar tare da gyara riƙon igiyar jakar da yayi, kana yace.
"Allah ya nuna min wannan lokacin, in sha Allah sadakin aurenki Garken shanu ɗari
zan bada".
Cikin mmki ta zaro ido tare da cewa.
"Kai Ya Ba'ana garke ɗari bama shanu ɗariba, ya bana ina zaka samu wannan shanun
kaida garken naku ko shanu hamsin bai cikaba".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Allah zai kawosu kafin lokacin auren namu".
A hankali tace.
"Allah ya kawosu".
Amin Amin yace tare da ɗan juyowa ya kalleta, murmushi yayi mata, kana ya miƙo mata
jakar tata cikin so yace.
"Mun iso bakin Gari ki shiga.
Ni zan koma baya dama rakoki nazo nayi kar shaiɗanun bakin kogi su cutarmin dake".
Kai ta ɗan jinjina tare da cewa.
"Ya Ba'ana lokacin sallah ya kusa fa ai gwara ka shigo sai kayi salla ka koma".
Bakinshi ya ɗan tabe tare da cewa.
"No bar sallan nan sai bayan mako biyu ina ƙara dafa jikinane kuma in nayi al'walan
duk aikin zai karye".
Dafa kanta tayi da sauri tare da cewa.
"Wa'iyazubillah Wayyo Allah na Ya Ba'ana ka gane mana wannan abin da kakeyi shirka
ne,".
Kanshi ya jujjuya tare da cewa.
"Shiga cikin gari zanzo musha hira da daren".
To kawai tace mishi ta juya ta nufi cikin garin.

Tana shiga ta kama hanyar gidansu, tana gab da shiga gidane ta haɗu da ɗan
makotansu Iro cikin girmamawa tace.
"Ina wuni Ya iro".
Fuska cike da fara'a yace,
"A a lale marhabin da ƙanwarmu yar al'barka anyi hutukenan?".
Kai ta gyaɗa mishi sannu da hanya ya mata sannan ta wuce ya wuce.

A gindin bishiyar mangoro dake kofar gidansu gab da zaure ta hango Bappanta yana
zaune bisa dakalin dake wurin yana al'wala, da sauri ta nufi in da yake fuska cike
da jin daɗi.

Shima Bappa da sauri ya miƙe yana murmushi yake cewa.


"Maraba lale da ƴar al'barka."
Da sauri ta iso inda yake tana murmushi mai nuna tsantsar jin daɗinta tace.
"Oyoyo Bappa na, Alhamdulillah na sameka lfy, ya Ummey na da Innata?".
Dariya yayi tare da matsota yace.
"Duk muna lfy".
da sauri suka juyo ta cikin gida jin muryar yayunta suna cewa.
"Oh wato mu kam bakiyi kewarmu bama ko?".
Da sauri tayi gabansu cikin jin daɗi tace.
"Oyoyo ƴan uwana Ya Gaini, nayi kewarku mana, musamman Ya Giɗi sarkin son girma".
Murmushi sukayi dukansu,
Seyo ne ya kalleta tare da cewa.
"Wallahi yanzuma mgnarki mukeyi da Ummey, har Junainah na cewa wai ai duk munfi
sonki".
Dariyar jin daɗi tayi tare da cewa.
"Ayyah ƴar ƙanwaliya tawa mai kishidani".
Murmushi sukayi baki ɗaya kana Lado ya kalleta tare da cewa.
"Shiga gida mu zamu wuce masallaci ne".
To tace kana ta nufi cikin gida tana cewa.
"Yauwa yaya Giɗi dan Allah a kawomin rake".
Kai ya gyaɗa mata kana suka wuce ita tayi cikin gida.

Tana shiga da fara'ar jin daɗi da ɗan karfi ta buɗe murya tare da cewa.
"Assalamu alaikum, gani na dawo, ina Inna ina Ummey, Junainah ina kike?".
Ai kusan a tare suka fito gaba ɗayansu, wani irin tsalle Junainah ta buga tare da
rugawa ta nufi kan yayar tata cikin ihu da ɗaga sauti take cewa.
"Oyoyo Addana oyoyo".
Da sauri Ummey ta harateta tare da cewa.
"Ke Junainah magriba cefa, kike irin wannan ihu ke sam baki da nitsuwa".
Ita dai batama jitaba.
Da gudu ta faɗa jikin Aysha, itama Aysha wurgar da jakarta tayi ta ruggume yar
uwarta.

Inna da Ummey kam ido suka zuba musu, suna masu jin daɗi irin soyayya da shaƙuwar
dake tsakanin yaran nasu.

Dariya sukayi baki ɗayansu, cikin jin daɗi inna tace.


"To yanzu dai lokacin salla yayi ku shigo kuyi salla tukun sai ayita murna dan yau
dai kam nasan kwanan zaune za'ayi".
Murmushi Shatu tayi tare da karasowa gabansu cikin ladabi ba biyayya tace.
"Inna ina wuni".
Fuska a sake tace.
"Lfy lau Alhamdulillah ya karatu".

"Alhamdulillah karatu dai mun samu ɗan hutu."

"Masha ALLAH yayi kyau".


cewar Ummey
hannun Ummeyn ta kamo tare da cewa.
"Ummey ina wuni".
Murmushi tayi tare da shafa kekyawar fuskarta tace.
"Lfy lau Shatu muje muyi salla ko?".
Kanta ta ɗan sosa tare da cewa.
"Ummey ni nayi sallana a mota".
Dariya Ummey tayi domin ta gano cewa Shatu na fashin salla,
Ita kuwa Junainah baki ta tura tare da cewa.
"To ba gashi ba, ba yanzu muka gama musuba ya Giɗi ba nace mishi nafi Addana son
salla, tunda ni kullum sai nayi ita kuma wata rana sai tace a a ita tayi a makka ko
kuma tace wai ai tayi kuma babu wanda zai ganta tanayin sallan".
Ummey ce ta.
Buge bakinta tare da cewa.
"To Aku uwar mgna maza wuce kiyi salla, babu wanda ke son jawabin ki".
Tura baki tayi kana ta wuce cikin ɗakin nasu, tana cewa.
"Ai dama nasan kunfi sonta".
Ita kuwa Ummey harara ta watsawa Shatu tare da cewa.
"Ke kuma kada dai ki rinƙa kiyaye bakin wannan magananniyar".
Murmushi tayi ta bita kana ta ɗauki buta ta shiga bayan gida dan gyara jikinta,
sannan ta dawo.

Tana shiga ta samu Junainah ta idar da sallan,


Gefenta ta zauna, tare da jawo jakarta, sweet ɗinta data seyo mata, ta kwaso ta
fitar mata.
Ai kuwa tuni fushi ya ƙare, tazo ta raɓa jikin yayartata.

Ummey kuwa da Inna saida sukayi sallan isha, kafin suka, fito tsakar gida dan tuni
hadarin nan ya watse sai iska mai sanyi daketa kaɗawa.

Bappa da su Ya Ladoma saida aka idar da sallan isha kafin suka dawo gida.

Gaba ɗayansu a tsakiyar gidan suka zauna bisa manyan taburmaii guda biyu mazan na
kan ɗaya matan na kan ɗaya.

Abinci sukeci mai rai da lfy, tuwon faran ɗanyar shinkafa, da miyar ɗanyar kuɓewa
data sha man shanu da tantakwashi, sai kifin banda sabi kifi na araha a wurinsu.

Sai kuma zazzafan kunun nono da yaji nono da zuma.

Sunaci suna ira ga hasken farin wata daya fito yayi ral ya haska ko ina na gidan.

Cikin jin daɗi, Giɗi yace.


"Shatu hutun mai tsawone ko gajere?".
Kunun nonon data kurɓa ta haɗiye kafin tace.
"Eh to Yaya Giɗi hutun sati uku ne muka samu".
Seyo ne ya amshi zancen da cewa.
"A hutun da ɗan yawa".
Shi kuwa Giɗi dariyar mugunta yayi tare da cewa.
"Ai kuwa naji daɗi wlh sai kinyi kiwo kema kiji hazar da muke ji".
Bappa ne ya amshi zancen da cewa.
"Giɗi mugunta ba kyaufa, Wato kai wuya kakeso tasha".
dariyar ƙeta ya kumayi tare da cewa.
"Ai naga duk anfi kashe mata kuɗi kuma muke wahalar kiwo, makarantar da takeyi
kawai duk shekara kusan million 1 takeci muko sai wuyar tsiya da muke ci".
Gaini ne yace.
"To ai kuma ita bata da shanu ko ɗaya kaikuma garke biyu kakeda naka na kanka haka
kuma muma".
Ladone ya ɗanyi murmushi bayan ya haɗiye lomar da yasa a baki yace.
"Ato gaya mishi kam".
Ummey ce ta ɗan kalli Shatu tare da cewa.
"Kici abinci ki dena shan ruwan kunu ba rike miki ciki zaiyiba".
Da sauri Junainah tace..
"A a Ummey ai Inna tana tasa an yanka zabbi zata gasa mana Adda karkici tuwo".
Dariya sukayi baki ɗayansu dan duk kowa yasan Junainah tsakaninta da.
Nama akwai ƙauna.

Haka dai sukaci gaba da hira da dariya,


Hatta makiyayan gidan nasu wanda ba yan gidan bane saida suka shigo akayi ta hira
da dariya dasu.
Suna cikin hirar ne yaro yayi sallama cewa Ba'ana yana kiran Aysha, cikin sauri
Aysha ta konta tare da lumshe idonta, ganin hakane yasa Ummey cewa yaron.
"Ayyah kaje kace mishi yayi hakuri AYSHA har tayi bacci, in ba matsala yaje sai
gobe, in kuma da matsala a tada ita".
To yaron yace ya juya ya tafi.
Fitarshi bada daɗewa ba ya dawo,
Yace,.
"Yace a barta tayi baccinta gobe da safe zaizo".
To sukace kana yaron ya fita ya tafi. Sukuwa sukaci gaba da hira.

Gashin zabbi mai kyau Inna tayi musu gashin da yaji haɗi, nan ta ware na maza ta
basu kana ta ware nata da Ummey sannan ta bawa Aysha da Junainah, nan fa sukaci
gaba da ci, suna hirarsu ta zumunci wanda ko yaushe haka suke duk daren kuma anan
Bappa ke karantar dasu.

Bayan duk sun fara miƙewa da dare ya fara nisa, a hankali Bappa yace.
"Aysha kinyi baccine?".
Cikin sauri ta miƙe zaune daga konciyar da tayi kanta na bisa cinyar Ummey, a
hankali tace.
"A a Bappa idona biyu".

Tashi zaune yayi tare da fuskantar ta, ganin haka yasa ta rarrafa a hankali ta iso
gabanshi, cikin kulawa yace.
"Ya karatun naki?".
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
"Alhamdulillah Bappa karatu na tafiya yadda ya kamata".
Kanshi ya jinjina tare da cewa.
"Baki da matsalar komai dai ko?".
Da sauri tace.
"Babu matsalar komai Bappa na".

"Masha ALLAH haka nake son ji, Allah ya miki al'barka dake da sauran ƴan uwanki
baki ɗaya. Allah ya miki zaɓi da miji na gari".
A hankali suka amsa da Amin Amin gaba ɗayansu.

Daga nan kuma yayi ta mata nasihar ta kama kanta,


Jin sanyi ya fara yawane yasa sukayi saida safe kowa ya nufi makoncinsa.

Yayinda a can cikin garima masu hira a dandali duk sun watse.

Al'walan konciya bacci sukayi kana suka shiga, ɗakin Ummey da yake mai girma da
faɗi an laileyeshi da siminti da leda carpet, kana ga jere da gadajenta biyu masu
kyau,
Ita da Junainah suna kan babban gadon ita kuwa Ummey tana kan ƙaramin gadon.
Hira sukaci gaba da yi irin hira ta tsakanin uwa da ƴarta, cikin sanyi tace.
"Aysha, kinji Hashimu ɗan Arɗo ya rasu ko?".
Da sauri cikin razana AYSHA ta tashi zaune tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Ummey banjiba yaushe ya rasu meya sameshi?".
Ta jero tambayoyin a tare kana ga hawaye na kwaranya cikin sanyi Ummey tace.
"Kwanan ya rasu, yankan rago akayi mishi sai tsintar gawanshi akayi a burtali ana
zaton Ɓachamawa ne suka kasheshi".
Cikin shessheƙan kuka tace.
"Allah sarki Ya Hashimu Allah ya jiƙanka da rahama yasa ka huta, Allah ya saka maka
duk wanda ya kasheka Allah ya toni asirinshi."
Sai kuma ta konta tana kuka sosai saida tayi kamar 3 minute tana kuka kafin tace.
"Yanzu shike nan Ummey duk wanda zai soni ƙarshensa yankan rago?".
Cikin yin ƙasa da murya Ummey tace.
"Ba dukaba in sha Allah akwai wanda zai soki ya kuma rayu dake bisa lfy".
A hankali tace.
"Ummey wa zai soni a irin yadda kullum ya Ba'ana yake kara zama masafi mugu, wa zai
tsira da tarkonshi?".
Da sauri Ummey tace.
"Wanda yake mai ƙare rayuwarsa a amɓaton Allah da kekyawar zuciya."
Kai kawai ta kife tana mai kukan rasuwar Yaya Hashimun ta, a haka dai sukayi ta
hira har bacci ya sacesu.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa.


Bayan anyi sallan ishane, Sheykh ya fito cikin shirinsa na tafiya, riga da wondon
yaɗin wagambarine a jikinsa sai bakar alkyebbarsa dayasa kana sai hiraminshi fari
da kuma bakin tarden dake saman kanshi.
Sai takalman sarautar da ya saka, suma farare kalar hiraminshi.
Jamil ne ke biye dashi a baya yana riƙe da ƴar madai-daiciyar jakar Hamman nasu,
kana hannunshi ɗaya na riƙe da jakar System ɗinshi, shi kuwa Sheykh woyoyinsh ya
zura a al'jihunshi.

Tare suka fito, a mashigar ƙofarshi nan sukayi kiciɓis da Jalal, da Jakadiyarsu,
cikin muryar da bata cika fara'aba Jalal yace.
"Please Hamma Jabeer, dan Allah karka daɗe".
Kafaɗanshi ya dafa tare da cewa.
"In sha Allah bazan daɗeba Jalaluddin, ka kula da kanka da Yah Jafar".
Kanshi ya gyaɗa alamar to, Jakadiya kuwa, ido ta zuma musu tana jin so da ƙaunar
yaran kamar itace ta haifesu a cikinta.
Cikin girmamawa Sheykh yace.
"Ummi bari inje in sallami Yaya Jafar".
To tace kana ta juya ta nufi sashin, Hajia Fatima, tsakar gidan Maigirma
Habibullah.

Su kuwa suna shiga a falo suka samu Yayan nasu da iyalanshi, a hankali Sheykh ya
ƙaraso gaban ɗan uwan nashi, cikin sanyi yace.
"Ya Jafar zan tafi Leddi julɓe Sitti ta nemi muje gidansu, can ƙasar saudia, Abba
ne da kanshi yace inje badon hakaba babu inda zanje in barka a haka, zanje ƙasa mai
tsarki tushen mahaifiyarmu da kakarmu da take jininsu, in sha Allah zan nemi
al'farman a buɗe min ka'aba zan shiga har ciki inyi maka addu'o'in samun lfy, kuma
bazan daɗe ba zan dawo kajiko Ya Jafar?".
Bai kulashiba kana kuma bai bar karatun da yakeyiba, sai dai hawaye daya fara
zubdawa a jere-a jere. Jamil kam juyawa yayi ya fita da jakar ɗan uwan nashi dan
yasan zaiyi kuka.

Ita kuwa Juwairiyya cikin sanyi tace.


"Babu komai Sheykh Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy in sha Allah zanyi ta kula
dashi yadda ya kamata".
Jalal kuwa tattauna laɓɓa shi kawai yake tamkar zai hudasu, tabbas sunada ciwo a
cikin zuƙatansu musamman Sheykh da yasan shike ɗaukan damuwarsu kab harda ta
mahaifiyarsu".

Shi kuwa Sheykh hannu yasa yana sharewa Yayan nashi hawayen, a hankali suka juyo
suka kalli ƙofar ɗakin Hajia Mama ce, ta shigo hadimanta na biye da ita a baya.
Gefen Juwairiyya ta zauna ta zubawa su Sheykh ido, lokacin ɗaya hawaye ya fara
kwaranyowa da idanunta, cikin rawan murya tace.
"Sheykh lokacin na tafiya, Maimartaba ya aika a kirawo ka a zatonsa kana sashina,
tashi kaje, Allah ya kiyaye hanya karka damu yayanku na ƙarƙashin kulawata
musamman".
A hankali ya miƙe ga mamakinsu sai gashi shima Jafar ya mike hannunshi yasa ya
kamo ƙanin nashi,
cikin rauni Sheykh yace,
"Hajia Mama kodai in tafi dashine, kingafa baya son in tafi in barshine".
Hannu tasa ta share hawayenta kana a hankali tace.
"Bazai yiwu ka tafi da shiba, karka damu Jabeer komai zai wuce".
Kai ya gyaɗa mata, sannan ya juya, ya nufi hanyar fita yana riƙe da hannun yayan
nashi, Jalal na biye dasu a baya,
Hajia Mama da Juwairiyya da yaranta na biye dasu.
Koda suka zo tsakiyar farfajiyar gidan cikin bada umarni Hajia Mama ta kalli Sheykh
tare da cewa.
"Jabeer kuje sashin Hajia Fatima ka sallamarta".
Ɗan jim yayi, a hankali ya kalleta, ita kuwa da sauri tace.
"Umarnine ba shawaraba".
Kanshi ya gyaɗa alamun to.

Daga nan suka shiga sashin nata, bayan Jakadiya tayi musu iso.

A folon forko suka Sameta, tana hakimce hadimanta na zagaye da ita.


Tana ganinsu ta tashi ta zauna, cikin sanyi tace.
"A a Sheykh da kanka".
Ɗan rusunawa yayi tare da cewa.
"Zanyi tafiya Hajia mamace tace inzo in sallameki".
Da sauri tace.
"Ayyah, to Allah ya kiyaye hanya ya kaika lfy ya dawo da kai lfy". Amin yace a
takaice kana ya kama hannun Ya Jafar ɗinshi suka fito.

Nan suka raka'a zuwa sashin Gimbiya Aminatu nan suka sameta a falon, sukayi sallama
da ita.
Daga nan ya wuce fada, Hajia Mama kuwa ta koma sashinta da hadimanta bayan ta mishi
addu'o'in insa lfy.

Juwairiyya kuwa parking lot ɗin su inda ta hango an jera motoci. Ta nufa inda Jamil
ke tsaye da alamun waya yakeyi da Malika sahibarsa sabuwar budurwar da yayi.

Shi kuwa Sheykh yana shiga fada ya samu Waziri ne kaɗai da Maimartaba da alamun
zaman jiransa sukeyi.
A gaban Maimartaba ya rusuna, tare dasa hannu ya tura hularshi ya maidashi baya,
Cikin kulawa Sarki Nuruddeen yasa hannu kan tsakiyar kanshi ya dafa tare da cewa.
"Allah ya kaika lfy, ya dawo da kai lfy, ya baka sa'an tafiya, ya kareka a duk inda
kake".
Amin Amin suka amsa baki dayansu, kana Waziri ma ya mishi addu'o'in sannan suka
miƙe gaba ɗayansu sukayi woje dan mishi rakiya,
Sarki Nuruddeen da bayinshi wazirinsa da bayinshi, shina Sheykh da bayinshi, sai ya
zama rakiyar ta samu taron mutane,
kana ga bayin Ya Jafar, nan suka shishshiga tsala-tsalan motoci a ƙalla motoci goma
sha biyar ne sukayi mishi rakiya zuwa Airport.

A wurin rabuwarsa da Ya Jafar ne yasa zuciyar kowa raunata domin Jafar kuka sosai
yayi tayi da kyar dai suka dawo gida bayan jirgin su Sheykh ya tashi zuwa birnin
Jalaluddin.

Cikin abinda bai gaza awa ɗaya ba sai gasu a birnin Jalaluddin.

Kafin jirginsu ya sauƙama a ƙalla motoci goma ne suka zo tarbansa, a ciki kuwa
harda mai Alfarma Sarkin Musulmai Jalaluddin.
Koda yaga jikan nasa mota ɗaya suka shiga,
suna isa fadar musulunci,
suka fito daga cikin motocin da sauri Sarki Jalaluddin ya zagayo ya kamo hannun
jikan nashi, suka nufi sashin Amaryarshi Gimbiya Kulsum, jikanshi Kabir na biye
dasu a baya, suna isa falonta gaba ɗaya ma'aikatanta suka fita ganin mai alfarma da
kanshi, shi kuwa Jalaluddin cikin ɗan ɗaga murya yake cewa.
"UmmuKulsum! UmmuKulsum!! Ga Jazlaan ya iso, gashi na kawo mikishi har ɗauki".
Wata kekyawar tsohuwar balarabiyace ta fito da sauri, cikin tsananin soyayyanshi ta
ruggumeshi,
shima ruggumeta yayi cikin harshen larabci Sheykh yace .
"Ana uhubbiki hubban axeeman ya Sitti".
Kanshi ta shafa cikin tsananin son jikan nata tace.
"Laisa li misluka abadan ya habibee".
Murmushi mai faɗi yayi tare da bin bayanta, kai tsaye dinning area ta nufa dashi
Kabir da Sarki Jalaluddin na biye dasu, da kallon sha'awa.
Kujera taja ta ajiyeshi, kana ta jawa Jalaluddin tasa kujerar nan kabirma ya zauna,
Suna zama sai ga wasu dattijan mata su uku sun shigo a jere a jere, suna zuwa duk
kanshi suke shafawa shi kuwa sai murmushi yayi tare da kallon Mai alfarma Sarki
Jalaluddin yace.
"Malam kace su dena shafa min kai haka na gaji".
Murmushi sukayi baki ɗayansu kana suka zauna, cikin kulawa babbar cikinsu tace.
"Kazo lfy, ya jikin Jafar?".
A hankali ya ɗan kalleta tare da cewa.
"To Alhamdulillah jiki da sauƙi zance".
Allah ya ƙara sauƙi cewar Jalaluddin Amin Amin suka amsa baki ɗayan su, ƙaramar
cikinsun ce ta ɗan kalleshi cikin tsokana tace.
"Ina mai gidanmu Sarki muminai".
Taɓe baki Sheykh yayi tare da cewa .
"Uhumm Jalal ne Sarkin Musulmai ko? Baki sanshi bane".
Dariya sukayi duka kana suk gaggaisa sannan suka fita gaba ɗayansu, ita kuwa Sitti
abinci tayi ta bashi har saida ya kwaɓe fuska tare da cewa.
"Na tuba ki barni haka na ƙoshi".
Kai ta gyaɗa kana suka dawo falo zata fara hira, yace shi dai ya gaji bacci yakeji
hakanne yasa, Jalaluddin da kanshi ya kaishi makwancinsa.

Asuba ta gari al'ummar Sokotawa

A nan Ɓadamaya kuma cikin Rugar Bani


Washe gari da hantsi, bayan duk sun karya, kowa makiyaya duk sun tafiya kiwo,
manoma kuma duk sun tafi noma, kana mata masu shiga tallan nono cikin gari sun
tafi, garin yayi tsit kamar yadda aka saba

Ba'ana kuwa da Shatu suna zaune a ginɗin bishiyar mangoro dake bakin zauren su, ita
tanata.
Ciki shi kuma yanata woje, cikin sakin fuska ya kalli Junainah dake gefensu yace.
"Junainah je cikin gida kice a baki ɗanyen kwai ki kawo mana in dafa mana".
Da mmki Shatu tace.
"Ka dafa mana kuma?". Kai ya gyaɗa mata, ita kuwa Junainah uwar kwaɗayi tuni ta
tafi cikin gida Inna na tambayarta me zatayima Bata kulataba, sai ɗan kwano data
ɗauko a konɗonsu kwan zabbi ta ɗebo a kalla sun kai goma, kana da gudu ta dawo
wurinsu.

Da sauri yasa hannunshin ya amshi robar, ita dai Shatu Ido ta zuba mishi taga ta
ina zai dafa kwan,
shi kuwa Ba'ana hannunshi yasa ya fara tona ɗan ma dai-dai cin rami, da mmki Shatu
tace.
"Ya Ba'ana me zakayi da tona rami kuma?".
Cikin murmushi yace.
"A ciki zan dafa mana kwan".
Junainah kam gabanshi tazo ta zauna, tana kallonshi har ya gama tona ramin.
Kana ya zuba kwayayen a ciki ya maida ƙasar ya binnesu.
Sannan ya juyo ya kalli Shatu yace.
"To musha hirarmu kafin kwan ya nuna".
Junainah ce tace.
"Ya Ba'ana ta yaya zai nuna kuma babu wuta?". Kamo hannunta yayi tare da cewa.
"Ke dai zauna ki jira ki gani ƙaƙara".
Kai ta gyaɗa tare da gyara zama, shi kuwa Ba'ana murmushi yake a baiyane a ranshi
kuma cewa yakeyi.
"Uhummm shi Bappa dan ina son yarsa bazai hanani yashe Garkensa ba, kuma da koyayen
gidanshi kawai zan iya karya kafin da yayiwa garkenshi".
A zahiri kuwa kallon Shatu a yayi tare da cewa.
"Zakiji girkina mai daɗi". Kai ta jinjina tare da cewa.
"Uhumm girki ko al'mara."
Kanshi kawai ya gyaɗa alamun zaki gani daga nan sukaci gaba da hira.

Bayan kamar 42 minutes ya fara tono wannan ramin daya tona a gabansu babu wuta ko
ɗigo ya binne ɗanyen koyaye, sai gashi ramin yana tururi tamkar an bude tukunyar
dake tafasa, da sauri Aysha ta waro idonta.
Junainah kuwa sai tsalle take,
shiko Ba'ana saida ya kwatso ƙoyayen kab kana ya sasu a robar da aka kawosu a ciki,
Ɗaya daga ciki yasa a gefen dutsen da yake zaune ya konkotsashi kaɗan kana ya
ɗagoshi, yatsunshi biyu yasa yafara ɓarewa.

Cikin mamaki Shatu ta zazzaro idanunta woje tare da cewa.


"Hehhhhh...!

Ga masu buƙatar biyan kudi littafin mutanen Niger ga number da zakuyiwa mgn
+22799460151 in kun biya ta wurinta ita zata turo min number ku in saku cikin
group.

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 7

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*Littafina na kuɗine, turo 1k domin karanta part 1 cikin mako biyu, ko ki turo 300
domin karanta part 1 a kwanaki talatin, da izinin ubangiji. Turosu ta asusuna na
Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank, Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo min shaidar
biyanki ta number da nake whatsapp dashi. 09097853276, in da hali bana son kati,
amman in babu dama turo katin ba matsala, domin wani baida damar turowa ta bank
ac.*

*Ayyah masuyi mun voice note Dan Allah ku rinƙa ɗaga murya, baku saniba ko inada
matsalar kunne bayan na idon. In kinga kinyi min mgn ban amsaba wata ƙl fahimceki
bane, ko kuma mgnarki bata da amsa a wurina, kana abubuwa suna min yawa, irin asha
hira a chart ɗin nan bazai yiwuba, kuyi haƙuri masoya, yawan maimata min slm ince
wslm ayi sama da sau goma yana sa in share mutun tsakani da Allah sabida kamar
bashi da abin faɗane so Please na tuba,🙏🏻 a ɓari kada kice ina muku wulaƙanci.*
Ido ta zazzaro tare da cewa.
"Hihhhhhhh, ya dahu?". Kanshi ya rausayar tare daci gaba da ɓare kwan saida ya
ɓaresh tas ya fito subul gwannin ban sha'awa, sai turiri yaketayi, Junainah ya
miƙa.
"Karɓi kici kiji mana, kwan ya nuna ne Ƙanwaliya".
Da sauri tasa hannu, zata amsa, cikin sanyi Aysha tace.
"Ke uwar kwaɗayi bazaki ciba".
Rau-rau tayi da idanu alamun zatayi kuka, shi kuwa Ba'ana fuskarshi ya haɗa tare da
kafeta da ido, da sauri tayi ƙasa da kanta, tana mai wasa da ƴan yatsun hannunta,
dubanshi ya maida kan Junainah tare da cewa.
"Kici abinki Junainah". Fuskarshi ya ƙara haɗawa jin Aysha ta kuma cewa.
"Dan Allah Ya Ba'ana kada taci".
Ba tare daya kalleta ba, tace.
"Kema zakici ai bare ita". Da sauri ta ɗago kanta tare da girgiza kan tace.
"A a ni kam ngd bazanci abinda ban san da me aka dafashi ba".
juyowa yayi ya kalli Junainah da tuni ta fara cin kwanta, tana lumshe ido baki cike
da kwan tace.
"Ya Ba'ana bari inje cikin gida in kawo mana yaji mai daɗi Addana bata cin kwai
saida yaji".
To yace mata, tuni ta juya tayi cikin gida.

Kallonshi ya maida kan Shatu cikin haɗe fuska yace.


"Mata kina tunanin zan cutar da kene?".
A hankali ta jujjuya mishi kai alamun a'a, gyara zamanshi, yayi tare da cewa.
"To baki yarda dani bane?".
A hankali ta buɗi bakinta tace.
"A'a ni dai tsoron abun naji, ka toni rami mai danshi da sanyin yashin damina, ka
binne ɗanyen kwai mai sanyi ka fito dashi da zafi a dafe ni kam ina tsoro ban san
da wutan me ka dafashiba".

Fuskarta-ta yayi da kyau kana, ya fara magana.


"Ki yarda dani Mata, bazan taɓa cutar dakeba a rayuwa, duk abinda zakiga inayi,
zanyine dan kare lfyarki da kuma baki kariyar. Jikin ki, kici kwannan, babu abinda
zai miki".
A hankali tace,
"Ni bana cin kwai dama, kuma ai shi kariya Allah ke hadashi ga dukkan bayinsa".
hannu yasa ya amshi robar dakekken yaji da Junainah ta miƙo mishi, wacce yanzu ta
dawo wurin.
Wani kwan ya kuma ɓare mata, ya miƙa mata, tanaci tana lumshe ido saida taci biyar,
sannan tace.
"Ya Ba'ana na ƙoshi". Shatu ya ɗan kalla tare da cewa.
"Saura biyar kuma nakine, in kin shiga gida kicishi, sannan kuma akwai wani haɗin
maganin da zan kawo miki kiyi amfani dashi. Ni yanzu zan tafi".
Kai ta gyaɗa mishi alamar to, kana kuma tace.
"Ina zakaje yanzu? Tunda naga lokacin tafiya kiwo dai ya wuce".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Zan shiga ƙauyen Bonon ne".
Da mmki a fuskarta tace.
"Ya Ba'ana me zakayi kuma a ƙauye Bonon garin masafa kafurai ƙabulun Ɓachama".
Ido ya zuba mata har saida taji tsoronshi a hankali yace.
"Kema watan watarana zakije, ki tuna da kyau Mamata ƙabilar ɓachama ce, ƴar garin
Bonon kinga kuwa dole inje can tunda kawuneina ƙannen Mama da yayunta da iyayenta
duk suna can".
Ya ƙarishe mgnar kamsr yaji zafin zancen ta,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Kayi haƙuri". Kai ya juya mata alamar babu damuwa.

Daga nan ya juya ya tafi, ita kuwa tacewa Junainah su shiga gida.
Suna shiga cikin gidan ta harari Junainah tare da kai mata bugu cikin faɗa tace.
"Hegiya kwaɗayayya maza ki zubar da sauran kwanan jakar yarinya ai sai ya ciyar
dake guba tunda kince ke kwaɗayayya ce".
Ihu Junainah ta kurma tare da cewa.
"Wayyoooooooo Inna kin ganta ko tana cin zalina". a guje tayi gaba, ita kuwa Shatu
tabi bayanta da sassarfa tana cewa.
"Wallahi sai kin zubda ƙoyayen nan".
A haka suka isa har gaban Ummey da inna da suketa tafasa nonon da aka tatsa a
sanyin safiyar yau, wanda a ƙalla ya kai jarka goms sha uku, so masu gidajen fura
da nono na cikin Shikan ɗin nema suke saya, dan matan gidan Bappa kab bai lamunce
da zuwansu tallan nono ba.

Inna ce tayi saurin kare Junainah dan saura ƙiris ta abka cikin tafasasshen nono da
yanzu aka sauƙeshi, cikin tsoro tace.
"Kai ya ilahi ku dai bazaku zauna lfy ba". Cikin nitsuwa Shatu ta zauna gefen Ummey
nan ta labarta musu abinda ya faru da yadda ya dafa kwan ta ƙara da cewa.
"Amman da yake Junainah uwar kwaɗayi ce, a take a gabanshi taci kwai biyar cas
tanaci tana lumshe ido".
Cikin tarin mamaki Inna da Ummey sukayi ta salati tare da tafa hannu, a tare
sukace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, oh wannan yaron anya kuwa mutun ne ba shaiɗan
ba?".
Cikin rau-rau da ido, Shatu tace.
"Ni ina jin tsoronshi, bana sonshi bazan aureshiba, mutumin da komai nashi na
tsafine Inna ki cewa Bappa ya rabani dashi mana".
Cikin alhini, Inna tace.
"Rashin sani yasa Bappanki dama ke kanki kukayi mishi al'ƙawarin shine mijinki duk
rintsi, gashi yanzu ya zame mana masifa.
Juyowa sukayi suka kalli Ummey da idonta ya ciki da hawaye a hankali tace.
"Dana sani wlh da ban bar haka ta faru ba".
Shiru sukayi cirko-cirko a wurin, saida suka jiyo ƙaurin nono na zuba cikin murhune
suka dawo haiyacinsu.
Kana suka juya suka ci gaba da aikin su.

A birnin Jalaluddin kuwa ƙarfe tara na safiyar ranar, dai-dai jirginsu Sitti da
jikanta Sheykh ya tashi zuwa ƙasa mai tsarki da sauran taro al'ummar Annabi masu
zuwa Umrah.

Soyayyar da Sitti keyiwa Sheykh soyayyace mai tarin yawa, wanda ko uwa iya son da
zatayiwa ɗanta kenan, tana ji dashi tamkar ranta, wata ƙil hakan baya rasa nasaba
da tsananin kamanni da yakeyi da mahaifinta wanda shine baida lfy yanzu kuma shine
tsohon Limamin Harami yanada zuriya mai tarin yawa yayansa na cikinsa zalla su
arba'in da bakwai.
Bar jikoki da ƙanne da yaran yan uwa, sai dai ya tsufa sosai tun shekaru ashirin
da suka gabata ya ɗaura babban ɗanshi wanda yake ƙanin Sitti ne uwa ɗaya uba ɗaya a
matsayin shi.
Zuwa yanzu tsotsai tsufa ya kama Sarki Abdulkarim, Hairan wanda yake da shekaru
ɗari da biyar a duniya, sai dai sufarsa suface mai tsabta tsuface da ka gani
kasan an rainin ƙuruciyarta da tsoron Allah da ibada. Shiyasa babu gigita ko fita
haiyaci, yana son diyarsa Sitti kakarsu Sheykh kenan so mai tarin yawa ko dan tayi
nesa da shine, wacce ita kuma tun tanada shekaru ashirin da uku, Sarkin Musulmai na
ƙasar Kautal na wancan ƙarnin yazo da babban ɗansa, Jalaluddin wanda a nan yaga
UmmuKulsum Sitti kenan, ya sota, kuma Allah cikin ikonsa suka dai-dai ta, haka yasa
kafin ya koma ma da amaryarshi ya koma dan sitti ta kafe ita dai tana son Bahaushen
ga, duk da tasan yanada mata biyu, tace ai a gidansuma bata tashi ta samu
mahaifiyarsu ita ɗaya ba.

Tuni ita kam Allah ya mata rasuwa mahaifiyar Sittin kenan, yanzu mahaifinta ne
kadai a raye, sai kuma ƙanninta da yake matsayin ɗaya daga cikin manyan limaman
harami a yanzu sai sauran zuriyarta da yayu da kannenta.
Kowa na ahlinsu yasan Sheykh domin Sitti tana yawan zuwa dashi tun yana ƙarami,
kana tana zuwa da sauran ma baki ɗaya, to shi Jabeer anan ƙasar saudia ya haɗa
digiri ɗinshi na forko dana biyu. Shiyasa ya zama duk zuriyar an sanshi farin sani,
ga kuma tarin kama da yakeyi da mutanen zuriyar wanda da zaran ka ganshi kasan
jininsu ne.

Tafiya mai tsowo sukeyi cikin sararin samaniya suna keta gajumare, a ƙalla tsawon
aha huɗu kenan suna tafiya.
Kafin suka sauƙa cikin babban Airport ɗin jidda, wanda yake tamkar zai fashe da
jirage, ko wacce ƙasa ta duniya tanada jirginta cikin wannan babban Airport ɗin,
tashin jirage da hawa da sauƙansu tamkar babu wani abun hawa a duniya sai jirgi.

Koda suka fito daga jirgin, wani jirgine na musamman suka shiga wanda yake daga
fadar Mai Alfarma masarautar garin. Wanda ya turo a tarɓi ƴar uwar abokinshi da
mahaifinsu keta begen gani.
A take suka shiga jirgin ya wuce dasu, asalin cikin garin makka, wanda pilot ɗin
kuma ɗane ga Umaymah ƙanwar Mamansu Sheykh wato shima jikan Sitti ne ɗan Umaymah
sai kuma Jannart wacce ta biyo Haroon Dan tarban kakar tasu wacce ita kuma ƴace ga
babban ɗan Sitti wato ƙanwar Juwairiyya ce kuma anan take karatu.

Suna sauƙa a Airport ɗin,


suka fito, a jere, yana gaba yana rike da hannun Sitti tana biye dashi a hankali
tana taka step ɗin Jannart kuwa tuni itace a gaba.
Haroon ne wanda yake biye dasu a baya yana kallon yadda kakar tasu ke taka step da
kuma yadda ɗan uwan nashi ke rike da hannun ta, murmushi yayi tare da jingina a
ƙofar bakin jirgin cikin harshen larabci yace.
"Ko dai zaka goyeta ne ka sauƙar da ita".
Sheykh bai kulashi ba, har saida suka sauƙo ya gyarawa Sitti tsayuwarta, kana ya
miƙawa Jannart hannun Sitti alamun ta rike musu ita. Cikin jin daɗi Jannart ta riko
hannunta tare da cewa.
"Ana Uhubbiki ya Sitti". Cikin jin daɗi da son jikokin nata tace.
"Ana". Sai kuma suka juyo suna kallon Sheykh dake tsaye cikin shiga ta al'farma
shigar salihan bayi, wata dandatsetsiyar al'kyabbace mai masifar kyau ruwan ƙasace
al'kyabbar sai surfani da aka sarrafa a jikinshi wanda yake da kalan gold, haka
takalmanshi da hiraminshi duk masu ratsin Golding color ne, cikin tsananin jin daɗi
Haroon ya fara sauƙowa daga step ɗin, yana kallon ɗan uwan nashi manda suke
sa'anni, ruggume juna sukayi, cikin jin daɗi Haroon yace.
"Marhabin da zuwa Al'Sheykh, ya gida?, ina ƙannena? Yaya jikin Ya Jafar? Ya Hajja
Mama da kowa da kowa."
Kwaɓe fuska ya ɗanyi tare da janye jikinshi daga na Haroon cikin sanyinshi yace.
"Duk in kana son ganinsu kaje Nigeria zaka gansu, kana nan kullum sai yawo a jirgi
kamar turuwa a daji, duk ƙasashen duniya ka gama zagayesu".
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
"To ai dama na sani bakinka ɗaya da Umaymah'nka, zan koma ne in sha Allah, zan koma
inyiwa ƙasarmu aiki, suma ai suna buƙata na".
Fuskarshi ya ɗan kauda tare da cewa.
"Da yafi kam". Juyowa sukayi jin Sitti na cewa.
"Kai Haroon ku taho mu tafi, ka tsareshi da surunka tun daga nan ko?".
murmushi Haroon yayi kana ya nufi inda take tare da cewa.
"Oyoyo My Sitti". Kai ta juya tare da cewa.
"Rabu dani ba kaga ɗan uwanka ka shareni ba".
Ruggumeta yayi ta baya tare da cewa.
"Na isa in share uwar gida ran gida a gidan Sarki Jalaluddin". Jannart ce tai
dariya tare da cewa.
"Sitti karki yadda da daɗin bakinshi".
Hannunshin yasa ya ɗan dungure kan Jannart tare da cewa.
"Kishi ko dan kinga gani ga uwar gida".
murmushi Jannart tayi tare da jan hannun Sitti sukayi gaba, shi kuwa Haroon baya ya
dawo ya saita da Sheykh suka fara tafiya a jere,
duk wanda yaga salo da tsarin tafiyar Sheykh zai gane cewa jini na sarauta na
gudana a jikinshi, zai kuma gane nitsuwa ta addinin musulunci da kamala da haiba na
hasken imanin ya game jiki da zuciyarshi.

A haka suka jera suna tafe, suna hira wacce ƙarfinta duk Haroon ke yinta.
Suna tafiya kaɗan.

Nan suka samu wasu irin zafafan tsala-tsalan motoci masu masifar kyau da tsada,
suna jere a ƙalla sun kai goma sha biyu, motocine masu azabar kyau da sabunta da
sheƙi da kyelli suna jere.
Kana ga kekkyawa fararen larabawa yan uwa da abokai
Da sauri suka rinka ɗan rusunawa suna, gaidasu Sitti da jikokinta, wani cikinsu ne
da yake jikin wata dan datsetsiyar mota ƙirar Mercedes Benz maybach Exelero wacce
kuɗinta zai kai kimanin $8 million dollars.
Motace mai masifar kyau da tsada, tana da inƙancin da ko bilet baya shigarta. Bisa
dukkan alamu kuma sabuwa ce dal.
Direban dake jingine da ita ne yayi maza ya budewa Sitti bayan ta, a hankali suka
ƙaraso gaban motar gaba ɗaya ma'akatan sunyi musu ƙawanya, cikin so da ƙaunar
jikokin nata, ta yiwa Sheykh nuni daya fara shiga, ba musu kuwa ya shiga, motar,
kana itama ta shiga sannan Haroon ya shiga, ya zamana sun sata a tsakiya,
Jannart kuma gaba ta shiga gefen drivern, suna gama shiga aka maida ƙofofin motar
aka rufe.
Kana duk sauran hadiman suka shishiga motocin.
Kana suka fara tafiya a jere-a jere, tafiya sukeyi cikin salama da nitsuwa da bin
doka da ƙa'idar tuƙi, kai tsaye suka wuce tushen ahlin nasu.

Wanda kafin su zoma, duk labarin zuwansu ya riski al'ummar family, kamar yadda aka
saba, haka aka shirya musu tarba ta musamman an gyara sashin na musamman wanda
nanne masaukin Sitti asali kuma sashin mahaifiyartace, anan cikin sashin kuma duk
ahlinta da zaizo daga ƙasar Kautal nanne masauƙinshi, kuma kullum hadimai da bayin
dake kula da wannan wurin suna nan suna tsabtace wurin. Suna isa fadar mai darar
Sheikh Aliyu da kanshi ya fito tarbar babbar yayarshi wacce take a madadin uwa a
gareshi a yanzu.

A wani falo da yafi dacewa da a kirashi al'jannar duniya, suka haɗu, a hankali
Sheykh Aliyu ya ɗaga hannunshi alamun dakatar da ko wanne hadimi, a tare suka
rusuna tare da komawa baya gaba ɗaya su.
Da sauri ya karaso gaban Sitti Ruggumeta yayi irin ruggumarsu ta jinin larabawa,
murmushi mai cike da jin daɗi ƙauna haɗida bege Sitti tayi tare dasa hannunta
tsakiyar kanshi tace.
"Masha Allah, ɗan uwana na sameku lfy?".
Saketa yayi tare da ruggume Sheykh yana murmushi tare da cewa.
"Alhamdulillah yar uwata, Barka da zuwa lfy".
Cikin kula da zaƙuwa tace.
"Yaya jikin Baba".
Murmushi ya kumayi still yana ruggume da Sheykh yana shafa bayanshi, yace.
"Alhamdulillah jikin baba da sauƙi kewarkice tafi damunshi".
Sai kuma ya kalli Sheykh bayan ya sakeshi yace.
"Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero, barka da zuwa Doctor, ya gida ina
Jafar da ƙannenka".
Cikin son dottijon Sheykh ya ɗanyi wani ɗan guntun murmushi wanda shima sai yayi
tsawon lokaci bai yishiba, cikin sassanyan murya yace.
"Suna lfy, sun gaidaka".
Haroon ya tura baki tare da cewa.
"Wato mu ko ƴar ruggumar ma ta zumunci baza'ayi manaba, dan mu mun dade, nima zamu
koma ƙasarmu mu rinƙa kawo muku ziyara jifa-jifa dan naga baƙi farinjini garesu a
ahlinmu".
Dariya sukayi baki ɗayansu,. Yayinda duk mgnar da sukeyi da harshen larabci sukeyi.

Wani faffaɗan corridor mai girma suka ratsa, wanda suka riski wani babbanshi na
musamman, inda gaba ɗaya yayan family suke nan zaune dan mahaifin nasu a
tsakiyarsu.
Wanda yake tsakiyar gatan duniya, farin dattijone wanda tsabar tsufa har ya juye ya
koma tamkar ƙaramin yaro, ya ƙanƙance, yana hango Sitti, ya rinƙa sakin murmushi
tare da miƙa mata hannunshi alamun tazo.
Da sauri ta nufi inda yake su Sheykh na biye da ita a baya, yayinda duk sauran
mutanen ketayi musu barka da zuwa.
A gaban tsohon ta rusuna, tare da sunkuyowa, hannunshi ya saka bisa kanta yana jero
mata addu'o'in da sanya mata al'barka, ita kam sitti da sauran ƙannenenta wanda a
ƙalla sun kai arba'in sai Amin Amin suke amsawa,
Koda ya gama da Sitti jawo Sheykh yayi ya manna kanshi da cinyarshi,
Shikuwa Sheykh. Motsoshi yayi da kyau Cikin wani irin mashahurin daɗin da sai in
yana gaban tsohon nan yakejin daɗi yasa hannunshi biyu ya kamo hannun dattijon ya
ɗaura tsakiyar kanshi kana ya ƙara manna kanshi da cinyar tsohon tasbihi yakeyiwa
Allah mai rayawa mai kashewa.
Ya sani shi kanshi da macece shi da yanzu yanada ya budurwa amman gashi wai a gaban
kakan mamanshi, ga kuma kakar tashi da sukewa kallon tsohuwa itama gata gaban
mahaifinta wannan abu shine abu ɗaya da yake sashi kuka muddin yana gaban tsohonda
kullum in yazo irin gaisuwar da sukeyi kenan.
Shi kuwa Sarki Abdulkareem cikin rawan jiki irin na tsoffi yake shafa kan Sheykh
tare da kallon taron ahlin naahi cikin muryarsa da bata fita sosai yasa suke
sanƙala mishi na'urar ɗaga sauti a jikin alkyabbarsa, shiru sukayi gaba ɗayansu
suka dakata da ruggume-ruggumen da sukewa Sitti,
Cikin rawan muryan da alamu tsohon kuka yakeyi a hankali yace.
"Ku bashi dukkan kulawarku, domin yana cikin Magauta, yanada tarin ƙunci da ƙuna a
rayuwarshi, matsalolin rayuwar duniya sun mishi ƙawanya, saukinshi ɗaya Allah yayi
mushi dafa'i da hasken imani da riƙo da ibada, damuwar tana daƙushe duk wani farin
cikin rayuwarsa rashin fara'a ba izza bace damuwace, yana cike da al'hinin kula da
ahlinshi,".
Shiru ya ɗanyi tare da zubawa gaba ɗaya ahlin nashi idanu, sawon wasu daƙiƙu shiru
falon babu sautin komai sai sassanyan sautin shessheƙan kuka da Sheykh a hankali,
sai kuma sautin ƙaran A/C.

A hankali Dottijon yaci gaba da cewa.


"Kanshi akwai wani abu mai girma a tare dashi, yanada manyan baiwowi a jikinshi,
sai dai kuma akwai tarin ƙalubale, zai ɗauki nauyi da yawa a kanshi".
Ya ƙarishe mgnar yana shafa tattausan suman Sheykh.
Shiru sukayi baki ɗayansu Sitti kuwa Hannu tasa bisa haɓar Sheykh tana share masa
hawaye, Haroon kuwa Umaymah ya kira tun shigarsu tana jin duk kalaman kakan nasu
haka yasa taketa kuka.

Sosai yayi jawabai masu ratsa zuciya kafin daga bisani, ma'aikatan gidan suka shigo
suka rinƙa gabatar musu da abubuwan ci da sha a nan suka zauna ana ɗan ciye-ciye da
taɓa hira,
Ganin lokacin salla yayine kab kowa ya miƙe dan yin al'wala su tafi harami.

Kamar koda yaushe Sashin Sitti suka wuce wanda yake a gyare, Jannart da Sitti side
ɗaya suka shiga.
Haroon da Sheykh kuwa Side ɗaya suka shiga.
Ruwa suka ɗan watsa sannan duk sukayi al'wala suka fito suka kimtsa cikin manyan
alkyebbars masu taushi da masifar kyau wanda sabbine dal akazo aka shirya musu a
drower'n. Koda suka gama a tare duk mazan suku tafi Harami.
Haka dai rayuwa tai ta gudana a cikin kwanakin nan.

Randa suka cika kwana uku da zuwa a ranar ne Sitti ta samu mahaifinta da ƙaninta a
kan batun tana son kafin tabar ƙasar nan ayiwa Sheykh aure, ta kuma bada zaɓin
yaran yan uwa wanda suke larabawa, nan take kuma Sheykh Aliyu da kanshi yace ya
bawa Sheykh Jabeer auren diyarsa Jazrah...

Rugar Bani Ɓadamaya state.

Yau kusan kwanan Shatu biyar da dawowa hutu, kuma kullum da salon da Ba'ana yake
zuwar mata dashi, wannan abu shine abinda yafi tada hankalin Malam Liman Bappa
kenan, wanda yana yawan tattauna matsalar da Ardo Bani kamar yadda yanzuma haka
suke tare su daddatawa biyar,
Cikin kamala da harshen fillanci Arɗo Bani yayi gyaran murya tare da cewa.
"Koda Hashimu ya rasu, in sha Allahu bazamu zuba ido a aurawa Shatu wannan fasiƙi
fajiri mushirkin yaron nanba, Salmanu zai fito zai nemi aurenta,in Allah ya yarda
kuma zamu cire batun shaɗi tunda, mun sani cewa, bulalin da Ba'ana yake amfanin
dasu wurin shaɗi da manema auren Shatu bulalin sihirine wanda duk wanda ya daka
dasu ƙarshe mutuwa yakeyi ko ya haukace, to a karon nan zamuce babu shaɗi domin ai
shi shaɗi al'adace ba shariya ba.
Zamu kuma bawa salmanu dakarun tsaro masu bibiyar lamuranshi a sirri dan gudun kada
ayi mishi yankan rago kamar yadda akayiwa Hashimu duk da dai bamu da sanin shin
Ba'ana ne koko kafuran Ɓachamawa ne".
Da sauri ɗaya daga cikin dottawan yace.
"Yo ai shima Ba'ana kusan kafurin ne, tunda baya salla kuma matsafine".
Bappa ne ya nisa tare da jan dogon numfashi mai tsawo sannan yace.
"Bazai yardaba duk yadda za'ayi sai yace dole ayi bulalin Shaɗi, kana kuma muddin
akace baza'ayi Shaɗi ba to haƙƙun zai kashe Salmanu kisan da bazamu samu huja ko
madafaba".
Shiru sukayi baki ɗayansu cikin kamala da nitsuwa da rauni Bappa yace.
"Kaɗan kenan daga illar riƙo da Al'adar daba addini ne ya tanadar dashi ba".
Ardonne yayi gyaran murya cikin sanyi yace.
"Ya Allah ka kawo mana mafita kan wannan bawa naka Ba'ana daya zame mana masifa a
rayuwarmu".
Ɗaya daga cikinsu wanda tunda suka zauna baiyi mgna bane ya gyara zama tare da
cewa.
"Gashi shi kamar ibilis yake, ya rigada ya gama dafa kanshi wuƙa ko bindiga basa
shigarsa bare banzan abu shi bulalan Shaɗi shiyasa kullum shine da nasara a
rayuwarsa".
Shiru sukayi suna kallon ɗaya daga cikinsu wanda ya kasance malamin da suke sawa
yana bincikar musu jikin Ba'ana wato Chubaɗo yana cewa.
"Akwai bulalin da zasu shigeshi su kuma karya duk wasu manyan sirrukan dake
jikinshi, ta kuma sashi yayi kuka,cur-cur da hawayenshi, to amman bazasu taɓa
samuwaba bamu da hanya ko damar samunsu, domin bulaline da a ƙalla sun shekara ɗari
biyu a murde kuma suna cikin tsumin ma'jiya mai cikar tarihi da girma bulaline da
tsawon shekara ɗari da ashirin da biyar kenan rabon da ayi amfani dasu, kuma an
killacesu, killacewa mai tsauri, shi kanshi Ba'ana yana neman bulalin ruwa a jillo
domin babban dodon tsafin Bonon ya sanar mishi saida bulalin zai samu nasarar da
yake so, to amman bai san bulalin ina bane baisan a ina sukeba bai kuma san ta ina
yake nemansuba an dai bashi yaƙini a hannun Fulani yake wannan dalilin ne yasa ya
baza jakadunshi duk ƙasar da takeda Fulani."
Da sauri Suka zuba mushi idanu baki ɗayansu cikin zaƙuwa sukace.
"To Chuɓaɗo kai kasan inda bulalin suke e?".
Kanshi ya jinjina musu tare dayin ƙasa da murya yace.
"Eh na sani".
Cikin sauri sukace.
"Bulalin inane a wacce ƙasar suke?".
Cikin tsoro yace.
"Bazan fadaba bazaiyiwu in faɗaba".
Magiya suka fara yi mishi amman fir yaƙi yace mutanen jikinshi sun hanashi faɗa,
dole haka suka haƙura suka tashi daga taron ganin dare ya raba tsakiya kowa ya koma
gidanshi.

Washe gari da Asuban fari Rasuwar Chubaɗo ya zagaya garin Rugar Bani wanda akayi
hira dashi lfy lau kawai washe gari aka riski ya rasu da alamun kuma ɗaure mishi
wuya akayi ya rasu har lahira.
Wannan rasuwa ya jijjiga zuƙatan dottawan nan huɗu da suka rage Arɗo Yabani da
Bappa, da kuma Alhaji Ja'eh da kuma Malam Umaru.
Sun shiga jimami mai yawa.
A haka dai akayi mishi sutura aka binneshi akayi zaman makoki na tsawon kwana uku,
randa akayi sadan uku duk hankali mutane huɗun nan ya ɗan konta ganin ba'a sake
kashe wani ba a cikinsu.

Yau tun da yamma Ba'ana ya matsa aka kira mishi Shatu wacce dolece tasa taje, inda
yake har rugar shanunsu bata damuba sanin bai taɓa koda yunƙurin cewa zai taɓa koda
ƴar yatsartace,
Cikin sanyin jiki ta sallami aminiyarta Bintu ƴar gidan malam Umaru, sannan ta tafi
bakin rugagen.

Zaune ta sameshi cikin ƴar bukkarshi da yayi a cikin tsakiyar turken garken nasu,
A hankali ta ƙaraso wurin ta sunkuya zata zauna ne a saman farin yashin dake wurin
yayi maza yace.
"Mata a ƙasa kuma? A a gskiya kada ki zauna a ƙasa.
Ga buzuna zauna a kai".
Kanta kawai ta jinjina shi kuwa shimfiɗa mata buzun yayi, a hankali ta zauna tana
fuskantar cikin ƴar bukkar da yake zaune a cikinta ɗin.
Shima gyara zama yayi tare da fuskantarta,
Kwaryar dake gabanshi ta zubawa ido, shi kuwa. Cikin yin murmushi ya sa hannunshi
yana gauraye magungunan dake ciki tare da cewa.
"Matar dafaki nakeso inyi, irin dafar da muddin mutun ya tuna zai miki sihiri,
misali ya miƙa hannu zai amshi mgnanin da zai samiki to zai kuturce in kuma baki ya
buɗe zaiyi mgna kan a miki sihiri to zai kuramce".
Cikin sanyi ta kwaɓe fuska tare da cewa.
"To ni kuma wa zaimin sihiri a duniya wayama damu dani?".
Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace.
"In an nemi mijinki ba'a sameshiba dole kanki za'a dawo shiyasa nake shiryaki
sabida kar Ni in an jefeni bai sameniba ya sauƙa kanki".
Ya ƙarishe mgnar da miƙo mata ɗan ƙaramin korya yace.
"Ingo ki fara shan wannan".
Kai ta gyaɗa ganin madarar shanuce da aka tatsa da ɗuminta.
Cikin takaicin halinsa tace.
"Me wannan kuma?". dariya yayi tare da cewa.
"Baki da yarda ki yarda dani wata rana zaki tuna nayi miki gata, wlh bazan taɓa
cutar da keba mata, kisha madarace da zuma nasan kinaso".
Cikin sanyi tace.
"Sai dai in na koma gida zansha".
Murmushi yayi tare da zuba mata ido kana a hankali yace.
"Fulaku ko? Nasanku fulanin da kunya wato irin bazakici abu a gabana ba, to ai
kafin ki koma gida zaiyi sanyi, bari in tafi can bayan bishiya in barki ke ɗaya
kisha abunki da ɗuminshi".
Ido kawai ta zuba mishi domin tabbas badon halin banza da Ya Ba'ana yake dashiba ya
cancanci ta soshi tabbas tasan ko ba yayi mata alherin da bazata taɓa mancewa ba a
rayuwarta.
Ko komai nashi na duniya mara kyau ne to soyayyarta kekkyawace a zuciyarshi ya
sota tun tana yar mitsitsiyarta kuma bai taɓa yunƙurin cutar da itaba ya kuma yi
mata halacci.
Murmushi yayi tare da cewa.
"Mata nayi miki kyau ne?".
Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh, cikin jin daɗi ya juya ya tafi, can nesa ya ɓuya,
ita kuwa a hankali ta fara shan madarar nonon da yaji zuma mai daɗi, kasan cewar
nonon ɗan kaɗanne a take ta shanye.
Saida ta goge bakinta tace mishi.
"Na shanye kazo". Da sauri ya fito ya dawo gareta cikin bukkar ya koma ya zauna
wani nonon ya ɗibo ya miƙa mata amsa tayi cikin sanyi yace.
"Me kika gani a ciki?".
Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.
"Nono fari ƙal mana".
Amsar ƙoryar yayi ya koma cikin bukkar dashi, jin kaɗan ya kuma fitowa ya miƙa mata
tare da cewa.
"Me kika gani?". Tura baki tayi tace.
"Farin nono mana". Kanshi ya jinjina tare da cewa.
"Da kyau, yanzu kiyi kamar zakisha ki gani".
Ido ta zuba mishi tare da cewa.
"Sha kuma?".
Kai ya jijina mata kana yace.
"Eh amman ba shan zakiyiba kiyi dai kamar zaki kaishi bakinki da niyar sha zakiga
wani abu".
Jim kaɗan tayi jin yana ce mata sha mana, yasa ta ɗan ɗago kwaryar ta nufi bakinda
kamar zata sha.

Wani irin wawan zabura tayi jiki na tsuma da karkarwa cikin tsananin firgita da
tarin tsoro ta sake kwaryar....!

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 8

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

Kada dai ku mance Free page ne, yana kuma gab da karewa.

*Ga mai buƙatar saya ga number ta, 09097853276 turo ɗari uku ko dubunki ɗaya kacal
domin samun damar karantawa cikin salama, Ga Ac ɗina 0005388578 Jaiz bank Aisha
Aliyu Garkuwa, in kin biya sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276
in ba halin turawa ta ac bisa dole turo katin mtn.*
Ta saki kwaryar, a sorace, da sauri yasa tafin hannunshi, biyu ya tare kwaryar.
Cikin tsoro jiki na rawa ta zazzaro idanunta woje kana murya a hargitse tace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Ya Ba'ana mekabani? Me ka shayar dani? Na shiga
uku me kasa nasha?".
Gaba ɗaya ta gigice tana rawan jiki da murya, ga hawaye kuma tuni suke shatata.
Ganin yadda ta firgitane ya sashi matsowa gabanta cikin ɗaga murya yace.
"Ba komai ba abinda na shayar dake Mata, wallahi Allah ki yarda dani wancan da
kikasha babu komai a ciki".
Da sauri taja da baya tare da cewa.
"Ban yardaba me ka shayar dani?".
Sai kuma ta fara kakarin amai da ƙarfi, ganin kamar aman bazai zo bane yasa ta tura
yatsunta biyu a baki, amman ina aman yaƙi zuwa sam.
Kawai sai tasa mishi kuka.
Cikin tashin hankali yace.
"Kiyi haƙuri Mata wlhi bazan taɓa shayar dake wani abu na guba, ko na ƙiba, duk
abinda nasan bazaki shashi da sanenki ba bazan taɓa bakishi a ɓoyeba.
Ki yarda dani wlh ban shayar dake komaiba".
Ina taƙi ta saurareshi sabida tayi matuƙar firgita da tsananin razana da ganin
abinda ke cikin kwaryar, cikin sauri yasha gabanta tare da cewa.
"Ki gani mana ki duba babu komai a ciki fa madarar shanunce".
Tsayuwa tayi tare da zubawa cikin kwaryar ido tas farin nonone kamar ko wanne nono
da bashi da gamin komai".
Hannutasa ta mutstsuke idanunta tare da kuma sake kallon, cikin tuhuma ta maida
idanunta kanshi tana mishi kallo mai cike da tuhuma.
A hankali ya sunkuya ya ajiye akwaryar kana ya taso ya fuskanceta da kyau fuska ya
haɗe tare da cewa.
"Sam bakya min adalci Mata, na lura dake, wani mugun zato da zargina kikeyi.
A zatonki wai zan iya cutar da kene? Shin kin mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake
sonki ne? Da inada mummunar niya a kanki da na cutar dake tun kina ƙarama.
Kullum idanunki na nuna min baki yarda dani ba. Me kike nufi?
ko dai wani kikeso ba niba?".
Ya ƙarshe tambayar da taune bakinshi kana ya tsareta da idanunshi, da sauri ta
sunkuyar da kanta tare da cewa.
"A a ni kam babu wanda nakeso."
Kanshi ya ɗan rausayar kana ya dawo ya zauna a bakin bukkar tashi, cikin kakkausar
murya yace.
"Dawo ki zauna".
A hankali ta dawo gefen gaban bukkar ta zauna,
shi kuwa wani ɗan randar ƙasan dake gefenshi ya buɗe, cikin haɗe fuska ya ɗan
kalleta tare da cewa.
"To zakiyi sabon Saurayi. Salmanun Arɗo Yabani, zai fara nemanki, kamar yadda
munafukan tsoffin rugar nan suke tsarawa, dan ana son rabani dake".
Da sauri taketa jujjuya kai tare da cewa.
"A a Wallahi ni Yaya Salmanu, ba sona yakeba, ka sani tun ina ƙarama duk abinda ya
shafi karatuna shike koya min har dai yasa aka sani.
Makaranta kai kuma baka hanaba".
Cikin haɗe fuska yace.
"Ehh ai nasan ke baki san yana sonkiba, amman na lura shi yana sonki, kuma zanci
ubanshi da bulalin shaɗi bashi babu sake kallon duk wani abu da nakeso".
Cikin tarin tsoron kada a cutar da Yaya Salmanun tace.
"Wallahi ƙarya ake mishi, baice yana sona ba, shi yama tsaneni ne yanzu, dan Allah
Ya Ba'ana kada ka yarda da ƙaryar mutane".
Kai ya rausayar tare da cewa.
"Uhum kinga nan cikin ranɗar nan, to bulaline wanda nake shaɗi dasu, yanzu tsawon
shekaru biyu kenan da aka hana shaɗi basu samu wanda suka dakaba, na tsumasu da
tarin tsumi mai zafi, wanda muddin na zana jikin mutun dashi sai ya fashe,
Kuma gasu a ƙalla sun kai tamanin a cikin randar nan kuma a ƙa'ida da guda goma sha
bibbiyu kawai zakayi shaɗi to kinga kenan zan iya shadi da mutun sama da shida dasu
basu ƙareba".
Kanta taketa jujjuya mishi tare da cewa.
"Ya Ba'ana kada ka yarda da sharrin mutane kasanfa Yaya Salmanu shike karantar
dani, tun ina ƙarama kuma ko yanzu dana girma tunda shi ya rigada ya gama digiri
ɗinshi shike fahimtar dani duk abinda ya shige min duhu, kuma tunda nazo hutun
nanma ban haɗu dashiba".
A hankali yace.
"Eh ai yau kam zaki haɗu dashi".
Yunƙura tayi ta tashi tare da cewa.
"Uhumm, shike nan ni bari in tafi gida an fara kiran salla."
Da sauri ya miƙe ya fito yabi bayanta tare da cemata.
"To Mata jirani inzo in rakaki Mana".
To kawai tace mishi, a haka suka jero suna tafiya yana gaya mata irin tsumin da
yayiwa bulalin nashi.

Suna isa dai-dai garken su Shatu, ta ɗan tsaya hango yayunta sun dawo daga kiwo,
cikin jin daɗi ta ɗan juyo ta kalleshi tare da cewa.
"Bari inje wurinsu Ya Giɗi, in tayasu ɗaure shanun".
Murmushi yayi kana yace.
"To Mata ki kulan min da kanki kada shanu ya taɓa min ke, dan akan ɗan mai shanun
zan rama miki ba kan shanu ba".
To tace tare da juyawa ta nufi cikin tsakiyar taron dabobbi su da aƙalla zasu kai
guda dubu da yan ɗaruruwa tsakanin shanu, tumaki, awaki, rakuma.
Da sassarfa take kutsa tsakiyar dabobbin tana cewa.
"Yaya sannunku da dawowa".
Da sauri Giɗi da Seyo suka juyo murmushi sukayi tare da cewa.
"Yauwa ƴar ƙanwarmu, daga ina kike?".
Da ido ta nuna musu Ba'ana dake tsaye can gefe ya zubawa dabbobin nasu idanu tamkar
mai ƙidanya su.

Gaini ne da Lado suka zuba mishi ido domin gaba ɗaya ya shagala da kallon da
yakeyi, har wani ƙan-ƙance idanu yakeyi.
Sam bayaji kiran da Babanshi Bukar ke auna mishi.
Har saida Giɗi yace.
"Heyy Ya ba'ana Ubanka na kiranka".
Ya ƙirishe mgnar da bagwariyar hausarsa.
Shi kuwa Ba'ana da sauri ya juya ya nufi wurin babanshin da yanzu ya dawo kiwo.

Cikin sakalci da gajiya Giɗi ya kalli yayunshi mazan tare da tura baki gaba yace.
"Wayyoooooooo Allah bayana zai karye, Ni dai na gaji bazan iya sunkuyon ɗaure shanu
ba, ga Shatu zata tayaku".
Sai ya kuma kalli yadda duk suka sunkuya sunata ɗaure dabobbin suna ɗan dariyar
yadda itama Shatu ta dage tana tayasu.
Junainah ce wace dama duk lokacin dawowarsu zata kawo musu sassanyan kindirmo susha
tun a nan kafin su koma gida.
Da saurinta take ratso cikin shanayen tana cewa.
"Ya Giɗi tareni, na gaji ga damunku".
Da sauri ya nufi inda take kwaryar ya amsa kana suka dawo gaban bukkokin da nanne
ma kwancin masu gadin dabobbin suke.

Zama sukayi ludeyayen dumar dake kan fefeyin daya rufe kwaryar ya ɗauke kana ya
buɗe kwaryar, ludeyi ɗaya ya sa musu a ciki.
Aysha dake kusa da sune ta zauna tare da cewa.
"Ya Giɗi kama ka bani". Kai ya gyaɗa mata kana ya cika ludeyin yasha sannan itama
ta ɗebo rabin ludeyin tasha, kana ta bawa Junainah itama ta kamfato ta cika ludeyin
ko rabinshi bata zuƙaba.
Ta miƙawa Ya Seyo dake tsaye gefensu, da murmushi a fuskarshi ya amsa ya sha,
sauran nata,
Shatu ce ta gyara zamanta ta matso kusa da ɗan uwanta tsokonta Giɗi abokin
tsamarta, gyara zamanta tayi kana tace.
"Ya Seyo zauna ga fili."
To yace kana ya zauna suka fara sha,
Lado ne ya kallesu cikin gajiya yace.
"To wai mu aka kawowa ko kune?".
Shiru babu mai magana sai kamun ludeyin da sukeyi,
Gaini ne ya matso gefe shima ya zauna kusa da Junainah yasa hannu ya ɗauki wani
ludeyin, nan suka zauna suna sha, ganin hakane, Ya Lado yace.
"To ni naci girma".
Da sauri Shatu ta mike wurinda ta tashi ta nuna mishi tare da cewa.
"A a ya Lado zauna kusha ni na ƙoshi". Murmushi Bappa dake gefensu yayi, wanda
yanzu ya iso da jarkan ruwa a hannunshi,
Cikin kallon so da tausayin yaran nashi yakeyi,
Cikin kula yace.
"Sannunku- sannunku da rana, Allah yayi muku al'barka".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu,
Sai kuma ya kalli Aysha da Junainah yace.
"Ayshatu maza kama hannun Junainah ku koma gida, kinji an fara kiran salla".

To tace tare da kamo hannun ƙanwar tata suka nufi gida.

Su kuwa Bappa da yaranshi da makiyayanshi anan sukayi al'wala, kana suka juya suka
nufi cikin Rugar tasu dan zuwa masallaci.
Yayinda ko wanne garke an bar mutun ɗaya sabida tsaro...

Bayan sallan isha sunci abinci sun ɗan taɓa hira, kaɗan kana Bappa ya tarasu yana
karantar dasu kamar yadda ya saba duk dare, da kuma safiya kafin a tafi kiwo
shiyasa sam ahlin wannan Rugar Bani ba jahilai bane.

Suna zaune, yaro yayi sallama, yace.


"Wai ana kiran Shatu a woje".
Ummey ce ta ɗan juyo ta kalli yaron tare da cewa.
"Wake kiranta?".
"Wai yace ince mata inji Ya Salmanu ne".
Yaron ya faɗi.
Da sauri Ummey tace.
"A a Salmanu ne ya zobe? To maza kace ya iso mana ya zai tsaya a waje kamar baƙo".
To yaron yace kana ya juya ya fita.
Jim kaɗan sai gashi ya dawo gefen Ummey ya rusuna tare da cewa.
"Yace wai ince mata, ta fito woje".
"Da mamaki Ummey tace to gata nan zuwa".
Sai kuma Inna ta ɗan kalli Shatu tace.
"Tashi kije ai mun gama aikin ma".
Ita kuwa Aysha dake zaune gaban Inna suna gasa tattabarun da aka yanka tunda yamma,
kwano ta ɗauko a konɗonsu kana tasa gasassun tattabarun guda biyu.
Tasa yaji a gefe, ta rufe, kana ta gyara wuyan hijabinta sannan ta miƙowa Junainah
kwanon.
A hankali ta ratsa gefen su Ya Giɗi ta wuce.

Ummey kuwa da ido ta rakasu tana fatan Allah yasa fata da shirin Bappa da Arɗo
Yabani ya tabbata.

Suna fita suka sameshi zaune bisa dakalin ƙofar gidan nasu.
Da sauri Junainah ta isa gareshi tare da cewa.
"Oyoyo yaya Salmanu".
Ajiye kwanon tayi a gefenshi.
Da sauri yasa hannunshin suka tafa da hannunta data miƙa mishi, cikin sakin fuska
da nitsuwa yace.
"I miss you ƙanwali".
Dariya mai ɗan sauti tayi tare da cewa.
"Miss you too my dear".
Dariya mai sauti sukayi a tare cikin jin daɗi wanda aka kira da Salmanu ya lakace
hancin Junainah tare da cewa.
"Alhamdulillah alama ta nuna ƙanwaliya tana zuwa makaranta babu wasa".
Cikin jin daɗi tace.
"Sosai ma ya Salmanu yanzu ajiyana huɗu fa, yanzuma dan hutu mukeyi, kuma gashi ko
a gidama Ina karatu".
Jinjina mata yayi da hannunshi kana, ya jawo kwanan data ajiye tare da cewa.
"Ƙanwaliya me kika kawo mim ne?".
Cikin murmushi tace.
"Gasheshen naman tattabarune Ya Salmanu barima in koma ciki inci rabona inci na
Addana".
Kafin ya ankarama tuni ta juya da sauri tayi cikin gida.

Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da kallon Aysha dake jingini da bakin kofar zauren,
Cikin sanyi yace.
"Kamar bakiyi farin ciki da zuwana ba? Ko dai in komane?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu nadai ga kamar kafi farin cikin ganin Junainah ne akai na".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Kin rama kena".
Murmushi sukayi dukansu, cikin sanyi yace.
"Ga wuri kizo ki zauna mana".
A hankali tace,
"A a Ya Salmanu mu shiga cikin gida mana".

"Kina tsoron kada saurayinki yazo ya ganmune?".


Salmanu ya faɗa a hankali.
Da sauri tace.
"Eh".
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
"Babu abinda zai faru sai al'khairi zoki zauna, ki gayamin me kike tsoron?".

A hankali ta zauna gefenshi ɗan nesa dashi.


Shi kuwa juyowa yayi ya fuskanceta a hankali yace.
"Gaya min me kike tsoro?".
Kallonshi tayi cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ina tsoron kada Ya Ba'ana ya cutar da kai, ina gudun kada sakaiyar alaƙarmu ya
zama cutarwa, sabida Ni kamin rana a rayuwata, rana kuma ta al'khairi shiyasa bana
son abinda zai cutar da kai".
Murmushi mai yelwa yayi kana a hankali yace.
"Ina sonki zan kuma aureki da izinin Ubangiji zan rabaki da wannan taƙadirin, domin
baki cancanci zama matar mushurkiba".
Da sauri tace.
"Kada kace haka Ya Salmanu Wallahi zai cutar da kai, kada ka bari wani yaji, bare
mgnar ta koma kunnenshi".
Murmushi yayi tare da jawo kwanon ya buɗe. Numfashin yaja jin ƙamshin naman a
hankali ya fara ci, saida yaci ɗaya kab sannan ya rufe kwanon yace.
"Ga rabonki dan nasan Junainah ta cinye naki rabon".
Cikin yanayin nitsuwarta tace.
"A a kaci kawai Ya Salmanu".
Da sauri yace.
"No kada kimin musu".
Shiru tayi jin yaci gaba da cewa.
"Muddin dai ina raye in sha Allah.
wallahi Allah bazan bari Ba'ana ya aureki ya lalata miki rayuwaba, zan jure duk
azabar da zai shayar dani na shaɗi in Sha Allah zan aureki".
Ido ta zuba mushi tana kallon shi cikin kamalarsa, ganin sam hankalinta ba'a kwance
yakeba, yasashi ce mata ta shiga gida zasuyi mgna a waya, haka kuwa akayi, ta juya
ta shiga gida shi kuma ya nufi hanyar gidansu.

A dandalin wurin da yake kamar kasuwar garin nasu ya samu abokanshi, kowa da
budurwarshi suna ɗan hirarsu
Can gefe kuma ga yara nata wasansu, ga farin wata ya fito yayi ras, kana iya ganin
komai.

Ita kuwa Shatu, bayan sun gama shirin baccinsu, ta kalli Ummey tare da cewa.
"Ummey".

"Na'am". Ta amsa mata cikin kula, sai kuma tayi shiru, ita kuwa Ummey ido ta zuba
mata,
ganin hakane yasa a hankali tace.
"Ummey Ya Salmanu". Still kuma tayi shiru,
Cikin kulawa da shaƙuwa wanda ke tsakanin uwa da yarta Ummey tace.
"Gaya min mana, me Ya Salmanun yayi?".
Konciya tayi gefen Ummi dake bisa sallaya, kana a hankali tace.
"Wai yana sona, Ummey ina tsoro Ya Ba'ana zai illata mishi rayuwa, gashi kwanan nan
Ya Hashimu ya rasu, kuma shima ance kasheshi akayi, Ummey ki cewa Bappa na, yacewa
Baba Arɗo ya hana Ya Salmanu cewa yana sona, kinji ko Ummey?".
Kai Ummey ta jinjina mata tare da cewa.
"To zaki aureshi kenan duk da kinsan baya salla kuma yana tsafi".
Kai ta juya tare da cewa.
"Bazan aureshiba Ummey, amman ya Salmanu yayi shiru, bari in gama karatuna, in sha
Allah akwai mafita in na gama karatuna, Ummey kin gane ai ko? Kin tuna ko".
Murmushi Ummey tayi kana tace.
"Eh na gane, yanzu konta kiyi baccinki".
da haka suka konta bacci.

Bayan kwanaki, sosai lamarin Ba'ana yake bawa mutane tsoro, mutun kamar ifiritu,
dan yanzu yanayin sihirinshi ƙaruwa yakeyi sosai,
Wasu lokutan ba hawa ba sauƙa sai dai kawai ka ganshi a gabanka sabida yanzu layan
ɓatarshi tama fi ta baya ƙarfi, ya dage wai zai bawa Shatu taƙi fir daya matsama
kuka tasa mishi hakanne yasa ya hakura ya barta.

Ya Salmanu kuwa yanzu ya dage kan batun soyayyarsa da Aysha, ita kuwa tsoron abinda
zai faru ya hana yarda da kowa, gaba ɗaya kuma yanzu Ƙabilar ɓachamawan nan masifa
tuƙuru suke neman fulanin Bani dashi sabida baƙin ciki da hasadar ganin yadda
shuke-shuken wurin fulanin yayi kyau, shinkafa, masara, dawa, gero, maiwa, wake,
gyaɗa, gujjiya, riɗi, da dai sauransu.

Ga tarin bishiyoyi dorowa da suke zagaye da garin wanda kan ko wacce bishi akwai
jingogin zuma, shiyasa garin suke da tarin zuma.
To waɗannan abubuwan sune suke ƙara tunzura kafuran, sabida gani suke aifa da filin
nasune, sun mance kafin a saida wa fulani filin kufayine, fulaninne suke tafe da
al'barkasu a jikinsu.

Zuwa yanzu kowa na Rugar Banin da kewaye yasan masoyan Shatu biyune, kuma za'ayi
shaɗi, wanda tsawon shekaru biyu kenan ba'ayin ba.
Kowa in yaji da Salmanu za'ayi ana tausaya mishi domin shi mutunne mai laushin jiki
shiyasa tun yana ƙaraminshi aka meda hankali kan karatun da yakeso, hakane yasa
yayi karatun shi yanzu haka yana zama cikin Shikan ne inda yakeda shagunan kayan
tireda sabida bazai iya noma da kiwo ba, kuma Alhamdulillah kasuwar ta amsheshi.
Shiyasa shi zuwa yakeyi Rugar Bani ɗin.

A can ƙasa mai tsarki kuwa,


Yau kwanansu Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da Sittinshi goma da
zuwa, to kasan cewar zasu gudanar da aikin Umarne yasa tun randa suka cika kwana
uku da zuwa suka tafi, Madina,
Kuma sun bar mgnar batun Jazrah cewa sai sun gama gudanar da aikin Umararsu kafin
su shaida mishi, kana in sun dai-dai ta da Jazrah sai su shaidawa Mai alfarma Sarki
Jalaluddin, shi kuma yaje har Ɓadamaya ya shaidawa mai daraja sarki Nuruddeen
Bubayero, da kuma Habeebullah, batun auren in yaso su shirya suzo ayi ɗaurin auren.

To yau kwanansu takwas a Madinah kuma yaune suke shirin dawowa makka.

Kullum sai sun gaisa dasu Hajia Mama dasu Jalal.


Kullum yakan kira Juwairiyya.

Da maraicin suka isa cikin Makka kai tsaye masarautar suka wuce.

Bayan sun gaggaisa, Sheikh Aliyu yace suje su huta, kafin su gaisa da Sheykh
Abdulkareem domin yana tare da manyan baƙi.

Haka kuwa akayi, bayan duk sunyi wonka suka dawo falon Sitti.

Suna zaune cikin shiga ta al'farma a wuri na al'farma, an zagayesu da dukkan kayan
jin daɗin rayuwar duniya,

Sitti na zaune bisa tsakiyar falon akan wani tattausan carpet, Jannart da Jazrah
suna gefenta, cikin shiga ta al'farma,

Sheykh kuwa zaune yake bisa wata lumtsimemiyar kujera kana sawunshi na kan wasu
tim-tim masu masifar kyau da taushi, wasu kyawawan larabawane guda biyu suke zaune
a gaban Sitti sawunta dake bisa tim-tim ɗin sukeyiwa tausa.
Yayinda wasu hadiman kuma ke shirya musu ababen ci dasha dangin yayan itatuwa
kamarsu, Inabi, tupa, ayaba, dabino, gabaruwa, sai zam-zam kana, saisu shawarma and
pizza da kuma wasu irin manyan Foodflaks da aka cikasu da danƙawa-ɗanƙwal dajaja
sai sauran abincinsu na larabawa.

Haroon kuwa gefe yake kusa da Jannart suna ɗan taɓa hira.

Wayarshi ce ta fara ringgin a hankali, idonshi ya ɗan juya ya kalli wayar ba tare
daya juya kanshiba,
Da idonshi ya nunawa hadimin dake gefenshi wayar,
da sauri ya ɗauko wayar ya miƙa mishi, ganin Hajia Mamace ya sashi amsa kiran.
Kara wayar yayi a kunne cikin girmamawa yace.
"Barka da dare Hajia Mama".
A can gida kuwa cikin wani irin salo na musamman Hajia Mama ta rufe idanunta tare
da cewa.
"Uhum ka manta Jabeer mu nan yammane".
Idonshi ya ɗan ɗago ya kalli agogon dake jikin ginin, a hankali yace.
"Haka nefa Hajia Mama. Ya gida yasu Jalal".
Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"Suna lfy gasuma nan kusa dani, Jamil ne ya tsokano Jalal shine suka shigo sunata
muzurai".
Kanshi ya jingina da jikin kujerar, a hankali yace.
"Hajia Mama kiyi musu faɗa kice su barifa sun girma".
Murmushi mai sanyi tayi tare da cewa.
"Na gaya musu sunma daina gasu nan sunata hira kuma".
Gyara zamanta tayi kana taci gaba da cewa.
"Ina Sitti na?". A taƙaice yace.
"Gata nan kusa dani".
Cikin yanayin jin daɗi tace.
"Bata waya". To yace kana ya miƙa Sitti daketa kallonshi wayar, da sauri ta amsa
tare da karawa a kunne, murmushi tayi jin muryar Hajia Mama na cewa.
"(Allah beddu sabbugo Sitti), Allah ya ƙara nisan kwana Sitti". Amin Amin tace,
kana suka gaisa cikin tsananin jin daɗi.
Bayan sun gama wayarne kuma Juwairiyya ta kira Jannart nan suka gaisa ta bawa Sitti
wayar hirar tasu kab kan ya Jafar ne. Saida suka gama wayarne ta kalli Sheykh dake
kishinƙiɗe ya lumshe ido a hankali tace.
"Juwairiyya tace , yau tun safe Jafar ya shiga sashinka yayi ta nemanka ɗaki ɗaki,
da bai gankaba yaƙi fitowa sai kuka yake tayi, har saida yammane da Jalal ya dawo
gida shine ya lallasheshi ya maidashi sashinsu.
Hannu tasa ta share hawayenta da ke kwaranyowa, Haroon ma hawayen ne ke zubo
mishi,
Haka Jazrah da Jannart,
Shi kuwa Sheykh cikin sanyi yace.
"Lamiɗo ya gaya min ɗazu da mukayi waya".
Shiru sukayi baki ɗayansu, a hankali Haroon ya miƙe kwance tare da faɗawa nazari
mai zurfi.
Nan kuma kiran Umaymah ya shigo wayar Sitti still hira sukayi sosai wanda ta kontar
musu hankali kafin, sukayi sallama da juna.

Yau jumma'a ne gajeren lokacine basa kai yamma a wurin kiwo, kafin azahar suke
dawowa, shiyasa yau Shatu tace da ita za'aje kiwo.
Dariya kawai sukayi mata dan sun san ba iya jurewa zatayiba amman tunda ta kafa ta
tsare cewa dole zataje, sai aka barta.

Kasan cewar basu kai yamman bane yasa kuma suna tafiya da wuri.
Bayan duk an kunce dabobbin gaba ɗaya, hakama sauran makiyayan baki ɗaya, sahu-
sahu shanayen keta wucewa.

Sun tafi tun shida da rabi na safe,

Kafin zuwa tara na safe sunyi nisa cikin wurin kiwonsu, inda nan kuma Aysha ta samu
su Hindema sunzo kiwo, wanda su kullum dama suna zuwa.

Wani irin hadarine mai ƙarfi ya taso daga ƙasa, ganin hakane yasa, Gaini kwallawa
Shatu kira wacce take can cikin ƴan uwanta mata makiyaya, jin shiru bata amsa bane
ya nufi wurin da suke zaune,
Cikin kula yace.
"Aysha tashi keda Hinde dasu Mero duk ku tafi gida, kunga hadarine mai ƙarfi ke
tasowa daga ƙasa da alamun za'ayi ruwa mai ƙarfi".
Cikin ƙarfin hali da son wasa cikin ruwan da taketa hari murya a sanyaye tace.
"Ba komai ya Gaini zamu jiraku ai lokacin tashi kuma ya kusa ko?".
Su Giɗi dasu Aro da sauran makiyayan ne sukace.
"Ya Gaini barsu mana ba kiwo zasuyi ba ai makiyayin shanu da tumaki baya gudun ruwa
duk yawa shi".
Cikin jin daɗi sukace, eh mana,
Shi kuwa Ya Gaini murmushi kawai yayi tare da cewa.
"Shike nan yau zakusha dukan ruwa".
Murmushi sukayi sukace "Babu matsala". daga nan mazan duk suka koma wurin kula da
dabobbin nasu da suka duƙufa cin koren ciyawa.

Su kuwa Shatu da Hinde a hankali sukaci gaba da tafiya, sosai tsarin wurin da
yanayin shigar suturar dake jikinta yayi tsananin dacewa da ita.
Doguwar rigace irin tamu ta fulani, yadin farine, sai daga samanshi akayi mishi
kolliya da zaron huɗu, mai color red white, blue, yellow, and green, wanda aka
ƙawata saman rigar da kolliyar zanen ɗawisu, inda daga kafaɗunta har zuwa saman
ƙirjinta, duk an shimfiɗa zaren, bisa wuyan rigar mai V.
sai kuma hannun rigar shima duk an zagayeshi da kolliyar,
Kana sai tsakiyar rigar dai-dai kan ƙugunta shima an ƙawatashi da wannan kolliyar
ulu irin namu na fulanin daji,
Kana sai ƙasar rigar can itama an ƙawata da wannan zaren.

Sai dogon gashin kanta da yake zube a kafaɗunta, yayinda daga saman goshinta kuma
tasa, bandana amman irin namu na fulani mai kalolin ƴaƴan tsakiya, ta zagaye kanta
dashi, sai kolliyar da tayi a fuskarta irin ta asalin fulani, a goshinta zanen kan
shanu tayi, shaidar cikekkiyar bafulatanace, sai kuma ƙasan lip ɗinta na ƙasa zuwa
kan ɗan gemunta shi kuma taja zane da kuma yin ɗigo-ɗigo a gefenshi.
Sai wata kekkewar jakar sakan ulun mai kalolin kolliyar jikin rigarta data rataya a
hannun damanta, wanda cikin jakar kuma ruwan shantane a ciki sai sassanyan kinɗirmo
da goran zuma, sai ɗan sandar mu ta gado, takalman sawunta irin sau cikin nanne
daku mutanen cikin birane kuke masa laƙabi da tashi kabi shanu.
Tayi masifar kyau a cikin wannan shigar tamu ta gado, kyau iya kyau farar fatarta
ta baiyana tamkar balarabiya gashin girarta ya konta lib lib.

A hankali suke ɗan tattaki a cikin dogayen saunukan, da koriyar ciyawa da tayiwa
ƙasanshi ƙawanya. suna ɗan tafe
Suna ɗan tsinkar ya'yan kanya da gwandar daji da suke cike da wurin Chaɓɓulle wato
tsada.

Hadari kuwa sai gamgami yakeyi gabas da yamma kudu da arewa, ko ina yayi dib babu
motsin komai sai nasu dana dabobbin su,
Iska ta tsaya cak koda ganye ɗaya baya kaɗawa duhu ya kareɗe illahirin yankin.

A hankali Hinde ta kalli sararin samaniya cikin tsoron ganin gaba ɗaya duniyar tayi
baƙiƙƙirin ko ina yayi dib, hakanne yasata ɗan zaro ido tare da cewa.
"Kai Shatu, kalli sama, fa hadarin nan yayi duhu da yawa gsky mu tafi gida".
Da sauri ta ɗago kanta kana tasa hannunta na hagu ta ɗan kare saman goshinta kaɗan,
ware idanunta tayi ta kalli sararin samaniya, wani irin azabebben firgita da
tsorone ya rufeta wanda yasa ta juya da azaban ƙarfi ta ruggume Hinde dai-dai
lokacin, sukaga wani irin tartsatsin azabebben igiyar...!

Dan Allah da Manzonsa in dai kin san zaki sayi littafinane ɗan ki fiddashi na
roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar su. Kada ki saya bana so, ki riƙe kudinki.

By
*GARKUWAR FULANI*[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇
🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 9

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘
*FREE PAGE*

*TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta wannan number 09097853276 DOMIN SAMUN DAMAR
KARANTA littafin GARKUWA, ba tare da haƙƙin kowa a kankiba. Akwai Special Group shi
kuma na 1k rak, ki turoshi ta asusuna na Jaiz bank. 0005388578 jaiz bank Aisha
Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai ta WhatsApp
09097853276*

~Ga masu buƙatar kayan gyara na amare, akwai set-set masu kyau, a ƙananan robobi
masu sauƙin kuɗi, akwai kuma na manyan robobi masu zafi, akwiasu dai-dai da tsarin
al'jihun mai ƙarfi da mai rauni, ina araha ina hana bashi. Koda kuɗinka saida
rabonka, kayan Kamfani daban dana shago.~

*Al'ummar Hausawa mazauna Saudiya wannan shafin nakune kyauta gareku, domin jiya da
yau saida mai zaton babu wasu masu karanta littafi sama daku. Nasha mamaki da
sanyin safiya naita cin karo da numbers ɗin ƙasa mai tsarki suna ta antayo min
manyan kuɗi na ƙasa mai tsarki tun ina ƙidaya numbers ɗin +966 har dai abun yaci
tura sabida yawansu, ashe daga zauren Umar Maisanyi sukayi ta antayowa gareni.
Godiya mai tarin Yawa Umar maisanyi mai Tsakar gida You tube limamin tsakar gida*

Walƙiya mai tsananin haske da tartsatsi wanda saida ya haska gaba ɗaya, dajin ya
zamana, har kana iya ganin inuwar dogayen bishiyoyin wurin da sukayi musu ƙawanys.
Wani irin tsoro da firgici da karkarwan ne ya bijirowa Aysha.
Cikin dauriya da sabo da ganin ire-iren irin waɗannan ababen a wurin kiwo, Hinde
ta kamo hannun Shatu tare da cewa.
"Kai Aysha babu komai fa walƙiyace kawai fa kai".
Sai kuma tayi dariya tare da cewa,
"Uhum a hakan kike tunanin jurar taraddadin da muke gani cikin tsaunuka in muna
kiwo".
Janye jikinta tayi daga jikin Hinde, hannun tasa ta tattare gashin kanta dake baje
a kafaɗunta, tubkeshi tayi cikin, fidda numafashin tsoro take karisa addu'o'in
datake tayi a bakinta, a hankali taja da baya ta jingina da jikin ƙatuwar bishiyar
Gamji dake gefensu, jingina kanta tayi jikin bishiyar gamjin tana jin yadda
zuciyarta ke harbawa, pat-pat da azaban ƙarfi domin tasan Hinde bata san me idonta
ke shirin hango mataba,
ita kuwa Hinde, a gabanta take tsaye ya zamana sun fuskantar juna.
Su Ya Gaini kuwa sun duƙufa kiwonsu kamar dai yadda suka saba, ruwa ko iska ko
zafin rana da ƙishi baya kora makiyaye daga kiwo a daji ya dawo gida.
So duk kowa yana yankin da yake bawa dabobbin tsaro, sam basuma hango su Aysha
sosai.

Ita kuwa Shatu idonta dake lumshe ta fara ƙoƙarin buɗewa sabida wani irin tashi da
taji tsikar jikinta nayi.
Hinde kuwa ido ta zuba mata tana ganin yadda ƙirjinta yake sama da ƙasa alamun
tsananin firgita.
A hankali ta ware manyan kyawawan idanunta.
Wani ƙaton curi, dake can bayan Hinde ta zubawa ido sabida wani abu da take gani
kamar hayaƙi yana fitowa ta ƙananan ƙofofin curin. Ita kuwa Hinde bata san meke
wakana ba sabida, ita baya ta bawa curin, asalima yanzu kanta ta ɗaga sama tana
shan ruwan dake cikin goranta.

Ita kuwa Shatu so take ta janye idanunta daga kan wannan CURIN amman sai taji ta
kasa, bugun da zuciyarta keyine ya tsananta, lokaci ɗaya jikinta ya fara tsuma da
karkarwa zufa mai azabar zafi ta fara tsastsafo mata tako wani hudan gashin
jikinta.
Yayin da zuciyarta. Ke harba jini one litter. A Cikin ko wanne one second. Bakinta
ta buɗe da nufun furta addu'o'in dake jere a zuciyarta amman sai taji ta kasa,
zuru-zuru tayi da idanunta lokacin da taga wani dogon abu yana fitowa daga cikin
babban ramin dake tsakiyar CURIN nan, a hankali ta ɗaga kwayar idanunta sama tana
bin abin da kallo, wani irin dogon numfashi taja, ganin abun nan yana miƙewa yana
yin sama, abun dogo kamar igiya sai dai kuma yanada zane kala-kala red, yellow,
green, blue.
Kuma abun biyune ɗaya a sama ɗaya a ƙasa, cikin ranta take iya ammabaton sunan
Allah ganin zahiri fitowar bakan Gizo daga cikin curi Allah ya nuna mata, ras zanen
bakan Gizon nan yayi kama da kalolin kolliyar jikin rigarta,
Kanta ta ɗaga sama, tana bin Bakan Gizon da kwayar idanunta, tana gani har ya
haura sama can ya konta a gicciye gabas da yamma kudu da arewa, kana kuma mai
hasken ras yana sama mai ɗan dishi-dishin yana ƙasa. Wanda a falsafar al'ummar
Duniya ake cewa suma mata da mijine, muddin kaga mai hasken in ka zuba ido zakaga
mai dishi-dishin wanda akecewa, mijin shine dishi-dishin kuma shike goyo matarsa
shiyasa sai ake ganin mai hasken shine a sama.

Wasu irin numfarfashi take ja da azaban ƙarfi da razana, kar-kar haka jikinta ke
rawa.
Cikin tsoron halin da take ciki Hinde ta wurgar da goran dake hannunta, tare da
cewa.
"Hande en boni, yau munga ta kanmu Shatu me haka meya sameki?". Ina babu mgna sai
zamewa da ta farayi tanayin ƙasa alamun zata faɗi, ganin hakane yasa, Hinde juyowa
da ƙarfi ta fara rabƙawa su Ya Gaini kira.
"Ya Gaini! Ya Seyo! Ya Lado, Wayyo Ya Giɗi kuzo kuga abinda Shatu keyi".
Maganarta ta karshece ta sasu, tasowa a guje gaba ɗayansu suka nufosu da gudu,
kafin su isoma Aysha ta faɗi ƙasa zaune, sai karkarwa da rawan sanyi takeyi.
Suna isa Ya Gaini yasa hannu ya tallabota ganin yadda taketa karkarwa, idanunta na
rufewa,
Seyo ne ya kalli Hinde cikin kiɗima yace.
"Subahanallahi Hinde me ya sameta?".
Cikin kuka Hinde tace.
"Ban saniba wallahi haka kawai naga tana karkarwa".
Giɗi ne ya zauna kusa da yayan nashi kanshi ya sunkuyo kanta yana kiran sunanta a
jere a jere.
"Aysha! Shatu. Ayshatu tashi buɗe idonki ki gaya min meya sameki meke miki ciwo".
Ina babu magana saima kara rumtse idanunta da tayi tare ƙara ƙaƙƙame jikin Ya
Gainin nata.
Ya Lado ne da Seyo suka sunkuyo kanta addu'o'in suka rinka tofa mata, duk addu'ar
da tazo bakinsu tofa mata sukeyi, Giɗi kuwa ruwa yasa a tafin hannunshi yana shafa
mata a fuskarta.

Cikin al'hini sauran makiyayan duk suka iso kansu, ganin yadda suke birkice ne ɗaya
daga cikin ƴaƴan Alhaji Haro da kuma Alhaji Umaru sukace.
"Gaini mu tafi gida da ita, tunda dama lokacin tashinmu yayi, an kusa fara tafiya
masallacin juma'a."
Cikin damuwa Giɗi yace,
"To ai bazata iya tafiya ba".
Seyo ne ya miƙe cikin sauri yace.
"Bari inje in kawo doki sai mu ɗaurata a kai".
Da sauri Manu ɗan Alhaji Haro yace.
"Yauwa yi maza, kunga ku kuma Gidi kuje duk ku haɗo mana kan dabbobi ku fuskantar
dasu hanyan gida".
Ai kuwa haka akayi sauran yaran duk suka kaɗa shanun.
Koda Seyo ya kawo dokin, shida kanshi ya hau baya sannan aka ɗaura mishi ita a
gabanshi, a haka suka nufi gida.

Koda suka isa gida, da kanta ta taka har zuwa cikin gida, suna biye da ita a baya.
Kai tsaye ɗakin Ummey ta shige, bisa gado ta konta ta duƙunƙune tana rawan sanyi.
Da sauri Ummey da Inna da Junainah suka biyota a baya.
Cikin tsoro Inna tace.
"Subahanallahi Shatu meya faru".
Ummey kuwa gefenta ta zauna, tare da jawo borgo tana rufe mata jikinta.
Giɗi ne da yanzu ya shigo, shine ya basu lbrin iya abinda suka sani.
Seyo kuma cewa yayi a mata hayaƙi.
Haka kuwa akayi sukayi mata hayaƙin kana Ya Gaini ya zauna yayi mata rubutu nanma
aka wonke aka bata.

Jin jikinta yayi zafi jau ne, alamun zazzaɓi ne ya rufeta yasa, Ya Lado yaje ya
ɗauko mata mgnin a ɗakin Bappa, nan Ummey ta bata tasha, a take bacci ya ɗauketa.

Ummey kuwa da Inna woje suka fito sunata dariya dan su a zatonsu ko gajiyane yasata
hakan tunda ita dai bata saba zuwa kiwoba tunda tanada yayu maza da yawa.

Koda akayi sallam Juma'a aka idar, su Bappa da yaranshi kab basu dawoba saida akayi
sallan la'asar kafin suka dawo gida.

Ummey kuwa da Inna aikin abincin dare sukeyi wanda girkin ranar jumma'a na dabanne,
zabbi biyar suke yankawa kullum jumma'a wata rana kuma tattabaru wani lokacin kuma
jan nama Bappa ke saya to yauma hakanne.

Inna ce zaune tanayi musu wonke-wonke yayinda Junainah kuwa keyin shara, dama
wonke-wonke aikintane to duk randa takeji tsiya sai tayi ta ƙorafi, shiyasa yau
tana farawa Inna ta fara aikin.
Ummey kuwa tana cikin kitchin ɗinsu, wanda dama da Shatu lfyarta lau muddin tana
gida ita keyi musu, girki domin Ummey ta horeta da iya girke-girken na ban mamaki.

A hankali Shatu ta bude idanunta daga baccin da takeyi,


Cin karfin jikinta ya ɗan dawo, a hankali ta tashi zaune, da sauri ta fito woje,
sabida ganin ita ɗaya ne a ɗakin.

Da sauri ta fito, Inna ce ta ganta cikin kula tace.


"Shatu kin taso?".
Kai ta gyaɗa mata alamar eh.
Cikin kula tace.
"To ya jikin naki?".
A hankali tace.
"Da sauƙi, Inna zanyi wonka".
Mikewa tayi dan dama ta gama wonke-wonken. Botiki ta ɗauka kitchin ta shiga, ruwan
zafi ta ɗebo nan take cewa Ummey.
"Shatu ta farka".
Murmushi Ummey tai tare da cewa.
"Na jita ai wai zatayi wonka, ke kuma harda biye mata kamar ta shekara ba lfy,
Shatu ba dai rakiba".
Dariya suka ɗanyi, ita kuwa a tsakiya gidan ta zauna kan dakalin da ke gindin
bishiyar ceɗiya dake wurin.

Bayan inna ta kai mata ruwan ne ta kalli Junainah cikin sanyi tace "Junnu zoki
rakani inyi wonka Mana."
Ido Inna ta zaro tare da cewa.
"Hahhh Shatu yau kuma ta rakaki wonkafa kikace".
Kanta ta gyaɗa cikin raunin fuska tace.
"Eh Inna tsoro nakeji shiyasa".
Ummey dake kitchin ne ta fito rike da aikoshn data zuba zabbin data soya a ciki,
tace.
"Shatu ki rage tsorofa".
Kai ta gyaɗa kana taja hannun Junainah tare da ɗaukan kondon kayan wonkanta,
A bakin ƙofar mashiga bayan gidan tace.
"Yauwa Ƙanwaliya jirani a nan".
To Junainah tace,
haka ta tsaya tana jiranta,
Ita kuwa wonkanta tayi, a nitse kana, tana fitowa.
Tayi al'wala, ɗakin Ummey ta shiga, sallan azahar da la'asar ɗin tayi, sannan ta
zira wata tattausar doguwar riga.

Turare ta ɗan fesa kana, ta fito,


Gefen katangar kitchin ɗinsu ta samu Ummey tana haɗa wuta a murhun dake wurin.

Inna kuwa zaune take a gefe, da turmi a gabanta, kana tana jajjaga tattasai da
tumatur da kuma tarugu da al'basa.

Taburman data fito dashine ta shimfiɗa gefensu.


Inna ce ta kalli Junainah da itama yanzu ta fito wonka tace.
"Yauwa Junainah zoki kawowa Addanki abinci."
To tace kana tazo ta shiga ɗakin Inna.
Ta fito da tire a hannunta da wasu ƴan kananun robobi guda huɗu a kai masu marfi,
sai kuma kula a tsakiyarsu.
A gaban Shatu ta ajiye kular.

Kana ta wuce ta nufi ɗakin Ummey.


Ita kuwa Aysha kular ta buɗe, dambun zogalenen a cikin wanda yaji, ganyen zogalen
da kuma al'basa, sai tururi yakeyi.
Ƙananan robobin kuwa, ɗaya dakekken yajin ƙaragone wanda yaji magi da borkino da
kuma tafarnuwa.
Kana ɗaya robar kuma, soyayyan man shanune a ciki.
Ɗaya kuma yankekken al'basane da kuma tumatur, sai dafeffe kwai duk a yayyanka,
Kana ɗayan kuma dambun namane mai laushi, a ciki,
ɗan karamin aikoshin dake gaban Ummey taja, ta zuba dambun, kana ta zuba sauran
kayan hadin.
A hankali ta fara ci.
Junainah da ta fito yanzune ta kalla tare da cewa.
"Junainah bani ruwa".
To tace kana ta juya ta nufi gindin randunarsu inda suke jere a ƙalla sun kai shida
ko dan ba manya bane dukansu na taɓone masu ɗan karen sanyi, ga kuma inuwar
bishiyoyin ayaba da sukayiwa randunar ƙawanya,
Shiyasa ko yaushe ruwan zakajishi kamar na firiji,
A kofin silver ta ɗebo mata kana tazo ta zauna gefenta, sunaci a tare.

Ummey kuwa tukunyar ƙasa ta ɗaura a wuta tare da tsulala man shanu, a ciki.
Kayan miyan da inna ta kirɓa ta amsa ta zuba a cikin manda yayi zafin ta fara soya
miyar, zabbin da zatayi musu.
Kana ɗaya murhun kuma ruwan tuwo ta aza a tukunyan ƙarfe.
Inna kuwa data gama kirɓa kayan miyar, shinkafar tuwon ta ɗebo tazo tana wonkewa.

Suna cikin haka su Bappa da yayunta maza suka dawo.


Nan suka shimfiɗa katuwar taburma a tsakar gidan.
kana Giɗi ya ajiyewa inna ledodin tsarabar jumma'a da Bappa kanyi duk ranar sati.
Tirirruka Ummey ta miko mata ta baza, juye kayayyakin a cikin.
Reke,Lemu, kwakwa, da Giginya, da kuma dafaffiyar gyaɗa, da ƙosai mai zafi da
biredi da soyayyen doya da fulawa mai jawa.
kayan cimarmu kenan fulani

Zubawa maza nasu akayi, aka basu a tsakiyarsu suka ajiye sunaci da mahaifin nasu.
Shatu kuwa da Junainah aka basu nasu. Ummi da Inna kuwa sun ajiye nasu dan aiki
sukeyi.
Ya Gaini ne ya ɗan danki ƙosai da bredy yasa a bakinshi,
tauwana yayi kana idanunshi na kan Aysha saida ya haɗiye kana yace.
"Shatu, ya jikin naki?".
Murmushi ta ɗanyi sai kuma ta ɗan harari Junainah dake cewa.
"Uhum ta worke ai dama kawai hegen tsorone da raki".
Dariya sukayi baki ɗayansu. Seyo ne wanda yakeda tarin jinƙai da nitsuwa,
ya ɗan afa geɗan daya ɓare a bakinshi tare da cewa.
"To Amman Shatu meya samekine lokaci ɗaya kika firgita?".
Giɗi ne da shi kuma doya yakeci yace.
"Kamar mai cutar al'janufa ta zama".
Bappa ne ya ɗan kalleta cikin kulawa yace.
"Shatu meya sameki ne?".
Murmushi ta ɗanyi tare da kallon Ummey dake cewa.
"Uhum tsorone da gajiya fa".
Kai ta jujjuya a hankali tace.
"Allah ko Ummey ba tsoro bane".
Sai ta kuma meda hankalinta kan Bappa cikin sanyinta tace.
"Bappa naga abinda ya firgitanine.
Shin Bappa dama bakan Gizon cikin curi yake fitowa ne?."
Cikin mamaki suka zuba mata ido baki ɗayansu.
Bappa ne da kanshi yace.
"Ban fahimceki ba Shatu".
Bredy dake gefenta ta gutsura kana ta dandola da zuman data sa Junainah ta kawo
musu, a baki ta ɗansa ta tauna kana a nitse ta basu labarin abinda ta gani da kuma
yadda taji, ta ƙara da cewa.
"Bappa dama bakan Gizo a curi suke fitowa ne?".
Cikin mamaki da al'hini yace.
"Allahu al'alamu. Sai dai koma menene, lallai tabbas akwai abinda ke tunkarar
rayuwarmu, fatana mu dage da addu'a koma menene Allah ya kawo mana shi kan
al'khairi ya kuma sauƙaƙa manashi, zan kuma bincika in sha Allah.
Sannan kada ku gayawa kowa mgnar nan".
Ya karishe mgnar da kallon Junainah.
Wannan labari ya sasu cikin dogon nazari. haka dai sukaci gaba hira kamar yadda
suka saba.

A can cikin yola kuwa, yau tunda Ya Jafar yaje sallan juma'a ya dawo baiga Ƙaninshi
Sheykh ba, gaba ɗaya ya tashi hankalin ƙanenneshi da iyayenshi.
Domin kama hannun Jalal yayi yana kuka, yana jan Jalal zuwa sashin Sheykh koda suka
shiga, Jamil kuwa sashin mahaifinsu ya nufa. Ba tare da ya saurari
Hadiman ba ya wuce.
A babban falon ya samu , Abba
Haurawa sama yayi yana shiga kuwa ya sameshi a falo shida jarabebboyar amaryar tasa
cingom dinshi.
Sai dai tana konce bisa kujera,
Shi kuma yana zaune bisa sallayane ya fuskanci al'ƙibla, da ƙur'ani a gabanshi yana
karatu cikin suratul Khafi.
cikin rauni Jamil ya ƙaraso gabansa.
Bai kulashiba har saida ya kai ƙarshen surar kana ya shafa addu'a.
Cikin haɗe fuska da alamun faɗa yace.
"Jamil lfy kuwa mehakan?".
ido na zubda hawaye yace.
"Abba Ya Jafa".
Rai a hade yace.
"To me zan mishi?".
Cikin zubda hawaye yace.
"Abba tunda aka dawo aka sauƙo sallan jumma'a fa yaketa kuka yana bin Jalal yana
kuka alamun a kaishi wurin Hamma Jabeer, yau ko abinci baiciba, Aunty Juwairiyya ma
sai kuka takeyi hakama su, Jiddah."
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
"To ni zaka gayawa? Kaje ka gayawa Mamanku mana".
Wasu sabbin hawayene suka zubowa Jamil a hankali ya juya ya fita".

A can sashin Sheykh ya samesu, Juwairiyya da Jalal ɗin da Affan sun tasashi a gaba,
Affan yanata kuma, shi kuwa Jalal sai tattaune laɓɓansa yakeyi, da sauri Jamil ya
iso cikin sanyi yace.
"Affan je ka gayawa Mama".
Da sauri Affan ya juya har zai fita kuma ya dawo jin Juwairiyya na cewa.
"No Affan kada kaje, ka gaya mata, nasan yanzu tana bacci ne".
Shi kuwa Ya Jafar sai ya shiga ɗakin nan ya fito ya shiga wancan ya fito yana kuka
kuma.

Shigowar Abbane ya sasu su Jalal duka fita.

A hankali Abba ya kamo hannunshi suma suka fito, da mamaki a fuskar Jamil ya bisu
da ido.

Shi kuwa Abba yana riƙe da hannun babban ɗan nashi suka wuce har makoncinsa,
Gefen gado ya kontar da dashi, kana a hankali yake shafa kanshi cikin taushi da
tausayawa yace.
"Jafar kayi haƙuri kayi baccinka kabar kuka, Sheykh yana lfy lau, ya tafi ƙasar
Saudia ne shida kakarku Sitti."
Shiru yayi yana kallon mahaifin nashi.
Shi kuwa Abba, kanshi yake shafawa yana kontar mishi hankali a take yayi baccinsa.

Bayan sallan ishane Jamil yaje wurin Kakansun ya sanar mishi halin da ake ciki ya
ƙafarsa cewa.
"Allah rene, magar gsky kace Hamma Jabeer ya dawo, sabida abin ya Jafar yana
tsananta in bayanan".
Murmushi kakan nasu yayi tare da cewa.
"Uhum ai Allah ya sauƙaƙa abinda zai taso Sheykh ya dawo ba tare da an gama dai-
dai-ta abinda ya kaishi ba Dole shi wannan mai saɓulellen mondon Jalaluddin shi zai
dena yawon iskanci ya zauna ya kula dashi tunda yafi kallonshi a madadin Sheykh".
Cikin takaici Jamil yace.
"To ni zan kai Ya Jafar saudia wurin Sheykh ɗin suci gaba da zama a can in sun so,
tunda dai kun san Sheykh shine GARKUWAnmu".
Cikin kontar da murya kakan nashi ya ɗan tausasashi kana yace in yaje ya turo mishi
Jalal.

A can Saudia kuma, sosai aketa shirya yadda ɗaurin Auren Sheykh da Jazrah zai
kasance, duk da basu sanar mishiba, sabida kashedin da Sarki Jalaluddin da
Nuruddeen sukayi musu dan ko yaushe in dai ana shirya batun aurenshi muddin yaji
sai yaƙi fir yayi ta kaucewa dole a ƙarshe aure ya fasu, to wannan abunne yasa ba'a
sanar mishiba.
Sai dai yasan batun zuwan da Jazrah take sashinsu wai nune da ita suke zaɓa mishi
in tayi mishi.
To shi kuwa bayan gaisuwa ko sannu bai taɓa haɗasu da itaba.

Haroon kuwa da Jannart sunata shirye-shiryen dawowa gida Nigeria.

A garin Bani kuwa,

Yau tun bayan sallan isha'i yaro ya shigo yace, Ya Salmanu yana sallama da Aysha,
haka kuwa ta fita taje,
Suka zauna a dakalin ƙofar gidan nasu suna hango yadda,
Yara keta wasa a dandali domin ranar jumma'a tafi ko wacce rana a garesu wurin
shanawa.

Ya Gaini ne ya fito riƙe da hannun Junainah, a bakin ƙofar suka wuce Su Shatu
Bayan sun gaisane ya wuce riƙe da hannun ƙanwar tasa,
Murmushi Salmanu yayi tare da cewa.
"Shatu, inaga dai aurenmu dana babban yaya rana ɗaya za'ayi shi".
Murmushi itama tayi, tare da cewa.
"Tab shifa har an kai kayan aure".
Ido ya ɗan lumshe tare da cewa.
"To ai in kin bani dama nima gobe-goben nan sai a kawo kayan aurenmu ko?".
Da sauri tasa tafin hannunta ta rufe fuskarta, alamun jin kunya.

Su Ya Gaini kuwa kai tsaye ƙofar gidan Ahaji Haro sukaje,


A bakin ƙofar suka tsaya, sunkuyowa ya ɗanyi a hankali yace.
"Yauwa ƙanwaliya maza shiga cikin gidan kicewa Addanki Bintu tazo".
Cikin happy tace. To kana ta shiga cikin gidan da sallama.

Kamar yadda gidansu yake hakama gidan Ahaji Haro duk suna zaune a tsakiyar gida da
yaranshi da matanshi sunata hira, bayan ta gaidasune taje gefen Binto cikin raɗa ta
gaya mata saƙon ƴaƴansu.

Wani ɗan kekyawan matashi ɗan kimanin shekaru sha takwas mai sunan Junaidu ne ya
kalli Junainah cikin tsananin so da ƙaunar yarinyar yayi murmushi tare da taɓa
mamanshi cikin raɗa yace.
"Inno ga surkarki in Allah ya yarda".
dariya suka ɗan yi dan kowa yasan Junaidu yasan son da yakewa Junainah tun tana
ƙaramar ta.

Ita kuwa Junainah hannun Binto ta riƙo suka fito tare,


Junaidu na biye dasu a baya,
Koda suka fita, Gaini ne ya kalle Junaidu tare da cewa.
"Yauwa Junaidu raka min Junainah gida ko".
To yace kana yabi bayanta suna tafe suna hira, sunzo dai-dai ƙofar gidansu Ahaji
Umaru ne suka samu Ya Seyo da Hinde suna hirarsu.

Koda suka wuce, murmushi Junaidu yayi tare da cewa.


"Junainah sai yaushe zan fara zuwa muma muyi hira ne?".
Cikin yin ƙasa da murya tace.
"Sai na ƙara girma kafin nan Addana tayi aure".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Ko dai bakya so nane".
Da sauri cikin yarinta tace.
"A a ina sonka mana".
Dariyar jin daɗi sukayi baki ɗayansu, sun zo kusa da ƙofar gidansu.
Ya Ba'ana ne sukayi kiciɓis dashi, murmushi yayi tare da cewa.
"Yauwa Ƙanwaliya kuzo mu shiga in baki aike ki kaiwa Shatu".
To sukace kana sukabi bayanshi, a tsakar gida suka samu, Iya Bultu majaifiyar Ya
Ba'ana kena ƙatuwar mace baƙa ƙarin da ita, ga jajayen idanu, fuskarnan a haɗe ta
kalli Junainah dake gaidata da fullanci cikin tsananin tsawa tace.
"Ke tafi daga nan ƴan iskan fulani masu jajayen kunnuwa, dan uwarki Ni ba fillatace
da zaki gaidani da fullanci, hegu kwarkwasa fidda mai gida a gidanshi yan iska masu
kama da al'janu, in sha Allah ƙarshen zamanku a wannan yanki yana nan tafe".
Da sauri Junainah ta koma bayan Junaidu, shi kuwa Junaidu wani irin tafasa
zuciyarshi keyi akanme zata zagesu dan kawai sun gaidata da fullanci.
Bukar ne mijinta wanda yake babarbaree ya kalleta tare da cewa.
"Kuma dai al'barkacin fulanin kikeci".
Ba'ana ne ya ɗan harari mahaifin nashi tare da waskewa yace.
"Fulani kecin al'barkacin ta dai, tunda kowa ya sani wannan yankidai na Ɓachamawa
ne, ba fulaninba".
Cikin ƙarfin hali Junaidu yace.
"Ato ai dai ba kyau aka bamuba da kuɗin mu aka bamu, kai kamma ya Ba'ana kaifa
bawanmu ne tunda kai babarbarene".
Wani irin suka kalawan yaron suka mishi a ƙahon zuciyarshi amman sai ya dake,
ledan su ayaba da inabin ya bawa Junainah tare da cewa.
"Uhu Junaidu kenan aini ba bakanuri bane ni ba Bachamene, Dan da in zama bawan
fulani gwara in zama bawan karnuka".
Haka nan kalamansu ke tafasa zuciyar Junainah da Junaidu, haka yasa fuska a hade
suka juya suka tafi, har sunje bakin ƙofar fita Ba'ana yace musu.
"Yauwa kuce mata ina zuwa yanzu bari inyi wonka".
To sukace kawai suka fita suka tafi.

A ƙofar gidansu suka tsaya gaban Ya Salmanu da Aysha, ledan Junainah ta ajiye a
tsakiyarsu cikin jin haushi tace.
"Addana gashi inji ya Ba'ana wai in kawo miki, yace kuma yanzu zaizo wai wonka
kawai zaiyi".
Tana kaiwa nan tayi cikin gida shi ma Junaidu Binta yayi a baya, har gabansu Ummey
ya tsuguna suka gaisa kana yace.
"To Ummey ga Ƙanwaliya na rakota Ya Ganin ne yace in rokata har cikin gida".
Murmushi Ummey tayi tare da cewa.
"Mun kuwa gode, ka gaida min Innonka kace mata, in Allah ya kaimu gobe ta turo min
Hari tazo tamin kitso".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"To saida Safe Bappa".
Allah ya bamu al'khairi sukace baki ɗayansu.

Daga nan ya fito, har ya wuce Ya Salmanu yace.


"A a Junaidu zoka amshi tsarabar mana".
Cikin girmamawa yace.
"A a Ya Salmanu ya isheni".
Cikin kula Salmanu yace.
"Ni kam yaushenene zaku koma school?".
Da sauri yace.
"Saura kwana biyar hutunmu zai ƙare".

"To Allah ya taimaka yanzu aji nawa kane".

Murmushi ya ɗanyi tare da cewa.


"Ina SS 3 ne fa, Ya Salmanu na kusa gamawa ai".

"Masha Allah, Allah ya taimaka".

Amin Amin yace kana ya juya ya tafi.

Ita kuwa Shatu cikin tsoro ta kalli Ya Salmanu a hankali tace.


"Ya Salmanu tashi ka tafi kada yazo ya sameka".
Cikin harshen fillanci yace.
"To shi mala'ikan ɗaukan raine? Ko dai so kike in guje masane Shatu, kina son ragon
mijine?".
A hankali tace.
"A a Ya Salmanu zai cutar da kaine nake tsoro".
Da sauri ya katseta da cewa.
"Babu mai rayawa da kashewa sai Allah, ko yaya zaiyi bashi da ikon kasheni sai in
kwana-nane ya ƙare. Ko ciwon kai bai isa ya samin ba".
Shiru tayi tana kallonshi.
Sai kuma tai maza ta miƙe tsaye ganin kamar daga sama aka jefo Ba'ana gabansu.

Kallon kallon sukeyiwa juna shida Ya Salmanu, cikin wani irin mugun kallo mai cike
da mugunta yayi kwaffa tare da cewa.
"Uhummm Salmanu manyan gari, wato har an samu wani mai yar guntuwar jarumtar da zai
iya haɗa so dani a kan Shatu, to bazan ce maka komaiba, amman ka shirya ranar
litinin zamuyi shaɗi muddin ka cini na bar maka ita duniya da lahira, zan kuma bar
garin Bani, da ƙasar nan gaba ɗaya zan koma ƙasar Cameroon, in kuwa na cika zaka
bar duniya baki ɗayanta!".
Cikin tsananin tsoro da kaɗuwa Shatu tace.
"A a fa Ya Ba'ana wlh ba sona yakeyiba, karatu yake koya min".
Da sauri Salmanu ya katseta da cewa.
"Sonta nakeyi Ba'ana so kuma na aure, na kuma yarda zan shiga gasar Shaɗi da kai a
ranar Litinin na amince".
Wata irin muguwar dariya yayi wacce har tasa Aysha kowa cikin gida da gudu, shi
kuwa saida yayi dariyar mai isarshi kana yace.
"Lallai gidan Arɗo Yabani na gab da rasa motsin ɗana miji".
Yana faɗin haka ya murza layar zananshi, sai gashi ya ɓaci.

Cikin ƙarfin hali Salmanu ya nufi gida.

Shi kuwa Ba'ana yana ɓacewa a tsakiyar dottawan Fadan Arɗo Yabani ya baiyana,.
Wanda badon tsoffin makiyayene sun saba ganin abinda yafi haka ba tabbas watsawa
zasuyi.

So amman suka dake, cikin kamala Bappa ya kalleshi tare da cewa.


"A a Ba'ana lfy kuwa?".
Sunkuyar da kanshi yayi kamar mutumin kirki, cikin danne fushinsa yace.
"Ku gafarceni Bappa nazone da batun neman al'farma fagen shaɗi, nida Salmanu ɗan
Arɗo zamuyi gasa kan Shatu, na kuma yarda, muddin yayi nasara akaina na bar mishi
Shatu zan kuma bar Rugar Bani baki ɗaya".
Da sauri Bappa yace.
"A a".
Da sauri Arɗo Yabani yace.
"A a Malam Liman ba komai, na amince na basu damar yin gasar Shaɗi mai nasara yaci
gasar".
Jin haka yasa dattawan nan duk sukayi shiru.

Shi kuwa Ba'ana cikin tarin ƙeta jikinshi har tsuma yakeyi yana maganar zuci.
"Uhumm zan kashe Salmanu kuwa kisa mafi muni zaku gane kurenku hegun fulani kunzo
garin daba nakuba kun fisu dukiya zan kashe Salmanu irin kisar da ban taɓa yiwa
waniba kisan da zaisa har abadan babu wanda zai sake cewa yana son Shatu".
A zahiri kuwa, godiya yayi musu kana ya juya ya tafi.
Nan dattawan kuma sukaci gaba da tattaunawa yadda Shaɗin zai kasance.

Washe gari ranar asabar da sanyin safiya akayi shelar sanar da gasar Shaɗi da
za'ayi jibi litinin, da kuma, waɗanda zasuyi gasar da sunan wacce za'ayi dan ita.

Gaba ɗaya magarna ta cika Rugar Banin da kewayenta, duk wanda yaji yana firgici,
Maman Salmanu kuwa tuni taketa kuka tana cewa ita kam so ake a ƙarar mata da
yaranta an kashe mata Hashimu yanzu kuma ace da Salmanu za'ayi gasar Shaɗi da mutun
da sun san ba'a taɓa nasara a kansa a.,
Mutanen sauran rugogin Fulani dake mutunci da Arɗo Yabani kab sai gudumowar
magunguna suke kawo na dauri dan a tsuma jikin Salmanu.

Sosai kuwa babanshi da yayunshi mata da maza da abokanshi keta tsumashi.

Shi kuwa Ba'ana tun ranar ya ɗauki tunƙur ƙasar da yake tsuma bulalinshi, ya kaishi
Ƙauyen Bonon, gaban dodon tsafinsu,
Anan tukunyar ta kwana bulali tamanin dake cikin tunkuyar nan aketa tsumawa da
tsafi.
Kana an jikasu da ruwan gishiri sannan an juye kunamai sama da ɗari a ciki, irin
baƙaƙen kunamun nanne masu mugun dafi, an sasu ciki sunata harbin bulalin nan suna
sa dafinsu a jiki. ranar lahadi da yamma ya amso tukunyar,
Har zauren gidansu Shatu yaje yasa aka kira mishi ita bayan ta fitone yace ta leƙa
cikin tukunyar, a hankali tace.
"Me zan gani a ciki?".
Kanshi ya jinjina mata tare da cewa.
"Nazo in nuna miki bulalin shaɗi nane, ki gansu da kyau, dan ki cewa wancan
koɗeɗden ya shirya shan zabga".
Kai ta jujjuya tare da cewa.
"Ni ba sai na ganiba".
Murmushi yayi tare da buɗe tukunyar kana ya karkatar mata shi gabanta.
Da sauri taja da baya tare da cewa.
"In......

Littafina na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ko karanta a nitse.

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 10

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🕊️🐄🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

LITTAFIN GARKUWA NA KUƊINE, TURO KATIN MTN NA ƊARI UKU KACAL ta number 09097853276
domin samun cikekken labarin, ko kiyi min transfer ɗin 1k ɗan samun SP GROUP ta
asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta
wannan number 09097853276

FREE PAGE

Cikin tashin hankali tace.


"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ya Ba'ana me wannan, abu kamar macizai". Da
sauri ya meda ya rufe kana ya miƙe cikin yin ƙasa da murya yace.
"Kinga ni kada ki tayarmin da hankali kinsan bana son ganinki cikin tashin hankali,
in sha Allah nine da nasara ko dai bakya so nane".
Da sauri ta girgiza kanta tare dasa tafin hannunta ta rufe bakinta.
Ganin haka ya kwashi abinshi ya tafi.
Ita kuwa koda ta shiga gida, gefen Inna ta zauna tare da cewa.
"Inna ku cewa Bappa ya cewa Arɗo ya hana gasar nan, kada a cutar da Ya Salmanu".
Cikin sanyin jikin da duk kwanan haka inna ta zama, a hankali tace.
"Uhumm ba komai Shatu in sha Allah duk abinda zai faru da sanin Allah.
Yanzu ke yaushe nema zaki koma hutunmu?".
Kanta ta gyaɗa a hankali tace.
"Rana ita yau zan koma kimga saura mako ɗaya kenan".
Ummey ce dake gefe ta ɗanyi ajiyan zuciya gami da cewa.
"Alhamdulillah ni in kin komama hankalinmu zaifi konci, domin muddin kinanen sai
Ba'ana yayi ta kalato fitina".

Shiru sukayi baki ɗayansu, jin an fara kiran sallane tasa, duk kowa yayi al'wala
haraman salla.

A daren ranar kuwa Ya Salmanu da abokinshi Sale suka zo, wurinta, nan take ce musu
ita kam bata son wannan gasar da za'ayi kuma tunda an kafe sai anyi sam ita bazata
jeba.
Haka dai sukayi ta hira daga bisani suka tafi.

Washe gari ranar Monday kuwa, tun da sanyin asuba aketa gangamin.
Haɗuwa a filin da za'ayi shaɗi.
Mutanen sun cika maƙil dan anfi yawan yin gasar da safe, sabida da rana duk
makiyaya sun tafi kiwo manoma sun tafi daji.
Tuni matasan Fulani na rugogin nesa da Bani ma sun zo.

Bukar kuwa tunda aka fito sallan asuba yaje. Gidan Arɗo Yabani, yaso ace an janye
gasar tun randa aka shelanta amman Arɗo yaki,
still yanzuma da yazo, bayan sun gaisane ya ɗanyi gyaran murya tare da cewa.
"Haƙiƙa naso a janye wannan shaɗi, domin nasan abun bazaiyi daɗin ganiba ace Ba'ana
na zane Salmanu ɗan Arɗo ga wannan rugar, amman kaƙi ka saurari zancena,
Dan haka ni ba kada wani abu ya faru ku kuskura kuyi kuka dani, duk abinda ɗana
yayiwa ɗanku kune kuka saya mishi da yawun bakinku kun rigada kun san bazaku taɓa
samun wanda zaifi ƙarfin ɗanaba".
Shiru Arɗo Yabani yayi yana nazartan kalaman Bukar,
ganin yayi shirune alamun ya gama magarsa cikin sanyi Arɗo Yabani yace.
"Duniya da faɗi take, Bukar Mai kanwa a kwana a tashi watan-wata-rana zakaji zaka
gani da idanunka za'a samu wanda zaifi ƙarfin ɗan ka, Allah zai bijiro da wanda zai
iya jure bulalin ɗan ka".
Cikin wani irin yanayi Bukar yace.
"Babu mamakin a samu mai iya, jure bulalin, tabbas babu mamaki. Sai daifa abun da
bazai taɓa yiwuwa bane har illa masha ALLAH ace an samu wanda zai iya nasara a
kanshi babushi babu namijin da zai iya sashi jin zafin bulala bare ya zubda hawayen
da zaisa ya rasa Shatu".
Wani dogon numfashi Arɗo Yabani yaja tare da cewa.
"Uhummmmmm". Daga nan bai kuma cewa komaiba,
Shi kuwa Bukar tashi yayi ya kakkaɓe rigarsa ya juya ya tafi yana faɗin.
"In dai kunne yaji gangan jiki ya tsira".
Da ido Arɗo Yabani ya rakashi, yana maiji a cikin ransa inma ace yanada dama, inama
ace zai samo wannan bulalin da Malam Chuɓaɗo ya gaya musu, da tabbas ya samu hanyar
da zai cire mugun iri a garinshi.

A haka Salmanu da abokinshi, sukazo suka sameshi zaune. Bayan sun gaisane Sule ya
ɗan matso kusa da Arɗo a hankali yace.
"Allah rene, duk wuri an taru mu ake jira, shi Ba'ana tun da asuba yana can, yanzu
Iro yazo yake ce mana gacan fili ya cika, mu kaɗai ake jira, har wasu nata
maganganun wai Salmanu ya ji tsoron Ba'ana ya gudu".
Murmushin da yafi kuka ciwo Arɗo Bani yayi dafa tsakiyar kan Salmanun yayi kana
yace.
"Kuje Salmanu, Allah ya bada sa'a Ubangiji yaga niyarmu na son tseretar da wannan
yarinyar daga fadawa auren wannan mushurkin, taƙadiri in Shatu matarkace Allah ya
baka sa'a in kuwa ba matarka bace, Allah ya baiyono mata wanda zai zame mata
GARKUWA daga faɗawa auren wannan azzalumin".
Amin Amin sukace baki ɗayansu kana su sukayi gaba.
Shi kuwa Arɗo, saida ya jira su Malam Liman Bappa kenan dasu Ahaji Horu, da Ahaji
Umaru da Garbati.
Koda sukazo ba ɓata lokaci suka nufi, farfajiyar wurin da aka tanada dan shaɗi.

Filin ya cika ya batse tako ina mutane zuwa sukeyi arna da musulmai fulani da
hausawa da ƙabulun, Ɓachamawa, domin duk yankin nahiyarsu an san babu taƙadiri sama
da Ba'ana sabida tunda ake gasar Shaɗi da kuma gasar kokuwa yayin nunan sabon gero
ba'a taɓa cin nasara kanshiba, muddin ya shiga gasa tofa shine da nasara.
Har ta kai da in dai ya ɗaga hannun to babu mai ɗagawa.
To sanadinshi aka hana Shaɗi a Rugar Bani, tsawon shekaru biyu sai gashi yau an
dawo dashi.

Wannan dalilin ne yasa gaba ɗaya Rugar Bani ta cika maƙil da mutane maza da mata
manya da yara,
Ga mai busar sarewa kuma yana tsakiyar taro inda akabar filin da za'a gobza yanata
rere kirari wa Ba'ana.

Isowar su Arɗo yasa aka basu hanya har suka iso gaba inda aka tanada musu, kujerun
zama. Na bencin katako.
Daga nan manyan Dattawan duk suka Zazzauna.
Bisa ƙa'idar gasar Shaɗi wanda ya fara cewa yana son yarinya shi zai fara duka, in
wanda yace yana sonta daga baya ya ƙetare bai zubda hawayeba baiyi kukaba, to sai
asa kwanaki sai yaje yayi jinya ya worke daga zabgar da yasha, sai ya dawo ya ɗauki
fansa, to in ya zana wannan yayi kuka shike nan yayi nasara in kuma wannan ma baiyi
kukaba za'a sakeyi har sau uku to nan in babu wanda yayi kuka cikinsu sai yarinya
ta zaɓi wanda takeso, don anada yaƙinin duk wanda ta zaɓa, zai iya kare kanshi
tunda ƙarfinsu yazo ɗaya.

Bayan an gama dai-dai-ta komai, Salmanu ya cire rigarsa kamar yadda ƙa'idar gasar
take, ya rage dagashi sai gajeren wondon.
Shi ma Ba'ana ya cire rigarshi ya zama dagashi sai gajeren modo, irin masu zuwa har
guiwa ɗinnne.

To dole a ƙa'ida Ba'ana ne zai fara duka, amman da yake ya shiryawa abun sai yace,
shi ya amince a fara dashi, kuma shima yau zai rama Ba sai an ware kwanakin zuwa
jinya ba.

Nan kuwa take al'kalin gasa Barmuji yace an amince.


Daga nan aka zaro bulalin shaɗi na cikin tanɗun masarautar Arɗo Yabani wanda an
ƙara tsumasu suma.

A hankali Barmuji ya miƙa wa Salmanu, bulalin,


kana ya ɗaga hannunshi ya dawo dashi ta bayan Ba'ana.
Shi kuwa Ba'ana tsayuwa yayi ƙam tare da ɗan ware sawunshi,
Busar sarewar da mai busan yayine alamun a fara,
Ai kuwa cikin kuzari da jaruma Salmanu ya ɗan ja da baya,
kana ya tattaro ƙarfin shi ga ba daya, ya ɗaga kitsetsten bulalan nan, ya taƙarƙara
ya zabgawa Ba'ana shi a tsikar bayanshi,
Wanda a take taron matasan dake wurin suka kurma ihu mai karaji,
Yayinda shi kuwa Ba'ana, ƙim ya tsaya kamar ba shiba, domin ko idonshi bai ƙebtaba.
Sake taƙarƙarewa Salmanun yayi ya kuma zabga mishi bulalar a inda ya kima mishi na
farin.
Still ihu, taron matasa sukasa, tarin ƙabilar ɓachama kuma dake wurin sai rurrufe
idanunsu sukayi da ƙarfi sabida wai bazasu iya jurar ganin ana zabgar jakadan suba.
Mai irge kuwa da iya ƙarfinshi yake kware baki yana cewa.
"Ɗaya! Biyu! Uku! Huɗu! Biyar! Shida! Bakwai!!!".
Haka yaketa irga duk bulalar da aka kaiwa Ba'ana amman wannan tagadirin mutumin ko
a jikinshi kamar dutse ake zanawa ba shiba.

Ƙa'idar bulalin shaɗi Hamtsine akeyi.


Haka Salmanu yake ware iya ƙarfinsa yana zabgar Ba'ana, yana tsaye ƙiƙama. In
wannan bulalan ya lauye, sai a bashi wani bulalan.
Har akaje arba'in da takwas ko gezau.
Gaba ɗaya hankalin mutanen kirki ya gama tashi, domin sun sadakar da nasara ta
kubcewa, Salmanu.
Shi kuwa Salmanu tattaro sauran ƙarfinshi kab yayi,
ya narka mishi bulala ta 49-50".
Amman shirunshi.
Ihun da kafuran ƙabilar ɓachama suka sakine ya tabbar an gama, nan take suka shigo
filin da gudu ruggumeshi suketayi suna shafa bayanshi, da yayi shati-shati.

Shi kuwa Salmanu gaban Arɗo yaje ya zauna, nan aka basu ruwa sukasha gaba ɗayansu.
Hutun 30 minutes sukayi aka koma fagen fama.

Da ƙarfi mai busan sarewa ya busa alamun a fara,


wani irin kafurin murmushi Ba'ana yayi tare da gyara riƙon da yayiwa bulalar tashi.
Cikin tsananin mugunta ya ɗan koma da baya, kana ya ɗago bubalar da masifan karfi
ya zabgawa Salmanu ita a tsakiyar fatan bayanshi.

Wani irin gan tsarewa Salmanu yayi, sabida wani irin masifeffen azaba mai girgiza
zuciya da yaki yana ratsa dukkan sasasan jikinshi.
Bai gama dawowa daga gigi da azabar bulalar forkoba, yaji ta biyu,
Rumtse idanunshi yayi da azaban ƙarfi, gaba ɗaya inda bulalar ya taɓashe, harbin
kunama yakeji yana ratsashi.
Wani irin numfarfashi yaka lokacin da aka zabga mishi bulala ta goma.

Gaba ɗaya hankalin mutane ya tashi domin kowa yaganshi yasan yana jin azaba.
Bulala ta ashirin da biyar da akayi mishine ya sashi buɗe idanunshi da suka koma
jajazir dan azaban da yakeji.
Su kuwa kafuran nan sai ihun farin ciki sukeyi.
Shi kuwa Barmuji zagayawa yayi gaban Salmanu wai yaga ko idonshi ya kawo ruwa,
babu ruwa kam sai azabar da yakeyi tamkar idanun zasu faɗo ƙasa, ci gaba da irgens
yayi.
"Ashirin da uku! Ashirin da huɗu!!".
Wani irin tsalle Ba'ana ya buga da iya ƙarfinshi ya tsulawa Salmanu bulala ta
ashirin da biyar.
Wani irin duhune ya rufe ganin Salmanu, saiga wasu zafafan hawayen azaba sun
kwaranyo masa, ihu ya kuma zurma jin zafin bulalar ta isa kan mazantakanshi.

Gaba ɗaya su Bappa dama matasan kowa rufe ido yayi sabisa dukan da akewa Salmanu
dukane na son ɗaukan rai.

Aysha kuwa tana gidansu kamar kullum tajiyo ihun Ya Salmanu kamar yadda kullum ihun
wanda ake gasar dasu ke shaida mata sun faɗi.

Cikin kuka konta bisa cinyar Ummey tare da cewa.


"Shike nan Ummey zai kashe ya Salmanu".
Tuni itama Ummey da Inna hawayen suke zubdawa.

A can gidan Arɗo Yabani kuwa inna laure Maman Salmanu, kuka takeyi tamkar zata
shiɗe domin yaranta mata sun zo sun gaya mata halin da yake ciki.
A can wurin gasar Shaɗi kuwa, ganin tuƙuru Ba'ana so yake ya kashe Salmanu ne yasa,
matasan Fulani sukayi kanshi dan dukanshi yake harda tattakashi kuma tuni ya wuce
balali hamsin ɗin ƙa'idar gasar.

Koda matasan Fulani suka shiga dan crton ran Salmanu kawai sai ga ƙabilar
ɓachamawan nan, sun fara zaro makamai sun rufa duk wani ba fulatani da duka da
saran wuƙa.

Lokaci ɗaya wurin ya hargitse gaba ɗaya.


Aka kaure da faɗa saida.

Ganin wurin ya hargitse ne yasa,


Gaini yayi saurin kiran hukuma mafi kusa ya sanar musu.
Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa suka iso.
Hakane yasa duk ƙabilun Ɓachamawa suka gudu.
Allah ya takaita faɗan baiyi nisa ba, a take ɗaya daga cikin police ɗin wanda yake
abokin Salmanu ne ya kwashesu suka tafi asibi.

Bayan garin ya lafa, kowa ya dawo haiyacinsa ne.


Isa ƙanin Salmanu ya tafi asibiti dan jinyar ɗan uwanshi kuma Alhamdulillah da yake
ya samu taimakon gaggawa komai yazo da sauƙi.

Shi kuwa Ba'ana daga nan izayarsa ta ƙaru manufarsa shida ƙabilar ɓachamawa shine.
Su tarwatsa al'ummar fulanin Rugar Bani baki ɗayansu.

Zuwa yanzu kuma ko ƙudane in dai na mijine to bazai sauƙa kan jikin Aysha ba,
sabida asirce, asircen da yakeyi da kuma tsoronshi da akeji.

Aysha kuwa ko zuwa dubo Salmanu ya hanata domin yace muddin taje a bakin ransa.

Yau kwana huɗu da faruwar abun, ya da faruwar abun kuma yau ta kasance jumma'a ne.

Kasan cewar jummace yasa gaba ɗaya makiyayan suka taso kiwo da wuri, sabida son
samun jam'in sallan jumma'a.

Iro ɗaya daga cikin yaran Ahaji Horo, wanda yake yayan Binto da kuma Junaidu.
Kusan shine karshen dawowa kiwo.
ya taso ya taso tarin dabobbin sa a gaba kenan ya haɗu da gungun matasan Ɓachamawa,
har sun wuceshi, sai kuma suka bishi a baya, cikin izaya babban cikinsu yace.
"Kai ɗan fullo nan garin ubankane ko garin ubanmu?".
Cikin jarumtar jinin fulani yace.
"Gari dai da daji namune tunda iyaye da kakannimu sun saya, in kuma kuna maganar
tushen nasabane, to Adanawa Yola dama kewayenta duk namune fulani".
Cikin mugunta ɗaya daga cikinsu ya kai mishi mari da addan dake hannunshi".
Murmushi Isa yayi cikin hausar fulani yace.
"Kada ka sake dukana".
Kusan a tare suka haɗa bakin wajen cewa.
"In mun dakeka sai me?".
A kufule yace.
"Wallahi sai in rama, yawanku ba shine abin tsoro ba".
Ai kafinma ya rufe baki suka haushi da duka,
da sauri ya fara kare kanshi tare da kai musu duka,.
Kamar da wasa su rai shida sun gaza ji da ɗan lenge-lengen saurayi matashi ɗan
Fulani.
Ganin kamar zaici galaba a kansune, yasa, ɗaya daga cikinsu ya dawo baya-baya ya
zaro wukar dake ƙugunshi, da ƙarfi ya dawo kan Isa, ya luma mishi wuƙan a cikinsa
wani irin ƙara isa ya sake, sai dai babu mai jinsa bare ya kawo masa agaji domin.
Dai-dai wannan lokacin duk wani musulmin wannan yankin yana masallacin jumma'a,
Da wannan damar suka samu suka kashe isa,
wanda suka daddatseshi da wuƙa.
Daga nan suka kira Ba'ana a waya, nan take ya kaɗa shanayen yace. "Yauwa aikinku
yayi kyau, yanzu kuyi maza kuyi gaba da shanayen kasar Cameroon, zaku nufa birnin
Yahunde kuna isa bakin boda yarana na kasar zasu amshi shanayen ku kuma sai ku
dawo, kafin nan ma komai ya lafa baza'a zargekuba".
Haka kuwa sukayi, suka kaɗa kan shanu suka fasa daji, suka nufi hanya, shi kuma ya
dawo cikin gari ya wuce ɗakinsa bayan ya bawa uwarsa lbri.

Koda aka taso sallan jumma'a, anyi mmkin ganin isa bai dawoba, shiru-shiru dai har
akayi sallan la'asar babushi, tofa daga nanne hankali ya ƙara tashi.
Cikin kiɗima suka fara shiga daji a duba ko lfy bai dawoba.

Ai kuwa nan maza matasan Fulani suka watse cikin daji,


Bayan sun gama bulayin nemane babushi babu shanunshi, suna cikin zagayawan ne Sale
yayi arba da gawar Isa dake malale cikin jini.
Nan suka ɗauki gawa suka koma cikin gari dashin.

Wannan rana hankali Fulanin Rugar Bani yayi masifar tashi, gaba ɗaya ma sai
ba'amaida hankali kam ɓatan shanunba,
Hankali ya tashi, ɗauki ɗai-ɗai da akeyi musu ya fara hautsuna musu tunanin,
Gashi kisane da babu wanda za'a iya kamawa, koda aka sanarwa hukar cikin Numan sai
suka korasu da case ɗin, sabida a lokacin da suka zo shigar da report babu musulmi
a police cikin officers ɗin shiyasa suka korasu da batun.
Salmanu wanda shine ɗan bokon da kan iya jagorantan lamarinsu, yana gadon asibiti,
bisa ƙarƙashin kulawar abokinshi badon hakaba da tuni Ba'ana ya kasheshi.

Koda fulani suka hatsala kamar kullum haka Arɗo Yabani ya tarasu ya taushi
zuciyarsu, da kuma shawarar, su kai kukanmu ga sarkin Numan ɗin, tunda ya hanasu
samun damar ganin sarkin Nuruddeen Bubayero.

Koda sukaje masarautar Numan ɗinma abin da akayi musu a police station, fiye dashi
akayi musu.

Dole suka dawo suka nade hannun suka kai kukansu ga, Allah, sai dai sun ɗauki
mataken kare kai da kai, bisa shawarar daddatawa cewa kada makiyayan ko manoma su
yarda su rinƙa rabuwa a daji ya zama suje tare su dawo tare da hakane zasu gane mai
ke musu ɗauki ɗai-ɗai ɗin.

Yau la'hadi tunda safe, Aysha keta shirin komawa makaranta. Sabida hutunsu ya ƙare.

Tafiyan safe takeso tayi shiyasa ta gama shirinta da wuri.

gaba ɗaya suna tsakiyar gida Yayunta maza sune zasu rakata bakin hanya.

Haka nan taji bata son tafiya ta barsu, tsoro mai yawa ya rufeta Especially in tayi
tunani da yadda ake kashe makiyayan.

Durƙushe take gaban Bappa yana yi mata masiha mai ratsa jiki da zuciya ya kare
nasihar tashi da cewa.
"Allah ya miki al'barka Shatu, Allah ya kaiki lfy."
cikin sanyin murya tace.
"Amin Amin Bappa ngd matuƙa".
Sai kuma ta kalli Ya Giɗinta da ya zuba mata ido tamkar bai taɓa ganintaba, cikin
sanyin murya yace.
"Yanzu shike nan zaki tafi ki barmu, ki tafi can ke ɗaya ki zama baki da kowa naki
a kusa".
Haka nan kalamanshi ya karyar mata zuciya, sai kuma taji hawaye nason zubo mata.
A hankali tace.
"Ya Giɗi bazan daɗe ba zanzo".
Cikin sanyi Seyo yace.
"Allah yasa ki samemu in kinzo ɗin".
Da karfi ƙrjinta ya bada wani sauti mai karfi, ta buɗi baki zatayi mgna kenan Ya
Lado ya ɗanyi murmushi cikin sanyi yace.
"To Shatu Ni zan tafi inje in kunce dabobbin, bazan samu daman rakakiba, Allah ya
kaiki lfy, ya ƙaddara saduwarmu kan al'khairi, ki yafe".
Kawai sai taji hawaye na zubo mata, cikin dariya ya Gaini yace.
"To kunga kun sata kuka, Shatu ko dai bakya son komawane?".
Cikin rawan murya tace.
"Inaji bana son rabuwa daku".
Murmushi inna tayi tare da cewa.
"Ai kuwa dole ki rabu damu, domin lokaci yazo".
Ummey dai ido ta zuba musu.
Shi kuwa Ya Lado da murmushi a fuskarshi ya fita yana ɗaga mata hannu.
Bappa ne ya ɗanyi murmushi cikin sanyi jiki yace.
"Maza tashi ki tafi, ki gaida Aminiyarki Rafi'a, Seyo Giɗi Gaini ku rakata har
bakin titi".
Da sauri suka miƙa.
Ita kuwa Aysha kamo hannun Junainah tayi wacce tayi kasake tana kallonta cikin
sanyi tace.
"Ƙanwaliya, sai na dawo".
Kai ta gyaɗa mata cikin sanyin da sam ba ɗabi'arta bane a hankali tace.
"Addana, bana son ki tafi".
Shafa kan Junainah tayi, kana ta faɗa jikin Inna, tana zubda hawaye, sake Inna tayi
sannan ta faɗa jikin Ummey, murya can ƙasa Ummey tace.
"Tashi ku tafi, Allah ya sadamu da al'khairi, Shatu".
Da kuka ta fita, ta barsu jiki a mace.

A hankali suke tafiya tafiya, suna hira, kayan lambu da suka cika mata bakko dashi
na hannun Giɗi, jarkan nonon kuma na hannun Seyo, ya Gaini kuma, jakar kayantane a
hannunshi, da kwaryan kwan zabbi, kamar dai yadda suka saba, suna tafe suna, hira
suna gab da bakin hanya.
Ba'ana ya isosu aka ci gaba da tafiyar,
suna isa motar da zata wuce cikin Yola (Ɓadamaya) na isa,
saida suka samata kayanta, kafin, tazo har zata shiga taji Giɗi na riƙe da hannunta
juyowa tayi ta kalleshi cikin murmushi yace.
"Kinsan abinda zamu iya aikatawa a duniya da abinda bazamu iya aikatawaba".
Kai ta gyaɗa mishi alamar eh, murmushi yayi kana yace.
"To ki ƙara yarda zamu zamu zama GARKUWA'nki muddin muna raye."
Murmushi tayi cikin ɗan jin daɗi tasan akan mgmar auren Ba'ana yake nufi.
Ido ta zubawa Ya Seyo shi kuma sai murmushin shi nan yake mata,
Ya Gaini kuwa hawayene ya cika masa ido shiyasa ya juya ya bata baya.
Cikin sanyi Seyo ya matsota kana a hankali yace.
"Ki sanarwa duniya halinda muka ciki in kin samu dama Aysha, ki sanarwa duniya
Fulani ba ƴan ta'adda bane ba ƴan bindiga daɗi bane ba kuma ƴan Garkuwa da mutane
bane, wasu kesa rigar Fulani ke wanzar da ɓarna da wasu ƙalilan na mugayen daji."
Cikin rauni ta zuba mishi ido tana kallon kekyawar fuskarsa, da gyaɗa mishi kai.
Ba'ana ne ya ɗan kalleta tare da miƙo mata damin kuɗi yace.
"Mata zanyi kewarki, amman ba matsala duk ƙarshen mako zan ke zuwa."
Drivern ne ya katse su da cewa ta shigo su tafi, haka yasa ta juya da sauri ta
shiga, yaja suka tafi tana ɗaga musu hannu, suma basu tafiba saida sukaga motar ta
ɓace musu.

Juyawa sukayi suka nufi cikin gari.


Shi kuwa Ba'ana da ido ya rakasu a a baiyane yace.
"Zanga ta yaya zaku zama GARKUWA'nnata, dan na fahimci duk bakwa son aurena da ita,
toko zanyi mgninku."

Su kuwa basuma juyo sun kalleshi ba.

Ita kuwa Aysha tana komawa ta samu, Rafi'a ta dawo ta gyara musu komai na ɗakinsu,
to samun Rafi'a da tayine yasa ta ɗan samu nitsuwa, ranar kam wuni sukayi suna
hira, darema haka sukayi ta hirar yaushe gamo.

A Rugar Bani ( Rugar kikan) kenan nake nufi. kuwa, su Ya Gaini suna komawa suka
tafi kiwo, kamar dai yadda suka saba, sukaje kiwo lfy suka dawo lfy.

Washe gari ranar Litinin!

Saudia.
Sheykh ne konce, bisa wani fitinenne gado yayi lib cikin tattausan blanket,
bacci yakeji yasa gaba ɗaya jikinsa yayi lakwas sabida jiya a harami ya kwana
ɗawafi, shiyasa yana dawowa ya konta. Yanayin wayarrshi na bada ɗan sassanyan
sautin,
wani irin ɗan gajeren tsaki yaja, ba tare daya buɗe idanunshiba ya miƙa hannun kan
bedside drower'n glass dake kusa dashi, lalubo wayar, yayi tare da ɗan liƙa
yatsarsa kan gilashin wayar ya amsa kiran, kana ya ɗauwara wayar bisa kunnenshi a
hankali cikin muryar bacci yace.
"Assalamu alaikum, Umaymah".
Murmushi Umaymah tayi cikin son ɗan yar uwartata tace.
"Na'am Jazlaan ya akayi".
Cikin murya baccin ya kuma gyara konciya tare da cewa.
"Umaymah baki amsa sallamar ba".
Da sauri tace.
"Afwan Jazlaan, Wa alaikassalam".
shiru yayi.
ita kuwa murmushi tayi tare da cewa.
"Naji kamar bacci kakeyi ko?".
Murya can ƙasa yace.
"Uhummmm".
Da sauri tace.
"To yi baccin sai ka tashi muyi mgna nasan a harami ka kwana".
Da sauri yace.
"No Umaymah gaya min menene?".
Dan shi a zatonshi ko akan Ya Jafar ɗinshi ne.
Ita kuwa Umaymah cikin hikima tace.
"Uhum dama batun Jazrah ne".
Fuska ya kwaɓe kamar yana gabanta cikin nuna ko in kula yace.
"Menene kuma hakan? Umaymah".
Kai ta jinjina dan tasan a rina, cikin tsare gida tace.
"Ina nufin Jazrah ƴar Ƴayan Sitti Uncle ɗinmu Aliyu".
Numfashin ya ɗan fidda cikin ƙosawa da zancen yace.
"Ni ban santaba. Umaymah zanyi bacci, kaina ciwo.
Kin yarda in katse kiran Please Umaymah kada kicemin a a dan Allah".
Murmushi tayi wato duk yadda mutun ke zaton Sheykh ya wuce tunanin mai tunani a
hankali tace.
"Kashe, Allah ya muku al'barka".
Da sauri yace Amin Amin kana ya katse kiran,
hannu yasa ya cusa wayan ƙasan pillow'nshi.
Kana ya gyara konciyarshi afili yace.
"Ni ina zan kai mace? Toma me zanyi da mace a rayuwata.
Zakuna damuna da wata Jazrah mai koɗeɗden fuska".
Daga nan ya lumshe ido yaci gaba da baccinsa.
Haroo dake bakin kofar shigowane yayi dariya kana yace.
"Uhum zaka san me zakayi da ita ai Ustadz ai ba'a gane maci tuwo sai miya ta ƙare,
dama kirarinku ustazu ƙalilan iya shege kasiran, wai me zanyi da mace, hmmm
miskilanciba ba".
Daga nan ya koma da baya dan dama Sitti ce ta aikoshi ya kira mata Sheykh ɗin, akan
yazo yaci abinci kafin yayi baccin wai.
Koda ya koma sanarwa Sitti cewa yama rigada yayi baccin sai suka zauna na nan
sukaci gaba da hiransu...

A nan gida Nigeria kuwa cikin Rugar Kikan.


Tunda safe duk makiyayan garin suka tafi kiwonsu.

Sosai suka shiga irin tsakiyar tsaunuka, wasu na nan wasu na can suna dai hango
juna da, sabida abu na kiwo bazai yiwu su zauna wuri ɗaya ba, dama sai in zasu
komane suke haɗuwa baki ɗayansu.

Misalin karfe uku da rabi na yamma, duk kowa ya fara ɗan zagawa cikin kwazozzobon
dake gefensu da. Yin ɗaharan yin al'wala.

Ya Gaini ne ya fara gangarawa cikin korin babu sanda bare wuƙa a jikinshi. Ko buta
babu a hannunshi Don akwai ruwa a cikin kwarin dashi suke al'wala, a hankali ya
tsuguna yayi buƙatarsa kana.
Ya dawo wurinda suke al'wala ya tsugana yayi al'wala.
A hankali ya yunƙura ya tashi.
Ɗago kanshi da zaiyi yayi dai-dai da.....!

By
*GARKUWAR FULANI*

Wasa farin girki, yanzu ake nutsawa ciki.

Da yawa naga basu fahimci banbancin. Garinsu Parvina da kuma Rugar Bani ba. To ku
saurara, Rugar Arɗo Babayo, itace Rugarsu Parvina, kuma a can ƙasar Cameroon yanki
Yahunde Rugar take.

Sai kuma ɗaya rugar wacce a nan ƙasarmu Nigeria take yankin Adamawa state, wani
dalili yasa na sakaya sunayen garuruwa da ƙasar tamu da masarautun. Amman nasan duk
mazauna Nigeria Adamawa zasu gane Rugar Kikan nake nufi nasa Rugar Bani Numan nake
nufi nasa Shikan, dama duk sauran jihohinmu na sakaya sunayensu sabida wani dalili
Amman nasan duk munsan inda tushen ƙabilar ɓachama suke.
Amman ba mmki in medasu yadda zakufi ganewa.
Ba wata ƙasa bace Kautal Nigeria nake nufi🤝🏻🥰

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🦚🐍
🐍🤴🏻💘
🤴 🏻 💘

*GARKUWA*
PAGE 11

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🕊️🌈🦚🐍
🐍🤴🏻💘
🤴 🏻 💘

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta layin nan
09097853276 domin KARANTASHI daki-daki, ko kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na
Jaiz 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, kana sai kiyi screenshort na shaidar
biyanki ki turo min ta WhatsApp number ta 09097853276. Special Group ne 1k cikin
mako biyu za'a gaba wani sashi na littafin.

Ido ya zubawa mutanen da yayi arba dasu, dai-dai lokacin daya.


Ɗago kanshi, yayi arba, da wasu mutanen, da shigar hukuma (police), da sauri ya
miƙe tsaye yana ware hannun rigarshi da ya naɗe dan yin al'wala, tare da cewa.
"Lfy? Ku su wayene?."
Basu kulashiba, sukayi kanshi gadan-gadan, cikin dakiya yace.
"Me hakan?". Still no respond.
Sai matsoshi da suƙa ƙarayi, cikin dakiya da jarumtar jinin fulani ya gyara
tsayuwarshi, yana binsu da ido ganin zagayashi da suka farayi, da ido yake binsu a
zatonsa faɗane shiyasa bai guduba, domin, duk da yawansu bai Karaye ba, dan zuciyar
gskya ce dashi kana jinin fulani ke yawo a jikinshi.
Su kuwa mutanen, na gabanshi ne ya ɗan fesa mishi wani abu mai kamar turare a
fuskarshi.
Da sauri yasa hannunshin wai zai kare fuskarshi, cikin dakiya da haɗe fuska ya buɗe
baki yace.
"Me kuka fesa meeeen."
Sai kuma kawai yayi lu ya lumshe idonshi ya faɗi nan kamar gawa.

Da sauri biyu daga cikinsu suka ɗaukeshi tsallaka korin sukayi sukaje suka ajiyesu
cikin motorsu dake can bayan lampon dake bayan korin.

So biyun kuma komawa mafakarsu sukayi.

A can wurin kiwon kuwa, Seyo ne ya ɗan kalli Giɗi tare da cewa,
"Bari in shiga muyi al'walan,in mun fito, sai kai da ya Lado ku shiga mu kuma mu
tsare dabobbin namu gudun kada su shiga gonakin manoma."
Kai Giɗi ya gyaɗa mishi daga, nan ya gangara ya shiga cikin korin.

Yadda sukayi Ya Gaini haka sukayi mishi, shima.

Giɗi da Ya Lado sunata jira, shiru-shiru ba motsinsu,


ganin hakane yasa, Giɗi ya fara kiransu.
"Ya Seyo!, ku fito mana, Lokacin sallafa na tafiya".
Lado ne ya kalleshi cikin sanyi jiki yace.
"Shiga ka kirawosu".
To yace kana ya juya ya nufi cikin korin,
har yaje inda zai gangara ya shiga sai kuma ya juyo ya kalli Ya Lado cikin sanyi
yace.
"Ya Lado ka kula da dabobbin nan fa kada su cutar da manoma kaga kai ɗaya ka rage
mai kula dasu, kada ka bari suyi nesa dakai".
Lumshe ido Ya Lado yayi cikin wata sassanyan murya mai cike da rauni yace.
"Zaku dawo ai, kuɗin sai ku kula dasu da kyau in yaso ni sai in tafi".
Kai ya gyaɗa tare da yiwa yayan nashi murmushi ya shige cikin korin.

Yana shiga ya fara dube-dube babusu babu dalilinsu, cikin ciyawa da kozozzaban ya
fara leƙawa yana cewa.
"Ya Gaini! Ya Seyo!! Ya Gaini!!!".
Jin shiru babu amsarsu bare motsinsune ya sashi ci gaba da waige-waige tare da
cewa.
"Ya Gaini ina kukene? Yaya Seyo, ina kuke ban gankuba, kuyi mgna mana".
Cikin fargaba yake lelleƙa wuraren, da yake ganin mutun zai iya fakewa a wurin.
Yana sunkuyowa cikin wani sunkurun kawai sai ya koma luuu ya faɗa ta baya sabida
abinda suka fesa mishin yasashi bacci.

Daga nan suka ɗaukeshi sukaje suka sashi cikin motar da suka saka sauran yayunshi.

Da suke konce kamar gawarwaki.

Tsaye suke jikin motar, yayinda biyu daga ciki dakeda uniform ɗin police officers,
kuma suna cikin motar da itama ta police ɗinne.

Ɗaya daga cikin mutun huɗu dake gaban motarne, yasa hannu ya rufe ƙofar, sannn ɗaya
kuma ya kira waya, cikin yaren Ɓachamanci yace.
"Mun sace mutun biyar, uku yaran gidan Malam Liman ne, biyu daga ciki yaran gidan
Ahaji Horo ne".
Ɗan jim yayi alamun karɓar umarni.
Tsawon daƙiƙu biyar sannan ya ƙatse kiran kana ya juyo ya kalli, sauran tare da
cewa.
"Yace ku, ku tafi dasu a cikin motar, ku wuce dasu,inda kuka shirya, mu kuma yace
mu ɗan tsaya nan, yanzu zaiyiwa shanun Rugar Malam Liman kiranye da dogon fito.
To in shanun suka nufi inda yake ba mamaki wasu su biyo shanun daga cikin
makiyayan, to yace idan sun biyosu mu kashesu!".
Kusan a tare suka sara mishi tare da busa sigarin dake hannunsu.
Nan mutanen cikin motar sukaja, suka tafi.

Su kuma saura mutun huɗun, komawa mafakarsu sukayi.

Can cikin tsunƙurun dajin kuwa.


Ba'ana ne zaune cikin taron matasan ƙabilar ɓachama da a ƙalla sun kai goma, cikin
kausasa murya da bada umarni yace.
"Zanyi fito ɗaya zuwa uku, cikin daƙiƙu 10 shanayen Malam Liman da Alhaji Haro da
wasu. Zasu baiyana, a nan.
Suna zuwa ku jasu ku fuskanci gabas, ta ƙasar Jihar Gombe zaku ratsa, kana ku nufi
ƙasar chadi daga can."
Shiru ya ɗanyi tare da zuba musu idanu, wani irin azzalumi murmushi yayi cikin
barbarci ya kalli biyu dake kusa dashi wanda ƴan ƙanwar Bukar ne su barebari ne,
cikin izaya yace.
"Kada ku kauda ido akan ko wacce gonar makiyayin da zaku wuce ta gabanshi, ku shiga
gonakin manoma, kuyi kiwo a ciki.
Idan manoman suna cikin gonakin in sun muku mgna ku kashesu, sannan ku gudu da
dabbobin yankin wurin".
Cikin barbarci ɗaya daga cikin su yace.
"Ba'ana, tsayuwa kiwon bazai ja mana tsaikoba, har cekiyar ya riskemu ba tare da
munyi nisa ba".
Murmushi yayi mai cike da fajirci sumar kanshi ya shafa tare da cewa.
"Ba'akana Ku kiwaci duk gonakin manoma, hakanne zai jawo faɗa tsakanin MAKIYAYA da
manoman, daga haka saiku gudu, kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, domin su
mutanen duniya sun ɗauka duk wanda suka gani da dabobbi yana kiwo, BAFULATANI NE,
sam mutane sun kasa ganewa cewa ba sai Fulani kaɗai ke kiwoba, kaga mun tada faɗa
mun kwashi dabobbinsu, mun kashesu mun gudu, kuma in sunje kai korafinsu ga hukuma
a kamasu ko a korasu ko azagesu, ace suke haddasa faɗa tsakaninsu da manoma, sun
zama ƴan ta'adda a idon duniya. Mun kwashe dukiyoyinsu".
Dariya sukayi baki ɗayansu, kana suka sara mishi, juyawa yayi, ya fuskanci gabas
kana ya durƙusa, ya zuba guiwowinsa duka biyu a ƙasa, yatsarsa manuniya ta hannun
hagu ya kafa a ƙasa, kana yatsarsa ta hannun dama kuma, ya toshe kunnenshi na dama,
da ƙarfi ya rufe idanunshi kana, ya tsuke bakinsa ya rinƙa zuro iskar wata zazzafar
fito mai bala'in sauti.
Su kuwa sauran duk rufe ido sukayi dan jin fiton sukeyi tamkar zai fasa musu dodon
kunne.

Shi kuwa Ya Lado yana cikin kiwonshi kawai yaga gaba ɗaya, shanun sun juya sun
fuskanci gabas, kana sun ɗaɗɗaga kunnuwansu sama, daga baya kuwa sunata karkaɗa
binɗinsu.
Cikin mamaki yake ratso tsakiyarsu.
Dan in makiyayi yaga dabbobi suna haka yasan akwai abun da suka gani, ko mutun ko
iska, ko maciji ko dai wani abu na daban to sukanyi wannan alamar dan sanar da
makiyayinsu.
So ganin hakane yasa Lado ya ƙara kutso kai cikinsu.

Su kuwa dabbobin gaba ɗaya fiton da Ba'ana yake hurawane ya cika musu kunne, ai fa
a take suka nausa a guje suka fuskanci gabas, da wani irin masifeffen gudu.
Shanu da dawakai na gaba tumaki da awaki na baya hatta belbelun dake cikinsu, suna
kiwo binsu sukayi.
Cikin ƙarfi Ya Lado yayi wani irin ihun wanda dashi suke kiran dabbobinsu, amman
ina basu juyoba.

Da gudu ya fara binsu kana yana ihun neman taimako a wurin sauran makiyayan su.

Amman da yake gudun dabba dana mutun ba ɗaya ba,


Sun mishi nisa mai tarin yawa, hakanan shi kuma yayiwa sauran makiyayan dake
biyoshi a guje su kawomishi agaji ya musu nisa.
A haka suka rinƙa gudu,
waɗannan mutun huɗun dake laɓene suka fito suka, tareshi ba zato ba tsammani kawai
yaji an burma mishi wuƙa juyowan da zaiyi kuma yaji an kuma burma mishi wuƙaƙe a
tako ina na jikinsa.
A nan take ya faɗi babu rai.

Su kuwa nan sukabi shanun da gudu.

Koda sauran makiyayan suka iso inda gawar Ya Lado take.


Hankalinsu yayi masifar tashi.
Tabbas sun san babu masuyi musu wannan aikin sai ɓachama.
Ko hanƙo kurar dabbobin basayi.
Hankalinsu yayi mummunan tashi ganin gawar Lado, ga kuma tashin hankali da firgici
rashin ganin su Gaini da Giɗi da Seyo Manunu da Sale.
Junaidu ne yayi sauri ya kira mahaifinsu Ahaji Horo a waya ya sanar mishi halin da
ake ciki.

Wannan mummunan labari yayi matukar firgita al'ummar Rugar Bani hankalin kowa ya
tashi.

Hankali Bappa kuwa in yayi dubu to ya tashi,


kuka cur-cur yakeyi da idanunshi.

Junainah kam kuka da ihu harda burbuwa takeyi tana cewa.


"Wayyo Ya Lado, Bappa ku nemo min Ya Gaini na da ya Seyo".
Sai ta kuma faɗa jikin Ummey daketa kuka tamkar ranta zai fita,
cikin kukan take cewa.
"Ummey kicewa Bappa suje su nemo min Ya Giɗi na, kada su bari a kasheshi kamar
yadda aka kashe Ya Hashimu da Ya Isa, da kuma Yaya Lado".
Babu mai iya bata amsa a cikin wannan gida.
Duk da tarin maƙota da suka cika gidan.
suna zagaye da Inna wacce, take sume tunda taji yaranta Rai uku babusu babu
dalilinsu su ko gawarsu ba'a ganiba ga kuma mutuwar Lado wanda shine yasata,
sumewa.
Faɗin tashin hankali da mutanen Rugar Kikan ke ciki bazai taɓa misaltuwa ba.
Saidai ƙunane wanda duk mai imani zai iya ƙiyastashi a ranshi.

A cikin garin kuwa tuni Arɗo Yabani yasa anyi shela anyi taron gaggawa, kowa ya
shirya za'a shiga daji neman su Gaini, ko Allah zaisa a samosu.

Haka matasa kusufa-kusufa suka rinƙa kusa kai cikin daji suna ratsa tsaununka da
kozozzabai.

Bappa kuwa da Arɗo Yabani da Ahaji Haro, da Ahaji Umaru ne da sauran dattawan
rugarsu dana kewaye, gawar Lado suka ɗauko suka dawo gida da ita da sauran
shanayensu gaba ɗaya matasa kuma suka bazama nemansu Gaini.

Su kuwa sauran matasa majiya karfi daji suka rinƙa ratsawa.


Amman babu koda kurar dabbobin nan, bare alamun su Gaini illa iyaka dai takalmansu
da suka tsinto.

A Rugar Bani kuwa, hankali na matukar tashe, Bappa ya tasa gawar Lado a gaba wacce
sunyi mata wonka sun kimtsata cikin sutura kamar yadda shariya ta tanadar.
Kuka mai tsananin cin raine ya kwabcewa Bappa, yana ruggume da gawar.
Inna ma da yanzu ta farfaɗo da kukan ta farfaɗo, kuka takeyi tamkar ranta zai bar
gangan jikinta.
Hakama sauran matan maƙota.
Hiden da Binto ma kuka sukeyi sosai a gidajensu sabida ɓacewar samarin su.

Dattawan ne sukayi ta bawa Bappa haƙuri da tausan zuciyarshi.


Ganin dare yayine yasa akace dole a bar gawar tayi kwanan keso.

Su Sule, Iro, Ado, Junaidu, Madu, Ari, Sani, Ibi, ja'eh, Ori, Binbi, dama sauran
samari majiya karfi kuma kab sun cikin daji.

Haka suka kwana a can. Suna tafiya suna nema, kafin gari ya waye, wasu sun isa har
jihar taraba, wasu Gombe, wasu har bauchi, wasu har cikin iware da mutun biyu na
taraba,
Wasu sun nausa da nisa, sabida in dai tafiyace bata taɓa bawa bafulatani tsoroba
domin anyi ittifaƙin duk ƙabilun duniya babu ƙabilar da takai ƙabilar fulani saurin
tafiya da jumurin doguwar tafiyar ƙafaba, bayan laraban da.

Washe gari Litinin.


ɗin, sauran dattawan garin suka sallaci Ya Lado, kana suka zauna amsar gaisuwa.
Suna kuma jin labarin inda yaransuke.
Ganin sunata wahalar tafiya ba lbrine yasa.
Bappa yace su dowo. Domin wanna abu addu'ace mgninshi.
Sannan kuma wannan karon bazasu saurari masarautar Numan ba , gangami zasuyi su kai
kukansu, ga masarautar Joɗa, wanda a cikinta ne GARKUWAN FULANIN ƙasar Nigeria gaba
ɗaya yake.
Da fari Arɗo Yabani bai gamsu da hakanba saida Bappa yayi mishi bayanin.
Dolefa suna da buƙatar hukama mai tsarki ta shiga tsakaninsu da ƙabilun Ɓachamawa
nan, kana dole mgnar ta isa ga babbar masarautarsu, wacce za'a miƙa mgnar ga
Ƙungiyar *TABITAL POOLAKU, DA KUMA ƘUNGIYAR.*
*MIYETTI ALLAHA*
Wannan dalilin ne yasa Ardo Yabani ya umarci gaba ɗaya matasan da suka bazama neman
su Gaini su juyo su dawo gida.
Haka kuwa akayi kafin yamma sai gasu duk sun daddawo domin.
Wasu da yawa motoci suka shigo.

Bayan sallan ishane suka zauna zaman mitin domin sun gama shirya komai gobe dai kai
tsaye masarautar Joɗa zasu wuce.

Bayan sun gama tattauna yadda abun yake suka tsaida zance kan cewa dattawansune
zasuje.
Daga nan Duk suka tashi taron kowa ya koma gidanshi da tarin al'hini a zuƙatansu.

A can cikin birnin Ɓadamaya kuwa cikin makarantar su Aysha.

Zaune take bisa salla hannunta riƙe da carbi tana ja.


Kana hannunta ɗaya kuma rike da wayarta, wacce taketa kiran yayunta kab baya shiga
tun jiya da yamma.
Cikin kula Rafi'a ta kalleta a hankali tace.
"Aysha ba komaifa, kinsan garin naku kunada matsalar Network, wasu lokutan kuma
kinsan basu da cajine".
Kanta ta jingina da jikin gini, murya can ƙasa tace.
"Gaba ɗaya fa, woyoyinsu basa, shiga, na maƙotanmu kuma ko sun shiga basa ɗagawa,
Rafi'a hankalina ya tashi."
Da sauri Rafi'a tace.
"No kada ki damu tunda kikaga basa ɗagawa alamun kenan woyoyinsu na wurin cajine
ko?".
Idonta ta lumshe tare da cewa.
"Zuciyata na yawan sinkewa Rafi'a, fargaba nakeji".
Cikin sanyi Rafi'a tace.
"Yauwa to ki kira Ba'ana mana".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Eh hakane fa".
Ta karishe mgnar tana dannawa wayarshi kira.
Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga,
Da sauri tace mishi.
"Ina wuni ya Ba'ana".
Ba'ana dake zaune tsakiyar ƙabilun Ɓachamawa suna mitin yadda zasu farma garin
Rugar Bani da yaƙin sunƙuru gobe, murmushi yayi cikin sonta yace.
"Lfy lau Mata, ya karatu?".
Alhamdulillah tace tare da cewa.
"Ya Ba'ana ya garinmu ya lbrin gidanmu duk suna lfy?".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Duk suna lfy garinmu duk anata kewarki ɗazuma na wuce ya Ladonkin a kwance yanata
shan baccinsa babu ruwanshi da damuwar duniya".
sam bata kawo komai a rantaba kan mgnarshi ta ƙarshe, saima sanyi da ta ɗanji daya
bata tabbacin, suna lfy, sabida iya tsawon zamanta da Ba'ana bai taɓa yi mata
ƙaryaba, koda zaiyiwa duk mutanen duniya ƙarya to ita baya mata ƙarya, kuma duk
zafin gskyar mugun abunda yakeyi zai gaya mata. Abu biyu ya ɓoye mata a rayuwarshi
sata da kisan da yakeyi, sai dai yana gaya mata in dai a kantane zai iya kashe kowa
ma.
So cikin sanyi tace.
"To yasu Ya Gaini kuma".
Murmushin mugunta yayi tare da cewa.
"Shima na wuceshi wurin Binto sunata hirarsu har tanata raira masa waƙoƙin
soyayya".
Murmushi ta ɗanyi tare da cewa.
"To ka gaida min su bari in ɗanyi wonka".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To Mata kiyi wonkanki anjima zan kiraki muyi hira".
To tace mishi kana ta katse kira, tare da cewa Rafi'a.
"Alhamdulillah duk lfyarsu lau ashe".
Itama Rafi'a murmushi tayi kana sukaci gaba da hirarsu sai dai still fa tsoro da
fargaba da bugawar da zuciyar Aysha keyi bai bariba, ganin hakane yasa Rafi'a,
kallonta kasancewar Rafi'a ƙwararriyar mai koyar da girgirkene, a zahiri cikin
makarantar tasu, da kuma social media. Cikin kula da son samawa aminiyar tata
nitsuwa tace.
"Yauwa GARKUWA, zomu shiga kitchin, muyi ɗan alalan kwai, naga kin kawo mana koyaye
da yawa."
Murmushi Aysha tayi wace, akefi kiranta da ƙarshen sunanta.
hannun ta miƙa Rafi'a, cikin sanyi tace.
"Help me my friend, jikina yayi sanyi da yawa, ji nake kamar bazan iya tashiba".
haka nan itama Rafi'a jikinta ya fara sanyi, sai dai sanin in ta baiyana kasalarta
tashin hankali Aysha zaifi tsananta ne yasa ta dake, cikin sauri ta kamo hannunta
ta jata-ta miƙa kana suka shiga kitchin ɗin.
Nan suka fara aikin sunayi tana ɗan janta da hira.
a haka dai har suka gama, kana, ta shiga wonka.

Shi kuwa Ba'ana maida woyarshi yayi cikin al'jihunsa, kana ya kalli Sarkin mayaƙan
ƙabilar ɓachama da yake ce mishi.
"Shege Ba'ana wato, yana bacci cikin kabarinsa babu ruwansa da damuwar duniya".
Dariyar mugunta sukayi dukansu,
wanda yake gefenshi ne ya kece da wata dariyar tare da cewa.
"Wai ita kuma Binto kukan natane waƙen SOYAYYA ko?".
Kanshi ya gyaɗa musu cikin muguwar fuskarshi.
Wannan matashin ɗaya fara sokawa Ya Lado wuƙane lokacin da suka kasheshi. yace.
"Ita kuma da yake sokuwace har ta yarda k...".

Wani irin tashi sukayi gaba ɗayansu sabida wani irin shaƙa da naushi da Ba'ana ya
kai mishi, wanda a take ya fara kakarin mutuwa.
cikin zafin rai ya hankaɗa tarin mutanen dake son cotan yaron daya shaƙe ɗin amman
ina sun kasa, wata zabgegiyar wuƙa ya lumtsumamishi a ciki wanda yasa sauran duk
suka watse tura gawarshi yayi gaban su cikin ɗaga murya yace.
"Ina kashe wanda ya yabi Shatuma yace yana son Shatuma bare wanda ya zageta, duk
wanda baya son ransa ya aibata min Shatu a gabana ya gani".
Cit kake jinsu sabida masifar tsoronshi sukeji.
Dan ya fisu taƙadiranci dan Ba'ana mugun babarbarene mai baƙar zuciya.

Haka dai aka tashi wannan taron da yake dama sun gama tattauna yadda zasuyi
farmakin.

Washe gari ranar wata Tuesday 21 November 2017 itace ranar da har abada al'ummar
Rugar Bani bazasu mance da itaba a tarihin rayuwarsu, itace ranar da duk motsin da
numfarfashi Shatu zatayi sai ta tunashi ranace data girgiza, zukatan al'ummar
musulmai, ranace da tasa duk wani bafulatani makiyayi jin ƙuna da tafasar zuciya.
Ranace da tada hankalin al'ummar ƙasarmu nan dama maƙotanmu.

Tunda safiyar ranar, dattawan garin suka gama shirinsu cikin shigarsu ta al'farma,
Malam Liman (Bappa) Arɗo bani Jauronsu, Ahaji Horo da Ahaji Umaru, kana Malam Yero,
da kuma Alhaji Sa'idu.
su rai takwas dai suka shirya cikin kamala da mutunci. Junaidu ne yake cikin Shikan
ya samo musu mota kirar siyana wacce suka ɗauki shatarta, domin zai kaisu har cikin
fadar masarautar Joɗa kuma zai jirasu. Su dawo tare.
Nan suka shiga Mota gaba ɗayansu, suka tafi.

Kai tsaye har bakin masarautar suka tsaya dan an hanasu shiga,
sai da ɗaya daga cikin hadiman dake tsaron ƙofar, yaga duk manyan daddatawa ne yasa
yaje ya samesu bayan sun gaisane sukayi mishi bayanin abinda ke tafe dasu.
Jin abin babbane yasa yaje yayiwa sarkin ƙofa bayanin.
Nan shima yaje suka gaisa suka ƙara jaddada mishi, zancen abinda ke tafe dasu,
sannan
sukayi musu izini suka shigo cikin asalin farfajiyar mashigar masarautar.
Kan kujerun dake jere a wurin suka nuna musu su zauna.
Bayan sun zaunane sarkin kofa yaje, wurin sarkin fada ya sanar mishi, to nan sarkin
fada ke cewa.
"To ai babu abinda zamu iya musu, tunda shi GARKUWAN FULANI, baya ƙasar waye zai
saurari kukansu, suje sai ya dawo su sake zuwa".
Cikin rauni sarkin ƙofa yace.
"Ranka ya daɗe sarkin fada, da dai an nema musu izinin ganin mai martaba, domin
bazaiji daɗi ba in yaji sunzo kuma an medasu".
Cikin isa da izaya sarkin fada yace.
"A kul sarkin ƙofa ka tsaya iya matsayinka, kaje kace suyi maza su bar nan domin
GARKUWANSU baya nan".
Cikin sanyi da mutuwar jiki sarkin ƙofa ya juya ya fita, koda yaje ya sanar musu,
abinda sarkin fada ya faɗa hankalinsu yayi masifar tashi.
Cikin tashin hankali Arɗo Yabani yace.
"Shikenan danmu fulanine makiyaya mazauna daji, sai ya zama matsalarmu ba abar
dubawa bace, wa al'ummar birane, duk inda muka kai kukanmu sai a koramu".
Cikin sanyi sarkin ƙofa yace.
"Kuyi haƙuri ba korarku akayiba, in sha Allah za'abi kadunku, wlh shi kanshi mai
martaba in zaiji abinda sarkin fada yayi to zai barranta dashi, kuma haka nan shima
GARKUWAN FULANI in da zaiji abinda sarkin fada yayi wallahi zai haɗu da fushinsa
mai tsauri, domin shi zuciyar Sheykh zuciyace mai cike da imani da tausayi".
Cikin rauni Alhaji Haron yace.
"Ana binmu ana kashemu, ana sace yaranmu ana kora dabbobinmu.
Munje Police station an koramu, da mukaƙi tafiya suka watsa mata tiyagas, muje
masarautar Numan akaci mana zarafi, sannan yanzu mun gudo gareku da yaƙinin zakubi
kadunmu sannan kuma zaku koramu, so kuke mu ɗauki makami domin ramuwa ne?".
Da sauri suka juyo gaba ɗayansu jin muryar Jamil da yanzu ya iso wurin da
hadimanshi, cikin sanyi yace.
"A a Baba kada ku ɗauki makami domin ramuwa zuwanku nan shine babban abinda ya
dace".
Cikin jin daɗi suke kallonsa, murmushi sarkin ƙofa da sauran hadiman sukayi dan sun
san yanzu dai sarkin fada bai isa ya hanasu ganin Maimartaba. Domin yanzu bai fito
fada bama tukun so zasu ganshi a kebantaccen wuri na musamman.
Cikin kulawa da sakin fuska Jamil yace.
"Baba ku biyoni".
Cikin jin daɗi sukace mishi to, kana suka bishi a baya.
Ta gaban shashin Sarkin fada suka shiga, kai tsaye har cikin fada ya shiga dasu,
shida kanshi yasa hadimai suka kawo musu ruwa.
Sannan a nitse yace.
"Baba ku zauna a nan zanje in sanarwa mai martaba, duk sanda ya fito daku zai fara,
tattaunawa
In da masu buƙatan zagawa gacan wancan kusurwar in kumbi cikinta zata sadaku da
bayi".
Cikin jin daɗi sukace.
"Mun gode yaro Allah yayi maka al'barka".
Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita.
su kuma sukaci gaba da zaman jiran fitowan sarki.
A can kasa mai tsarki kuma,
Sheykh ne zaune a gaban Sitti, kana Haroon da Jannart na gefenshi Sheykh Aliyu
Abdulkareem, kuma da Sheykh Jabeer Aliyu da wasu manyan malamai na zuriyar tasu duk
suna zaune a cikin falon.
Jazrah kuma na gabanshi da wani tray mai masifar kyau da tsada.
Madara da zuma take zuba mishi a cikin wasu ƴan kananun kofuna masu masifar kyau da
ɗaukan hankali.

Wannan ya kasance al'adarsuce ta baiyana nuna yarda da soyayya ko akasinshi, indan


ana son a haɗa yara aure, to za'a tattauna tsakanin manya, bayan sun gama dai-dai-
ta magana tsakaninsu kamar yadda yanzu su Mai alfarma Jalaluddin da Sarki
Nuruddeen, da kuma su Sheykh Jabeer Aliyu da babban babansu Sheykh Aliyu
Abdulkareem da kuma Sitti suka gama haɗa zancen auren Jazrah da Sheykh Jabeer, to
yanzu ta zuba mishi madara da zuma a gaban kowa, ta ajiye mishi, idan ya ɗauki
kofin madara to yana nufin yana sonta ya kuma amince da ita da aurenta.
In kuma ya ɗauki kofin zuma, to yana nufin ya tsaneta baya kuma sonta bazai kuma
auretaba bare ya zauna da ita.
Za'ayi komai a gaban manya ne, don suga zahiri kuma a tsarin ko ɗan uwanka zai iya
yi maka zaɓin da kuma in dai am zaɓa maka sai ka aura.

Shiru sukayi baki ɗayansu falon, kowa da tunanin da yakeyi.

Sheykh Jabeer dake zaune a tsakiyarsu cikin shiga ta al'farma sai sheƙi al'kyabbar
sa keyi, ga tattausan hirami a kanshi, ido ya lumshe daya gane manufarsu.
"Domin shi basu gaya mishi cewa, zasuyi wannan abun bane daya sani wallahi da yasan
duk yadda zaiyi ya gudu, ya tafi harami, har sai sun gaji sun watse.
A hankali ya kalli Sitti dake kallonshi cikin rauni da alamun.
"Dan Allah kada kace, a a yar ɗan uwanane, kada ka bamu kunya nida kakanninka maza
yar uwarkace kasan tarbiyarta".
Kauda idonshi yayi daga kallon Sitti, wani irin kallo yayiwa Haroon daketa yi
mishi, murmushin muguntan yau dai an titseka baka da hanyar tsira.
Cikin ranshi yake mgnar zuciya.
"Ta yaya zan amince ince zan aureta? Dame zan zauna da ita?".
Sai kuma ya ɗan fidda nannauyan numfashi.
"To idan ban amince da aurentaba me zamcewa, waɗanannan bayin Allah'n da sukayi min
dukkan gatan duniya, na zauna a gidansu tsawon shekaru masu yawa nayi karatuna har
na gama, sukemin komai na rayuwa, suna nuna min soyayyar da mahaifinama baya nuna
min, da wanne idon zan kallesu inna ɗauki zuma alamar na tsani yarsu?".
A hankali ya buɗe idonsa, jin muryar. Sheykh Aliyu Abdulkareem kakan Mamanshi
kenan, baban kakarshi Sitti dottijon daya yake sonshi tamkar ranshi yana cewa.
"Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, kayi zaɓin da ranka keso, bamu
da nufin yi maka dole, sai dai ina da burin aurar maka jikata Jazrah ɗiyar mai
sunanka. Ina so da fatan ganin nasabarka ta cika, cikar nasabarka kuwa, shene
aure."
Wani irin sassanyan numfashi ya shaƙa a hankali, wasu irin zafafan tunanuka ne ke
zirya a zuciyarshi".
Cikin harshen hausar katsinawa, Haroon yayi mgna can ƙasa yadda ko Sitti bazata
jisuba.
"Sheykh kafa, shanyamu, nifa zan ɗaukar maka Madara".
Ido ya lumshe tare da ɗan jingina da jikin kujerar da yake zaune, wanda yake kusa
da Sheykh Abdulkareem.
Sitti ce ta ɗan kalli Haroon tare da mishi alamun ya taɓo Sheykh.
cikin harshen larabci Haroon ya kalli kakar tasu, tare da cewa.
"Sitti ai nasan zaɓinsa, bari ki gani in nuna miki".
Ya ƙarishe mgnar yana kai hannunshi kan kofunan.
da sauri Sheykh Jabeer ya buɗe kekkyawar ƙwayar idanunshi da wasu ke kiransu da
zaiba, wato kamar idon mage, idon ya ɗan zaro ganin Haroon yasa hannunshi kan kofin
M...!
😂😂😂😂😂

Masu cewa na kulle musu kai kada ku damu zan kuce kawunanne, lokaci ne😂🙏🏻🤝🏻

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 12

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🤴🏻💘
🦚🤴 🏻 💘

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku ta wannan number 09097853276.
KO kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz domin samun shiga Special Group,
wanda cikin kwanaki ƙalilan za'a gama littafin da izinin ubangiji. Ga asusun kamar
haka 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, 1k ne SPG sai ki turo min shaidar
biyan
ki ta wannan number 09097853276.

Gareku iyayen ƴan mata da za'a aurar, akwai sittin amare mai kyau na gyaran jiki,
bisa farashi mai sauƙin, akwai na manyan robobi akwai na ƙananan robobi, akwai
haɗin masu jego, da na maida tsohuwa yarinya, sayan na gari meda kuɗi gida, in
kayan gyaran kikeso ki fara min text message ta inbox ta wannan number 09097853276
sai ki gaya min kaya kikeso, kana sai ki kirani to nan zan ɗaga kirankin sai muyi
mgn zaki turo kuɗi ta ACCOUNT number ni kuma zan tura miki kaya ta mota, duk garin
da kike a Nigeria ina aikawa, in dai ba lungu yayi sosaiba. Kana mutanenmu mazauna
ƙasashen ƙetare kamarsu Saudia, India, Gabon, Ghana, Niger, Cameroon, da dai
sauransu in kinada dalili kayana na zuwa can cikin salama. Ina saida kaɗan-kaɗan
ina kuma bada sari.

A dai-dai kan kofin madarar ya sa hannunsa, alamum zai mishi zaɓi kenan, murmushi
yayi dan ya samu damar, da zai tserewa tsarinsu. Cikin ihima da sanin makaman
kariyar kai daga jin kunya ko yin abinda zai ɓata ran wani, ƙafarshi ta dama dake
kusa da hannun Haroon yasa cikin hikima ya bugi hannun Haroon da ke gab da ɗaukar
kofin.
ture hannun yayi da babbar yatsarsa, wanda, hakan yasa hannun Haroon ya bugi
kofunan da ɗan karfi, sai gashi duk sun tuntsure a tsakiyar tiren madarar da zumar
kab suka malale cikin tray ɗin.
A tare suka zubawa tray idanu gaba ɗayansu.
Sitti kuwa wani irin kallo tabi Madarar dashi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, cikin iya taku da kamalarsa murya a mutunce ya kalli Haroon
daya kafeshi da idon tuhuma, cikin harshen larabci da kamala yace.
"Harooon meyasa baka da nitsuwa?".
Cikin tarin mamaki Haroon ya gwalo ido tare da cewa.
"Haaahh".
sai kuma ya kalli Sitti da ta kwaɓe fuska tamkar zata kurma ihun takaici.
Shi kuwa Sheykh Jazrah ya zubawa ido, ganin yadda ta zuba mishi kekkyawan idanunta,
wanda suke sheƙin hawayen dake nuni da zazzafan son da takeyi mishi.
Kauda kwayar idanunshi yayi, da sauri.
Jannart kuwa hannun Sitti ta kamo ganin zata jawo tray.
A hankali Sheykh Khalillullah wanda yake ƙanin Sitti ya gyara zama cikin sakin
fuska da murmushi ya kalli jikan nasu, nitse yace.
"Laaba'as". Dib-dib haka ƙirjin Sheykh Jabeer Habeebullah ya fara bada sauti,
fahimtar kakanun nashi zasu ɗaura zabin kan, fahimtar lafazin Haroon.
Shi kuwa Haroon, wani irin murmushi jin daɗi yayi.
Shi kuwa dottijon nan, ido ya zubawa ƴaƴanshi da jikokin ƴaƴan nashi, da wasu
jikokinshi. Kallonsu yake yana nazartansu.

A hankali wayar Sheykh Jabeer ta fara bada wani sauti mai masifar sanyi da daɗin
sauraro, sautin gwauraye yake da kukan sassanyan tsuntsaye.
da sauri ya zaro wayar a al'jihun tattausan al'kyabbar tasa.
Ganin sunan Maimartaba Nuruddeen ne, ya sashi sakin wata sassanyan ajiyan, cikin
ladab ya kalli Sitti, kana a hankali ya kalli Sheykh Abdulkareem, cikin sanyi da
nitsuwa yace.
"Mai martaba Nuruddee ke kirana, bisa alamu da babbar mgna domin baya kirana haka
banza".
Murmushi dottijon yayi, domin ya fahimci hanyar fecewa, Sheykh yake nema, hakan
yasa ya mishi izinin tafiya.
Cikin sauri Sitti ta yunƙuro da niyar yin mgna, sai kuma tayi shiru, sabida nuni da
tayi shirun da mahaifinta yayi mata.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya yunƙara, ya miƙe ya nufi hanyar fita bayan
yayi musu, su huta gajiya.

Kai tsaye Side ɗinsu ya wuce.


Yana shiga kai tsaye bedroom ya wuce, gyara al'kyabbar jikinshi yayi kana, ya zauna
bisa wata tattausar doguwar kujera.

A nan ƙasar kuma, cikin faɗar masarautar maiartaba Sarki Nuruddeen.

Bayan Jamil ya fita, wurin da yayiwa su Bappa Masauki,


kai tsaye, sashin kakanin nashi ya nufa.
Bayan an mishi isone, ya shiga, ya gaisa da kakan nashi kana ya ƙara da cewa.
"Mai martaba, akwai baƙi ma buƙatar kulawarka, suna tsumayinka".
Murmushi mai cike da kamala farin dottijon bafulatanin yayi, cikin ratsin sarauta
yace.
"Yau ka zama, sarkin fada kenan, kaine mai yiwa baƙi iso ko?, ko dai matane baƙin
dan nasan ta nan kafi ƙarfi". Ya ƙarishe mgnar da yanayin tuhuma.

Kanshi ya ɗan shafa, kana a hankali ya girgiza kansa tare da cewa.


"A,a mazane dattawan Fulanin dajine,".
Ido ya ɗan zuba mishi kana yace.
"Kaje kace a kula dasu, gani nan zuwa yanzu".
Kanshi ya ɗan rusunar tare da cewa.
"Nasa an basu dukkan kulawar da zasu, buƙata, zuwa yanzu sunfi buƙatar ganinka fiye
da komai".
Kai ya ɗan jinjina alamar to.
Yunƙurawa yayi tare da cewa.
"A fito lfy".

"Allah yasa".
"Amin Amin". Yace kana ya fita.

Shi kuwa Sarkin ya fara shirin, fitowa fada.

A can sashin Sheykh Jalal ne, zaune da Ya Jafar, Aunty Juwairiyya na gefenshi.
karatu yakeyi kamar koda yaushe, tun jiya yaƙi barin sashin Sheykh, koda aka kira
Sheykh Jabeer video call, ya ganshi sai yayi ta kuka.
Wannan abun shiya ƙara tada hankali Sheykh Jabeer.

Yana yawan, bin Jalal, wanda mutane ke zaton ko dan tsananin kamannin da Jalaluddin
keyi da Sheykh Jabeer ɗinne yasa, yake ganin kamar shine, to sai dai sam Jalal baya
iya mu'amalantar Babban yayan nasu, kamar yadda Sheykh keyi har yake sama mishi
nitsuwa, sai dai shima yana iya yinshi.

Shigowan Hajia Mama da hadimanta ne, yasa Juwairiyya, jin rauni, a take hawaye ya
cika mata idanu. A duniya bata da babbar matsala sama da larurar mijinta.
Ita kuwa Mama, gefenshi ta zauna, cikin sanyi ta kalli, Jalal da fuskarshi ke
murtuƙe kamar ko yaushe,
cikin baiyanar damuwa tace.
"Ya za'ayi ya samu gamsuwa da kulawarka, a yadda kake haɗe fuskarnan tamkar wanda
aka sanarwar labarin mutuwar uwarshi, ba haka Sheykh ke mushiba, yana kula dashi,
da tausayawa da sakin fuska tunda yasan larurar haukace dashi, amman kai ko yaushe
kana nan kamar boss".
Sai ta kuma kalli Jakadiyarsu Kana, ta kalli Jamil dake waya da alamun da
budurwarshi yake mgna, hararanshi tayi tare da cewa.
"A haka kuke samawa kanku tabon nunawa a rayuwarku, shi wannan ya zama, mahaukaci,
shi Jalal ya zama tantiri ɗan shaye-shaye, kai baka da aiki sai bin matan banza.
Kuna samin ciwo a raina, shima kanshi Sheykh duniya ta zata fara zargin cewa
mazinacine shiyasa yaƙi yin aure ya zauna, sinƙitin fakitin. Shi kuwa Affan in
banda shashanci da tarin ƙuruciya babu abinda yasa a gaba.
Ya kukeso inyi, ya kuke son mahaifinku yayi? Yana da yaya maza har ku shida, amman
ku biyar manyan duk kun zama, ababe masu taɓo a idon duniya, ya za'ayi yayi mararin
gadar mulki a hannun mahaifinshi, tunda yasan shi bashi da masu gadarsa, a kusa,ku
duba, Imran da yake uwarsa ta tambaɗaku, ta nesan taku da mahaifinku, sai ta
kusanta ɗanta da mahaifin naku.
Shiyasa mahaifinku keta ƙin amsar sarautar har sai randa Imran ya mallaki
hankalinshi, ku kuwa kun zama ababen kyarata. Yaya zanyi da raina.
Shiru sukayi gaba ɗayansu,
Shi kuwa Ya Jafar sai ƙara sautin karatun yayi. Yanayi yana zubda hawaye.

Shi kuwa Jalal, shiru yayi yana riƙe da hannun Jafar ɗin.
Jamil kuwa katse kiran yayi.
Affan kuma wanda dama tare suka shigo, fuska ya ɗan kele, cikin irin matsayin da
ƴan auta kedashi a wurin iyayensu yace.
"Mama, shifa zato zunubine koda ya kasance gsky. Ki dena jifar Mommy da batun wai
ita ta tambaɗamu, ya za'ayi keda kanki ki rinƙa suffantamu da marasa nagarta mu dai
gsky ba a tamɓaɗe mukeba,
Menene a cikin mulki da sarauta, Mama akwai wani mulkine matabbaci a duniya banda
mulkin mahaliccin mu, in ma Imran ya gaji sarauta menene a ciki ɗan uwanmu nefa".
Cikin sanyi ta girgiza kanta a hankali tace.
"Ɗan uba dai ba ɗan uwaba".
A tare suka zuba mata ido baki ɗayansu.
Aunty Juwairiyya kuwa, ruggume yarta kawai tayi, tana jin ranta na suya.

A cikin fada kuwa, tun tuni Maimartaba ya fito, yana shigowa suka gaisa dasu Bappa
ya amshesu a mutunce, cikin kulawa, da mutuntaka, bayan sun gaisa ɗinne suka koro
mishi jawabin abinda ke tafe dasu.
Shiru mutanen fadar sukayi baki ɗayansu, sai muryar Ardo Bani, da yake ƙare
zancensa da cewa.
"Babban tashin hankalinmu, kullum ɗauki ɗaɗɗayan da akeyima yaranmu da tsoffinmu.
Kana a sace dabobbin mu, in mun kai kukanmu ga hukuma ko masarauta sai ayi burus
damu, koma a ƙara mana da cin zarafi ko ƙazafi. To gashi yanzu ankai matakin ana
sace mana yara, ko gawarwakinsu ba'a bar mana, shiyasa mukayi tattakin isowa gareka
adalin shugaba, ka duba lamarinmu."

Wani irin zafi da ƙuna ne ya cika zuciyar, Maimartaba Lamido, zalumci yayi yawa.
Gyara zaman babbar Al'kebbar sarautar dake jikinsa ya ɗan yi, yana maijin ƙuna da
tafasa a zuciyarshi, fargaba da tsoron, haƙin bayin Allah'n da aketa kashewa ya
cika mishi zuciya, sabida sanin shine sarki kuma shugaba, ga duk wani mutun dake
yankin.
Wani nannauyan numfashi yaja mai ƙarfi.
Juyawa yayi ya fuskanci maga takardar fadar tashi, cikin bada umarni yace.
"A rubuta takarda a aikawa Haman-Ɓachama cewar ina bukatar ganinshi, da gaggawa.
Kana ya tabbatar kafin ya isoni yankin da yake mulka babu sauran zalumci, ko
ƙabilanci!".
Cikin cika umarnin da maga takardar ya ɗan rusuna, tare da cewa.
"An gama ya Mai alfarma Sarki Adalin Sarki."
Waziri, Galadima, Wambai, Sarkin fada, kana da sarkin dogarai, duk, shiru sukayi
sabida a zahiri ake iya hanƙo tsantsar tashin hankali da ɓacin rai a fuskar adalin
shugaban nasu.

Su kuwa su Bappa sosai sukaji sanyi, a zuƙatansu, sabida nuna kulawarshi garesu,
cikin iya sarrafa harshe da tausasan laffuza mai martaba sarkin Nuruddeen Bubayero
Joɗa yace.
"Kuyi haƙuri, ku gafarceni, bani da labarin dukkan abinda ke faruwa daku, sai
yanzu, naji daɗi da kuka nemeni, da matsalarku, In sha Allah ni kuwa zan ɗauki
mataki, da izinin ubangiji koda belbelun dake cikin shanunku baza'a sake kashesuba,
bare dabobbin ku, bare a kai ga rayukanku. Zan kirayi GARKUWAN FULANI, yanzu, zan
sashi maza ya taho ya dawo ƙasar sa,
Domin shiga lamuranku nauyin a kanshi yake."
Sai kuma ya ɗan numfasa kana ya kalli wani bafadensa dake tsaye bayanshi yanayi
mishi fifita da maficin da akayishi da gashin kekkyawan ɗawisu.
Cikin bada umarni ya umarceshi daya koma gefe,
Da sauri ya rusana ya koma gefen.
Shi kuwa Sarki Nuruddeen, wani ɗan kekyawan matashi dake gefen damanshi ya kalla
tare da cewa.
"Imrana, kiramin Sheykh Jabeer."
Kai ya ɗan rusunar kana yasa hannu ya amshi wayar da Kakan nashi ke miƙa mishi.
Amsa yayi, kana ya kira Sheykh Jabeer, wanda shi kuma a dai-dai lokacin yana gaban
Sheykh Aliyu, Abdulkareem, Jabeer, Sitti, Jazrah, Haroon. Da dai sauran ahlin
nasu.

Wanda kiran ne yasa ya samu ya fece daga tarkon da ake naɗa mishi.

Jin wayar tayi ringing har ta katse ba'a ɗaga bane, yasa Imran ɗan rusunar da
kanshi tare da cewa.
"Wata ƙil baya kusa da wayar."
Kai ya jinjina mishi tare da cewa.
"A a zai kira, bayan amsa kirana yanzu zai kira".
Kai ya gyaɗa alamar gamsuwa.
Suko su Bappa duk suna zaune cikin kamala.

Shi kuwa Sheykh kamar yadda ya saba, hakane baya amsa kiran kakan nashi, sai dai ya
bari in tayi ta katse sai ya kira, shiyasa, yanzuma ya bari saida ta katsen sannan
ya kira.
Gyara zamansa yayi tare da kara wayar a kunnensa na dama.

Imran kuwa yana ganin kiranshi yayi maza ya amsa,


cikin tarin girmamawa yace.
"Barka da hantsi, Hamma Jabeer".
A can gefen Sheykh Jabeer ɗin kuwa, ido ya lumshe cikin yanayinshi da sun rigaya
sun saba yayi shiru.
Da sauri Imran ya kuma ɗan rusunar da kanshi yace.
"Afwan Sheykh Assalamu alaikum ".
Murya can ƙasa yace.
"Wa alaikassalam".
Cikin ɗan tura baki Imran ya kuma maimaita mgnarsa ta forko.
"Barka da safiya, Hamma Jabeer ya, Sitti?".
A taƙaice yace.
"Alhamdulillah".
Da sauri Imrana yace.
"Masha Allah, ga Lamiɗo".
"Na'am". Yace a takaice.
Shi kuwa Imran miƙawa kakansu wayar yayi.
A hankali Sheykh ya ɗan buɗa laɓɓansa cikin zazzaƙan sautin muryarsa yace.
"Assalamu alaikum".
Murmushi mai cike da so da ƙaunar jikan, nasa yayi tare da amsa sallamar tasa.
Gaisawa sukayi, bayan sun gaisa ya tambayi labarin su Sitti da ƙanennenta da kuma
mahaifinta, sai kuma ya kora mishi jawabin abinda ke faruwa a jihar tasu.
Kana, ya ɗoro da cewa.
"Ka dawo, kayiwa lamarin tubkar hanci". Cikin sanyi yace.
"In sha Allah. Ina nan tafe, nanda kwanaki uku. Ina jajanta musu, abinda ya faru,
kuma in sha Allah.
hakan bazai kuma faruwa ba.

Da haka sukayi sallama.

A can garin Numan kuwa cikin Rugar Kikan.

Gaba ɗaya garin shiru yayi, dan wannan abunda ya faru yayi masifar shiga jikinsu.
Da dama maza matasanmu sun tafi kiwo, kamar yadda suka saba, rayuwar yau da kullum.
Saura sai irin dattawan da aka bari, da mata da yara maza da mata.

Cikin garin Bonon kuwa, gaba ɗaya, matasan garin dama ƙauyuka gefensu na ƙabulun
Ɓachamawa, duk sun hallara wuri ɗaya, suna cike gaban dodon tsafinsu, wato Bonon
ɗin, giyar burkutu mai ɗan karen tsami da wari, suketa sha, tamkar zasu fasa
cikkunansu.
Yayinda gefe guda kuma, maƙerar dake gefe wasu matasa su ne maƙera keta wasa ababen
faɗansu, kamarsu wuƙaƙe, Adda, sitaka, barandami, mashi, kibau, da dai sauran
mugayen makamai, sai sheƙi sukeyi.

Suna cike a wurin, Ba'ana ya iso, cikin wata shigar rigar saƙi.
Hanya suka rinƙa buɗa mishi, hardai ya isa ga sarkinsu, dake zaune gefen dodo sun.
Zama yayi kusa da sarkin nasu ya sasu a gaba,
Cikin harshen ɓacamancin yace.
"Ku hanzarta, ku shiga, duk matasansu majiya ƙarfi, sun tafi kiwo. Dottijan su kuma
sun tafi, kai gulmarku, ga Sarkin su wannan karon basu tsaya ga sarkinku na nanba,
ina da yaƙinin kuma za'a sauraresu a can.
Yanzu matansu da ƴaƴansu, ƙanana mata da mazane suka rage a garin.
Sai wasu dattawansu dake, dakon dawowar magulmatan can.
Kuyi maza, kushiha kafin su dawo, ku share garin kab.
Ku kashesu gaba ɗaya babba da yaro mace dana miji."
Da sauri wani daga cikin su yace.
"Harda gidansu Shatu?".
Cikin izaya yace.
"Harda su, domin Mata, bata nan, ku kashe kowa nata, ta hakane zata dogara dani
kaɗai tunda bata da kowa nata a duniya, dole Ni zan zama mijinta ubanta yayunta
ƙannenta uwarta, in zama Garkuwarta in zame mata duniyarta ta hakane zata yarda
nine ɗaya gatanta kuma duniyarta, ba tare da ta zargeniba, a hankali wata rana in
sata tayi ridda, musha giya, muyi tsafi tare da ita, bazatayi min musuba, mu haifi
ɗanmu na forko mu bawa dodonmu yasha jininshi yasa mana al'barka a aurenmu".
Wani irin ihu da sowa na tsantsar jin daɗin bayaninshi sukayi baki ɗayansu.
Hakama dodonsun, saida ihunshi ya firgitasu baki ɗayansu.
Dariya mai amo mara daɗin ji. Sarkin nasu yayi, kana ya busa ƙahon dodonsun, alamun
ya basu izinin tafiya.

Nan fa duk suka rinƙa shiga, cikin maƙerarnan suna ɗaukan makamai, suna nufar garin
Rugar Kikan (Rugar Bani) kenan a guje...

Cikin garin Shikan kuwa, Bani rana ta fara tasawa, mata masu zuwa tallan nono cikin
garin Numan, suka fara ɗaukar ƙorarensu, suna fita garin.
Yara maza da mata kuwa, wasu na wasa wasu na ɗebo ruwa, wasu na ɗebo kayan lamɓu.
Yayinda wasu kuma suka dawo break dan tara tayi.

Cikinsu kuwa harda Junainah.

Tafe take da saurinta da ɗan tsalle-tsallenta tana rataye da yar jakarta,


da sauri ta tsaya ganin Junaidu a gabanta rike da kwanɗon zabari wanda yake cike da
ƴaƴan itatuwa.
Murmushi ta ɗanyi tare da sunkuyar da kanta cikin surutunta tace.
"Har naji tsoro!".
ta ƙarishe mgnar tana kallonshi,
Murmushi yayi mata shima cikin son ƴarinyar yace.
"Haba dai, tsoron me kuma zakiji, tunda gani, babu abinda zai sameki muddin ina
raye, zan zame miki Garkuwa".
Da sauri tasa hannu ta rufe bakinta tare da cewa.
"Kai! Kai! Ya Junaidu, sunan Babanmufa ka kira".
Murmushi mai kama da dariya yayi kana yace.
"Au na manta ashe sunan surki nane".
Kai ta gyaɗa mishi kana tasa hannu ta amshi, nonon inabin da yake miƙa mata,
baki ta buɗe da nufin sawa a baki,
sai kuma ta tsaya tare da tura baki jin yana ce mata.
"No kada kici ba'a wonke bafa."
Sai kuma ya ajiye kondon, ya amshi inabin ya ɗan gangara, gefe kaɗan ya wonkeshi a
bakin ruwan wutsiyar Kogin da yayiwa Rugar tasu ƙawanya.
Ya tahowa tana kallonshi.

Koda ya iso miƙa mata yayi,


kana ya ɗauki kondon, ganin still tanata kallonshi ne ya sashi cewa.
"Ya dai?".
Kai ta kauda tare da fara tsinkar ƴaƴan inabin tana afawa a baki tana taunawa,
Murmushi ya kumayi ganin yadda ta lumshe idonta.
A hankali tace.
"Ya Junaidu kayi kyau sosai yau, har kamar ka fini kyau".
Dariya ya ɗanyi kana yace.
"Yo dama ai na fiki kyau".
Maƙe kafaɗa tayi tare da cewa.
"Uhum a a kam".
A haka dai suna tafe suna hira.
Can cikin gida kuwa, Ummiy ce zaune bisa kujera ƴar tsuguno da buta a gabanta,
alamun al'walan sallan walaha, zatayi.
Inna kuwa, da wasu maƙotansu uku Biba, Hari, da Innawuro. suna zaune bisa taburma a
tsakar gidan. Suna amsar gaisuwa.

Can cikin garin kuwa su Alhamdulillah Manu dasu Siddine da dai sauran dattawan
garin ne zaune a fada.
Sai yara daketa kai komo.

Da sauri su Siddi suka miƙe tsaye ganin, matasan mayaƙan ƙabilar ɓachama, sunata
shigowa garin tako ina gabas da yamma kudu da Arewa, bisa dukkan alamu zobe
sukayiwa garin
Kana ga zurma-zurman makamai masu tsawo tamkar raƙumai. Sai sheƙi sukeyi.

Cikin ɗaga murya, Alhaji Manu yace.


"Kai lfy? me haka?".
Ganin sun nufosu gadan-gadan ne yasa, suka miƙe gaba ɗayansu, kowa ya fara, neman
makari, to amman ina, basu da zato ko sanin za'a far musu, shiyasa basu da shirin
komai na kare kai.
Ɗaya daga cikin sune, yace.
"Mu gudu kashemu sukeda shirin yi ba tare da laifin komaiba".
Siddine ya kuma ɗaga murya tare da cewa.
"To in mun gudu matanmu da yaranmu fa".
Ihun da sukajiyo tako wani sashi na garinne ya tambatar musu, ana karkashe su.
Gudu suka farayi kowa ya nufi hanyar gidanshi dan ɗaukar matakan kare kai.
Sai dai ina basu da hanya duk inda suka ɓullo sai sunci karo da, mayaƙan.

Lokaci ɗaya garin ya ruɗe ya birkice kota ina sai ife-ife da gudun ceton rai da
makiyayan Rugar Kikan keyi.

Wani irin sauti mai baiyana azabar fitan rai Alhaji Manu yayi, lokacin da wani
kafurin ya caka mushi sitaka a ƙahon zuciyarshi.
Siddine ne ya juyo da azaban razani, amman sai shima ya saki wani sauti mai
gigitarwa jin azaban sara da sukan da akeyi mishi.
Garifa ya kacame,
Hadi ne babban ɗa ga Alhaji Haro mahaifinsu Junaidun Junainah, ya nufi cikin
gidansu da azama,
Yana cike da fargaba, da tashin hankali domin wasu irin ihu da yake jiyowa a cikin
gidan nasu.
Yana kusa kai ya samu, makasan suna cike a gidan.
Suna ta'addanci, sun kashe kowa na gidan.
Ganin haka ya juyo yana juyowa. Yayi kiciɓis da abokinshi Sale, yana tafe jini na
zuba an farka mishi ciki.
Cikin magagin mutuwa yake cewa.
"Hadi sun kashe kowa na garin nan sai wanda baya nan.
Hadi na kira Hukumar yan sanda ta nan cikin Numan na shaida musu, amman kafuran nan
maƙiya Allah da Manzonsa sai cewa sukayi,
A kashe mu mana, ai an rage musu aikine.
Na kira su Arɗo Bani, suna ɗagawa katin wayata ya ƙare.
Hadi sun kashe kowa na gidanmu.
Taroshi Hadi yayi suka faɗa nan suna kuka mai cike da taraddadin rabuwa.
Cikin ƙarfin hali Sale ya ture Hadi tare da cewa.
"Ka gudu Hadi ku gudu, Ni nasan bazan rayuba.
Ka gudu.
Sun kashe min Kowa har jariren tagwayen da aka haifa min shekaran jiya, sun
kashesu.

Cikin kuka Hadi yace.


"Bazan iya guduba Sale su kasheni kawai, ina zanje bayan sunyiwa garin zobe.
Da ƙarfi Hadi ya abka jikin Sale Jin ansa gatari an sari kafaɗarsa ta dama,
Juyowar da zaiyi kuma aka tsira mishi mashi a ƙirji.
Nan take ya cika, hakama Sale.

Cikin gidansu Shatu kuwa.


Ummiy ta sallame sallan kenan, taji.
Inna dasu Innawuro suna kurma ihu da salati.
Yunƙurawa tayi da azama jiki na rawa ta nufo woje.
Fitowanta yayi dai-dai da lokacin da aka sare kan Innawuro, wanda kan yayi tsalle
ya faɗo kanta, kana ya gangara ya faɗa gabanta.
Wani irin ihu mai cike da karaji gauraye da salati ta kurma lokacin da taga an
burmawa Inna mashi a ciki.
Ihunta da salatinta ya jawo hankalin su, sukayo kanta.
Sai dai kafin su isoma ta yanki jiki ta faɗi babu numfarfashi tamkar matacciya.

Koda suka iso, dariya suka kece da ita cikin rashin imani ɗayansu yasa ƙafa, ya
taka ruwan cikinta, tare da cewa.
"Shegun FULANI ku mutu, mu huta, da ganinku a garinmu, gonakinku da dabobbin ku duk
sun zama namu.
Mu ɗauke yaranku mata mu maidasu karuwanmu, muyi musu ciki su haihu mu bawa dodo.
Muji daɗi dasu.

Ganin kamar ta mutune yasa suka tattakata suka wuce suka fita daga gidan.

Junainah kuwa da Junaidun, suna gab da shigowa garin suka fara jiyo ihun mutanen
garin.
Cikin azaban firgici Junaidu ya wurgar da kondon ƴaƴan itatuwan dake hannunshi,
da gudu yabi bayan Junainah data ruga a guje sabida hango, anata kashe mutane a
gabansu.
Cikin kuka da tarin kiɗima da fita haiyacinta take cewa.
"Wayyo Ummiy Wayyo Inna Wayyo Bappa, zasu kashemu.
Wayyoooooooo Adda Shatu zasu kashemu".
Riƙo hannunta yayi da ƙarfi cikin rawan jiki da murya yace.
"Junainah bazasu kashekiba, zan kareki da izinin ubangiji, zaki rayu, Shatu bazata
rasa kowa duniya ba.
Junainah zan zame miki Garkuwa zan fanshi ranki da nawa ran.
Ki zama tamkar yar tsira, Shatu ta zama tamkar yar jarida, ta rubutawa mutanen
duniya su karanta, kisan gillan da akeyiwa Fulani mazauna daji.
Da ƙarfi yasa hannu ya zaro wukar dake ƙugunshi wanda da ita ya yayyanki nonunan
ayaba dasu inabi.
Wayarshi ya kuma zarowa
Ya Salmanu ya kira,
Salmanu kuma dake, kwance a gadon asibitin nan Genaral Hospital Numan.
Wanda bai workeba tun dukan shaɗi da ba'ana ya mishi.
A hankali yasa hannunshin ya amsa kiran wayarshi ganin Junaidu ke kiranshi.
Cikin kiɗima da firgici Junaidu yace.
"Ya Salmanu, mayaƙan ƙabilar ɓachama sun shigo Rugar mu, sunata kashemu, mazanmu da
matanmu.
Ya Salmanu Junainah ina son ta tsira, ko dan ran Junainah ka kira mana hukumar yan
sandan cikin Adamawa, ina son su iso su ceci Junainah kada Shatu ta rasa kowa a
duniya.
Ban saniba ko zan gazawa bawa Junainah tsaro".
Gaba ɗaya jikin Salmanu rawa da tsuma yakeyi, katse kiran yayi da sauri ya kira.
"A.S.P Kabiru Nasir. Wanda yake, Hetkotan Adamawa.
Koda ya mishi jawabin abinda ke faruwa, a take. A.S.P ya kira.
S.P Daniyel dake Numan ya bashi doka da oda maza-maza su bawa fulanin Rugar Kikan
tsaro gaggawa, shima yana nan tafe da rundunar sa. Ya bashi umarni mai ƙarfi ya
ƙara da cewa, muddin yazo ya samu ba dai-dai ba ta ɓanƙaren tsaro, to akan
aikinshi.

Wannan abun na umarni daga samane, yasa mugun kafurin nan. Firgita gudun rasa
aikinsa, da tonuwar asirinsu da gudun kada a cireshi asa musulmi a kujerarsa, yasa
cikin gaggawa ya haɗa kan rundunar sa ya nufi.
Cikin Rugar Kikan.

Junainah kuwa wani irin karkarwa takeyi wanda, tuni fitsari ke tsiyaya yana bin
sawunta.
Wani irin ihu tayi, ganin wani kafurin ya kaiwa Junaidun sara a bayanshi.
Wani irin juyi Junaidun yayi ya farma kafurin da da wuƙarsa dan kare kansa da
Junainah.
Duk da su biyar suka zagayesu, basuyi nasara a kanshiba, yana kare kanshi da
Junainah, har saida suka tsira daga waɗannan.
Sai kuma wasu, mutun takwas suka cimmusu.
Da ƙarfi suka banƙaren Junaidun, suka fara kiciniyar zare Junainah da ya ruggumeta
da azaban ƙarfi da yayi.
Wani irin ihu yasa jin an caka mishi.
Wuka a gadon baya.
Still bai saketaba, sai yaƙin kareta da ya farayi, da iya ƙarfinshi.
Ita kuwa Junainah ganin an caka mishi wuƙane yasa ta sume.
Dai-dai lokacin kuma rundunar yan sandan suka iso.

Kamar bazasu guduba, dan sun san da bakin hukumar sukeyin aikin, to sai dai ganin
musulman cikin yan sandan suna sakin harbine yasa.
Suka ari ta kare.

Daga nan suka rinƙa gudu sunayiwa yan uwansu fito alamun su gudu.
Cikin ƙanƙanin lokaci duk suka gudu.

Su kuwa yan sandan, suka shiga cikin Rugar Kikan ɗin.


Hankalin musulman cikinsu yayi masifar tashi ganin irin kisan gillar da akayiwa
bayin Allah'n nan, kisa na rashin imani.
Nan take suka kira motocin asibiti.
Suka rinƙa jidon masu sauran rai suna sawa a motar ambulance suna kai cikin Genaral
Hospital Numan.
Kana suna harhaɗa gawakin kuma a tsakiyar garin.
Cikin mintuna talatin rundunar A.S.P ta iso.
Tare da yan jaridu.

Su Bappa kuwa. Koda suka gama tattaunawa da Maimartaba, sai ya umarci Waziri daya
hanasu tafiya a bisa adalcinsa.
Yace su tsaya suci abincin rana, kana suyi sallan azahar kafin su tafi.
To haka yasa suka zauna.
Waziri yasa akayi musu duk ihsanin da Maimartaba ya bada umarnin ayi musu.
Sukaci abinci sukasha, Sannan sukayi sallan azahar.
Daga nan aka sallesu suka tafi.

Tuni cikin gari kuwa gidajen rediyo sun ɗauka, batun faɗan FULANI makiyaya da
Ɓachamawa manoma, wanda akaso a juya rahoton da cewa makiyayan ne sukayiwa
manomanne ɓarna.

Bayan. Tafiyan su Bappa da kamar 30 minutes ne. Labari abinda ya faru ya riski
Maimartaba.
Nan take yasa Waziri da Galadima da hadimai mutun ashirin suka nufi cikin Numan dan
suje su tabbar da abinda akace ɗin.

Su Bappa kuwa, sam basuji lbrinba saida suka isa cikin Numan.
Ganin garin a hargitse ne yasa Arɗo Bani ya kalli Bappa da Alhaji Haro da suke
gefenshi cikin mmki yace.
"Lafiya kuwa? Meke faruwane a garin nan?".
Cikin kaɗuwa suka haɗa baki wurin cewa.
"Allahu alamu".
Drivern nasune, ya kallesu a tsorace yace.
"Anya kuwa yau ba faɗa akeyiba a garin nan ba".

"Kai ba lfy ba kam!".


Cewar Alhaji Umaru
Shi kuwa Drivern, bakin titi ya ɗan gangara ya tsaya, ya tambayi wasu yan agaji
daketa.
Shiga cikin wani babban Pharmacy da alamun magunguna suke saya,
koda suka mishi bayanin abinda ya faru.
Jiki na rawa yazo ya sanarwa su Arɗo Bani.
Lokaci ɗaya hankalinsu. Yayi masifar tashi.
Nan sukace ya wuce dasu.
Asibitin.

Koda sukaje hanasu shiga akayi.


Hakane yasa, sukace to ya wuce dasu Rugarsu.
Suga ko canma akwai uban da zai hanasu zuwa.

Nan ya nufi cikin Rugar tasu dasu.

Su Wazirima tuni, sun iso.

A can cikin masarautar kuwa,


Sosai hankalin Maimartaba ya tashi.

A can ƙasa mai tsarki kuwa.

Sitti ce tsaye gefen Sheykh lokacin da yake mgna da kakanshi.


Zama tayi gefenshi, tare da tsareshi da ido.
Baibi ta kantaba, ya ci gaba da sarrafa wayarshi.
Wata number, ya dannawa kira kana ya kara wayar a kunne, jim kaɗan aka amsa kiran.
Bayan sun gaisane, ya ɗan gyara zamanshi tare da ɗan kallon Sitti ta gefen ido
Cikin harshen fillanci yace.
"A haɗa min zama da Ƙungiyar TABITAL POOLAKU".
Sai kuma ya ɗan shaƙi sanyi da ƙamshin ɗauki ido ya lumshe cikin kamala da nitsuwa
yaci gaba da cewa.
"A kira min Ƙungiyar MIYETTI ALLAH, da gaggawa, ina da zama dasu.
Ranar Jumma'a in sha Allah".
Hannun damanshi yasa yana shafa sajenshi, tare da sauraron mgmar da. Arɗon Arɗaɓe
keyi.
"Ranar jumma'a kuma? Ka dawone?".
A takaice yace.
"Zan dawo!".
Cikin gamsuwa da mgnarshi sanin in yace eh, eh ɗince in kuma yace a a, tofa a ance.
Muddin kuma yace zaiyi abu to da izinin ubangiji sai yayi shi.
Cikin jin daɗi adalci da kulawarshi ga shugabanci da aka bashi yace.
"To Allah ya dawo da kai lfy".
Yatsun ƙafarshi ya sunkuyar saida suka ɗan bada sautin ƙaras, kana yace.
"Amin ya rabbil izzati".
Daga nan ya katse kiran.
Kamar bata wurin haka ya jawo System ɗinshi ya fara daddannata.
Kamar babu kowa kusa dashi haka yaci gaba da aikinshi.
A system, ita kuwa Sitti ido ta zuba mishi.
Tana kallon yatsun hannunshi da yaketa sassarfa, tamkar shiya haaliccin na'ura.

Yanajin idanunta na yawo a sasan jikinshi, hakan yasa, ya ɗan juya kwayar
idanunshi, ya ɗan kalleta ta wutsiyar idonshi, murya can ƙasa yace.
"Sitti wannan kallonfa, kin san bana son kallo kam ko?".
Ajiyar zuciya ta ajiye, kana ta ɗan janye Hiramin kanshi, da sauri yasa hannunshin
ya kame hiramin cikin kwaɓe fuska yace.
"Sitti ya haka, kinsan Haroon ba kan gadone dashiba, yanzu zai iya shigowa da yaran
nan".
Ido ta ɗan rufe kana tace.
"To su yaran mayune, ko yaushe kana rufe da Al'kyebba da hirami, kasha iska mana,
ko nauyi basa makane?".
Kanshi ya ɗan juya kana a hankali yaci gaba da aikinshi tare da cewa.
"Suturce jiki shine, zaiyiwa ɗan adam nauyi, Sitti, sannan ya za'ayi in bari ko
wani Tom and Jerry su kallarmin suman kai, ai shi hula da hirami kamar ɗan kwaline
wa mace".
Sai ya kuma ɗan juyowa ya kalleta tare da cewa.
"Yauwa Sitti, bana son ana sawa Jazrah tana samin abinci, bana so, sai a turrota
tazo taita kare min kallo".
Fuskarta ta haɗe kana tace.
"To yayi kyau, kawai in baka sonta, ka fito fili ka faɗa mana".
Kauda mgnar yayi tare da cewa.
Ki shirya in sha Allah zuwa ran jumma'a ina son in kasance cikin ƙasata ta haihuwa
a jiharmu a kuma masarautarmu".
Haroon da yanzu ya shigone ya ɗan kalli ɗan uwan nashi, cikin mmki yace.
"Sheykh kawai dan ana mgnar baka matar aure shine kake shirin guduwa zaka bar ƙasar
ba?".
Bai kalli Haroon ba kuma baice, komai ba, sai rufe system ɗinshi yayi kana ya miƙe
a hankali,
gaban drower'n gadon ya nufa,
buɗewa yayi, wasu E Passport guda biyu ya ɗauko,
Kana ya dawo gaban Haroon.
Hannun shi ya kamo ya danƙa mishi su, kana yace.
"Gasu, ina son zamu bar ƙasar nan ranar al'hamis."
Da sauri Sitti tace.
"Kaida waye zaku tafi".
Ba tare daya kalletaba yace.
"Da ke".
Kai ta kuma juyawa tace.
"A a kam ka koma kai ɗaya, ni ban gaji da ganin ahlinaba".
aKanshi ya kaɗa tare da cewa.
"Zafa ki koma, don bazan barki a kasar nanba, kiyi ta haɗa min tarko, dole tare
zamu tafi, inada zama mai mahimmanci, dole inje inji da matsalar al'ummar da aka
naɗani GARKUWANSU, tunda ke kika sa na amince da wannan naɗin, ina zamana lfya,
wani mulki ko sarauta basa jadawalin rayuwata, keda waɗancan tsofoffin sarakunan
kuka likamin wai GARKUWAN FULANI,
To sun samu matsala kuma dole inje in bincika".
Shiru kawai Sitti tayi ganin karfin hali ziraran miraran.
Zuwa yanzu ta dena mmkin, cewa akan abu biyu Sheykh ke iya doguwar mgna, akan
Alqur'ani, wanda shine zaka samu zai iya wuni a zaune yana tabsiri ba gajiya ba
yunwa bare ƙishi ko bacci.
Sai kuma akan wannan sarautar GARKUWAN FULANI da aka bashi shekarun biyar baya,
wanda harga Allah baison wannan Sarautar ko kaɗan sai dai dole da akayi mishi, da
fushin da Abbunsu ya nuna a kan haka.
Shiyasa duk sanda zaiyi ƙorafi yakan iya jera mgna biyar zuwa bakwai, wanda sam shi
tsarin rayuwarsu ba mai doguwar mgna bace.

Kai takaɗa jin yana cewa.


"Ku ɗan bani wuri".
Basuyi mgna ba suka fita, a tare, domin sun san Sheykh Jabeer mutunne mai tarin
tsananin al'kuyya da killace jikinsa, shi kanshi yana kunyar kanshi a rayuwarshi ta
duniya shi bai taɓa yin tsirara a kan kanshi wai yaga surar jikinshi ba, Allah
yasani yana masifar jin kunyan kanshi.
Haka yasa koda wonka zaiyi, baya yin tsirara,
yanada wasu tausasan gajerun towel wanda duk rintsi dasu yakeyin wonka a jikinshi.

Suna fita falo, Haroon ya tsaya yana kallon Jazrah, dake konce bisa kujera ta kife
kanta a cinyar Jannart tana kuka mai sanyin sauti.
Kai Sitti ta juya ta nufi ɗakinta,
Allah ya sani Jazrah na son Sheykh, shi kuwa bai nuna ya tsaneta ba, amman dai ya
nuna zahirin bazaiyi aureba.

Haroon da Jannart ne suka zauna suna bata baki.


Saida ta nitsune suka fita tare.

Shi kuwa Sheykh suna fita, ya maida ƙofar ɗakin ya rufe.


Kana ya dawo bakin gado.
A hankali ya zare tattausan al'kyabbar jikinshi, fararen kayan dake jikinsa suka
baiyana.
A hankali ya zare rigar ya ajiyeta gefe.
Zariyan wonɗon ya kunce, tare da zama, ya saɓule tare da matsawa gefe.
Ya rage dagashi sai fararen boxes da vest.
Juyawa yayi yana taku mai cike da nitsuwa,
ya shiga bathroom ɗin.
Yana shiga ya maida ƙofar ya rufe,
kana ya rage hasken ciki.

Sannan ya cire ƙananan suturun dake jikinshi tare da ɗaura towel ɗin, a ƙuginshi
zuwa kan cinyoyinshi masu yelwar gargasa mai taushi da tsulɓi da sheƙi tana,konce
lib-lib a farar fatar jikinshi.
A haka ya fara, wonkan, bayan yayi Brosh a hankali yake bin jikinshi da sabulun mai
ɗan karen ƙamshi, yanayi ya cuccuɗa jikinshin.
a hankali ya iso kan ƙugunshin, cikin sabo da iya ɗabi'ar tasa, ya cusa hannunshi
ta cikin ɗaurin towel ɗin, ya rinƙa cuccuɗa jikinshin da murza mishi daddaɗan
sabulun ya murje ko wani lungu da saƙo na sasan jikinshi ba tare da idanunshi ma,
sunga tsiraicinsaba.

A ƙalla yayi sawon daƙiƙu ashirin a bathroom ɗin kafin, ya fito,


yana ɗaure da wani babban towel mai ɗan karen kyau da taushi bayan ya matse wancan
ya shanya.

Yana saƙo ƙafarshi cikin bedroom ɗin ya...!

Solo-salo-salon GARKUWA na dabanne!

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 13

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🤴🏻💘
🦚🤴 🏻 💘

FREE PAGE

Littafin GARKUWA na kuɗine, Special Group 1k Normal 300, in kina buƙatar karanta
lbrin GARKUWA turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin 09097853276. Gareku
mutanen Special Group turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu
Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number 09097853276.

*Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki, in kin san zaki sayi littafinane dan ki
fitar dashi, na roƙeki da Allah da Manzonsa da darajar iyayenki kada ki saya bana
son kuɗinki, ki riƙe kudinki ki barni in riƙe littafina. Dan Allah nace badon
niba.*

Yaji anata bubbuga mishi ƙofar ɗakin,


bai kulaba, yazo a zauna bisa kujerar dreesing mirror, a hankali yake tsane ruwan
jikinshi, bayan ya gama ɗan tsane ruwanne ya busar da tattausan sumar kanshi, ta
hanyar na'urar busar da gashi.
Mai ya ɗan shafa, kana ya gyara gashin da kyau, sannan ya miƙe yaje gaban.
Drower'n, a nitse ya buɗe, wasu datsatstsun kaya riga da wondo na yadin Lamud,
yadin Sky blue ne mai masifar kyau. Sai kuma ya zaro wata farar al'kyabbar fara
ƙal. Da farin hirami.

Rufe wannan gefen yayi, kana ya buɗe ɗaya gefen.


Ƙananan kayan ne a ciki kamarsu Jallabiya da boxes vest dasu zagayen baƙin abin da
yake ɗaurawa kam hiraminshi.
Suma duk mafi akasari su fararene.
A bakin gadon ya ajiyesu.
Kana ya fara kimtsawa.

Bayan ya gama shirinsa ya fito ras cikin kalar sky blue and white sai Black half
cover da kuma baƙin zagayen saman hiramin.
Ya fito ras tamkar dai yadda zuriyar mahaifiyarshi da suke tsatson limamen Harami
suke fita.
Ko yaya ka ganshi dole kace shi balarabene, sabida komai nashi irin nasune. Kyau,
fari, gashi, ilimin addini, nitsuwa, imani, da kuma irin shigarsu, da shima ya
rainu da hakan tunda a cikinsu ya girma.

Wani turaren Oud Kareem ya feshe jikinshi dashi.


Lumshe ido yayi sabida shida kanshi ya shaida ƙamshin wannan turaren nashi iyakane.

A hankali ya nufi ƙofar fita yana tafe yana tasbihi.


"Astagafirullaha wa'atubu ilaik.
Astagafirullaha zunuba jami'an. Subahanallahi Wal'hamdulillah wa la'ilahaillahu
Allahu Akbar."
Da wuya ka iya jin abinda yake faɗin, sai dai ina ka lura da motsawan jajayen
laɓɓansa, masu kama da jajayen kunnen fire masu taushi zaka fahimci tasbihi
yakeyi.

Ba kowa a wurin sabida haka ya nufi falo a nitse,


A falon ya samu Sitti bisa dukkan alamu, shirin tafiya harami tayi.
Tana ganinshi ta miƙe tare da cewa.
"Muje ko". Kai ya gyaɗa mata, kana ya ɗan kalleta bayan ya ɗan tsagaita tasbihin
bakinshi yace.
"Zan shiga wurin Sheykh Abdulkareem".
Cikin kula tace.
"Muje sai mun dawo mana".
Kanshi ya jujjuya mata kana yace.
"Zan sanar dashi batun komawarmu".
Gyara matafinta tayi tare da cewa.
"Na sani ai, muje sai mun dawo".
Fuskarshi ya ɗan haɗe tare da cewa.
"Ni a harami zan kwana".
Ganin ya kafe tasan fa duk yadda tayi, hakan zaiyi,
binshi kawai tayi,
suna shiga suka samu kamilin dottijon nan, bisa tsakiyar yaranshi, da alamun suma
ɗin anjima zasu taho masallacin.
Yana hanƙoshi ya miƙa mishi, hannunshi na dama, da sauri ya isa gareshi, ya kama
hannunshi tare da rusunawa, ɗaura hannun yayi bisa tsakiyar kanshi, sannan yayi
shiru yanajin yadda dottijon ke zuba mishi addu'o'in.
Yayinda kamilan yaranshi ke amsawa da.
"Ahmeehn! Ahmeehnn!! Ahmeehnn!!!."
Bayan ya gama mishi addu'o'in ne, ya juyo ya gaida kakanun nashi, baki ɗayansu.
Kana ya shaida musu tafiyarsu data taso cikin gaggawa ya kuma sanar musu dalilin
tafiyan.
Sun gamsu da hakan, kasan cewar sun ɗan ɓata lokaci a nanne yasa. Tare suka tafi
masallacin baki ɗayansu.

Haroon kuwa cikin kwana biyu ya gama musu komai na tafiyarsu, gida dan shima dama
yana son tafiya gida shida Jannart ɗinshi duka.

A cikin makarantar su Aysha kuwa.


Sam bata samu lbrin abinda ya faru a rugarsuba.

Sai da yamma, nanma Rafi'a ce, dake riƙe da wayarta tana chatting.
A nan ne ta gani a kafafen yaɗa labarai cewa.
Anyi faɗa a tsakanin MAKIYAYA da manoman, a garin Kikan dake gaɓar kokin Namun.
Koda ta sanarwar Aysha.
Taga tashin hankali ya wuce zatonta,
hakane yasa ta bita suka tafi tare.

Su Bappa kuwa bayan sun nufi, rugar tasune, sukaci karo da motar police officers,
da kuma Ambulance ɗin, daya ɗebo su Ummiy dasu Junaidun da Junainah, kana. Da wasu
wadanda ake ganin kamar sunada ɗan sauran numfarfashi.

Da sauri C.P Daniyel yasa, drevernsu Arɗo Bani, ya juya dasu, dan suka nufi cikin
Genaral Hospital Numan ɗin, sabida yasan in sukaje suka, ga irin kisan gillar da
ƙabilun nan sukayiwa yan uwansu, tashin hankali zaiyi yawa ya kuma san A.S.P Kabir
da rundunarsa na, can, to zasuyi mishi bayanin da zaisa ya iya korarshi a aikinshi.
Shiyasa ya jasu suka koma, cikin asibitin.
A cewarsa su kula da mutanen su, saura kuma, kuma, akwai hukuma na, kula dasu a
can.

To wannan dalilin ne, yasa suka koma cikin asibitin,

Hakane yayi sanadin da koda Waziri da Matawalle da rundunar Hadiman da Sarki ya


aiko,
Suka zo, basu ga su Arɗo ba a cikin Rugar, kana kusan wuni sukayi a nan dan sai
yamma, suka juya suka koma masarautarsu.

Ita kuwa Aysha, suna zuwa, kai tsaye cikin asibitin suka nufa, dan tayi waya da
Bappa.

Koda suka iso, sosai hankalin ta ya tsananta gaba hankalinta ya tashi, ganin gaba
ɗaya asibitin a cike yake da mutane su,
sai dai ta ɗan samu nitsuwa kaɗan ganin Ummiy da Junainah sun farfaɗo,
sai dai duk basa mgna sunyi zurui dasu hakama sauran waɗanda suka samu suka farfaɗo
ɗin.

Koda ta tambayi Bappa inasu ya Giɗi sai cemata yayi suna gida, ya ɗaura da cemata.
"Yauwa Shatu ku zauna nan, ku kula da marasa lfyan, bari mu kuma mu ƙarasa can
Rugar tamu, mu duba meke faruwa a gidan".
Hannu tasa ta share hawayenta dake shatata daga cikin kumburarrun idanunta cikin
disashewar muryar da kuka yasa ta dishe tace.
"To Bappa kuje, zamu kuladasu, ga can Ya Salmanu ma, ya turo mana abokanshi, ga
kuma ƴan agaji, zamu zauna dasu".
Cikin tarin ƙuna da tafasar zuciya, Alhaji Haro, ya gyara gariyarsa tare da cewa.
"Mu tafi".
Arɗo Bani ne ya miƙe tsaye tare da yin gaba kana duk suka bishi a baya suka fita
suka tafi.

A hankali Rafi'a tasa hannu ta tallabi Aysha daketa kuka mai sosa zuciya, kuka mai
cike da rauni da taraddadi.
Zama sukayi cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Ki dena kuka Aysha, in sha Allah babu komai."
Murya na rawa hawaye na kwaranya ta buɗe manyan idanunta da suka rine sukayi jazir
da kuka da tashin hankali, cikin rauni tace.
"Rafi'a babu komai kuma?, ko dai komai ya faru, kalli fa halin da yan uwana da
maƙotanmu suke ciki, kinjifa ance an kashe mutun kusan 40, kuma kin san gidajen
rediyo suna ragewa nema wasu lokutan sabida kada, hankali mutanen duniya ya tashi.
Rafi'a banga Yayuna ba, ko ɗaya ban ganiba, banga Inna ba, kalli Junaidu, kalli can
Ya Mati yayansu Ya Salmanu. Kowa baya cikin haiyacinsa,
Ummiy ta zama kamar kurma meta gani ya gigitata haka, kalli yadda Junainah keta
fizge-fizge alamun taga mugun abun daya firgitane ya ɗimautata.
Rafi'a ga tozarci da cin fuskar da akeyi mana, kallifa babu likitan da yazo ya kula
mutanenmu, an barsu ciwukansu nata tsami,
sai Nurses keta, hararanmu.
Rafi'a ya zanyi in banyi kukaba, ina zansa raina, Ina Yah Giɗi, ina Yah Gaini, Ina
Yah Seyo? Rafi'a sun kasarani sun rabani da yan uwana."
Kife kanta tayi jikin gadon da Ummiy ke kwance a kai, cikin murya mai cike da rauni
tace.
"Ummiy kiyi min mgna mana, Ummiy na inasu Ya Giɗi na ina Ya Gaini, ina Ya Lado, ina
ya Seyo, meya hanasu zuwa wurinki na tabbar in suna raye cikin ƙishin lfy, dole zan
samu ɗaya daga cikinsu a wurinki".
Mari matar Arɗo Bani ce wacce ta ɗan dawo haiyacinta ne, ta rumtse idanunta wasu
zafafan hawaye ne suka silalo mata, cikin sanyi tace.
"Shatu sun tafi kiwo ne, zaki gansu".
Jajayen idanunta ta zura mata,
Alamun tana son tabbatar da abinda tace matan.
Fahimtar hakane yasa ta gyaɗa mata kai alamar eh hakane.
Cikin son kontar mata hanlali ne, Rafi'a, tace.
"Kinjiko Aysha, to kiyi haƙuri ki nitsu in sha Allah dukkan tsanani yana tare da
sauƙi".
Kife kanta ta kumayi tana mai sake kuka mai ciwo a zuciya, gaba ɗaya jikinta
karkarwa yakeyi.
Haka dai sukaci gaba da bata baki, wai dan ta samu nitsuwa amman ina, fargabanta
sai tsananta yakeyi.

Su Bappa kuwa, isarsu Rugar Kikan ya ƙara tada hankali matasansu da suka dawo kiwo
da matansu da suka dawo tallan nono wanda sanadin basa nanne yasa suka tsira.
Gaba ɗaya Rugar ta birkice ta kiɗime.
Hankali dattawan nan yayi masifar tashi, ganin duk an karkashe musu, mafiya yawan
matansu yaransu da jikokinsu.
Especially Alhaji Haro, da iya cikin gidansa kawai saida aka samu gawar mutun goma
sha uku.
Koda aka jera masa gawakin suma yayi. Sai ga Tsoffin nan suna kuka cur-cur da
hawayensu, gwanin ban tausayi.
Ganin yamma na rufawane yasa,
Dattawan maƙotansu, mazansu suka fara wonke gawakin maza kamar yadda addininmu ya
koyar da mu.
Mata kuma sukayiwa mata wonka,
Kana suka sallaci Gawarwakin da a ƙalla sun kai mutun Settin da uku 63.
Kana suka rinƙa binnesu da taimakon Hausawa musulman cikin Numan da maƙotansu
fulani.

Gaba ɗaya garin yayi tsit ya koma tamkar kufayi. Sauran rayayyun sunyi Kuka har
muryoyinsu. Sun disashe.

A cikin Genaral Hospital Numan kuwa.


Musulmai Hausawa da Fulani, sune suka rinƙa kawai Fulanin Rugar Kikan taimakon
abinci.
Hankalin Aysha ya ƙara tashi ganin, har dare babu wanda yazo.

Hakama da gari ya waye.

Su Bappa kuwa da Arɗo Bani, Alhaji Haro. Malam Manu, Alhaji Umaru, tashin hankali
da kiɗima da firgici da ɓacin ransu ya tsananta, sabida ganin.
Duk Hukumar ma sun tafi,
Gashi babu wani babba da yazo ya duba halin da suke ciki, sabida ai su basu san da
cewar su Waziri sun zo tun jiyan ba.
Ransu yayi matuƙar ɓaci, ganin Gwamnatin jihar,
da Masarautar jihar, babu wanda ya tako ƙafarsa, yazo ya dubasu ko ya turo
wakilinshi.
Wato matsalarsu bata shafi kowaba.
Wannan abun shine mafarin Fara da baƙar Kaddarar Shatu a tarihin rayuwar ta, domin
iyaye da yayun wannan Rugar sun tunzura sun hasala, iya hasala, sun cika fam da
tarin baƙin cikin rayuwa, an rigada an taɓo zuciyar Fulani haka yasa zasu iya
gayawa kowa mgna dai-dai da abinda yayi musu.

A can Saudia kuma, komai na dawowarsu Sheykh ya kammala, cikin kwana uku, domin
hankalinshi yayi matuƙar tashi, jin irin kisan gillar da akeyiwa makiyaya, wanda
Maimartaba ne, ya gaya mishi komai, ya ƙara da cewa.
Yayi maza ya dawofa, don yana jiranshi suje tare yaje ya danni fulanin ya basu
hakuri ya kuma taushesu kada su ɗauki mataki da sunan ramuwa ko ɗaukar fansa.

Hakane yasa, Sheykh ya uzzurawa Haroon dole ya gama musu komai.


A kwanaki ukun.
Ranar Jumma'a da azahar jirginsu ya sauƙa, a birnin Shehu Sokoto.

Mai Alfarma Sarkin Musulmi yaso. Jikan nashi ya kwana, sai dai ina ya tike dole a
lokacin Haroon ya kuma saɓan mota suka fara kita hanyan kawoshi Adamawa.
Wanda sai ƙarfe uku da rabi suka isa.
Kasamcewar dama basu taso da wuriba.
Kasancewar isar dare sukayi babu wanda yasan Sheykh ya dawo.
Ƙasar sai Lamiɗo da kuma hadimanshi, uku kacal da sune suka tarbesu.

Sai washe gari da. Asuba, sautin muryarsa yana karatun limancin Sallah asuba ne ya
shaidawa mutanen masarautar Joɗa dawowanshi.

Gaba ɗaya kowa ya cika da mamakin, kana da farin cikin dawowanshi.

Duk da kasancewar sa, mai larurar da wasu ke mishi kollo ko kiranshi majanuni,
yasan kiyaye lokacin salla dama yinta cikin kushu'i.
Wannan shine ya hanashi sallame sallar, da akeyi yana cikin sahu na tara,
wanda jin muryar ɗan uwanshi ƙaninshi, ya sashi zubda hawaye masu ɗumi.
Ya Jafar kenan.
Jalal kuwa dake gefenshi wata irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da lumshe
kekyawan ƙwayar idanunsa da suke iri ɗaya dana Sheykh, ga kuma bacci daya cikasu,
domin daren jiya, Ya Jafar ɗinsu ya hanashi bacci.
Jin muryar ɗan uwansu da shi kaɗai ke iya sarrafa babban yayan nasune ya sashi
sauƙe, numfashin.
Jamil da Affan kuwa, wani irin yalwataccen murmushi ya sake jin muryar ɗan
uwansun.

Abbansu kuwa, shi dai har yau yana rasa me yakeji a kan ƴaƴan nashi, Especially
Sheykh, yana jin zuciyarshi na mishi nauyi duk sanda yaron baya kusa dashi, sai dai
kuma in yana kusa dashi sai yaji tamkar bai taɓa wani farin cikiba a rayuwarsa.
Ya sani tabbas su abun tausayawa ne, suna buƙatar kulawarshi fiye data kowa a
duniya, to amman ya rasa meyasa yake jin kamar baya son kusancisa dasu.

Maimartaba kuwa, suna cikin sahun na forko bayan liman,


Sai da sauran malaman fada.

A cikin gida kuwa, jin sautin zazzaƙar miryarshi yana rere karatun al'ƙur'ani, ya
ida fatiha, kana ya ɗaura, Arrahama,
daga bisani ya rufe da lakadja'akum, kafin ya tafi zuwa ruku'uh.

Haka nan Juwairiyya ta tsinci kanta da zubda wasu zafafan hawaye, masu ƙuna a rai,
tabbas ta sani.
Kasan cewar Sheykh a masarautar nanne kaɗai yasa, suke a ciki.
Ta sani in badon daraja da al'farmarsa ba, da tun tuni, an tabbatar da sunan
mijinta mahaukaci.
Hannu tasa ta share hawayenta cikin sanyi ta miƙe dan gabatar da sallan asuba, a
zahiri tace.
"Allah ne gatanmu, kaine GARKUWAR mu, Sheykh in baka nan gidan kanyi mana duhu,
ƙasar tanayi mana zafi."
Daga nan ta tada kabbara.

Ummi Jakadiyarsu kuwa,


Tana bayan gida, tana al'wala ta jiyo muryarshi, wani irin murmushi tayi tare da
yin mgna a baiyane.
"Dan Halak kaƙi ambato, ɗa ɗaya tamkar dubu, maƙiyanka fadawanka, sunyi sake ɗan
zaki ya girma, in sha Allah zaka dawo da farin cikin masarautarnan, sunyi sake, sun
bar kari tun ran tubani,
Muhammad Jabeer bawan Allah".
Haka ta fito tana wasu irin kalamai masu wuyar fahimta.
A can sashin Hajia Mama kuwa,
Wata kekyawar budurwa, ce.
Konce kan gado gefen Mama, datake zaune bisa sallaya.
jiyo muryashine ya sasu saurin juyowa, suka kalli juna,
Cikin tsananin farin ciki da tarin shauƙi budurwar ta diro daga kan gadon gaban
Mama ta zauna cikin zaƙuwa tace.
"Lah Mama, yaushe ya dawo! Muryar Sheykh Jabeer nake jifa! Mama ko dai dama yana
nanne?".
Wani irin kallo Mama tayi mata cikin sanyi da murmushi a fuskarta tace.
"Batul shine, ya dawo!."
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe cikin tarin shauƙi tace.
"Yes Mama, farin cikina ya dawo, kamar yasan, nazo.
Alhamdulillah, Mama Allah yana sona, ki gani ina zuwa, na samu baya nan, naji baƙin
ciki kamar in mutu jiya kafin inyi bacci, sai gashi Allah ya turo minshi cikin
dare ɗaya."
Murmushi Mama tayi, tana mai jin mmkin yadda Batul ke masifar son Sheykh har take
gaza ɓoyewa.
cikin haɗe fuska tace.
"To yanzu dai, sai ki tashi kiyi salla, tunda kinji muryar da kikafi so a duniya,
kin sauƙo kan gadon, sau nawa ina tadake, sai kiyi miƙa ki kuma konciya".
Cikin jin dadi tace,
"Wayyo Mama baccinne bai isheniba Allah ko jiya kwana nai ina zulumi, sai 3:44 na
asuba na samu bacci."
Murmushi Mama tayi kana ta miƙe ta kabbarta sallan.
Ita kuwa Batul, miƙewa tayi da sauri ta shige, bathroom tana cewa.
"Bari inyi wonka inyi salla, in shiga kitchin yau nida kaina zan mishi breakfast."
Tana faɗin haka ta shige ciki.

A masallaci kuwa, ana idar da salla kamar koda yaushe, da yawa basu fitaba saida
sunata lazumi.
Yayinda Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero da kuma Sarki Nuruddeen
Bubayero, da Habibullah Nuruddeen Bubayero, suka jero, suka fito a jere, domin su
kullum ana idar da sallan asuba, suke fitowa su koma cikin masarautar, inda kowa
zai wuce Side ɗinsa,
Yayi karatun qur'ani da kuma, Dua Azkar, inda har sai rana ta fito, kana suke ɗan
maida bacci, to kuma sudayin breakfast sai 11.
Suna isowa tsakiyar masallaci, Sheykh yaji an ruggumeshi ta baya, yasan mutun ɗaya
ne rak zai mishi haka a cikin masallacin,
Ya Jafar ɗinsu.
Yana juyowa kuwa yaga shiɗin ne.
Ruggumeshi yayi gam-gam Jalal, kuwa ido ya zuba musu,
shi kuwa Sheykh hannu yasa shima ya ruggume ɗan uwan nashi.
Yayinda ya zubawa Jalal kwayar idanunshi, ya rame sosai, hancinsa ya ƙara fitowa,
sai sajenshi daya ƙara yin lib, da uban gashin daya tara, yayi wani kafurin aski.
Ramar da Jalal yayi ta daki zuciyarsa sosai baya son ganin ƙannen nashi cikin halin
matsala,
a hankali ya janye kwayar idanunshi ya maidasu kan Jamil da Affan dake gefen
damanshi,
Calikan ƙanenneshi kenan ba,
sheƙiyancinsu ɗaya, baki suka haɗa wurin cewa.
"Sabahul Noor Al'Sheykh".
A hankali ya ɗan motsa laɓɓansa, yana mai kallonsu yace.
"Sabahul khair ya Uktih".
murmushi sukayi, suna mai jin son ɗan uwan nasu,
Abbs da Maimartaba kuwa, kai suka ɗan jinjina kana sukayi gaba,
Ganin hakane suma suka bisu, a baya,
shi kuwa Sheykh hannu yasa ya shafa kan Imran da yanzu ya iso gabanshi cikin sanyi
yace.
"Hamma Jabeer barka da safiya".
jin yana shafa kanshine ya sashi lumshe ido, inama ace yadda Hammanshi ke nuna
mishi so haka zai shirya da Mom ɗin shi, yana masifar son ɗan uwanshi baya jin
daɗin yadda yake ganin wata iriyar mu'amala tsakanin Mom da yayunshi.

Ganin Sheykh yaja hannun Ya Jafar sun tafine yasashi bin bayansu.

Ƙofar dake cikin masallacin wacce zata ɓulla cikin masarautarsu sukabi.

Suna shiga, kowa yayi sashinsa sabida sun sani ko sunbi Sheykh yanzu ba lokacin
mgna bane, karatu zaije yayi.
Shi kuwa Sheykh yana riƙe da hannun Ya Jafar ɗinsa suka shiga side ɗinsa,
inda ya samu hadimai masu tsaron ƙofar, suna tsaye.

Suna shiga, tamtsetsen falon nashi kai tsaye ya nufi wannan babbar kusurwar da zata
sadashi da.
Big part ɗin shi,
Suna shiga suka ɓulla cikin wani mashahurin, falo, wanda yaketa tashin ƙamshi mai
masifar sanyi da daɗin shaƙa,
a hankali ya zauna bisa kujerar 3 str kana yaja hannun Ya Jafar ɗin suka zauna,
tare.
A hankali ya juyo kanshi ya zuwa ɗan uwanshi idonu,
Karatu yakeyi kamar koda yaushe, yanayi cikin tsantsar lugga da tajwid, kana ga
kushu'i,
Suratul yaseen yake karanta,
bisa alamu kenan ya kusa yayi sauƙa, domin step by step yake bin surorin, in yayi
sauƙa sai ya sako daga sama, baya mancewa, kuma baya birkitashi,
Wannan rahamar da Allah yayi mishi, duk da anso a maidashi majanuni, sai Allah yayi
mishi muwafaƙa da littafinsa maisarki, yazama sihirin yayi mishi tasiri tako ina,
amman banda gefen addininshi.

Wasu irin hawa masu ƙunu yaji suna tsatstsafo mishi, cikin jijiyoyin kekyawan
idanunshi,
sabida ganin yadda Ya Jafar ɗinshi ke karatu yana, kuka ya za'ayi ya sama mushi
farin ciki a rayuwarsa ta ina, zai san me ke cin zuciyar ɗan uwan nashi.
Jin yadda ransa ke ƙuna da tafasa ne, yasashi. Komawa ya jingina bayanshi da jikin
kujer, kamar yadda Jafar yake mahaddacin haka shima settin kab tana kanshi,
Ido ya lumshe tare da yin bisimilla kana ya fara karu inda ya ɗauko daga forkon
suratul. Noor ya farayin ƙasa.

Saida sukayi awa ɗaya cur kana,


Suka fara Azkar, wanda sai da sukayi 23 minutes suna, jero addu'o'in cikin harshen
dake nuni da cikekkiyar jimla ta larabci da lugga.
Koda suka shafa, sai ya ɗan kalli ɗan uwanshi dake riƙe da hannunshi gam.
Ya lura Ya Jafar na tsoron kada ya kuma tafiya ya barshine, yasan duk sanda yayi
doguwar tafiya ya dawo, haka yake liƙe mishi.
Hannunshi yasa, ya share mishi hawayenshi kana,
ya miƙa tare da jawo hannunshi,
yasani yanzu lokacin yin baccinsa ne,
Side ɗinsu, ya nufa dashi, ta wata ƴar siririyar hanyar dake tsakanin sashukansu.

A babban falon suka samu Juwairiyya.


Tana ganinsu, ta miƙe da sauri, fuska ɗauke da murmushi kana ido na tsatsafo da
hawaye tace.
"Barka da dawowa, Sheykh, Alhamdulillah zamu samu nitsuwar Ya Jafar".
Kanshi ya sunkuyar sabida bai son ganin hawayenta,
Hannunshi ɗaya yasa yana shafa, kam Mimi data ruggumeshi ta ƙafafunshi,
cikin murmushi ta nitsuwa yace.
"Mimina anyi sallako?".
Cikin sauri ta gyaɗa kanta alamar eh,
Shi kuwa kanta ya kuma shafawa tare da cewa.
"Kinyiwa Ya Jafar ɗina Addu'o'in Allah ya bashi lfy ko?".
Kanta ta kuma gyaɗawa tare da cewa.
"Eh nayi mishi".
A fakaice ya ɗan kalli Juwairiyya dake rugume da yarsu karamar, cikin sanyi yace.
"Kukan bashi da wani amfani, muyi ta mishi addu'a, in sha Allah dukkan tsanani yana
tare da sauƙi.
Ina roƙon Ubangijina mahaliccina a cikin dukkan Ayyukana, daya aramin rai da lfy,
kada ya ɗauki raina ko na ɗaya daga, cikinmu, har sai ya nuna mana lfyar ya Jafar,
ya faɗa mana abinda ya maidashi haka a dare ɗaya, nasani shine ɗaya rak yasan meya
faru, a dare mai duhu da muni na rayuwarmu".
Cikin sanyi tasa tafin hannunta ta share hawayenta.
Shi kuwa Sheykh, wucewa yayi da Ya Jafar ɗin har cikin ɗakinshi,
bisa gado ya zaunar dashi, kana yacewa Juwairiyya dake biye dasu a baya.
"Yasha mgninshi ne?".
Miƙo mishi gorar ruwa da magungunan tayi tare da cewa.
"Yaƙi sha, dan daren jiya kwana yayi, baiyi bacciba,
Jalal nan abin tausayi, ko nanda can bai isa ya fitaba,
sai ya bishi,
Kullum sai Jalal yayi kuka".
Wasu tafasassun hawaye ne suka cika masa ido,
A duniya shi baya son yaga ko yaji na miji na kuka, domin shi ya sani, duk abinda
kaga yasa na miji kuka to abun ya tsananta musamman maza irin Jalal yasan ba
ƙaramin raunine zaisa Jalal zubda hawayeba.
Shiyasa, shi kukan mace bai taɓa damunshi ba a zuciyarshi, domin mutane sunce in
kaga mace na kuka to kayi dariya kafin ka tambayi meya sata kukan. In kuma kaga
namiji na kuka to kaima ka fara kukan kafin ka tambayeshi meya sashi kuka.
Shiyasa shi kukan mace, bai shiga ranshi, sabida yanaga mata sun iya kukan
munafurci da kukan gulma dana ha'inci da yaudara,
shiyasa in yaga mace na kuka haushinta yakeji a ransa.

Maganin ya bashi sannan ya kontar dashi kafin ya wuce, ya koma sashinsa.

Yana shiga, falon, ya samu, Haroon ma zaune, shida Jakadiyarsu,


tana ganinshi ta faɗaɗa fara'arta cikin kula da so mai zurfi tace.
"Farin gani, Garkuwa, Sheykh, Limamin Masallacin Moddibo Joɗa Jikan sarki mai
hatimin sarauta."
Gefen Haroon ya zauna tare da rumtse idonshi cikin nitsuwarshi yace.
"Ummi ki bari mana, babu wani sarkifa sai Allah, Ummi nace ki dena min irin
waɗannan zantukan masu sa kan ɗan adam girma".
Murmushi mai cike da tarin so, sabida ita dai jinshi take tamkar ɗan da raina a
cikinta ta kuma haifeshi,
Koda yake hakan baya rasa nasaba, da cewar itace jakadiya gareshi tun randa aka
haishi bacci kawai ke haɗashi da Mamanshi. Sai dai takanzo inda suke su sashi a
tsakiya sunai mishi wasa da kallo mai cike daso."
Ganin tayi kasake tana kallonshi ne ya sashi ɗan gyara zama, cikin girmamawa yace.
"Ina kwana Ummi, ya su Jalal?".
Murmushi ta kumayi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah, Jalal ya zama mazaunin gida, tunda ka tafi sabida, duk inda
yaje , Jafar zai bishi,
sai dai kuma abokanshi masu shigar banza har gida suke biyoshi,
wani sa'in kwana kiɗe-kiɗe da rawa sukeyi a sashinsu, suna shan sigari.
Wasu lokutan dole, Jamil yake gudowa ya bar musu can yazo wurina yake kwana, ko ya
shigo nan wurinka".
Kanshi ya ɗan maida baya, a hankali yace.
"Ummi Jamil da mata?".
Kai ta ɗan kauda kana a hankali tace.
"Tafiyar bata sauya zaniba, kwanaki uku da suka wuce wata tazo daga, Kano wai ita
ƙawarshi ce, kwananta biyu, a sashin Juwairiyya, da Abbanku ya samu lbrine ya
korata".
Cikin sanyi yace.
"Ummi waya gayawa Abba?".
Kai ta jujjuya tare da cewa.
"Allahu alamu, yadai ji har yace zai kori Jamil ya bar mishi gidanshi, to da yake
Jafar yana wojen ne, sai ya riƙe hannun Jamil yayi ta kuka, hakane yasa ya barshi,
Mamanku kuwa kuka tayi- tayi".
Wani irin zazzafan numfashi ya fesar kana, ya juyo ya kalli Haroon a hankali ya
kuma kalli, Jakadiyarsu, cikin sanyi yace.
"Basaji Ummi suna samin tunani a raina, ga wannan kuma shima ƙato dashi, sai ya
ruggumi waya yayi ta chatting ko waya Da waccar yar mitsitsiyar yarinya Jannart
ɗin.
Da asuba nayi ta tadashi yafi sau uku baya tashi, sabida bai bacci da wuriba, gashi
ko cikekken jam'i bai samuba".
Ido Haroon ya lumshe tare da cewa.
"Jiya dai ba chatting ko waya da Jannart bane, ya hanani baccin da yasani makara,
Ummi ƙarshen darefa muka iso sabida ya sani dole sai mun taho nan."
Murmushi Ummi tayi kana tace.
"To Haroona ka kiyaye batun tsaida salla kan lokacin ta, kaji ko?."
Hararan Sheykh yayi tare da cewa.
"To Ummi".
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin muryar kula tace.
"Haroona yaushene bikin naku kam?".
Kanshi ya ɗan shafa kana yace.
"Uhum Ummi saura watanni bakwai in Allah ya yarda, Ni dai zanyi aure in bar babban
tuzurun".
Bai kulashiba saima tashi yayi ya nufi bedroom.
Ita kuwa Jakadiyarsu cikin yin ƙasa da murya tace.
"Yauwa ya dai-dai ta da Jazrah ko?".
Baki ya ɗan turo tare da cewa.
"Uhum Ummi gudowafa yayi, kuma wlh in ba dagewa kukayiba, wannan bauɗeɗɗen ɗan
naku, ustazu bazaiyi aureba, mutun duk yadda akayi dashi sai ya kauce".
Kai ta ɗan juya ta kalli ƙofar ɗakin daya shigan,
cikin yin ƙasa da murya tace.
"Uhum ga zahiri ko mgnar aure akayi sai ya bar wurin."
Haka sukayi ta hira da yake akwai sabo tsakaninta dashi.

A sashin Hajia Mama kuwa, ita da kanta da kuma, Batul suka shiga kitchin sai kuma
yardaddun hadimanta mutun biyu.
Breakfast mai kyau suka, haɗawa Sheykh.

Yayinda Aunty Juwairiyya ma ta shiga kitchin da kanta, ta haɗa mishi breakfast.

Jakadiyarsu kuwa da Jamil da Jalal da Affan Haroon suna falon sunata hirarsu.

A tare hadiman Mama dana Juwairiyya suka kawo, abin kari.


Suna fita ba da ɗewa, hadiman Gimbiya Aminatu kakarsu kenan.
Suka shigo suma da abun kari.

Suka jera komai kan babban dinning table dake dinning area'n dake falon.
Bayan sun fitane.

Suna cikin hira, sarƙin ƙofa, ya shigo, ya shaida musu, ga saƙo an kuma kawowa.
Jamil ne ya bada daman a shigo.
Nan ya juya ya fita,
jim kaɗan, aka turo ƙofar.
Cikin mamaki suka zuwa ƙofar ido.
Ganin M....!

*Wannan shafin nakine ke ɗaya MRS SARDAUNA, Sheykh yana godiya da soyayyarki
gareshi. Domin duk masoyanshi bayanki sunka biyo*

By
*GARKUWAR FULANI*[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 14

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🤴🏻💘
🦚🤴 🏻 💘

*Daga gobe ne, FREE PAGE zai ƙare, in da zan saki page 15-16 daga su kuma in kin
sake ganin littafin GARKUWA a woje ba cikin groups ɗin da na buɗe nasa wanda suka
biya ba, To na satane, na waɗanda basu san darajar iyayenka da girman Allah da
Manzonsa suka fitar ne, to ke kuwa in kin san darajan iyayenki da girman Allah da
Manzonsa, kada ki karanta na sata, akwai group ɗin ɗari uku kacal ban tsauwala ba
dan nasan halin TLC da muke ciki a ƙasar nan ga mai wadata wacce take da dama taga
zata iya biyan na Special Group 1k ne rak. Zaki turo ta asusuna 0005388578 Jaiz
bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai
09097853276, kuma ƴan 300 zaku iya turowa ta ac na ɗin, in kuma baki da dama to
turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number dai 09097853276. Dan Allah da
Manzonsa in kin san zaki fitarmin da littafi biyoni PC ki gaya min wlh zan baki
kuɗinki in fiddaki group salum-alum, ina kuma jin san saya zakiyi ki fidda na
roƙeki da Allah da Manzonsa wanda bayansu babu wani kada ki saya ki riƙe kudinki ki
barni in riƙe littafina🤗*

FREE PAGE, daga gobe dai zasu ƙare ki biya kuɗin ki in kinada niyan saya.

Ganin Mom ce, yasa fuskokinsu ya baiyana abinda ke cikin zuƙatansu.


Cikin ƙasaita, Mom ke tafiya, hadimanta biyu na biye da ita da manyan kuloli na
al'farma.
Jakadiyarsu ce tayi murmushi mai kama da yaƙe, tare da rusunar da kai, cikin
girmamawa tace.
"Barka da shigowa, Gimbiyar ahlin masarautar Joɗa.
Cikin isa da ƙasaita ta gyaɗa mata kai bayan ta zauna, gefen Jamil dake ruggume da
waya kamar, abin masifa,
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Jalal daya haɗe fuska,
Juwairiyya yace ta ɗan gyara zamanta tare da cewa.
"Barka da safiya Mom".
Murmushi mai wuyar fassarawa tayi, tare da taɓe baki, a gyatsine tace.
"Barka dai". Sai ta kuma juya ta kalli inda Jakadiyarsu ke zaune, cikin isa tace.
"GARKUWAN YA FITANE?".
A daƙile Jalal yace.
"Yana ciki kuma hutawa yakeyi".
Ko inda yake bata kallaba tace.
"Jakadiya ina buƙatar ganinshi, yanzu".
Cikin biyeyyarta tace.
"Ranki ya daɗe, in zaton bacci yakeyi".
A taƙaice tace.
"A tadoshi".
Haroon dai ido ya zuba musu yana ganin ikon Allah, kowa ji da kai da ƙasaita.
Juwairiyya ce ta ɗan kalli Haroon ɗin cikin sanyi tace.
"Ukhti, shiga ka sanar mishi".
To kawai yace, kana ya miƙe ya shiga bedroom ɗin, da Sheykh ya shiga mituna ashirin
baya,
kasake yayi a bakin kofar ganin babu kowa a cikin bedroom ɗin.
A hankali ya tako ya shiga ciki, bakin ƙofar bathroom ya ɗan matso, kunnenshi ya
kasa wai a lissafinshi ko zaiji mitsin ruwa.
Shiru babu kowa a ɗakin da kuma bathroom ɗin.
Ko ina yayi tsit sai wani fitinenne sanyi daya cika ɗakin, wanda sai sautin
A/C dake busawa shuuuuu a hankali.
Waige-waige yayi ganin babushi babu, motsinshi ne, ya sashi ɗan ɗaga murya yace.
"Jabeer! Jabeer!! Jabeer!!!".
Jin shirune yasashi sa hannunshin ya ɗan ƙonƙosa ƙofar bathroom, still shiru.
Hakane yasa ya ɗan tura ƙofar, wayam baya ciki.
Ganin hakane ya sashi juyawa,
shima ɗin cikin takun ƙasaitar ya fito gefen Jalal ya zauna tare da kallon
Juwairiyya,kana yace.
"Baya cikifa".
Wani irin kallo Mom tayi mishi, wanda yake nuna abinda ke bakinta, cikin ɗan sakin
fuska yace.
"Allah kuwa Mom baya ciki".
Kanta ta gyaɗa tare da yunƙura ta tashi tsaye.
Kana a hankali tace.
"Uhummm". Sai kuma ta juya ta kama hanyar fita, hadimanta na biye da ita a baya.
Har yaje bakin ƙofa ta juyo tare da cewa,
Ga breakfast ɗin Garkuwa".
Haroon ne yayi godiya kana ta juya ta fita.

Cikin mmki Haroon ya kalli Jamil tare da cewa.


"Jamil baya cikifa".
Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Kun dai haɗa baki, kunƙi ya fito, ya gaisa da Mamanshi".
Jalal ne ya ƙara tsuke fuskarsa tare da cewa.
"Mamarshi ko makirarshi".
Jakadiyarsu ta ɗan gyara zama tare da cewa.
"Uhummm, sanin halin mutum sai Allah".
Sai kuma ta kalli Haroon tace.
"Haroona kace mishi yazo yayi karin kumallo, kace mishi daga sashin Gimbiya Aminatu
ce, ga kuma na Juwairiyya".
Cikin jaddawa yace.
"Allah kuwa Ummi baya cikifa".
Da mamaki a fuskokinsu suka ɗan kalleshi, Jamil ne yace.
"Bai fita bafa".
Juwairiyya ce, ta amshi zancen da cewa.
"To kuma dai bai biyo nanba, tunda ya shiga bai fitoba".
Shi dai Haroon Ido ya zuba musu, ganin kamar basu yarda Jabeer baya cikiba.
Kuwa hakanne, saida Jamil yaje ya duba babu shi a ciki babu alamarsa.

Cikin tarin mamaki ya sanar musu, baya nan ɗinfa.


Jalal ne ya ɗan kauda tunaninsu da cewa.
"To kunata surutu, ta ina zakuga sanda ya fita, kai Jamil hankalinka duk na kan
waya ina zaka ganshi."
Cikin kula Jakadiyarsu tace.
"Kaga fitarsane?".
Baki ya ɗan taɓe tare da cewa.
"Ni ban ganiba, na dai san shi ba kuɗi bane bare ya ɓata, ku jira zaku ganshi".
Da haka sukayi amanna dan a zatonsu yaga fitarshi kawai bauɗewarshi ne yasa bazai
sanar musuba.

A can cikin fadar Masarautar Joɗa kuwa, falon sashin mai martaba Lamiɗo, cike yake
da ƴaƴanshi maza, ziryan, wanda kullum iwar hakan suke haɗuwa domin gaidashi kana
su gaisa da juna, ya tambayi lfyar ko wanne ɗanshi da ahlinshin.
To yau ta kasance jumma'atu babbar rana, wanda kuma, duk safiyar jumma'a.
Cikin wani ɗakin gadon sarautarsu, yakan shiga shida kanshi, yake tsabtace wannan
ɗakin duk ran jumma'ar duniya, a tarihi da tsarin masarautarsun babu wanda zai
shiga ɗakin sai wanda yake, matsayin Sarki.
Babu wani wanda ya taɓa shiga wannan ɗakin, sai wanda yake sarki.

Suna cike a falon a ƙalla sun kai su bakwai dukansu. Manyan mutanene masu tarin
wadatar duniya, jinin sarauta na yawo a jikinsu.
Suna zaune kamar yadda kullum suke zama, suna ɗan hira a tsakaninsu.

Habibullah ne, zaune a can tsakiyarsu a matsayinsa na shine babban ɗa ga Lamiɗo,


hannunsa riƙe da.
Carɓi, sai gefen damansa, Alhaji Sani, sai kuma Barrister Kamal, kana sai. Dr
Aliyu, kana sai, Badamasi, Nasiru, basiru.
Dr Aliyu ne, ke gefen daman Habibullah, bisa alamu duk mgna yakeyi mishi a kan
lfyarsa.
Bappa Nasiru, wanda shine, yake bin Habibullah a girma sai dai uwarsu ba ɗaya ba,
gyara zama yayi tare da jan dogon tsakin da yasa duk suka meda idonsu kanshi.
Cikin kula Habibullah yace.
"Lfy dai Nasiru?."
Wani irin kallo mara daɗin gani ya watsa mishi tare da cewa.
"Yes lfy lau, sai dai mu nan duk muna da aiki, ba zauna gari banza, irinka bane,
kowa yanada hidimar yi gashi har yanzu,
Lamiɗo bai fitoba".
Murmushi yayi ba tare da yaji ciwon abinda ya gaya mishibs, a hankali yace.
"To Nasiru, ai duk saurinka kayi haƙuri dai ya fito, kaga lfyarsa yaga taka, tunda
shi bai gajiya da bincikar lfyarmuba, ai muku wa bazamu gazaba.
Domin abune mai wucewa".
Wani irin kallo mai cike da tsana da tsoggoma ya mishi tare da kauda kanshi.
Basiru ne yayi dariya alamar jin daɗin kallon da ɗan uwanshi yayiwa Babban yayansu
da suke ƴan uba.
shi kuwa Habibullah Abbansu Sheykh, kauda kai yayi kar bai ganiba.

Kusan a tare suka miƙe gaba ɗayansu,


tare da haɗa baki wurin cewa.
"Barka da fitowa, Mai alfarma Lamiɗon Joɗa."
Murmushi yayi tare da kallon ƴaƴan nashi ɗaya bayan ɗaya, a hankali ya ƙarasa
fitowa, hannunshi sarƙafe da hannun Jabeer.
Wanda baiyanarsa yasa, gaba ɗaya suka zazzaro ido. Cikin tarin mamaki, al'ajabi,
firgici, kaɗuwa, gamida tsayawar idanunsu kan ɗan babban yayan nasu, cikin wani
irin daskarewa, suka juyo suka fuskaci, junansu wannan ya kalli Wannan wannan ya
kalli wancan.
Murya a daburce, Nasiru ya nuna Jabeer dake tsaye, cikin wani masifeffen al'kyabbar
mai masifar kyau da zadan gaske, cikin ƙafewan yawun baki yace.
"Ka gafarceni Lamiɗo, me idonuna ke gani, daga ina ka fito da Jabeer? Me kayi
dashi? Meye ma'anar hakan? Mu duk ƴaƴan ka bamu kai ka shiga damu ba sai shi?".
Cikin tsare fuska irin ta manyan sarakai dattawan,
ya zubawa, Nasiru idanu, wanda dole tasa ya hadiye rahowar maganar tasa.
Habibullah kuwa, wani irin rawa da karkarwa jikinsa ya fara.
Wani masifeffen tsoro da fargabane ya rufeshi akan ɗan nashi, koda dai baya jinsu a
ranshi kamar sauran ƴaƴanshi, hakan bai hanashi tsoro da fargabar abinda zai cutar
dasuba. Barrister Kamal kuwa.
Wata irinyar madifeffiyar zuface ta keto mishi daga saman kanshi har tsakiyar tafin
sawunshi.
Lokaci ɗaya yaji wani irin abu ya saki ƙahon zuciyarshi,
Maƙoƙoronshi ya bushe ƙamas,
duhun daya rufe mishi idone yasashi komawa zaune.
Dr Aliyu kuwa, wani irin murmushi yakeyi yana kallon ɗan babban wansun.
Shi kuwa Lamiɗo hannun Jabeer ya kuma ja, wanda yake motsa laɓɓansa a hankali yana
tasbihi kamar yadda ya saba.
Zama yayi kujerarsa ta musamman, kana Jabeer kuwa ya zauna gabanshi.
Cikin tattaro yawun baki Barrister Kamal yace.
"Barka da safiya. Sarkin Joɗo.
Sai ya kuma danne tarin baƙin cikinsa yayi mishi rumfa da fuskarsa ta zahiri kana
ya kalli Jabeer da ya ɗan sunkuyar da kanshi tare da gaidashi.
Cikin dakiya yace.
"Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Joɗa.
Yaushe a gari".
Kanshi ya ɗan kauda tare da cewa.
"Daren jiya".
Nasiru ne ya katsesu da cewa.
"Lamiɗo, ɗakin sarautar sarakunan Joɗa kuma ya zama kowa zai iya shigane?".
Bai kulashi ba, har saida suka gaisa gaba ɗayansu, kana, ya fuskancesu, duka cikin
hikima da, kaifin basira yace.
"Rigar sarautarsu ta GARKUWAN FULANI, na bashi.
Sabida akwai tafiyar gaggawa da zamuyi zuwa, Rugar Bani, da ƙaɓilun wurin suka far
musu da kisa."
Kai suka gyaɗa alamun gamsuwa, kana duk, ya sallamesu.

Duk suka fita kowa da abinda ke cikin ransa, da zuciyarsa.

Bayan fitansu ne ya kalli Jabeer cikin, tarin kula yace.


"Kaje ka shirya kazo mu tafi".
Kanshi ya kuma rusunarwa cikin ladab yace.
"Allah saine, mu bari sai bayan sallan, jumma'a ina munyi jam'i anan, mu tafi gudun
kada muje bamu dawoba kafin lokacin sallan."
Gyara zamanshi yayi tare da gyaɗa kai kana yace.
"Haƙƙun kayi, gsky to mu bari sai an sauƙo mutafi, in yaso muyi sallan la'asar a
can."
Da Wannan shawarar suka bari sai bayan sallan, azahar ɗin su tafi.
Sun daɗe suna tattaunawa kafin, ya sallameshi ya tafi, shi kuma ya nufi fada.

A falonshi kuwa, yana shigowa duk suka zuba mishi ido, da mamaki cikin zaƙuwa Jamil
yace.
"Hamma Jabeer wai ta ina kabi ka fitane? Duk bamuga fitankaba".
Kanshi ya mirgina, alamun gajiya, kana a fakaice ya kallesu baki ɗayansu, tare da
cewa.
"Sama".
Murmushi sukayi baki ɗayansu, sabida fahimtar amsar daya basu, na nuni basuga sanda
ya fita bane.

Bisa wata tattausar doguwar kujera ya zauna.


Kana ya fuskanci ƙannen nashi da kyau.
Jalal ne ya ɗan sunkuyar da kanshi, ganin yadda Hammanshi ya zuba mishi ido, Jamil
kuwa, kanshi ya ɗan rausayar tare da katse wayar da yakeyi, ya fuskanci ɗan uwan
nasu,
Cikin yin fiki-fiki da idanu yace.
"Barka da safiya Hamma Jabeer, ya hanya?".
Alhamdulillah, yace mushi a taƙaice, kana ya ɗan gyara, hiramin dake bisa
kafaɗunshi.
Jalal ne ya ɗanyi baya tare da lumshe idonshi cikin saisaita muryar da indai da
Hammanshi zaiyi mgna to sai ya nitsu ya gyarata,
Domin yakanji yanada rauni duk sanda yake gaban Hammanshi, yana ji tamkar a gaban
mahaifinshi yake.
Cikin sanyi yace.
"Ina kwana? Hamma Jabeer, ka dawo lfy t
yasu Sitti?".
Ido ya ɗan kauda kana yace .
"Alhamdulillah, Jalal ya jikin Ya Jafar?".
Kanshi ya ɗan jujjuya kana a hankali yace.
"Kalmace dai ta musulmi, koda cuta babu sauƙi ya zame mana ɗa'a muce, da sauƙin,
amman a zahirin gsky ciwon Ya Jafar babu sauƙin, komai yaci tura, abubuwan sun
yawaita".
Ya ƙarishe mgnar tamkar zaiyi kuka,
ganin hakane yasa Jabeer ɗan kauda kanshi, Allah yasani, baya son ganin ƙunci ko
baƙinci ko wata damu a fuskarsu, sabida ya ɗauka cewa Allah ya barshi da rai da lfy
ne a tsakiyarsu, su da akewa kallon marasa lfy ya zame musu Garkuwa. A hankali ya
miƙe cikin kula ya kallesu, murya a ɗan macce yace.
"Kuzu kuci abinci".
To sukace baki ɗayansu, kana duk suka nufi, dinning table ɗin.
Wanda yake cike da abinci kala-kala.
Juwairiyya ce ta sakawa kowa abinda yake buƙatar ci,
Shi kuwa Sheykh sai jujjuya mata kai yayi alamar babu abinda zaici.
Ya dai zauna yana kallonsu,
Ummi kuwa, tana gefenshi.
Kanshi ya ɗan juya ya kalli Haroon dake shan tea kuma still wayarshi na kunne yana,
mgna da Jannart,
ɗan gajeren tsaki Jabeer ya ja, jin Haroon na cewa.
"Ina yin breakfast ne, ke me kikeyi? Bacci? Ko kwaliya? Ko kallo?".
hannunshi yasa ya zare wayar kana ya katse kiran tare da mishi nuni yaci abinci
kafin ya tsaya yin waya.
Cikin haɗe fuska Haroon yace.
"Ka ganka ko? Ni shiyasa har tsoron zama kusa da kai nakeyi, sabida tsarabe-
tsarabenka nada yawa, yanzu zaka fara jawowa mutum aya da hadisai, kana wani, abu
kaza ba laduban kaza bane, in an jika kayi doguwar mgn to an sosa maka wuri biyu,
ko ayar Allah, ko wannan mulkin da kake cewa an liƙa maka jaraba".
Jamil ne yayi ƴar dariya tare da cewa.
"Mulkin nema jaraba a wurin shi ko? Gacan wasu na neman, zaunece sabida Garkuwan da
aka bashi".
Jalal ne ya ɗan tsuke fuskarsa tare da cewa.
"Ni kaina Wannan GARKUWAN bai wani burgeniba, sabida baya cikin, masu iya gadar
mulki, sabida shi ai ba jikan sarki ta wurin ƴa mace bane, jikanshi nefa ta wurin
ɗa namiji ta yaya zai bashi Garkuwa?".
Ummi ce taja wani dogon ajiyan zuciya tare da cewa.
"Uhummm ta yaro kyau take bata ƙarko, to kai Jalaluddin, yanzu Jafar da aka bashi
Galadima, wani hali yake ciki? Tun randa aka naɗa masa sarautar me mutane suke
kallon ya zama? Dukfa duniya kallon majanun akeyiwa Jafar".
Juwairiyya ce ta ɗan rumtse idonta tare da cewa.
"Ni banyi fataba, banso a sake bawa Kowa wani mulkin da nasan baza'a barku lfy ba,
shi Lamiɗo, meyasa ko ƴaƴan nashi babu wanda ya bawa mulkin komai?".
Da sauri Ummi tace.
"Sabida muddin yace zai basu sarautu, to wasu zasu hallaka wasu".
Cikin daƙilewa Jalal yace.
"Ok shine sai ya zaɓi ƴan ɗakinmu a matakan zakarorin gwajin dafi? Ya bawa Ya
Jafar Galadima, yaga yadda aka medashi dare ɗaya, da rashi da bazamu samu
madadinshiba a duniya, an cire hankalin mahaifinmu a kanmu, sannan ya kuma bawa
Hamma Jabeer wani mulkin, salon a sabautashi kenan, nest target nasu kuna, wato a
kanshi ne?".
Shiru sukayi jin Jabeer na cewa.
"Azzannu zambu walau kana haƙƙun, na haneku da irin waɗanan zantukan, babu wanda ya
isa, ya cutar da wani sai Allah, domin shine mai rayawa, kuma mai kashewa, mai
badawa, mai hanawa, mai cuta mai waraka. Ummi har kema, ya zakiyi ki zauna kina
gaya musu hakan, to waye zai cutar damu, acikin ahlinmu, daga ƙannen mahaifinmu fa,
sai ƙannen kakanmu, sai matasansu da jikokinsu, sai kuma ƴan uwanmu, dan Allah ku
bar munanawa mutane zato."
Juwairiyya ce ta ɗan girgiza kai.
Shi kuwa Jabeer, cikin bada umarni yace.
"Juwairiyya jeki duba Ya Jafar, nasan zuwa yanzu ya tashi daga baccin."
To tace, kana ta miƙe ta nufi tsakiyar falon. da sauri ta tsaya tare da ɗan raɓawa
gefe, sabida ganin Gimbiya Saudatu, na tsakiyar falon.
Da sauri ta ɗan rusuna tare da cewa,
"Barka da fitowa Gimbiya Saudatu".
Zama tayi bisa kujerar da Jabeer ke zama, ɗaura kafarta tayi ɗaya kan ɗaya.
Hadimanta, biyu ne suka zauna gefe da gefenta.
Fuskarta babu wata alamar annuri, sai tsantsar tijara, cikin isa da ƙasaita tace.
"Kai Jabeer!."
Ido Jakadiyarsu ta zazzaro cikin firgici da tsoro ta kalli Jabeer da a take
fuskarshi ta sauya launi,
cikin rawan jiki da tsoro tayi ƙasa da murya tare da cewa.
"Jabeer ka amsa, Gimbiya Saudatu ce, da kanta."
Jalal ne da Jamil suka kalli juna, kana suka maida idonsu, kan Hamman nasu, da ya
lumshe idonshi ya koma ya jingina tamkar badashi akeyi ba, kamar daga sama suka
jiyo muryar Gimbiya Saudatu tana ratsa kunnuwansu.
"Kai Jabeer, ka fito kazo nan, ina nemanka".
Still bai buɗe idanunshi bama, bare ya amsa ko yunƙurin tashi,
sai dai laɓɓan bakinshi da suke motsawa yana maimaita sunan Allah a zuciyarshi da
harshenshi.

Zuwa yanzu Gimbiya Saudatu tayi masifar kufula, cikin wani irin mugun kallo ta
kalli Juwairiyya da jikinta ke baiyana tashin hankali ta, cikin isa da ƙasaita
tace.
"Ke maza wuce, kije tun wancan karen larabawan da suka turo ahlin masarautun Fulɓe,
dan samun damar maida masarautun a hannunsu, kice mishi yazo dan kan uwarshi".
Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi, wani irin bugawa zuciyarshi ta farayi a
saba'in.
Ita kuwa Juwairiyya kasa motsawa tayi daga inda take tsayen.
Ummi kuwa cikin firgici, ta kalli Jalal daya miƙe tsaye tamkar wanda aka tsabura.
Jiki na rawa ya ture kujerarshi, zaiyi baya ya fita ya nufi inda taken.
da sauri ya juyo cikin tarin zafin rai jin an riƙe mishi, hannunshi.
ganin Hamma Jabeer ɗinsune ya damƙi hannunshi ne ya sashi, taune lips ɗinshi da
masifan karfi.
Jamil kuwa ido ya zubawa Hamman nasu yana ganin yadda jikinshi ke karkarwa, kowa ya
sani duk duniya babu abinda yake saurin harzuƙa Sheykh sama da a zagar mishi iyaye
Especially uwa! Haroon kuwa zuru yayi da idanu yana kallon ikon Allah.

Ummi kuwa cikin rawan murya da tsoro da firgici ta kallesu murya na rawa, tace.
"Dan Allah Jabeer, kaje, tashi muje ka amsa kiranta dan Allah badon niba, dan
darajar Manzon Allah".
Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin zubewa kan guiwowinta,
Jin kalaman da tayi mishi da gane nufinta na rusuna mushine ya sashi saurin miƙewa
tsaye.
da sauri suma duk suka miƙe tsaye.
Gyara kekyawar al'kyabbar jikinshi yayi wacce take ta limamaice bawai ta sarautaba,
jam hiraminshi yayi ya rufe sajenshi da kyau ya rage iya shatin fuskarshi dan yasan
dole tazo da hadimanta mata.
Jalal ne ya tsaya gefen damanshi, kana Jamil a gefen hagunshi, Haroon kuwa na
bayanshi, Jakadiyarsu kuwa tana gaba tanayi musu jagora.
A haka suka fara taki kan stpes ɗin sauƙowa daga kan dinning area ɗin, wani irin
taku sukeyi mai cike da ƙasaita da kwarjini. Yana tsakiyarsu tamkar sarki da
fadawanshi.
A haka suka nufo tsakiyar babban falon da ya kai wasu faluka huɗu.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu, wani irin hushi da numfarfashi takeyi tamkar wacce tayi
gudun fanfalaƙi,
cikin izaya da isa, take zaune bisa mazauninshi.
Tare da cewa.
"Ina karen Larabawan yakene, Dan kan uwark?".
Bata ƙarishe mgnar tataba, sabida ganinsu sun nufota gadan-gadan, wani irin
kwarjini yayi mata,
wanda yasa ta haɗiye ragowar mgnar tata,
shi kuwa Sheykh Jabeer, cikin wani irin taku naƙasaita suka karaso tsakiyar falon.
Ido ta zuba musu kana cikin tijara tace.
"Me zaka zo ka tsaya min a ka, ka zauna inada mgna da kai".
Cikin wata iriyar dakekkiyar murya mai cike da ƙasaita yace.
"Ai ba sai kince na zaunaba, dama dole in zauna, tunda ni ba bawanki bane, bazan
tsaya a kankiba, sabida Ni ba dogari bane".
Ido ta zazzaro woje alamun tarin mamaki, ajiyan zuciya ta sauke a ranta tace.
"Ehe mai jajayen kunnuwa, uwarka zanci".
Shi kuwa Jabeer, wani irin taku yayi mai cike da izza, bisa kujerar dake fuskantar
wacce take zaune a kai ya zauna, da sauri ta tsareshi da ido tare da cewa.
"Kai ina sama kana sama, haka aka koya maka irin tasu tarbiyar ta larabawan kenan".
Ƙafarshi ɗaya ya ɗaura ya ɗaurs kan ɗaya, kana ya gyara zamanshi da kyau,
cikin muryar ƙasaita yace.
"Ki dena yimin ihu a kai, nan ba fadar masarautar waɗancan surutattun bane, nan
fadace mai daraja masarautar Joɗa ce, kiyi hattara da lafuzanki, na baki mituna
biyar daga cikin wunin yau gaya min damuwarki in baki mgninta".
Jakadiya dai gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi.
Haroon kuwa, bayan kujerar da Jabeer ke zaune ya tsaya,
Jalal kuma yana gefenshi hakama Jamil.
Juwairiyya kuwa, tana inda take tun ɗazu.

Wani irin mugun kallo ta watsa musu, kana cikin zafi da azalzalar zuciya da jin
tarin tsanarsu ta gyara zama tare da cewa.
"Naji yau an ganka ka fito ɗakin sirri na masarautar Joɗa kaida mai martaba Lamiɗo,
me hakan yake nufi?".
Ba tare da ta gama rufe bakintaba yace mata.
"Ina ɗakin sirrin masarautar Joɗa akace miki na fito, ba ɗakin sirrin masarautar
kuba na fito?".
Cikin kufula tace.
"Itama ɗin wannan masarautar ai tamuce, tunda ƴaƴanane manyan jikokin sarkin
Nuruddeen, kuma babansune Galadima, shine kuka kasheshi, aka bawa wancan majanunin
yayan naki mulkin Galadiman, to yanzuma kuma ɗan tsurfa da tsiri uwar me kukayi a
cikin ɗakin sirrin? Me ya gaya maka? Me kuke shiryawa?".
Still harshenta ma bai gama komawa zaune ba ya jefa mata amsa.
"Ɗakin sirri mgnar sirri, tunda shi jakin daya kai miki rahoton, bai sanar miki me
muka tattaunaba, Ni sai in miki jagora zuwa wurin Lamiɗo ki samu ki ganshi yanzu
sai ki tambayeshi me yace min me mukayi, tunda kinsan in bani nai miki isoba sai ki
kai sati nan gaba baki samu damar ganinshi ba".
Ya ƙarishe mgnar yana tsareta da fitinennun idanunshi wanda babu tsoro a cikinsu.
Cikin kufula tace.
"Ba girin-girin ba tayi mai, ta yaro kyau take bata ƙarko".
Amsa ya kuma bata.
"Surkin nakine yaron? Mutumin daya haifa miki miji, kika aura har kika haifi yayan
da kike son su gajeshi, shine yaron? To asheko masarautar duk yarace, ke mulkarta,
tunda nasan ko tsohonki bai kai, Lamiɗo ba".
Ohoho ina wuta ta faɗa ciki, cikin kausasa murya tace.
"Ina mai umurtarka da kada ka kuskura ka amshi wani mulkin daya wuce Garkuwa".
Cikin taɓe fuska yace.
"Anƙi bin umarnin naki".
Wani irin Murmushi mai baiyana jin daɗi da tarin Mamaki Haroon da Jamil sukayi.
Jalal da kanshi yau Hamma Jabeer ɗinsu ya shayar dashi tarin mamaki, ashe shi nashi
ƙarfin halin da ake gani wasane, ga Jarumin da jarumtarsa ta girgiza, zuciyar
Jalal. Dan harga Allah shi dai ya sani bazai taɓa iya yiwa Gimbiya Saudatu abinda
Haammanshi keyi mata yanzuba, ashe dama haka yake, da kafiya da bada amsa tun kafin
ta huta. Muryar Gimbiya Saudatu ce ta kuma katse mishi tunani.
"Yanzu bakinka ke iya furta ka haka,, yaro zakaci kan uwark".. da sauri ta zaro
mishi ido jin yace mata.
"Kul kada ki ƙarasa, in kuwa kikayi gangancin ƙarasawa, zan". Katseshi tayi da
cewa.
"Zakayi me? Gaya min isshe ɗan fitsara me zakayi".
Jalal ne ya amshi zancen da cewa.
"Zan datse miki harshe, kika kuma zagar mana uwa".
Cikin tsananin tsana ta watsawa Jalal harara tare da cewa.
"Zaka aikata! Babu musu! Menene ɗan giya bazai iya yiba, menene, ɗan iska ɗan daba
bazaiyiba, banza ɗan sara suka, gwada datse min harshen ka gani, in akwai wanda zai
rage da harshe a zuriyar uwarku".
Jabeer ne ya ɗan taune leɓenshi tare da kaɗa mata yatsa kana yace.
"Kulfa, ki raba kanki da zagin mace mai daraja".
Cikin isa da ƙasaita tayi wani irin dariya, kana ta miƙe tsaye, gabansu ta ɗan
matso kana cikin izaya tace.
"Eh daraja ko? Uhummm lallai kam, aifa sai dai mace mai daraja."
Sai kuma ta ɗan ja da baya kana tace.
"Mace mai daraja ko mai zunubi, ai dai kun fara ganin sakayyar Allah tun a duniya,
waya san metayiwa ubangiji, y...."
Juwairiyya ce, tasaki wani irin ƙara da yasa duk sukayi shiru.
Ita kuwa ta faɗi kasa a sume alamun makaranta sun dawo.
Ganin haka yasa Jakadiyarsu tayi kanta da gudu.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"Haka dai. Duk a haka zaku ƙare, mulki kuwa sai dai ku ga anayi, GARKUWAN da aka
bakanma, zakaga me zai sameka dashi".
Tana faɗin haka ta juya ta nufi hanyar fita Hadimanta na biye da ita a baya.
Shi kuwa Sheykh Jabeer murya ya ɗan ɗaga a hankali yadda zata iya jinshi yace.
"Babu abinda zai sameni face dama Allah ya ƙaddara zai sameni, domin baki isa ki
cutar daniba".
Cikin harshen fillanci tace.
"A laran ai, zaka gani ai".
Bai kulataba.
Ita kuma fita tayi.

Jalal da Jamil kuwa, zama sukayi gefenshi, suna mai bin kofar fita da ido.
Haroon kuwa cikin rudu da ɗaure war kai yake mgnar zuci.
shin wai wannan wacce iriyar fitinenneyar masarautace, mai cike da tsarƙaƙiya,
yanzuma dama a irin wannan yanayin Jabeer ke rayuwa da ƙannenshi da yayanshi da
mahaifanshi.
To meyasa, bazasu bar musu masarautarba, tunda shi Jabeer bama son wannan mulke-
mulken yakeba.
Sassanyan zazzaƙar Muryar Sheykh Jabeer ne ta katse mushi nazari, jin yana rere
karatun Alqur'ani cikin nitsuwa yake, karanta fatiha.
Bayan ya kai ƙarshenta ya kuma yi bisimilla, ya fara Suratul Baqra, wanda yakeyi da
ɗan ƙarfi, tare da fuskantar inda Juwairiyya ke kwance,
Yanayin karatun cike da taƙawa da kekyawan tajwid, shiyasa in ya fidda wani harafin
kamarsu Khah sai kaji har ƙasan wurin yana amsa amon sautin."
A hankali Juwairiyya ta fara buɗe idanunta, tana mai bin karatun da takejin,
Cikin sauƙe ajiyan zuciya Jakadiyarsu tace.
"Alhamdulillah Jabeer ta farfaɗo".
Ta faɗi hakane sabida tasan duk sansa Juwairiyya ta faɗin in dai zai mata Rugyag
rufe idonshi yakeyi.
Jin Jakadiyarsu tace ta farfaɗo ne, tasashi, yin hamandala tare da cewa,
Jakadiyarsu ta meda Juwairiyya Side ɗin ta, kana ya kalli Jalal tare da cewa.
"Jalaluddin kaje, ka kula da Ya Jafar, ka bashi abinci kana ka shirya shi, shirin
zuwa sallan jumma'a kaima kaje ka shirya."
To sukace kana duk suka fita. har sunje bakin ƙofar fira yace.
"Jalaluddin kasa kayan mutunci".
Cikin sanyi yace.
"To". Sannan suka fita.
Kanshi ya ɗan juya ya kalli, Jamil, tare da cewa.
"Ka gyara mana bedroom."
Yana jin haka ya miƙe ya nufi bedroom ɗin.
Shi kuwa Haroon ido ya zuwa Jabeer, sabida gaba ɗaya muryarshi ta tabbatar musu,
yana cikin tsananin ɓacin rai, kai Haroon ya jinjina ganin Jabeer yasa hannu ya
janye hiramin dake kanshi, ya taune lips ɗinshi, kana ya rufe idanunshi, cikin
ƙarfi yasa hannunshi ya fara jan bakin hiramin , da yake sabo fil janshi yakeyi
alamun zai yagashi.
Shiru Haroon yayi baiyi yunƙurin hanashi ba, domin dama yasan za'a rina, sabida shi
Jabeer wannan itace babbar alamar tsananin ɓacin ransa, muddin fushinsa ya hauhawa
to, yakan yayyaga abu da karfi.
Fass haka Haroon yaji sautin, yagewar sabon hiramin nan.
Shi kuwa Jabeer idonshi ya ƙara rumtsewa yanayi mai ci gaba da fatattaka hiramin.
Murmushi Haroon yayi cikin tare da fara ɗaukar shi video.
Yanayi dan tsokana.

A can sashin Hajia Mama kuwa, ganin shiru-shiru Jabeer bai shigo bane, kamar yadda
ya saba in yayi tafiya ya dawo yakan,
Batul kuwa, ta gaza zaune ta gaza tsaye, ta ƙenƙesa ado da kwalliya tamkar mai zuwa
gasar kyau.
A karo na barka tai ta kalli Hajia Mama, cikin zaƙuwa tace.
"Yakura, muje, side ɗinshin mana, mu duba lfy kuwa har yanzu bai shigoba."
Ajiyar zuciya Hajia Mama ta sauke, tare da miƙewa tace.
"Muje Batul ni kaina, na banyi zaton zai kai iwar haka bai shigoba, dole akwai
abunda ya tsareshi".
Da haka suka fito, suka nufi sashin Jabeer ɗin.

Kasan cewarta matsayin uwa, yasa sam bata da hijabi da sashin, haka yasa, sarkin
ƙofar na ganinta suka rusuna tare dayi mata kirari kana ta wuce.

A falon suka samesu, zaune.


Haroon ya tasashi gaba da kallo da wayarshi, shi kuwa Jabeer, idonshi a rumtse,
bakinshi na motsawa a hankali, yana maimaita, tasbihen daya zame mishi abokan
rayuwa.
Kana hannunshi nata yage sabon hiraminshi.
Haroon ne ya amsawa Mama sallamarta, tare da cewa.
"Barka da fitowa Hajia Mama".
Da sauri ta ƙarasa gabansu, kujerar dake kusa dasu ta zauna,
cikin tarin kula tace.
"Haroon da kai ake tafe kenan? Ya yar uwata, yaushe ka dawo?".
"Haroon lfy kuwa me akayiwa Jabeer? Waya taɓa minshi? Waya taɓo ɗan lelen
Umaymah'nshi Da Sitti'nshi?".
Cikin lumshe ido Haroon yace.
"To Hajia Mama wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki, ta ƴar uwarki ko ta ɗan rigimarku,
mutun in yayi fushi sai yayi ta yage-yage, wannan in ya samu dama in yayi fushi ya
samu ya damƙi ƴar mutane a hannunshi tabbas zai yageta, dan ko namiji da kyar zai
iya ƙwatar kanshi".
Murmushi mai cike da kulawa tayiwa Haroon kana,
ta kalli Batul da zauna gefenta, ta zubawa Jabeer idonu tamkar zata cinyeshi ɗanye,
wani irin sonshi da ƙaunarshi takeji, jiki da zuciyarta,
Kekyawan sumar kanshi ta zuwa, idanu a hankali ta dawo da idon kam tattausan sajen
da yayi fuskarshi ƙawanya, har kan gashin gemunshi da ya kai kamu ɗaya, yayi baƙi
sitib dashi ya konta lib sai sheƙi yakeyi, jajayen laɓɓan bakinsa, da suke motsawa
ne ta zubawa kwayar idanunta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, sanadin tasbihin da yakeyi ne, yaji zuciyarshi tayi fes,
fushin da yakeji duk ya kau. A hankali yakejin tsikar jikinshi na amsa sautin yam-
yam tana sanar mishi ana kallonshi.
Yunƙurowa yayi ya tashi zaune, kana a hankali ya fara buɗe idanunshi.
Da sauri ya kauda ƙwayar idanunshi sabida ganin kwayar idanun Batul cikin nasa,
Hajia Mama kuwa, cikin sanyi tace.
"Innallaha ma'assabirin".
Idonshi ya kuma lumshewa, wannan abu shike ƙara sashi jin ƙarfin guiwar zama cikin
masarautarsun. Sabida yayi dace, da uwar da take ƙara bashi tarbiyar da yasan itace
dai-dai tana danne dukkan baƙin cikinta, domin ta sama mishi nitsuwa. Duk da
kasancewar shi malami.
Tana ƙara nusar dashi.
A hankali yace.
"Barka da safiya Mama".
Murmushi tayi kana tace.
"Barka dai, Muhammad Jabeer. Garkuwa mai nagarta,
Yau na tashi da tsantsar farin ciki , tunda maji muryarka da asuba, meya ɓata maka
rai daga dawowa?".
Cikin sanyi yace.
"Babu komai Mama, Sheykh Abdulkareem, da ahlinshin duk sun gaisheki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Tsoho mai ran ƙarfe, kakanmu bawan Allah, yana lfy ko?".
"Alhamdulillah". Yace mata, yana mai sa hannu ya ɗauki hular da Jamil ya ajiye a
kusa dashi ya ɗaura a kanshi, sabida wani irin kallo da yaga Batul nayiwa suman
kanshi.
Ita kuwa Batul ido ta ɗan lumshe, ganin yadda ya tamƙe fuskarshi ya watsawa gefen
da take kallon, ƙasaita.
A hankali ta buɗe idonta kana ta sauƙesu kan sajenshi,
Wani gajeren tsaki yaja,
tare da kauda fuskarshi.
Ita kuwa Butul mgnar zuciya takeyi.
"Masha Allah, Ya Jabeer, komai kayi kyau kakeyi, ya Allah ka tabbatarmin da
mafarkina mana, wannan kekkyawan bawa naka ya zamo mijina, domin shine mijin daya
dace dani, mijin kece raini da nunawa sa'a, Uhumm jin kai da ƙasaita ba, kayi naka,
kafin ka shigo hannuna, in sha Allah, sai na zama sarauniya ka zama bawana."
A hankali tace.
"Ya Jabeer ina kwana".
Shiru yayi kamar bai jitaba,
Allah ya sani ya tsani kallo a rayuwarsa ta duniya, baya kuma son mace, da rashin
kamun kai.
Hajia Mama kuwa ganin yadda ya takurene yayi kici-kici da fuska, yasa ta ɗan,
kalleshi tare da cewa.
"Jabeer Batul ke gaidaka, itama jiya tazo".
Kanshi ya ɗan rusunar tare da miƙewa tsaye, cikin sanyi yace.
"Masha Allah".
Daga nan ya ɗanyi taku biyu zuwa uku, kana yace.
"Mama barin inje inyi shirin jumma'a".
Murmushi tayi tare da cewa to. Dan ta fahimci zillewa yakeyi.

Daga nan shi dai yayi, ciki.


Su kuma suka, fita.

Haroon kuwa Data ya kunna,


Umaymah ya turawa video ɗin da yayiwa Jabeer da yana cikin fushin.

A can Rugar Bani kuwa, yau tun safe, su Shatu suka baro asibitin, sabida, matasan
mayaƙan cikin garin Shikan ɗin sai kai komo sukeyi, cikin asibitin. kana sai zuwa
sukeyi maja'iunsu, suna mitin.
Bisa dukkan alamu, sunada wata manufa, ganin hakane, yasa likitoci musulmai, suka
bada shawarar a kwashi marasa lfyar a medasu cikin asibitin babban birnin Ɓadamaya,
sabida su nan babban likitansu ya hanasu duba kowa.

Da wannan shawarar ne, aka kwashi duk marasa lfyan da taimakon yan agaji aka shiga
dasu cikin Adamawa.
Dan an fara rade-raɗin wai fulanin Rugar Bani sunce zasu ɗauki fansa, to shisa
ƙabilar ɓachama suma suketa guzurutsoma, har ta kai da matakin in dare yayi matasan
hausa fulani na cikin garin ma zauna cikin garin Numan, sai su futo suyi ta yawo da
makawai suna kare amguwanninsu.
Kana suma ƙabilar ɓachama sai su fito da makamai suna kare amguwanninsu.

Shatu kuwa basu wuce cikin Ɓadamaya ba, sabida Ummiy ta dawo hayyacina ta, hakama
Junainah ta dawo haiyacinta da ƙarfin addu'o'in da Aysha da Bappa keyi.
Dan haka su cikin Rugarsu-suka koma.

Shatu kuwa, tunda Junainah ta gaya mata batun ɓacewarsu Ya Giɗi da kuma kashe ya
Lado da akayi, har zuwa yanzu bata daina kukaba.

Koda Ba'ana yazo wurinta daren jiya, da yaji lbrin sun dawo babu abinda takeyi sai
kuka.
Shi kuwa Ba'ana, baƙin cikinsa shine da Ummiy ds Junainah da Bappa suka rayuwa,
Shiyasa yanzu, yayi musu nasu shirin mutuwa namu samman.

Inda Bugulu Maman Ma'ans ta gasa zabbbin da Ba'ana ya yanka, kana ta daka musu,
yajin borkono, da busasshen kan maciji.
Ta barbaɗa musu, kana ta yaryaɗa man shanune da ya gauraya da dafin macijin cikin
man shanun da tayi musu gashin dashi, kana ya nufi, bakin garkensu, da akoshin
gasassun zabbin.
Sannan ya aika aka kira mishi Shatu,
cikin kuka Rafi'a tacewa ɗan aiken yaje, ya zazzaɓi ke damunta.
Koda yaron yaje ya gaya mishi,
sai yace zai a kira mishi Junainah,
Koda yazo ya gaya musu,
Sai Junainah ta miƙe tabi bayan ɗan aiken.
Kasan cewar garken nasu ba nisa, tafiya kaɗan tayi ta isa, ta isa ta zauna a bakin
ƴar bukkarsa da yake, cikin.
cikin disashewar muryar hawaye na zuba tace.
"Ya Ba'ana, kaje ka dubo jikin Ya Junaidun ne?".
Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau, cikin sanyi yace.
"Eh naje na dubashi, jikinshi da sauƙi, ke ya naki jikin? Ya Ummiy da jiki".
Cikin sanyi tasa hannu ta share hawayenta dake shatata kana a hankali tace.
"Ummiy jikinta da sauƙi sai dai har yanzu bata mgn, Adda Shatu kuma sai kuka
takeyi".
Hararanta yayi a fakaice, ji yake kamar ya jawota ya caka mata mashi ya mata kisan
zahiri sai kuma ya fasa,
Kanshi ya kauda tare da tura mata akoshin gasassun zabbin nan kana yace.
"Ayyah sannu Junnuna, kiyi haƙuri dena, kuka, kici nama, sai kije kicewa Mata,
tazo zan gaya mata inda su ya Giɗi suke".
Cikin rawan jikin jin yunwa tace.
"Yauwa bani inci dama yunwa nakeji, tun jiya banci komaiba, tunda muka dawo, bamuyi
girkiba."
Da sauri ya turo mata akoshin tare da buɗe mata fefeyin.
Cikin rawan jiki irin na masu jin yunwa tasa hannu ta...!

Uhummm Allah kaimu gobe lfy, mu ƙara sa free page, daga PAGE 15-16 an gama.

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 15

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🤴🏻💘
🦚🤴 🏻 💘

*Littafin GARKUWA na kuɗine, daga wannan PAGE 15 da 16 FREE PAGE sun ƙare, turo
katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, ko ki turo dubunki ɗaya
rak dan shiga Special Group, wanda anfi yawan posting, ta wannan asusun zaki turo
1k ɗin 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta
wannan number dai 09097853276.*

```Dan Allah da Manzonsa da darajar iyayenki in dai kin san kin sayi littafina ne
ko zaki sayane ɗan ki fitar min dashi na roƙeki da Allah da Manzonsa🙏🏻 kada ki
saya, in kuwa har kin sayane kawai gaya min in biyaki kuɗin ki ki barmin littafina,
mu rabu innahu annahu.```

Akwai kayyakin gyara namu mata setin amare da masu jego, da masu kwaskwarima, idan
kina buƙatar saya ko sari, tuntuɓi wannan number tawa 09097853276.

Hannu tasa ta jawo pepeyin jin yana ce mata.


"Kici kije da gudu ki kira Mata, tazo in gaya mata, su Ya Giɗi sun kusa dawowa ta
dena kuka, anji lbrin inda suke".
Rufe akoshin tayi kana ta miƙe da sauri tace.
"Da gaske ya Ba'ana an ji inda suke?".
Cikin haɗe fuska yace.
"Na taɓa yimiki ƙarya ne?".
Da sauri ta jujjuya kanta kana tace.
"Bari inje in gaya mata tazo sai inci naman a gida".
Da sauri yace.
"A a jeki kirata, in tazo sai ki tafi da naman, kije kuci keda Ummiy da Bappa da
ita ƙawar Mata, ita kuma zan bata nata a nan".
Ai tana jin hakan ta juya ta tafi, da sassarfa.

Tana isa gida, ta kamo hannun Shatu, cikin haki tace.


"Adda Shatu taso, taso muje ya Ba'ana zai gaya miki inda su ya Giɗi suke, yace anji
lbrinsu".
Wani irin zabura tayi, hakama Rafi'a dake bakin ƙofar kitchin ɗinsu.
Cikin tarin kaɗuwa tace.
"Ke Junainah, kada kiyi mana ƙarya".
Cikin haki tace.
"Wallahi tallahi, haka yace min zo muje kiji".
Da sauri ta kamo hannun Rafi'a tace.
"Adda Rafi'a kema zo muje tare".
Cikin jin daɗi Rafia tace.
"A a Junainah kuje, Ni kuma kafin ku dawo nayi mana abinda zamuci, da sauri tace.
"A a Adda Rafi'a ki bari kar kiyi girki, Innar ya Ba'ana ta aiko mana gasassun
zabbi yanzu zan amso mana su sai muci".
Murmushi tayi kana tace.
"To sai kinzo".
Ita kam Shatu tuni ta fita, ta nufi Garkensu Ba'ana.

Ita kuwa Ummiy ido kawai ta zuba, musu tana son ta kira Shatu ta hanata zuwa amman
ta kasa.

Ita kuwa Rafi'a kitchin ɗin ta shiga.

A can garkensu Ba'ana kuwa.


Yana hango Shatu, ya saki wani irin ajiyan zuciya, ido ya zuba mata,
Gaba ɗaya ta rame tayi fiyau da ita, fuskarta tayi jazir alamun yawan kuka, kana,
ga kumbura da idanunta sukayi.
Da sauri take tafiya, sai dai tanayin takun a hankali ne, doguwar rigace a jikinta
ta atampa, hijabi da ta saka wanda yazo mata har guiwa.
Ta ɗan ja hulan kan hijabin dan ya ɗan kare mata kumburarrun idanunta.
Wani zafi yakeji a ransa, Allah ya sani baya son ganin Shatu cikin damuwa duk
ƙaƙantar-ta, yakanyi komai na zalumci, amman baya yi kan Shatu, shi kanshi ya yarda
shi tantirine, azzalumi, kuma mugu, hakanan kuma ya yarda so gsky ne kuma so ɗaya
ne tak kuma ya sani duniya ta sani yana son Shatu,
yana son sama mata farin ciki a rayuwarta, yana son su rayu tare. Shiyasa yake son
rabata da kowa nata wanda suke ƙoƙarin ganin sun hanasu Kasancewa mata da miji.
Wani farin buzu ya shimfiɗa mata a bakin ƴar bukkartasa, tun kafin ta ƙara so.
Tana isowa, murya can ƙasa tace.
"Assalamu alaikum."
Ido ya zubawa fuskarta cikin tausayawa yace.
"Mata ki zauna". Murya a disashe tace.
"Ya Ba'ana ka amsa sallamar mana".
murmushi ya ɗanyi kana yace.
"Mata na amsa bakijini bane".
A hankali ta zauna bisa buzun, cikin sanyi ta lumshe idonta da takeji sun tsastsafo
da zafafan hawaye, murya na rawa tace.
"Ya Ba'ana, wai anji lbrin su ya Gaini?".
Matsowa yayi bakin bukkar, ido ya ɗan zubawa fuskarta, sabida lumahe idon da tayi
batasan yana kallontaba ganin hawayenta na zubowa ne yashi yin mgna, a hankali
yace.
"Mata, kiyi haƙuri, ki kontar da hankalinki, in dai yayunki suna raye, zan nemisu,
ko dan farin cikinki, ki bar kuka Mata, bana son ganin hawayenki inajin ƙuna a
raina".
Ya ƙarishe mgnar murya can ƙasa.
Cikin rawan murya tace.
"Ya Ba'ana, ya zanyi? Ina zansa raina in ji sanyi, zuciyata tana ƙuna, Yayuna huɗu
kab na rasasu lokaci ɗaya, bani da wa wanda zan nuna a faɗin nahiyar nan ince ga
wani na a duniyar, babu ya Giɗi, wanda shine tamkar aboki ƙawa aminiya, abokin
faɗata abokin dariyana, Babu ya Seyo, yaya mai kamar uwa, sabida yawan tausayinshi
da nuna ƙaunarshi gareni, ko uwa iya abinda zata nunawa ɗanta kenan, babu ya Gaini
da yake tamkar uba, babusu babu gawansu babu lbrinsu.
An kashe min ya Lado da yake GARKUWA a gareni.
Ya Ba'ana, ya zanyi in banyi kukaba, Ina zan fara nemansu, Ni macece inada rauni,
ta ina zan nemosu? An kashe mana Innarmu".
Ta ƙarishe mgnar tana mai kife kanta bisa guiwowinta ta saki wani irin kuka mai
tsuma zuciya, cikin kuka taci gaba da cewa.
"An kashe Inna, sanadin haka Ummiy na ta zama tamkar zautacciya, duk gidan dake
cikin Rugar Bani babu gidan da ba'a kashe a ƙalla mutun biyarba a ƙaramin kari,
suwaye ne ya Ba'ana, me mukayi musu? Me suke nema damu? Me muka tsare musu? Me
laifinmu dan mun kasance Fulani makiyaya?".
Karon forko a rayuwarsa da yaji rauni har ta kaishi ga zubda hawaye, koda yake
raunin soyayyace, cikin zubda hawaye murya na rawa yace.
"Mata gani, zan zame miki madadin uwa, uba, yayunki, Inna, zan zame miki Garkuwa,
in sha Allah bazan bari ki cutuba, zan bada raina domin kare naki, zan nema miki
farinciki da dukkan abinda na mallaka na duniya, zan zame miki adalin miji, Mata ki
dena kuka, kiyi haƙuri".
Cikin shessheƙan kuka ta ɗago kanta, ta zuba mishi ido, tabbas kuka yakeyi kamar
yadda ta zata, cikin mamaki tace.
"Ya Ba'ana meyasa kake kuka?".
Hannun yasa ya sharce hawayenshi, karon forko a rayuwarsa da yayi abu ya gommace
bayiba karo na forko a rayuwarsa da yayi mugunta yaji dana sani kan sace su Gaini.
Da yatsarsa manuniya ya nunata, da mamaki tace.
"Nice na saka kuka?". Kanshi ya gyaɗa mata, cikin al'ajab tace.
"Me nayi maka?". Motsowa yayi ta bakin bukkar sosai can cikin sassanyan murya yace.
"Kukanki ne yasani kuka Mata,
farinci bazai samu gurbi a rayuwataba, muddin ke kina cikin ƙunci, dan Allah ki
daina kuka,".
A hankali tasa tafin hannunta ta share hawayenta.
Shi kuwa Ba'ana, wani babban kura tanɗu yajo, cikin sanyi ya ajiyeshi gabanta a
tsakiyarsu. Cikin sanyi yace.
"Shatu". Da sauri ta ɗago kanta ta kalleshi domin yauce karo na forko rana ta forko
a tarihin rayuwarta da taji ya kirata da Shatu, cikin mamaki tace.
"Na'am ya Ba'ana".
Girgiza kanshi yayi kana ya fara fito da wasu sabbin aska cikin zabirar da yanzu ya
jawota, a hankali ya ɗago ya kalleta cikin yaƙini yace.
"Shatu, zan faɗa miki abinda, babu wanda ya sani a kaina a duniya, Shatu zan nuna
miki abinda duk duniya ban yarda da in nunawa kowaba, sabida ban yarda da kowaba
sai ke ɗaya rak Shatu, nasan zuciyarki ciki da woje, ke mai imanice, bazaki taɓa
zalumtata ba, bazaki bari a kuma zalum ceniba. Na amince da soyayyarmu, zamu rayu a
tare har gaban abadan."
Ido kawai ta iya zuba mishi.
Ganin Junainah ta iso wurin ne, yasashi jawo akoshin gasassun zabbin gabanshi.
Ita kuwa Junainah da sauri ta kuma sa hannu zata jawo akoshin.
Kanshi ya jujjuya mata alamun ta bari.
Cikin kwaɓe fuska da ɗan karen kwaɗayi da yunwar da takeji yana azalzalar ƴaƴan
hanjin cikinta tace.
"Yah Ba'ana ka bani mana yunwa nakeji".
Cikin sanyi yace.
"Bazan bayar ba".
Da sauri tasa hannu ta zari akoshin tayi gaba
Shatu ce ta fara kiranta tana.
"Junnu! Junnu!!! Junnuhhh!".
Ina bata kulata bama bare ta juyo.
Shi kuwa Ba'ana ajiyan zuciya yayi tare da mgnar zuci.
"Uhummm ƙuda garin kwaɗayi kya mutu, kwaɗayinki ne zai karki". Kai ya gyaɗa wa
Shstu kana ya juyar da kanshi.
Ita kuwa Aysha shiru tayi tabi Junainah da ido.
Shi kuwa Ba'ana cikin sanyi ya wore ƙafafuwan sa,
takalmin roba na sau ciki wato, tashi kabi shanun dake ƙafarsa ya zare.
Sabbin askan ya ɗauka, kana ya fito da wasu ƴan kananun layu guda biyu.
cikin yaƙini yace.
"Shatu, kinga waɗannan layun?".
Kai ta gyaɗa mishi cikin yin kici-kici da fuska.
Jinjina mata kai yayi kana yaci gaba da cewa.
"Wadannan sune, maƙurar, mgnin kariya da zan saka a jikina, zan sasu a gaban
idonki, wannan ƙaramar ita zan saka a dundunyar ƙafar dama, itace kuma layar,
ƙarfe, mudin wannan laya tana jikina, to wlh babu wani ƙarfe dake kan doron duniya
da zai shiga jikina".
Cikin mamaki tace.
"Koda bulet ne!?".
Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Koda menene, kuwa su wannan sabbin layune, wanda babu makarinsu, sai dai ina na
ciresu a jikina,
ita wannan da zan saka a ƙafar hagu, layar zanace.
Duk sihirin mutun bazai karyashiba, zan iya ɓacewa inje ko ina, makarinta abu ɗaya
ne!".
A hankali tace.
"To menene makarinta?".
Cikin sauƙe wani nannauyan numfashi yace.
"Idan wata rana dubuna zaicika za'iya kamani, to ammanfa tabbas, zan iya ɓacewa sai
dai in ba'a barni na sha ruwaba, amman muddin akabani ruwa nasha zan iya ɓacewa."
Da sauri tace.
"Ya Ba'ana dubunka ya cika kuma, kamar wani mugu ko maiyin mugun abu".
Da sauri ya fizge mgnar da cewa.
"Eh to ai yanzu zan fara fataucin nemo. Suya Yaya Giɗi ne, kinga kuwa, sai yadda
hali yayi".
Ajiyan zuciya ta sauƙe kana tace.
"To ita layar ɓatan da ta ƙarfe menene makarinsu?".
Kanshi ya ɗan jingina da bakin bukkar ido ya ɗan zuba mata, kana cikin sanyi yace.
"Uhum makarinta sai in an samu maza tagwaye, da matar da bata al'ada sunyi tuwon
sabon geron da za'a shuka a tsakiyar garken fulanin kana tuwon za'ayishi da garin
dakan hannune, kuma maza tagwayen sune zasu tuƙa tuwon kana matar da mijinta ya
tara da ita batayi wonkan tsarkiba, ta kwashi tuwon , to su kam in naci, tuwon gaba
ɗaya sihirin jikina zai karye, in kuma ba haka sai dai ina an tsaga dundunyar ƙafar
tawa an ciresune kafin makami ya iya min illa".
Cikin wani irin sanyi tace.
"In sha Allah zaka nemosu lfy ka dawo dasu lfy, zanyi ta addu'a Allah ya
baiyanasu."
Kanshi ya tanƙwasar kana a hankali yace.
"Uhum sai daifa Shatu akwai wasu bulalin da aka bani tabbacin zasu worwore duk wani
asiri da kafi da nayiwa jikina,
Amman duk da haka bazasu worwore waɗannan layunba, sai dai an bani tabbacin,
muddinfa aka dakeni da wannan bulalin zan ji azabar dukan, da zai iya ɗauke raina".
Cikin mutuwar jiki tace.
"Bazama su dakeka ba, Ya Ba'ana".
Kanshi ya mirgina kana, yasa hannu ya ɗauki askarnan, kawai sai ya datsata kan
dundunyar ƙafar damanshi,
Da ƙarfi Shatu tasa salati tare da rufe idonta, gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi murya
na rawa tace.
"Innalillahi ya Ba'ana zaka kashe kanka".
Cikin harshen fillanci yace.
"Ai bazanji zafinba Mata, bari yanzu in ɗinkesu, buɗe idonki ki gani."
Cike da tsaro tace.
"Bazan iyaba, ina tsoro".
Jin hakane yasa bai kuma ce ta buɗe idonba, har saida ya gama cusa layun kana yasa
ƙayar aduwa ya rinƙa hudawa yana ɗinkawa da zaren, gashin bindin shanu, saida ya
gama yace ta buɗe idonta.

Cikin tsoron ta zubawa wurin ido, ga jini ya ɓata ko ina,


Sai kuma ta ƙurawa ƙafafuwan ido ganin yana shafa musu man shanu sai wani tafasa
wurin yakeyi, cikin mintuna uku duk wurin yayi tib-tib kamar ba shiba.
Cikin tsoro tace.
"Ya Ba'ana, ka dena irin wadannan abubuwa, wallahi shirka ne, tsafine babu kyau!
Haramunne."
Ganin yadda ya haɗe fuska ne yasa tace.
"Kayi haƙuri, shiyasa tun forko ina son ince maka ba kyau bana son kana irin
wadannan abubuwan".
Murmushi ya ɗanyi kana yace.
"In kin sake min mgnar, bulala ɗaya zan ɗauko cikin bulalin shaɗi na, in zaneki da
ita sau ɗaya kiji irin zafin da masu gangancin cewa suna sonki, sukeji a jikinsu."
Cikin tsoro tace.
"Bazan sake bama Ya Ba'ana wadannan, bulalin da kake tsumasu da dafin kunama ai Ni
kam na sani bulala ɗaya zakamin zan mutu".
Da sauri yace.
"Azubillah, Mata kada ki sake cewa zaki mutu, domin duk randa kika mutu nima zan
mutu, sai dai batun gsky ko Mata, duk mutumin da kikaga ya iya jure bulalin shaɗi
na, har ya kai matakin nasara, to wlh ki sani ki shaida, jarumine, irin jaruman da
sunyi ƙaranci a duniya."
Hannu tasa ta kange fuska daga wani irin kallo mai cike da so da yake mata,
Tabbas Ba'ana ba barbarene, amman yanada wani irin kyau mai ban mmki, a hankali
tace.
"Ya Ba'ana wai da waye kake kamane?".
Cikin murmushin da ya bayyana kyawawan haƙoransa yace.
"Ni da kakata Maman babana nake kama, ita kuma ba kanuribace, fulatamare ce ita".
Cikin sanyi tace.

Murmushi ya ɗanyi kana yace.

Cikin sanyi tace.


"Haba shiyasa mana kake da kyau sosai".
Wani irin kallo ya mata tare da cewa.
"Eyeh ashe Ni kekyawan ne Mata, ke dama shine baki taɓa gaya min ba inji daga bakin
wacca nafiso fiye da komai a duniya dan inji daɗi, kin bari sai wasu can keta cemin
wai ni kekyawan ne".
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
"Sai anjima, Mai kyau ka tashi kaje ka tafi masallacin kaga lokacin sallan jumma'a
yazo anata tafiya".
Da murmushi ya rakata. Ita kuwa da haka ta tafi gida, sabida tuni wasu masallatan
har sun fara huɗuban sallan jumma'a.

Tana shiga gida ta samu.


Rafi'a, Junainah, Ummiy da Bappa, gaba dayansu a.

Cikin Babban birnin Ɓadamaya, a cikin masarautar Joɗa, kuwa.


Tuni masallacin Lamiɗo Nuruddee, ya cika yayi maƙil da bani adam tako ina zuwa,
akeyi.

Masallacin ya cika tab tamkar zai fashe, shiru kakeji babu wani amon sautin ɗan
adam dake tashi, sai sautin muryarsa.
Yana tsayene cas kan ƙafafunshi,
Wata dan datsetsiyar, shaddar Super Nour ce a jikinshi wacce take Brown color a
ƙalla kuɗinta zai kai dubu ɗari da ashirin, shaddar irin mai mai ɗinnane,
Yayi kauri cikin kayan ko dan yanayin suturar da ya sakane, boxes ce fara ƙal yasa
a ciki, sai snglet itama fara ƙal, kana sai Rigar half jomfar yaddan dake jikinshi
sai wonɗota, wanda sunyi cib-cib da madaidaicin jikinsa,
Kana sai watta tattausar doguwar al'kyabbar sa, Golding color, sai wani irin sheƙi
takeyi, sai hirami fari daja irin mai ɗigo-ɗigo nan, yayi masa sakin manyan
Dattawan bai lonƙosashi, ya barshi a zube bisa kafaɗunshi, sai ta gaban goshinsa da
ya ɗan matseshi ya bada ɗan tsini dai-dai kan karan hancinsa,
Sai baƙin zagayen daya ɗaura bisa kam hiramin.
Kana sai wasu takalman shi dake can bakin ƙofar shuga masallacin ta ƙofar liman,
takalman irin na sarauta ne half cover, wanda suma fari da ɗigon jane.
Yayi wani irin kyau mai ɗaukar hankali haibarsa da kimarsa da dottakunsa sunyiwa
fuskarshi ƙawanya, sajen nan nashi yayi lib-lib tamkar anayi wa koren ciyawa bayi,
sai wani irin sassanyan ƙamshin turaren OudKareem ɗin sa, dake tashi a jikinsa.

Muryarsace ta cika ko ina na yankin.


Shiru mutanen wurin sukayi kowa na jin, wa'azin yana ratsasu.
Yana Hudbane akan, wuraren da ya dace namiji ya gani a jikin matar da yake neman
aurenta,
yana kan hankali, bisa wuce gona da iri da mafiya matasan yanzu keyi, a kan wannan
dama da Allah ya basu.
Gyara tsayuwarshi yayi, tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya, ya haɗe bakin
al'kyabbar jikinshin. Cikin tattausan lafazi mai ratsa kunne da zuciyar duk mai
sauraro da imani yaci gaba da cewa.
"Aure wata muhimmiyar hanya ce, wanda idan aka ƙullashi zai bawa ma'auta daman
saduwa, tsakaninsu, ba tare da wata ƙyama ba, kuma ta hakane ma'autan zasu zama
sutura ga junansu. Kamar yadda Allah maɗaukakin sarki ya faɗa, a Suratul Baƙara
aya ta , 187:-
(HUNNA LIBASUN-LAKUM WA, ANTUM LIBASUN-LAKUM). Ma'ana su mata suturane gareku
maza, sannan ku maza suturane garesu (Su Matan)."
Gyara zaman al'kyabbar sa yayi tare da kallon tarin dubban al'ummar Annabi dake
zaune gabansa, hankalin da nitsuwar kowa na kanshi.
Sai ɗan haskem cameras da yake gilmawa ta kanshi da sauran na kusa dashi, shaidar
ana naɗar sautin muryarsa nayin huɗuban. Cikin nitsuwa yaci gaba da cewa.
"Saboda haka, ya zama dole mutun, ya nitsu ya maida hankali ya zaɓi abokiyar zama
ta gari da zata zame mishi sutura ya zame mata sutura, wajibine kuma kayiwa kanka
da jikinta iyaka har sai an biya sadaki, an kuma ɗaura aure, shaidu sun shaida
sannan zaka samu nitsuwa da ita.
Domin shi aure, yana samar da nitsuwa tsakanin ma'auranta. Ɗan Adam bazai samu
cikakkiyar nitsuwa a gidansa ba sai in har yanada mata, wacca ya aura. Domin zata
ɗebe mishi kewa, ta sa shi ya samu nitsuwar hankalinshi. Saboda zamansu tare, a
ƙarƙashin inuwar aure zatayi mishi maganin kaɗaci. Kamar yadda Allah, (A.A.W) ya
faɗi a Suratul Rum aya ta 21:-
(WA MIN AYATIHI AN KHALAKA LAKUM MIN ANFUSAKUM AZWAJAN LITASKUNUW ILAIHA WA JA'ALA
BAINAKUM, MA WADATAN WA RAHMA INNA FII ZALIKA LA AAYAATIN LIKAUMIN YATAFAKKARUN).
Yana daga cikin ayoyin da Allah mai girma ya halitta mana mataye daga kawunan mu.
(Mataye da muke aure da su) domin su sami nitsuwa junanku, sannan kuma ya sa muku
soyayya a tsakanin ku tare da Rahma da tausayawa juna. Lallai a cikin wannan
al'amari akwai ayoyi abin lura ga jama'a'an da suke masu tunani".
Gaba ɗaya taron al'ummar babu, hayaniya ko motsi shiru kakeji,
Baba Nasiru kuwa, yana dai zaune ne cikin sahun da masallacin amman ji yake tamkar
ya shaƙo wuyan Jabeer sai ya kaishi ƙiyama, Baba Bashiru ne dake gefenshi, ya ɗan
kalleshi tare da yin ƙasa da murya yace.
"Ya Nasiru ka nitsu mana ka koyi danne abinda ke ranka".
Cikin tarin baƙin ciki yace.
"Haba Bashiru ya zanyi in iya danne abinda ke raina, bayan da kai sani dama duk
sauran yan uwanmu, mahaifinmu ko sarautar sarkin ƙofa bai bamuba,
Tunda ya bawa Ya Muhammad, Galadima, yana rasuwa, madadin a maida sarautar Galadima
kaina, ko kan Hashim tunda shi ubanshine Galadima, sai ya ɗauki wannan sarautar ya
bawa, Jafar shi ɗan rashin adalci."
Murmushi Baba Bashiru yayi tare da cewa.
"To ai kuma dai gashi ya haukace ko? Ina dai yanzu sarautar tafi ƙarfinsa, dole dai
ya barta".
Cikin fusata Baba Nasiru yace.
"To ɗaya barta ya haukace ɗin ma, ya maidota ga ƴan ɗakinmu ne, inji, wancan tsohon
ya bawa, waishi ya bawa ƙaninshi, ai shima ɗan tsohon sarkine
Sannan kana ganin yadda ya kuma ɗaukar sarautar GARKUWA ya bawa Jabeer, sannan
babban tashin hankalin kanaga yau tare suka fito ɗakin labbare dashi wannan
munafikin yaro, waishi Sheykh ɗan iska anyi asiri anyi tsafi duk baya kamashi yadda
mukeso".
Barrister Kamal ne dake gefensu, yayi ɗan wani guntun tsaki cikin tsuke fuskarsa,
da jin haushin yan uwan nashi yace.
"Ya Nasiru kufa, ji tsoron Allah, ku tuna, cikin Masallaci kuke, kuma ba kyau liman
na huɗuba ana. Surutu."
Wani irin mugun kallo Baba Bashiru ya watsa mishi tare da cewa.
"To ɗan masu matacciyar zuciya, wa'azin da yakeyi ai tun kan a haifi uwarshi mun
sani".
A kufule Barrister Kamal yace.
"Ƙaryane, da kun san abunda ya sani wala Allah da zuciyarku ta tsarkaka".
Shiru yayi tare da fuskantarta Inda limamin take jin yana cewa.
"Halaccin kallon matar da mutun yakeso ya aura.
Haƙiƙa munsan matarka abokiyar rayuwarka ce. Kuma gonarka ce da zakayi shuka a
cikinta, sannan kuma gareta zaka samu konciyar hankali. Kuma shi manufar yin aure
ya hana kallon wata ko wasu matan wanda ba nakaba da dai makamantansu Irin hakan.
IN KUWA HAKANE TO LALLAI AKWAI BUƘATAR SAI MUTUN YA ƊARJE! YA ZAƁA. Haka kuwa baya
yiwuwa sai ka kalleta sosai da sosai. Saboda mahimmancin haka nema shariyar
musulunci ta yardar maka da ka kalli wacce kakeso zaka aura da kyau. Don ka
tabbatar da wancan abubuwan da aka ambata a sama.
Kuma wannan dama da Shari'a ta bada ta bada shine, a matsayin halasci na wurin
mafi yawan malamai, kuma wannan Halascin da akace halasne ya haɗa da cewa. Shin ta
yarda ka kalleta, ko bata yardaba, halasne in dai ka kalleta. Kuma wannan hukuncin
haka yake a wojen mafiya yawan malamai, sai dai Malikiya, sunce shi hukuncin
Halascin ya dogara ne, in ta bashi izinin amma in bata bashi izinin ba to bai
halasta ba.
Haka kuma shi wannan hukuncin halascin an samo shine daga, hadisin Abu Huraira
(Allah ya ƙara masa yarda) yace, wani mutun ya nemi auren wata mata, ƴar Madina,
sai Manzon Allah (S.A.W) yace masa: "Shin ka kalleta kuwa?". Sai mutumin yace,
wa Manzon Allah (S.A.W) "A'a ban kalleta ba". Sai Manzon Allah (S.A.W) yace.
"Tafi ka kalleta, domin mutanen Madina sunada wata illa a idanunsu."
A wata ruwayar kuma da Abu Dauda ya ruwaito.
Daga Jabir Bin Abdullahi cewa: Lallai Manzon Allah (S.A.W) yace.
"Idan ɗayanku zai nemi aure to idan ya sami ikon kallonta wato kallon abin da zai
burgeshi zuwa ga aurenta, to ya aikata hakan, (ma'ana ya kalleta) Jabir yace sai na
nemi wata mata, daga cikin ƙabilar Banu Salma na kasance ina bibiyanta har sai da
naga abin da zai birgeni a aurenta.

Ɗan zagaitawa yayi kana yayi gyaran murya tare da cigaba da cewa.
"To matasanmu na yanzu suna, fakewa da waɗannan hujjojin, suna fakewa da guzuma su
harbi karsana, suna fakewa da hadisai suyi haramtaccen kallo, wata sun fake da rama
suci ɗanyen gari. Hattara gareku iyayen yara maza da mata, Gargaɗi gareku matasa,
bari in tuna sar daku wuraren daya halasta ka kalla a jikin matar da kake son ka
aura.
Dangane da inda ya kamata ka kalla, a jikin macen da zaka aura. Malamai sun kasu
kan wannan hukuncin, saboda ba su, sami hadisin da ya yi bayani keɓantaccen wuri
wanda aka keɓe ko aka ce nanne kawai za'a kalla ba, wannan shi ne musabbabin da
suka karkasu kamar haka:
1 Mafiya yawan malamai sun tafi, cewa in mutun yana neman auren mace, yana iya
duban fuskarta da tafukan hannunta.
A Duba Fiƙhu wadi Juzu'i na 2. Shafi na 20 sannan kuma a cikin Fiƙhu Sunnah Juzu'i
na 2 shafi na 24 wasu malamai sun ƙara yin bayani da cewa idan mutum ya dubi fuska
mace, zai gane kyawunta, in kuma yadubi Fuskarta zai iya fahimtar cewa, mai
ni'imtaccen jiki ne wato mai tattausan fata jiki, ko kuma mata marar ni'iman
jiki.
Sheikh imamul Al-Auza'i yana cewa.
"Mai neman aure yana iya kallon wuraren nama dake jikin mace da zai aura.
Duba cikin Fiƙhu Sunnah Juzu'i na 2 shafi na 24.
Sheikh imamul Dauda kuwa yana cewa:
Mai neman aure yana iya kallon dukkan jikin matar da zai aura, shima an samu daga
Fiƙhu Sunnah Juzu'i na 2 shafi na 24.
Ɗan tsagaitawa yayi tare da ɗago kekyawan tsintsiyar hannunshi ya kalli agogon
Daimond dake ɗaure samfarin Gucci,
Ganin lokacin salla ya ƙara tone yasashi yin gyaran murya tare da ci gaba da mgna
gaggauce, yace.
" A wata ruwayar kuma da aka samo daga Abudurrazaƙ Umar Sa'idu ɗan Mansur yace,
(Amirul mu'minin) ya nemi auren ƴar Sayyidina Aliyu (R.A) wanda ake kira da Ummul-
Kulsum, sai, Aliyu ya ambata masa ƙanƙantarta, sai yace.
Zan turo ita idan ka ganta tayi maka matarka kenan, sai ya aiketa wuri shi.
Lokacin da taje sai ya yaye suturar da ya rufe ƙwaurinta.
Sai tace.
(Ba don kai Amirul mu'minin bane da na tsole ko buge idonka, (wato da na mareka)
idan muku dubi, wannan in har maganar ya inƙanta to ana iya yin hakan.

Anan kenan in har ka kalleta batayi maka ba, to ka kama bakinka kayi shiru. Kada ka
faɗi wata magana wanda zata iya cutar da ita.
In kana ganin kai bata baka sha'awa ba, to tana iya bawa wani sha'awa ya aureta,
domin ko wanne icce da ma tsincinsa, kuma abincin wani guban wani.
Allah yasa mu dace, lokacin salla yayi, bari muyi salla sai in Allah ya kaimu sati
mai zuwa sai muyi bayani kan halaccin mace ta kalli mijin da zata aura.

Daga nan yayi addu'an kana, ya juya ya fuskanci gabas, tare da tada iƙama bayan
yayi addu'an.

Bayan an idar da sallane, suka fito, a jere.


Ta ƙofarsun dai suka shiga, inda duk ahlin masarautar suke bin nan bayi da hadimai
da sauran fadawa kusa, duk ta babbar ƙofar suke bi.

Kusan a jere a jere suke tafi.


Kasan cewar zasuyi tafiyar zuwa Rugar Bani ne yasa Mai martaba Lamiɗo ke sauri.
Hakama Sheykh Jabeer, wanda Jalal, Jamil, Jafar, Haroon, Imran, Hashim ke tare
dashi,
A hankali ya tsaya jin muryar bappanshi ƙanin Abbanshi Baba Nasiru kenan na ce
mishi.
"Kai! Jabeer tsaya".
Tsayawa yayi cak ba tare daya juyo ba,
Suma sauran duk tsayuwa sukayi,
Kusan a tare Baba Nasiru da Baba Bashiru. Suka isosu.
Cikin haɗe fuska Baba Nasiri yace.
"Jabeer, in dai aure kake so ai gwara ka fito fili ka gaya mana, mu bazai gagara ba
mu aurar maka koda yar baiwace, tunda shi ubanka zuciyarshi ta mace, baya iya
tsinanawa kansa komai."
Da sauri ya rumtse idonshi,
Jalal kuwa wani irin kallo ya watsa bappanun nasu,
Shi kuwa Jabeer shiru yayi bai tanka musuba, Baba Basiru ne ya ne ya bugi
kafaɗarshi tare da cewa.
"Kodai kafi ganewa yawon zinace- zinacen daka saba ɗin ne? Kafin burin a barka ba
mata, kana zaune ka tsufe a gida ka fake da rigar malumta kana iskanci a cikin
tsarkakekkiyar masarauta ko".
Ido ya zuba mishi babu ko kebtawa, ganin haka Baba Basirun ya ɗauke hannunshi dake
kan kafaɗarshi.
Dai-dai lokacin kuma Barrister Kamal da Dr Aliyu suka iso wurin.
Suna isa Ya Jafar yayi saurin kamo hannun Ƙanin shi Sheykh Jabeer, ya fara ja da
sauri alamun su tafi su bar wurin gaba ɗaya, jikinshi rawa yakeyi.
Ganin hakane Haroon ya kalleshi cikin larabci yacewa Jabeer.
"Ɗan uwana mu tafi".
Barrister Kamal ne ya kalli Jabeer cikin sanyi yace.
"Jabeer jeka, ku tafi kada ka biye musu, tunda sun girma basu san sun girma ba."
Jin hakane yasa Jabeer ya juya ya fara tafiya.
Jalal kuwa wani harara ya watsa musu kana ya juya yabi bayan yayunshi.

Jafar kuwa Jan hannun Jabeer yakeyi a kiɗime gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi
tamkar mazari.
Ganin haka yasa Jabeer ya jashi ya kaishi sashinsu, ya damƙa hannunshi wa
Juwairiyya kana yace mata ta kula dashi, yanzu zai fita shida Lamiɗo.
Jiki a mace Juwairiyya ta mishi fatan a dawo 'lfy.

Ƙarfe biyu da rabi dai-dai suna cikin motoci, wanda a ƙalla sun kai su goma.
Motar forko Waziri ne wanda yake ɗane ga Yayar Lamiɗo.
Sai Galadima, da Wambai,
Ɗaya motar kuma Ɗan iyane da Sallama, da sarkin Dawaki, da sarkin fada,
Sai motar da Lamiɗo ke ciki, shida Garkuwa wato Jabeer sai Haroon sai kuma Hashim
da Laminu, ƙanin Hashim wanda duk yaran Gimbiya Saudatu ne matar babban yayansu
Habibullah wato Abbansu Jabeer, wanda da shine Galadima. Ɗaya rasune aka bawa Ya
Jafar sarautar wanda kwananshi goma da sarautar, komai na rayuwarsu ya sauya.

Sai motar dake binsu wanda Jalal, Jamil, Imran Sulaiman ɗan Barrister Kamal, suke
ciki.

Sai sauran motocin fadawa kamaru, Ɗan kazagi, mai yiwa sarki fadanci da kuna
dogari mai riƙewa sarki laima, da sarki mota da dai sauransu.
A jere a jere motocin ke tafiya.
Gudu sukeyi mai ɗan yawa sabida ganin yamma ta ƙarato, gashi basu je bama bare su
fara shirin dawowa.

Gudu sukeyi, kana fadawansu, rirtiƙe da bulalin dogaye.

Kai tsaye Rugar Bani suka nufa.


Koda suka iso cikin garin Shikan, sunga alamun garin babu lfy, har yanzu dan sai
matasan ƙabilar ɓachama da hausawa suketa yawo a garin ko wanne na bawa yankinsu
kariya.

Suna isa cikin Rugar Bani.


Gaba ɗaya mutanen Rugar duk inda suka gilma sai a bisu da ido,
Yara maza da mata sunata guduwa suna shiga cikin gidajensu.

Kai tsaye tsakiyar garin suka nufa wanda nanne fadar Arɗo Bani taken kuma lokacin
duk manya da yara maza tsoffi da dattawan garin duk suna harabar wurin sabida yau
jumma'a duk suna dawowa kiwo da wuri.
Kuma duk a tsakiyar garin suke taruwa sabida bawa garinsu kariya, domin har yanzu
suna cike da taraddadin abinda akayi musu.
Kuma ya rigada yanzu an ƙure haƙurinsu sunata shirin ɗaukan fansar rayukan da aka
kashe musune. Fiw-fiw haka motocin keta gilma mutane suna wucewa tara da tada ƙura
sabida babu kolta a garin sai yashi. Sai sauti da ƙugin mitocin ne ya cika kunnuwan
mutanen garin baki ɗayansu.

Motocin na isowa wurin. Gaba ɗaya mutanen Rugar dama baƙin mutanen maƙotansu sauran
rugage duk suka miƙe tsaye.
Tare da gya tsayuwarsu, suka gyara riƙon da sukayiwa sanduna su.
Ba tsoro ba fargaba sukayiwa motoci goma nan zobe, suka sasu a tsakiya.
Cikin sauri Sarkin dogarai ya buɗe marfin motar da yake ciki, ya fito tare da
zungureriyar bulalarashi. A take kuma Ɗan zagi ma ya fito.
Da sauri duk sauran fadawanma suka firfito kowa da zungureriyar bulalarashi.
Cikin ɗaga murya ɗanzagi yake cewa.
"Ta kawarka lfy Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa, sarki ɗan sarki jikin Sarki,uban
sarki kakan sarki. Jama'ar gari sun gaisheka,
Da sauri duk sauran fadawan suka, firfito cikin motar.
Sarƙin motane yazo ya buɗe wa Sarƙi ƙofar.
Dogari kuwa matsowa yayi da sauri ya buɗe wata ƙatuwar laima, gaba ɗaya sukayiwa
ƙofar motar labule da mamyan jajayen rigunansu, yayin su duk sawunsu babu takalma,
sannan kawu nansu naɗe cikin wasu ƙatti-ƙattin rawanunnuka masu girma babu kunne ko
ɗaya a jiki.

Gaba ɗaya mutanen Rugar kuwa, sai ƙara tsuke fuskokinsu sukeyi, cikin jin haushin
zuwa sun.

Can cikin motar kuwa Haroon ne saƙale da wayarshi a kunne cikin sanyi yake mgn
sabida kada Lamiɗo ya jiyoshi, haka kuwa babu mai jinshi sai Jabeer.
Cikin sanyi ya ɗan kalli Jabeer kana yaci gaba da mgna a hankali yace.
"Umaymah ni dai hankali na ya tashi, da irin wasu mutane da wasu abubuwan da
akeyiwa su Jabeer a masarautar su, Umaymah, meyasa bazasu bar musu sarautar da
Masarautar tasu gaba ɗaya bane, sai kinga fa yadda Jazlaan dinki ke fuskanta
ƙalubale fa."
Cikin wata iriyar murya Umaymah tace.
"Yanzu kuna inane?".
Kanshi ya ɗan jujjuya kana yace.
"Uhum ni ina zan san inda muke, na dai san munzo wata Rugar fulani ce, wai GARKUWAN
FULANI nasu ya kawo musu ziyara dan ja-janta musu abinda ya faru, kuma gaba ɗaya
mutanen rugar naga sai
Wani irin kallo suke mana kamar dai zasu huce a kanmu ne".
Cikin wani irin tattausan murmushi mai nuna jin daɗi tace.
"Bawa Jazlaan wayar".
A hankali ya miƙa Jabeer wayar tare da cewa.
"Umaymah ce".
Cikin sanyi yace.
"Kace tayi haƙuri sai mun koma zan kirata".
Da sauri ya like mishi wayar a kunne jin tana cewa.
"A a amshi wayar".
Ɗan haɗe fuska yayi kana ya amshi sallamar da tayi mishi.
Kana ya meda kai jikin kujerar murya can ƙasa yace.
"Umaymah, Na gaji tunda muka dawo ban hutaba, yau da sassafe wannan tsohon ya sani
shara kamar wani bawanshi haka ya sani na share mishi wannan ɗakin nasu na gado
wanda in dan ta nine rusashi za'ayi gashi yanzu kuma ya kwasoni zuwa wata rugar
FULANI da duk makamaine a hannunsu, ko wa zasu daka".
Cikin wani irin jin daɗin daya bashi mamaki mai yawa tace.
"Ko kai zasu dakane Jazlaan, Sheykh Jabeer, yasha zana a hannun Fulani".
Cikin sanyi yace.
"Su kashe Ni dai Umaymah, ke kin sani tunda nake a duniya, ba'a taɓa dukana ba,
sabida koda iba yaroma ban taɓa yiwa Mama da Ummi laifin da zai kaisu ga yimin
dukaba, Abba na kuma baya dukanmu, Umaymah kema baki taɓa koda marina ba, to kuma
wa kika ga zai dakeni a faɗin duniyar nan banda ruwan sama".
Murmushi tayi wanda har saida yaji sautin cikin sanyi tace.
"Allah ya tabbatar da al'khairi cikin tafiyar naku, ka dai lura kaine GARKUWAR dole
da duk abinda zai cutar da Lamiɗo ko masarautarku ko sunanta dole kai ne zaka zame
musu Garkuwa, so dan Allah bana son kayiwa Lamiɗo musu bare gardama a cikin duk
abinda zai umarceka".
Cikin sanyi yace.
"To Umaymah, in na koma zamuyi mgna".
Daga nan sukayi sallama, cikin mamaki ya kalli yadda gaba ɗaya manyan hakimai sun
firfito, ga Lamiɗo ya fita amman yana tsaye bakin ƙofar motar.
Cikin sauri ya kalli Hashim tare da cewa.
"Hashim Lfy kuwa naga duk suna tsaye, garin basu da abin zamane daza'a karrama
baƙi?".
Cikin nitsuwa Hashim yace.
"Uhum cewa sukeyi, wai sun yafe ziyara da ja-jantawar Lamiɗo".

A wojen kuwa, cikin ɗaga sauti Danzagi yace.


"Hattara dai fulani mai ƙasar ne gaba ɗaya, ke tsaye tsakiyar garinku, maza ku bada
masauƙi".
Ya ƙarishe mgnar yana jujjuua bulalar hannunshi haka sauran fadawan.
Cikin fillanci ɗan aiken Arɗo Bani ya buɗe murya da ƙarfi cikin harshen fillanci
tare da cewa.
"Maza ku bada hanya mai martaba ya iso fadar Arɗo Bani".
Jin haka gaba ɗaya taron al'ummar fulanin suka fara buɗa hanya,
Har gaban rumfar da Arɗo Bani ke ɗauke baƙi, inda aka shimfiɗe wurin da manyan
taburmaii kana aka malale manyan kilisai irin namu na fulanin dawa.
Bappa Malam Liman Alhaji Haro Alhaji Umaru, Musu, da kuma Ardo Duno da Arɗo barwa
maƙotansu, duk suka mimmiƙe tsaye sai dai gaba dayansu fuskokinsu babu wal-wala,
asalima wasun cikinsu jikinsu har ɓari yakeyi, dan fushi da zafin zuciya.

A can cikin ƙauyen Bonon kuwa, Ba'ana da sauran ƙabilum ɓamawam duk suna gaban
dodon tsafinsu Bonon ɗin,
Da gudu Maman Ba'ana ta iso wurin cikin Yaren ɓacamancin ta sanar dasu zuwan, sarki
Lamiɗo da tawagarsa, jin hakane yasa, Ba'ana ya miƙe jiki na rawa ya nufi
rugartasu.
Su kuwa sauran yace in yaje yaga da matsala zai kirasu.
Nan ya tafi su kuma sukaci gaba da dariyar mugunta.

A cikin Rugar Bani kuwa, Bukar Baban Ba'ana ne yayi wata iriyar fitinenneyar
murmushi mai cike da mugunta dan son haddasa fitina, ta yadda zai samu masarauta
Joɗo da kanta ta shiga matsala.
Kutsawa yayi tayi cikin mutane har ya samu ya shigo gaba-gaba.
Lamiɗo kuwa da tawagarsa taku sukeyi cikin al'farma da ƙasaita.
Su Waziri, Galadima, Wambai, Ɗan iya, ɗan buram, duk suna biye dashi a baya,
Dogari na rike mishi da laima, fadawa kuma na zazzaune a ƙasa, gefe da gefe,
Ɗanzagi kuwa muryarsa ce cika wurin baki ɗaya duk da hayaniyar da wurin kedashi.
A hankali Jabeer ya sako sawunshi woje, yana taka ƙafarshi ta dama kan ƙasar garin,
yaji zuciyarshi ta buga da azaban ƙarfi har saida ta kaishi da rumtse idonshi tare
da ambaton.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
A saman red lips ɗinshi.
da ƙarfi yasa hannunshi ya dafe ƙahon zuciyarshi, tare da kuma maimata.
"Hasbunallahiwani'imanwakil".
Sabida ji yayi tamkar zuciyarshi zata fasa ƙirjinshi ta faɗo ƙasa. Jalal, Jamil,
kuwa ido suka zuba mishi, sabida ganin yadda ya rumtse idonshi, sabida suna bakin
ƙofar motar, sune ma suka buɗe mishi marfin.
Haroon kuwa da Hashim da Laminu, jira suke ya fita kafin su fita.
Cikin mugun tsana Laminu ya kalli Jabeer ɗin da ya yunƙura ya fita,
zuwa yanzu, wani irin harbawa da tsalle zuciyarshi keyi, wani irin masifeffen
fargaba, da kaɗuwa ne suka dirar masa lokaci ɗaya.
A hankali duk suma su Haroon suka fito, a tsakiya sukasa Jabeer kana bayinshi na
biye dasu a baya.
A hankali ya gyara tattausan al'kyabbar jikinshi, tare gyara hiramin kanshi ya
kange kekyawar fuskarshi.

Takun da yakeyi ne ya ƙarawa shigarsa ta al'farma daraja,


ya fito tamkar balarabe, gaba da baya, kamalarsa da kwarjini shi ya cika dukkan
idanun bani adam dake kan doron ƙasar wannan wurin.

Ya Hashimu ne da ya samu ya dawo gida jikinsa da sauƙine, yayi wani irin kabbara
mai ratsa zuciya, cikin sanyi yace.
"Ziyararku tayi haske sabida kun zo mana da mai hasken addini a jiki da
zuciyarshi".
Ga mamakinshi sai yaji Ɗanzagi na cewa.
"GARKUWA ya amsa Sheykh Jabeer Jikan sarki tsatson sarki gaba da baya".
Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali yake takunda yasa al'kyabbar sa buɗuwa tana
bajewa, sabida ɗaga hannunshi da yayi yanai musu sallama irin ta addinin Musulunci.
Mafi akasarin mutanen tafukan hannunshin suka zubawa ido, sabida kai da ganin tafin
hannunshi kasan ya gauraye da ni'imar ambaton sunan Allah da rike littafi
al'ƙur'ani, da kuma jin daɗin.
Shi kuwa Jabeer ƙara sarƙafe carɓin shi yayi cikin yatsun hannunshi, kana, ya
fuskanci gefen hagunshi, ya ɗanga musu hannu tare dayi musu sallamar kamar yadda
yayiwa yan gefen damanshi.
A haka har suka isa tsakiyar ƙaton filin.
Inda Lamiɗo da sauran tawagarsa ke zaune.
Bisa fararen kujerun robar da anka jera musu cikin rumfar suka zazzauna.
Bayan sun amsa musu sallamar da sukayi.
Cikin nitsuwa Lamiɗo ya kallesu tare gyara zamanshi.
Muryar Ɗanzagi ce ta karaɗe wurin da cewa.
"Gyara kimtsi. A saurara dai Lamiɗo jikan ɗan Lami Bubayero jikan Lamiɗo Joɗa
zaiyi mgna".
Wani irin harara suka watsawa Danzagin, shi kuwa Lamiɗo cikin nitsuwar datattaku
tace.
"Da farko dai zan fara da baku haƙurin zalumcin da akayi, muku, Allah ya jiƙan
wanda suka rigamu gidan gsky."
Da ƙarfi Ɗanzagi yace.
"Amin". Su kuwa dattawan ido kawai suka zuba mishi.
Shi kuwa Lamiɗo a hankali yaci gaba da cewa.
"Ina mai baku haƙuri da kuma umarnin kada kuce zaku ɗauki mataki domin ramuwa."
Kamar daga sama sukaji Muryar Bakur yana cewa.
"Babu wani sarkin da ya isa ya hanamu ɗaukar fansa sai, Ubangijin daya busa mana,
numfarfashi".
Da ƙarfi Wani dogarin ya ɗago zabgegiyar bulalarshi ya zabgawa Bukar.
Wanda saida yayi tsalle ya kurma ihu.
Cikin tsauri Lamiɗo ya ɗagawa duka fadawanshi da hadimanshi da dogara shi hannu
alamun kada su sake dukan kowa.
Saura su Waziri kuwa duk shiru sukayi,
Jabeer kuwa, a hankali yaci gaba da tasbihin da yakeyi, sabida danne abinda yakeji
zuciyarshi nayi.
Shi kuwa Lamiɗo cikin sanyi ya fara mgna, dan yasan zafin rashin da sukayi ne yasa
sukace sai sun rama, a hankali ya kalli fuskokin dattawan da yasan sunje mishi har
fadanshi dan neman zaman lfy, cikin kula ya kalli Arɗo Bani tare da cewa.
"Arɗo Bani zaku haƙura, hukuma da masarauta ta bi muku kadun cutar damu da akeyi,
ko zaku ɗauki makami dan ramawa?".
Cikin tarin kufula da harzuƙa da kuma son cinma wata gagarumar manufar da ya daɗe
yana fatan ya samu da sai yau, fuska a haɗe yace.
"Babu wani wanda zan kuma hana ɗaukan makami,
Dan kare kanshi da ramuwar kisar gillan da akeyi mana."
Cikin tarin Mamaki da al'ajabi Bappa da sauran dattawan suka buɗe baki tare da
kallon Ardo Bani, Jabeer ma idon ya buɗe cikin sanyi yace.
"Baba Ardo kayi haƙuri, muyi aiki da al'ƙalami, domin al'ƙalami yafi tokobi, ina
nan inata shirin samar da tsaro na musamman kan FULANIN ƙasarmu da nake
shugabanta."
Cikin nuna tsantsar fushi da son fusata Lamiɗo Arɗo Bani ya dakawa Jabeer tsawa
tare da cewa.
"Kada rufe min baki, meka sani akan Fulani? Me ruwanka damu? Damuwarmu ta shafeka
ne? Ina kake sanda ake kashe mana mata, yara, jikoki, mu kanmu bamu tsiraba, in
munje mun kai kukanmu a koremu tamkar karnuka, sabida duk baku san darajar fulani
ba."
Cikin sauri Ɗanzagi yace.
"Hattara dai Ƙaramin Ardo, wannan sarkine na fulɓe masarautar filɓe ce gaba da
bayanta".
Cikin ɗaga Muryar Ardo Bani yace.
"Tafi can baƙin bawa, bawan banza bawan wofi mai ka sani kan fulɓe, meka sani banda
bauta da fadanci, masarautar da kuke bautawa bata san menene fulɓe ba".
Cikin sauri Waziri ya yunƙura zaiyi mgna, da sauri Lamiɗo ya dakatar dashi, sabida
zuwa yanzu zuciyarshi ta fara tafasa, yaya daga kawowa mutane ziyara dan ja-jantawa
suke neman tozarta mushi masarauta. Cikin ɓacin rai ya kalli su Bappa daketa kama
hannun Arɗo bani daketa fizge-fizge yana kwaza musu baƙar mgna, cikin fushi yace.
"Masarautar Joɗa ɗince bata fulani ba?".
A harzuƙe Arɗo Bani yace.
"Tabbas dan data fulanice, da an bamu kariya da tsaro, da an duba kukanmu, a
kashemu a hanamu ɗaukar fansa, an kuma kasa bamu tsaro. Nan da mukaje ina shi jikan
naka da yake matsayin Garkuwan Fulani, yana can ƙasashen woje, da iya dukiyar da
ake bashi tsaro da kariya shi rai ɗaya ta kai a kula da fulanin daji dubu a kuma
basu tsaro.
Yau kwana uku da kashe mana mutane sai yau zaku ɗebo manyan riguna kuzo mana da
batun wai kada mu rama, sara da suka da yanka mana mutane da akeyi,
Kaida kab zuriyar ka da masarauta ka, babu mutun ɗaya da zai iya jurar koda bulalar
*(SHAƊI)* ma bare sara da yanka da suka da wuƙa a hakan kuke ganin kanku Fulani".
Cikin tarin zafin ƙuna da tafasar zuciya Waziri yace.
"To me kuke so muyi muku, tun randa akayi abun munzo bamu sameku ba".
A harzuƙe Bukar yace.
"Ƙarya ne babu wanda yazo".
A hankali Jabeer ya buɗe baki da nufin zaiyi mgna sai yaji Lamiɗo na cewa.
"Uhum jinina kuke cewa ba fulaniba, to ko jaririn da aka haifa yau a jikin
masarautar Joɗa zai iya jurarar bulalar SHAƊI bare manya ko ɗan baiwa zai iya bare
jinina ƴaƴana ko jikokina, ko kun manta masarautar Joɗa ce tushen Shaɗi?".
Cikin son harzuƙa Lamiɗo Arɗo Bani yace.
"A da can baya ba, yanzu kuma da aka san lusarai ake haifa a masarautar inji an
haramta shaɗi a masarautar, yau in kun isa fulani ka bada ɗan ka ko jikanka ayi
gasar Shaɗi dashi, in ya iya jurewa, to mun yarda mun gamsu ku fulanine ku
masarautar Fulani, in kuwa kun kasa fidda goninku to, ku ba masarauta fulɓe bace."
Wani irin karkarwa jikin Lamiɗo ya fara sabida fusata, wai suda masarautarsuce
tushen fulɓe a ƙasar, su ake cewa ba fulani ba, har ake kiransu lusarai, Galadima,
Waziri, Wambai, Ɗan iya, Ɗan buram, Ɗan Maliki, Sarkin Dawaki.
Gaba ɗaya hankalinsu yayi masifar tashi sabida ganin tsananin fushi da tashin
hankalin Sarki Lamiɗo.
Jamil Jalal Haroon kuwa , hankalinsu na kan Jabeer bisa alamun yana cikin wani
hali.
Shi kuwa Jabeer bugun da zuciyarshi keyi ne yasa,
Hankalinshi tashi, ƙarfin addu'o'in da yakeyi ne, yashi iya fahimtar abinda suke
cewa.
Kamar daga sama kamar cikin mafarki, sukaji murya Lamiɗo na cewa.
"Ga jikana, Jabeer GARKUWAN FULANI, na badashi a matsayin matashi mai yin gasar
Shaɗi ku fito da duk gwanin da kukega shine makurar gwayen yankinku. Ayi Shaɗi
dashi yadda zaku samu gamsuwar yakai matsayin ya kasance GARKUWAN FULANI".
Tunda ya amɓaci sunan Jabeer, Sarkin Fada yayi wani irin murmushi mai cike da jin
daɗin alamun burinshi zai cika.
Hakama Arɗo bani wani irin asirtaccen murmushi yayi.

Jala, Jamil, Haroon, Hashim, Imran, Galadima, kuwa wani irin zazzaro ido sukayi.
Cikin tsananin kaɗuwa da firgicin batun Lamiɗo suka zuba mishi ido.

Bukar kuwa cikin karaji yace.


"Ba'ana Bukar shi zai kara dashi."
Ya ƙarishe mgnar da fatan Ba'ana ya kashe wanda aka kira da Jabeer tunda jikan
Lamiɗo ne.

Jabeer kuwa wani irin kallo yayi kakan nashi, irin kallon nan.
Na lallai kam tsohon nan ka haukace, ka zauce, ai bani bakam ko inuwata bazaku kuma
gani a garinkuba bare kuyi wannan gwajin dashi.
Ga mamakinsu kab sai sukaji Arɗo Bani na cewa.
"A yau ɗinan kuma Yanzun nan, a kuma nan za'ayi gasar Shaɗi in har kun isa fulani."
Sosai Lamiɗo yaji hakan bai mishi ba dan a zotonshi za'asa ranane ya koma ya shirya
Jabeer kafin ayi gasar, to fahimtar ƙuresu suke neman yi, yasashi gyara zamanshi
cikin danne fargabanshi na anya Jabeer zai iya jura yace.
"Na Aminc....!

Yau bisa wani uzuri ban samu yin posting da wuriba, kana kuma ba editing a gurguje
na watsoshi, bari in nemo PAGE 16 ko zuwa yan da yamma ne.

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🐍🤴🏻💘
🦚🐍 🤴 🏻 💘

*GARKUWA*

PAGE 16

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🌈🤴🏻💘
🦚🤴 🏻 💘

*FREE PAGE SUN ƘARE DAGA WANNAN PAGE 16 DIN IN DAI KIKAGA LITTAFINA GARKUWA BA TARE
DA KIM BIYA NA SAKI A GROUP BA TO NA SATANE, DAN ALLAH DA MANZONSA KADA KU FITARMIN
DA LITTAFI DAN ALLAH KU BARI IN SAMU KUƊI zuwa makka😂😂😂*

*Littafin GARKUWA na kuɗine dan Allah da Manzonsa kada ki karanta na sata, kada ki
watsamin littafi a sata, turo katin MTN na ɗari uku kacal ta wannan number
09097853276 ki biya ki karanta cikin aminci ba tare da haƙƙi naba. Ko kuma ki biya
1k domin shiga Special Group wanda cikin sati biyu rak za'a gama Part 1, da izinin
ubangiji kana a shiga 2, turo dubunki ɗaya ta wannan asusun 0005388578 jaiz bank
Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo shaidan biyanki ta wannan number 09097853276 in
baki da halin biyan dubu ɗaya ko baki da ra'ayi kina iya turo ɗarinki uku kacal da
ban tsauwalaba sabida halin rayuwa da muke ciki. Dan Allah da Manzonsa da darajar
iyayenki kada ki sai littafina in dai kin san niyarki ki saya ki fitar da shine in
kuma. Har kin sayane to dan Allah da Manzonsa gaya min in baki kuɗinki in cireki a
group na, dan Allah🙏🏻 nace badon niba*

"Na Amince!". Cikin tarin mamaki Jalal, Jamil, Imran, Haroon, Hashim, da duk sauran
tawagar Lamiɗo suka, zazzaro ido cikin tarin mamaki da al'ajabi, sam basuyi zaton
jin haka daga gareshi ba,
Ya Salmanu kuwa wani irin farin cikin mara misaltuwa ne, ya rufewa, domin yana
ganin ikon Allah da yake nuna mishi zahirin abinda yake nuna mishi a mafarkansa
tsawon kwanakin da yake a gadon asibiti.

Ba'ana kuwa da tun ɗazu ya iso, wani irin ihu yayi mai cike da farin ciki, da jin
daɗin yana ganin zaiyi abinda gaba ko kashe mutanen Rugar Bani sukayi gaba ɗaya,
masarautar Joɗa bazata kulasuba,
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi sabida azabar muguntarsa dake tasowa.

Arɗo Bani ma wani murmushi manufa yayi tare da cewa.


"To, ina gwanin naku?".
Cikin karaɗi Ɗanzagi, ya kalli Jabeer tare da cewa.
"Malami ba faɗen Allah, malamai magada annabawa, Sheykh Jabeer Habeebullah
Nuruddeen Bubayero Joɗa, GARKUWAN sarki Lamiɗo, jikan sarki, mai martaba Nuruddee.
Jarumin Masarautar Joɗa."
Gimtse bakinshi yayi ganin wani irin kallo mai ma'anoni da yawa da Jabeer ke watsa
mishi,
Cikin yin ƙasa da murya tare da tsuke fuskarsa, ya ɗan ronƙofo kanshi, kusa da
Lamiɗo murya a kausashe yace.
"Wannan tatsuniyar da kukeyi, bafa koyarwan shariya bace".
Da sauri Lamiɗo ya katseshi da cewa.
"Eh amman koyarwar Masarautar Joɗa ce".
Cikin kufula yace.
"Ya ina ce maka Allah kana cemin gadon masarautar Joɗa ce".
Cikin haɗe fuska da ƙasaita Lamiɗo yace.
"Eh ba addini bane, kuma sai an yishi dan gadon masarautar muce".
Kanshi ya kuma motso dashi jikin kakan nashi cikin taɓe fuska yace.
"Okay to ai sai ka tashi, ka tsaya su zaneka ciki da woje".
Cikin kausasa murya Lamiɗo yace.
"Kai ne dai zaka tashi".
Cikin watsawa kakan nashi wani kallo na lallai ma tsohon nan kanka ya kwance yace.
"Ai bani bane sarkin, kaine sarkin ko?".
Cikin faɗa Lamiɗo yace.
"To ko Ubanka bai isa in sashi abu yace bazaiyi ba".
Jin muryar Lamiɗo ta ɗan yi samane, yasa fadawanshi suka miƙe tsaye,
Ware rigunansu sukayi, suka kamgesu da jajayen rugunan nasu, ta yadda babu mai
ganinsu,
Cikin haɗe fuska Jabeer yace.
"Yesss shi bazai ƙiba, tunda kai ubanshi ne, Ni kuwa babu wanda zai sani in zauna
in bawa wani ƙaton fatar jikina ya zane, kai jimin zancen son zuciya, kai ni
kaɗaine jikanka, a duniya, a nanma baga Ya Hashim ba ai shine babban jikanka,
zancen gsky na gaji da wannan tirsashe-tirsashen naku, kanada ƴaƴan ai, ka kira
ɗaya daga cikin ya'yan ka yazo ya wakil ceka mana, Amman ni dai kam Muhammad Jabeer
babu wani tsohon da zanyiwa mubaya'a in tsaya wani gardin makiyayi ya ɗimeni, tunda
ba faɗin Allah bane".
Ya ƙarishe mgnar yana yunƙirin tashi tsaye.
Da sauri Galadima yasa hannu ya kamo nashi, fuskar ya kwaɓe tare da komawa zaune
yana gyara hiramin kanshi da al'kyabbar jikinshi,
Cikin tausasa harshe Galadima yace.
"Jabeer kafa san ma'anar GARKUWA a masarauta."
Cikin sanyi da ganin kima da darajar dottijon Jabeer ya kwaɓe fuska tare da cewa.
"Nifa shiyasa wannan mulkin bawai sonshi nakeyi ba, sabida wannan tsarabe-tsaraben
daba na addiniba, a buwayi mutun dashi, yaya nasan abu ba Allah ne da manzonsa suka
wajabta mana shiba, ace in zauna a cutar dani."
Cikin sanyi Waziri ke jujjuya mishi kai a hankali yace.
"Jabeer Garkuwa fa, kake dole ka kare martabar Masarautarmu kana ka nunawa su
fulanin da kake Garkuwarsu kai Jarumine".
Rai a ɓace ganin sufa da gske sukeyi, cikin dakiya yace.
"Bana so, ita wannan sarauta ta GARKUWAN FULANI ku bawa duk wanda kukeso, ni ban
nemaba dama".
Shiru Haroon yayi dan gskya harga Allah shi wannan abun yazo masa a bazata.
Jalal kuwa cikin haɗe fuska yace.
"Wannan ma ai zancen banza ne,
An bawa Ya Jafar Galadima, ko kwana ashirin baiba a kai, aka birkita masa rayuwa,
kana yanzu kun likawa Hamma Jabeer wani GARKUWA kun kwasomu kun kawomu Rugar
fulani, wai kuna cewa ayi gasar duka dashi."
Da sauri yayi shiru ganin Jabeer ya ɗaga mishi hannu.
Jamil kuwa tuntuni idonshi ke tsastsafo ruwan hawaye dan gani yake so ake a kashe
Hammansu a ƙarar da ƴaƴan ɗakinsu,
Laminu kuwa ɗan Gimbiya Saudatu matar bappansu Sheykh kuma Kani ga Yah Hisham wani
irin dariyar jin daɗi yakeyi.

Shi kuwa Lamiɗo, wayarshi ya zaro, Mai alfarma Sarki Jalaluddin ya kira wanda yake
kane ga Jabeer. Wanda ya haifi Mamanshi.
Bayan sun gaisane yayi mishi bayanin abinda ke faruwa, jin haka yasa yace ya bawa
Jabeer wayar.

A tsakar filin Rugar Bani kuwa, tuni.


Arɗo Bani ya bada dama na suduka yana shekantawa gari cewa.
Ana gamgamin Shaɗi yanzu-yanzu tsakanin Ba'ana da kuma jikan Sarki Nuruddeen.

Tuni an firfito da ganguna anata kaɗe-kaɗe da bushe-bushen sarewa, kana ana buga
babban gangan dake tsanar da makotan Rugar Bani sauran rugage alamun za'ayi Shaɗi
yanzu.

Kafin kace kobo, Rugar Bani ta cika tayi maƙil da mutane, Maza da mata, matasa da
tsoffi, sabida an san duk sanda za'ayi Shaɗi ana bada sanarwar, kwana uku kafin nan
to jin wannan na gaggawa kuma da jikan Sarki za'ayi yasa, mutane taruwa, gashi
ranar jumma'ace, duk matasan rugogin suna, gida tunda suka dawo sallan jamma'a.
Rugar Bani ta cika tayi maƙil da bani adam, tako wacce kusurwa tsastsafo akeyi
kusufa-kusufa.
Jin karan tamɓarin ganganr Shaɗi ne ya ƙara gaiyato mutane harda na cikin garin
Shikan, tuni ƙabilun Bonon sun garzayo cikin Rugar Bani.

Bukar kuwa mahaifin Ba'ana shida kanshi yaje, cikin Garkensu ya ɗauko tukunyar
tsumin bulalim shaɗin da Ba'ana ke tsumasu da dafin kunamai da sauran sihirurruka,
na dodon tsafinsu Bonon.

Matasa majiya karfi ne keta ɗebo ruwa, cikin rijiyoyin garin.


Suna jiƙa taron wurin dandamalin, da za'ayi gasar kaɗe-kaɗen duk sun taru sun cika
kunnen kowa.
Jabeer kuwa bugun da zuciyarshi keyi shiyafi komai tada mishi hankali.

A can cikin gidajen Rugar kuwa, duk yan samari da yara sun firfito.
A gidansu Shatu kuwa,
Tunda taji Shelan da Nasuduka yakeyi cewa gasar Shaɗi tsakanin Ba'ana da jikan
sarki.
Kuka ta farayi, cikin tashin hankali da kiɗima ta kamo hannun Ummiy da tayi shiru
sai ido take binsu dashi, murya na rawa tace.
"Ummiy kijifa, zasuyi ya kashe, wani wanda baijiba bai ganiba, sunfa san illar dake
cikin bulalinshi."
Ganin Ummiy dai ba mgna zatayi ba, yasa ta kamo hannun Junainah cikin tsananin
tashin hankali tace.
"Junainah ki gudu, kije kicewa Bappa kada ayi gasar nan, Ni dai a bari na haƙura
zan auri ya Ba'ana a yadda yake, zan zauna dashi, zanyi ƙoƙarin gyara mishi, rayuwa
na gaji, kada a sake cutar da wani a kaina".
Da sauri Rafi'a ta kalleta jin ta kamo hannunta cikin zubda hawaye tace,
"Rafi'a wlh ya Ba'ana zai iya kashe mutun a kaina, da dafin kunamai yake tsuma
bulalinshi, da wani tsafin, me ribata ayi ta cutar da mutane a dalilina, babu fa
wani mahaluƙin da zai iya cin Ya Ba'ana gasar Shaɗi, babu wanda zai iya jurar
azabar bulalinshi fa."
Cikin sauri ta miƙe tare da miƙar da Junainah, sai kuma duk suka koma suka zauna,
Jin muryar maƙocibsu Sarkin aska, yana cewa.
"A a Shatu kada ki tura kowa, kada kuma kije kin tsumayi sakamakon gasar yau in sha
Allah zata banbanta da na baya .
Yanzu ma Arɗo Bani ne ya aikoni da in gargaɗeki."
Yana faɗin haka ya juya da sauri ya fita, kana ya nufi wurin gasar.

Da ido suka bishi. Ita kuwa Junainah da sauri ta miƙa ta nufi kitchin ɗin su, tana
cewa.
"Yauwa Adda Shatu, barin in kawo mana gasassun zabbin da Ya Ba'ana ya kawo mana
muci.
Ɗazu da nace muci Adda Rafi'a ce, tace mujiraki."
Cikin sanyi Rafi'a tace.
"Yauwa Junainah kawo mana, muci yau tunda gari ya waye bamuci komaiba."
Gyara zansu sukayi, kana ta kalli Shatu cikin kula tace.
"Dan Allah Shatu muci abinci, kinga Ummiy ma taƙi cin komai ganin, yadda kiketa
kuka tunda kikaji ɓatansu ya Giɗi da rasuwar Ya Lado da Inna."
Cikin zubda hawaye ta gyaɗa mata kai, sabida ita kanta tasan tana jin wani irin
masifeffen yunwa, tamkar zai kasheta.
Da sauri Junainah ta nufosu riƙe da akoshin gasassun zabbin da aka zuba dafin
macijin a cikin.

A can cikin tsakiyar garin Rugar Bani kuwa.


Tuni su Ba'ana an gama shiryawa zalumci, domin dama ai a ƙa'ida shi zai fara duka,
Yana tsaye sai zagaya filin yake yana zane iska, makaɗa da mabusa nata yi mishi
kirari.

A cikin wurin da Fadawa suka kange Lamiɗo da tawagarsa kuwa, anata kai ruwa rana da
Sheykh Jabeer,
Cikin kufula, yake cewa Sarki Jalaluddin da suke waya dashi.
"Nifa babbar matsalarta wannan abun da za'ayi ba *Sunna* bace ba kuma *Farilla*
bace, ba kuma *Mustahabbibace*, kai ko a babin *Makaruhi* ban taɓa cin karo da
wannan banzar al'adar da kukeso in yarda ayita dani ba,
Ina kuma da yaƙini in da zan bajeta a babin musulunci, kai tsaye za'a iya
karhantashi, sabida ai cutar da kaine kuma, Musulunci bai yarda mutun ya cutar da
kanshi ba, haka kurum kuce wai in tsaya a zaneni, inji shi kanshi kakan Lamiɗon
Joɗo da yaji haza a gasar Shaɗin shine ya hana wannan al'adar a masarautarsa sannan
yanzu ace za'a saketa a kaina bayan tsawon shekaru 145 ba'ayishi ba, tun zamanin
jahiliyan ma an bar abu sai yanzu ku tara abu a kaina, to wallahi bafa zai yiwuba."
Cikin kufula Sarki Jalaluddin yace.
"To ya kakeso ayi ɗan masu ilimi kowa jahiline sai kaine mai ilimi sabida tsabar
tsoro da ɗan karen son jiki kana gudun abinda zai taɓa lfyarka shine zakayi ta jawo
mana wasu dogin falsafofi, a hir ɗin kafa Jabeer ko uwarka bazan sata abu taimin
musuba".
Gaba ɗaya sun hautsuna mishi zuciya,
Ji yadda suketa zageshi, dan kawai yace bazaiyi abinda al'adace ba addiniba sai
wani ce mishi suke ko uwarka ko ubanka, bayan sun san baya kuran hakan, rai a ɓace
yace.
"Uwata kace ai tunda ita ai ka haifa ba niba ko?, zancen gsky bafa za'ayi wannan
abunba, sun daɗe basu ce mana lusaraiba, dolene, sai sun yarda mu fulanine, kai yau
nifa ba bafulatani bane.
A kirani da ko wacce ƙabilar ma in anga dama aikin kawai!".
Yana faɗin haka ya katse kiran.
Laminu kuwa da yake cikekken ɗan jarida, tuni yana naɗe komai a faifai jawaban su.

Shi kuwa Sarki Jalaluddin, ido ya zubawa wayar jin jikan nashi ya katse kiran,
murmushi yayi, irin nasu na manya, kana da sauri ya kira, Umaymah.
A can Babba birnin Katsina, kuwa Gimbiya Khadijah Umaymah kenan , wacce take matar
ɗan Sarkin Tsinako, Kekkyawar mata mai cikar haiba nitsuwa, tana kishinɗe, bisa
wata tattausar doguwar kujera, yayinda Hadimanta biyu ke mata tausa.
Jin wayarta na suwane, yasa ta buɗe idanunta dake lumshe, tunda sukayi waya d, ɗan
ta Haroon ke gaya mata inda sukaje da ƴaƴan ƴar uwarta mafi soyuwa a rayuwarsu ne,
taketa murmushi.
Ganin sunan mahaifinta ne yasa tayi saurin amsa kiran.
Bayan sun gaisane, Sarki Jalaluddin ya ɗanyi murmushi cikin nitsuwa yace.
"Khadijah, kira ɗan ki, ki bashi umarnin bin umarnin mu, domin yana nuna mana ai
bamu muka haifeshi ba, bazamu tirsasashi ba".
Cikin tarin girmamawa tace.
"Ranka ya daɗe, me kukeso in bashi umarni a kai nasan bazaiyi min musuba".
Cikin jin daɗi yace.
"Kice dashi ya amince da gasar da za'ayi".
Cikin sauri tace.
"To An gama yanzu kuwa, in sha Allah zaku sameshi mai biyayya a gareku".
Daga nan sukayi sallama,
Kana ta kirashi, sau biyu tana kiranshi baya ɗagawa, sabida kanshi ya ɗau zafi yana
ganin za'a tirsasashi ya cutar da kanshi.
Ga wani irin azabebben tsinkewa da zuciyarshi keyi,
Ji yake tamkar zata faso ƙirjinsa ta fito, tayi ta tsalle a doron ƙasa.
Gashi duk tsoffin Masarautarsun sun zagayeshi.
Kowa da abinda ke ce mishi.
Ga uban kiɗen-kiɗen dake hawa mishi kai.

Ita kuwa Umaymah ganin bai amsa kiran bane, yasa ta kira Haroon yana ɗagawa tace.
"Ina Jazlaan bashi wayar".
Da sauri yace.
"To Umaymah uwar Garkuwa gashi nan ido ya raina fata".
Cikin barkwancinta da yaron nata tace.
"Kaci gidanku Haroon Ni ɗana ba ragobane".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To mu gani a ƙasa mana Umaymah".
Yana faɗin haka ya miƙa Jabeer wayar wanda yake cewa Lamiɗo.
"Bafa zan yiba, tsohon nan gwara ka miƙe kaje ayi da kai tunda kaine sarkin
Masarautar Joɗa, Ni nan babu abinda na sani bayan nonon uwata sai al'ƙur'ani da
hadisai, sai likitancin da kuka sani na karanta a dole badon raina yasoba, tun
ina yaro kullum Ni a cikin sani dole kuke da tsabar rainin hankali, kaje a jibgeka,
Ni kuwa nayi al'ƙawarin zan jinyaceka, Lamiɗo Joɗa."
Ya ƙarishe mgnar yana amsar wayar da Haroon ke miƙo mishi cikin faɗa yace.
"Mitsss wai meye kaketa tura min wannan argar wayar taka ne?".
Cikin mamaki Haroon yace.
"Kan uba Jabeer wayar tawace ma arga, wayar da kuɗi ta sun kai rabin million To
inma argace Umaymah ce bisa layi".
Ba tare da ya kara wayar a kunneba yace.
"Hello Umaymah".
Cikin tausayi Jalal yace.
"Hamma Jabeer baka kai wayar kunneba".
Lips ɗinsa ya taune tare da cewa.
"Au, zama su sani yin abu da yawa".
Haroon kuwa mamaki yakeyi domin karo na forko kenan da yaji Jabeer yace Hello a
madadin Assalamu alaikum, da shine abinda yakeyi.
Ita kuwa Umaymah tana jin ya kara wayar a kunne shi ya kira sunanta cikin rauni.
Murya a kausashe tace.
"Jabeer".
Da mamaki ya amsa dan sama da shekaru goma sha biyu kenan da Jazlaan take kiranshi,
cikin sanyi yace.
"Na'am Umaymah". Cikin bada umarni tace.
"Jabeer ka tashi maza yanzu ka shiga fagen gasar nan ayishi da kai, bana son musu
umarnine ba shawara ba".
Cikin sauri ya zaro siraran kyawawan idanunshi,
Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo ya miƙe tsaye cikin tashin hankali da kiɗima da firgici
da baƙin cikin dakatar da gasar Shaɗi da akayi a masarautarsu ya sani da anayi da
Jabeer bazai ƙalubanceshi ba, cikin sanyi yace.
"Zanje za'ayi dani, zan tabbatar da darajar masarautatarmu bata rusheba."
Da ido yabi Dottijon kakan nashi wanda a ƙalla ya kai shekaru 91 a duniya.
Cikin kauda kai yace.
"To Umaymah yadda kikace haka za'ayi amman bari in kira Sheykh Abdulkareem in sanar
mishi in ya amince dai zanyi".
Da sauri tace.
"A a ban yafe ka kirashi ba, wato don kasan in ka kirashi zai kira Sitti da Mai
alfarma Jalaluddin da Sarki Nuruddeen ya dakatar da duk abinda za'ayin, tunda na
san cemishi zakayi ba addini bane, al'adace, to ban yardaba maza tashi".
Ganin Ya Hashim na miƙa masa wayarshi ne yasashi cewa Umaymah.
To cikin sanyi.
Yana amsa wayar da Ya Hashim ya miƙa mishi yaki Muryar, mahaifinshi cikin sanyi da
kuma alamun yana kukane yace.
"Jabeer ashe har kayi girman da Lamiɗo zai umarceka da yin abu kaƙi yi mishi
mubaya'a,
Ashe har na haifi ɗan da zai ja da mahaifina."
Cikin sanyi da rauni yake jujjuya kai murya na rawa yake cewa.
"A'a Abba, kayi haƙuri kada kayi kuka a kaina."
Bai kulashiba yaci gaba da cewa.
"Jabeer Ashe zuciyarka har tayi tauri da kangarewar da kanaji kana gani za'a daki
mahaifina a gaban idonka, bazaka zame mishi GARKUWA ba, Jabeer wannan shine
tukuicin tsantsar son da mahaifina keyi muka, wanda har ya jazamin ƙiyayya a wurin
yan uwana sunaga ya fifitaku kan sauran jikokinsa Especially ma kai Jabeer komu
daya haifa baya nuna mana son da yake nuna maka, shine zaka bari a dakeshi mutun
mai shekaru 91 da ɗaya a duniya kai me shekaru 30 bazaka iya zame mishi GARKUWA
ba?".
Cikin rauni da ƙunar zuciya, ya miƙe tsaye hannunshi yasa ya kamo na Lamiɗo cikin
tarin ƙuna da zafin rai da takaici yace.
"Na Amince, zanyi gasar na yarda, ka koma ka zauna".
Wani irin farin ciki ne ya ziyarci, zuƙatansu gaba ɗaya, sai dai kowa da irin
manufar farin cikinsa.

Jin haka yasa fadawan janye labulen da sukayi musu.


Shi kuwa Lamiɗo hannunshi yasa ya kamo hannun Jabeer, cikin tsantsar farin ciki da
al'fahari da ƙasaita ya fara taku, suna ratsawa cikin taron.
Kana fadawansu na biye dasu a baya.
Ɗanzagi yana.
"Takawarka lfy Sarki mai daraja Lamiɗo ɗan Lamiɗo jikan Joɗa. Gyara kimtsi".
A haka har suka isa cikin asalin dandamalin da aka jiƙashi jilak da ruwa, sabida
hana ƙura wanzuwa.

Gaba ɗaya taron mutanen wurin maza da mata manya da yara, Jabeer suka zubawa ido,
sabida duk wanda ya ganshi yaga sahihin Balarabe, mai kamala da nitsuwa, uwa uba
kima da haiba, ƙwarjini shi ya cika dukkan idanun magautanshi dake wannan yanki,
yayinda masoyanshi ke taraddadin abinda zai faru.
A tsakiyar filin suka tsaya, hannunsu dake raƙe dana juna Lamiɗo ya ɗaga tare da
fuskantarta gabas, kana ya juya yamma, ya kuma juyawa kudu da Arewa, sannan suka
dawo tsakiyar filin,
Cikin ƙasaita, yace.
"Ga GARKUWAN FULANI, kuma daga Wannan nasarar da zaiyi a gasar nan,
Zai tabbatar GARKUWAR Masarautar Joɗa, GARKUWA kuma mai ikon zama inda yaso a cikin
fada".
Dariya Bukar yayi kana ya ɗaga hannun Ba'ana da yaketa wani abu da ƙirjinshi kamar
damisa,
Cikin isa da yaƙini da al'fahari yace.
"Mu kuma ga namu Garkuwan, da muke da tabbacin bai taɓa gasa ya faɗiba".
Sake hannunshi Lamiɗo yayi kana ya juya ya koma ya zauna, cikin rumfar da akayi
musu masauƙin.
Al'ƙalin gasar ne yazo tsakiyar taro, kamar ko yaushe, hannun Ba'ana ya kamo, ya
ɗaga sama, hakan yasa, gaba ɗaya makiɗa da mabusa suka ƙara sautin kiɗe-kiɗen su,
wanda Jabeer ke jinsa har tsakiyar kansa, Allah ya sani, baya son hayani koda dai-
dai da ƙwayar zarra ne, ga wani masifeffen fargaba da tsinkewar da zuciyarshi keyi,
yanaji tamkar yasa hannunshi ya toshe kunnuwanshi.
Ɗan wani gajeren tsaki yaja sabida Allah ma ya sani baya son kallo, to kuma yanajin
yadda idanun mutane ke yawo a jikinshi.

Shi kuwa al'ƙalin gasar, yana sake hannun Ba'ana yazo ya kamo hannun Jabeer,
Da sauri ya juyo ya kalleshi sabida kamo hannunshi da yayi sai yaji tamkar hannun
jariri ya kamo dam laushi da taushin fatar, hannun sanyi ƙalau,
girgiza kanshi yayi cikin tausayawa, sabisa, ya za'ayi ace mai wannan taushin
hannun fatarsa ta iya jurar azababbun bulali masu masifar zafi.
Ɗaga hannun Jabeer yayi sama.
Yana mai nunawa taron mutanen shi a matsayin dashi za'a gwabza.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, duk abinda akeyi idonshi na cikin ɗan siririn farin galashi
mai garai-garai dake liƙe a fuskarshi,
Hannunshi kuma riƙe da carɓinshi, kana bakinshi ambaton sunan Allah.

Cikin tarin mamaki ya kalli,


Al'ƙalin gasar tare dasa hannunshi ya riƙe bakin al'kyabbar jikinshi cikin haɗe
fuska yace.
"Me hakan!?". Cikin saurin rusunar da kai Al'ƙalin gasar yace.
"Za'a cire kayan jikin naka ne!".
Cikin tarin mamaki ya zazzaro ido waje, a baiyane yace.
"Akan me kenan, suturar da Allah yayi min a matsayin mulmi, in killace kaina, shine
zaku yayemin a cikin dubban dubatan mutane?".
Cikin dakiya Al'ƙalin ya ɗan kalleshi domin kwarjinin Jabeer ya cika masa fuska
cikin sanyi yace.
"Allah rene, ƙa'idar gasar ce, ba'ayi da kaya a jikin mutun sai ɗan kamfai, kawai
ake bari a jikin mutun".
Cikin kufula da harzuƙa yace.
"To bada niba, Ni nan Muhammad Jabeer wallahi banyi lalacewar da zan tsaya tsirara
a gaban jama'a ba".
Yana faɗin haka ya juya a fusashe, zai fita cikin taron.
Ganin hakane yasa Galadima, yayi saurin tasowa, kana Ɗan buram na biye dashi a
baya, tareshi sukayi tare da kamo hannunshi.

Da sauri suka juyo suna. Kallon gungun wasu matasa wanda suka kece da dariyar ƙeta
cikin hausarsu ta ƙabilu suke cewa.
"To ku ɗan naku ko yadda ake gudanar da gasar ma bai sani bane? Ya zaiyi zaton da
wannan shigar tasa za'a dakeshi, to ai ko bulali dubu za'ayi mishi ba jinsu zaiba,
Kai Ɗan kazagi, ka gaya mishi nan ba cikin masallaci bane.
Nan wurin shaɗi ne".
Jiyo hakane ya sa ran dukkan musulman wurin ɓaci.
Sabida sun fahimci kafuraine masuyin wannan zancen.
Galadima kuwa da Ɗan buram sun ɗauka abin wasane, a zatonsu zasu shawo kan Jabeer a
sauƙaƙe, amman ina ya tiƙe yace babu wani zinɗiƙin ƙaton da zai sashi ya yaye
suturar dake jikinshi.
Dariyar da su Arɗo da sauran mutane keyine ya hautsuna lissafin Lamiɗo.
Cikin harzuƙa ya taso, har kamar zaiyi tuntuɓe ya nufi inda su. Waziri, Wambai, Ɗan
buram, Ɗurɓi, Da Galadiman, cikin tashin hankalin alamun akwai wata babbar manufa
da Galadima ke son cimmawa cikin lamarin ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa.
"Haba Jabeer kai wanne irin mutun ne mai kafiya da taurin kan tsiya, yaya muna
binka kana zillawa, muna haɗaka da Allah da Manzonsa amma kana tunzuramu, wallahi
da yau sai anyi gasar nan!".
Cikin tsananin ɓacin rai yace.
"In tsaya a tozarta ni kuke so.
Ayimin tijara kukeso, da wanne idon zan kalli al'ummar Annabi da jiki tsirara".
Cikin kufula Waziri yace.
"Waya ce maka tsirarane?".
Murya a sama yace.
"Tsirara ne mana! Tunda sunce wai dagani sai Boxes zan tsaya, ka kuwa san ko
Mahaifiyata data haifeni tun ina shekaru shida a duniya bana tsayuwa a gabanta
dagani sai ɗan kamfai, tunda nake Mahaifiyata, Mahaifina, Yayuna, Uncles, na
Aunty's na, babu wanda ya taɓa dukana, sabida ban cutar dasu da komaiba bare su
hukuntani da duka haka kurum rana tsaka kunce in tsaya a dakeni, na yarda, sannan
yanzu kuma ace nai tsirara, kai bafa wanda zan yiwa mubaya'a akan hakan..!."
Tas! Yaji sauƙan wani irin gigitaccen mari sai dai babu wanda ya ga sauƙan marin
sabida suna tsakiyarsu Waziri ne, kuma sauran mutanen garin duk kowa bayan su
Waziri suke iya gani.
A harzuƙe ya ɗago kanshi,
Lamiɗo ne ya gani tsaye a gabanshi.
Jan hannunshi yayi da iya ƙarfin shi na tsufa.
Tsakiyar filin suka koma, cikin fushi yace.
"Galadima zoka cire mishi kayan."
Da sauri Galadima ya motso gabanshi.

Su Waziri kuwa duk suka koma cikin Rufarsu masauƙinsu.


Wani irin tsuma da karkarwa jikin Jabeer ya farayi, tun sanda yaji sauƙan marin.
A take idanunshi nan su kaɗa sunyi wani irin masifeffen juyewa sunyi jazir,
Hatta lips ɗinshi karkarwa sukeyi. Wani irin tarin baƙin cikin da bai taɓa jin
irinsa ba a duniya ne, ya lulluɓe masa zuciya.
Koda randa Ya Jafar ɗinsu ya zauce, baiji makamancin wannan ɓakin cikinba.
Ji yakeyi Tamkar ya haɗiyi zuciyarshi ya mace ya bar duniyar kowama ya huta,
Rumtse idonshi yayi da azaban ƙarfi lokacin da yaji, Galadima ya gama komce
masaƙalan al'kyabbar jikinshi,
kana ya buɗe shi, yayi ƙasa dashi, har saida ya cire hannayenshi a ciki.
Haroon dake gefensu ya miƙa wa al'kyabbar, kana a hankali ya kuma matsowa gareshi,
hannunshi yasa saman kanshi ya ɗage zagayen baƙin abin da yake kan Hiramin, kana
yasa hannunshi ya janye hiramin.
Kekyawar fuskarshi ta fito ras, tattausan baƙin gashin kansa dake kwance lib-lib ya
baiyana, wanda hakan yasa kaso 70 cikin ɗari na dubban mutanen dake wurin suka zuba
ƙwayar idanunsu kanshi, da yawa tasbihi da ta'ajjudin irin kyau da haibar da Allah
ma ɗauka kin sarki yayi mishi sukeyi.

Jalal kuwa ji yake tamkar ya rinƙa kurma ihu, Allah yasani baya son abinda zai
cutar musu da Hammansun,
Jamil kuwa tuni hawaye yake zubdawa,
Ya Hashim, Imran, Sulaiman, kuwa dukkansu sunkuyar da kawunansu sukayi ƙasa.

Laminu kuwa wani irin masifeffen jin daɗi yakeyi, hakan yasa ya ƙara kutsowa cikin
filin hakan ya bashi daman yin viewing da kyau.

Shi kuwa Jabeer tafarfasar da zuciyarshi keyi yayi masifar tsananta lokacin da
yaji, Galadima ya zare mishi tattausar rigar shaddar dake jikinshi.
jin yasa hannunshi yana shirin zare mishi singlet ɗin jinshi ne yasashi, ƙara
ambaton sunan Allah da sauri-sauri, sabida ji yakeyi tamkar ya buɗe ido ya shaƙo
moƙoshin Galadima sai ya sumar dashi, tabbas da ace al'ƙalin gasarne ke cire mishi
kaya da tuni ya daku.
Cak ɓari da karkarwan da jikinshi keyi ya bari,
Lokacin da yaji Galadima yasa hannunshi ya kwance zariyar dogon wondon jikinsa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, Hasbunallahiwani'imanwakil.
Allahumma ajjirni fi musubati!!.."
Ƙasa idawa yayi, jin an saɓule wondon jikinsa yayi ƙasa,
da ƙarfi ya buɗe kwayar idanunshi da suka koma tamkar garwashin wuta. Tafarfasar da
jininshi keyi shine abu mafi tartsatsi a rayuwarsa.
Hannunshi Galadima ya jawo da ƙarfi wanda dole yasa ya ɗaga sawunshi ya tsallake
wondon ya zama babu komai a jikinshi dagashi sai Boxes wanda Allah yayi mai ɗan
tsawone yazo har kusa da guiwarsa saidai a matse yake.

A tsakiyar filin ya tsaidashi kana ya juya ya koma ya zauna kusa da Lamiɗo.


Jalal ne ya sunkuya ya ɗauki wondon da sauri ya miƙa wa, Haroon.

Shi kam Jabeer zuwa yanzu,


Ya sani a duniya ba'a taɓa yi mishi tozarci sama da wannan ba, ji yakeyi a duk
faɗin duniya babu garin daya tsana sama da garin Rugar Bani, bai taɓa jin haushi da
tsanar wani abu a duniya ba sama da mutanen garin Bani, ji yakeyi ya tsanesu gaba
ɗayansu, ya tsani komai nasu, baya so da fata da sha'awan komai nasu.
ƙasar garin ma da yake tsaye a kai ya zuba mata ido ji yake tamkar ya ƙonata ta
sauya launi daga farin yashi zuwa baƙin yashi.

A tsakiyar taron kuwa, da sauri al'ƙalin gasar ya jawo hannun Ba'ana da ya zaro
wata asirtaciyar bulalar tsamiya, daga cikin randar bulalinshi
sai wani motsi bulalar keyi tamkar tanada rai.

Bayan Jabeer al'ƙalin gasar ya kawoshi. Yana sake hannunshi masu busar al'gaita da
sarewa suka farayi da ƙarfin su.

Lokaci ɗaya kuma ranar data take buɗe tarwal ta lumshe.


Mutanen kuwa sai tasowa da ife-ife akeyi. Kallo kuma kab ya dawo kan farar
kekyawar fatarshi da kekyawan baƙin tattausan gargasa yayi mishi ƙawanya, iya kyan
fatarshi kaɗai ya ishi ɗan adam kallo.
Da ƙarfi Jabeer ya taune lips ɗinshi, yana maiji tamkar zai hudasu sai ambaton
sunan Allah yakeyi, babbar yatsar ƙafarshi ta dama yasa yana caka ƙasar garin, kana
yatsunshi na hannun kuwa yasa babban yana zagaye kan ƴar manuniyarshi.
A yadda yake jin zafi da ƙuna da baƙin ciki a cikin zuciyarshi ya tabbatar babu
wani abu da za'ayi mishi a yanzu yaji zafinsa fiye dashi, to me za'ayi mishi mai
zafi sama da tsiraiceshi da akayi.

Ba'ana kuwa cikin dariyar mugunta da sautin amo mara daɗin ji, ya taƙar-kara ya
ɗago bulaliyar asirin nan, da iya ƙarfin shi ya zabga mishi ita a tattausar fatar
tsakiyar bayanshi.
Da ƙarfi su Jalal kab suka rumtse idanunsu.
Lamiɗo kuwa wani irin kallo yayiwa Jabeer da yayi.
Wani ir.....!

Biya darinki uku kacal domin jin wannan labari har ƙarshe.
Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina.

Wannan shafin nakune gaba ɗaya waɗanda suka karanta FREE PAGE🤝🏻😘🥰
By
*GARKUWAR FULANI*[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: Ido Laminu ya
rumtse da ƙarfi.
Ganin Sheykh Jabeer yayi wani irin tsayuwa na ingarman, jarumin namiji nitsuwa da
kamala, sai lips ɗinshi dake motsawa a hankali yana ambaton Allah.
Shi kuwa Ba'ana cikin tsantsar mugunta, ƙeda, da zalumci ya ɗago bulalar nan da
azaban karfi ya zabgawa mishi ita a inda ya zabga ta forko.
Wanda yasa gaba ɗaya mutanen wurin suka rumtse idanunsu.
Especially Lamiɗo da tawagarsa,
Shi kuwa Sheykh Jabeer, zuciyarshi ta rigada ta gama tafasa, idonshi baya ganin
komai sai wani irin azabebben duhu, kunnuwanshi basa jin komai sai sautin muryar
mahaifinshi da kuwa Umaymah. Da suke bashi umarnin cewa dole yayiwa Lamiɗo
mubaya'a.
Wani irin azaba mai girgiza ran mutun a jikinsa yakeji yana sukarshi har cikin
ƙahon zuciyarshi, sai dai duk wani sihiri na jikin bulalar duk baya tasiri a
jikinsa illa dai dafin kuna min kam tabbas yana jinsu.
Barmuji wanda shine al'ƙalin gasar kuma mai irga bulalin.
Da sauri ya rumtse idanunshi lokacin da Ba'ana ya tsulawa Jabeer bulala ta biyar
waccee, a take jini ya fara tsastsafo duk inda ta konta.

Arɗo Bani kuwa da Bappa da Alhaji Haro da Alhaji Umaru, da Sarkin aska, da sauran
dattawan garin da kewayensa wani irin fargaba ne da taraddadi mai firgitarwa suke
ciki.
Gaba ɗaya bakunamsu addu'o'in ne a ciki.

Laminu kuwa tuni yanata ɗaukar duk abinda ke faruwa a ƴar ƙaramar na'ura sa.
Yanayi yana dariyar farin ciki.

Jalal kuwa da sauri ya rumtse idanunshi kana ya koma baya.


Jamil kuwa cur-cur yake zubda hawaye ganin yadda jini ke tsastsafo wa, a tsakiyar
bayan Hammansun.
Haroon da kanshi tsoro ya rufeshi, yaji ranshi ya fara zargin anya kuwa bada biyu
aka haɗa wannan gasarba.

Muryar Barmuji ce ta cika wurin gaba ɗaya da alamun tsananin tausayawa yace.
"Goma!".
Alamar anyi mishi bulala ta goma kenan.
Shi kuwa Sheykh Jabeer Idonshi a buɗe suke, sai dai basa ganin komai sai duhu na
tsantsar baƙin cikin abinda sashi yayi cikin bainal nasi a sashi tsayuwa da ɗan
kampai,
Idanun nashi suna buɗe ras.
Launin su kuma ya sauya daga farin zaiba, zuwa jazir tamkar wanda maciji ya watsa
dafi a cikinsu.
Gaba ɗaya fararen faratun yatsun hannunshi sun rine sunyi jazir tamkar wanda aka
ƙunsawa jan lalle.
Ji yakeyi tamkar tsikarinshi akeyi da bakin allurai.
Tabbas duk da bai san dafin kunama ko macijiba, ya gane cewa akwai gubar dafin wani
abu a jikin bulalin da ake tsula mishi tamkar za'a zare ranshi dasu.
duk ta inda hudar gashi yake a jikin shi, ji yakeyi tamkar ana soka mishi ƙarin
kunamai.

Bukar kuwa, wani irin murmushin farin ciki yakeyi, ji yakeyi kamar ya fito ya taka
rawa dan farin cikin ganin halin da jikan Sarki ke ciki.
Muryar na rawa Barmuji yaci ga da irge.
"Goma sha ɗaya! Sha biyu! sha uku! sha huɗu! sha biyar!!!."
Cikin sauri Haroon ya iso inda suke, hankali a tashe ya kamo hannun Barmuji cikin
sanyi yace.
"Kai kasheshi zakuyi ne? Bulalin har nawa ne za'ayi?".
Cikin rawan murya Barmuji yace.
"In sha Allah bazai mutuba, bulali Hamsin za'ayi a ƙa'idar gasar, ba abinda zai
sameshi tunda har gashi ya juri bulali 15 wanda a tarihin gasar Ba'ana babu wanda
ya taɓa jurar koda bulala biyar ne".
Da ƙarfi Hashim ya zaro ido tare da cewa.
"50 wannan ai zalumci ne".
Da sauri Galadima ya miƙa ya nufi tsakiyar taron ganin Jalal ya nufi inda suke
gadan-gadan bisa dukkan alamu kamo hannun ɗan uwan nashi zaiyi yaja su tafi.
Da sauri Galadima ya kama hannunshi cikin ɗaga murya yace.
"Kai Jalaluddin ina zakaje?".
Cikin faɗa yace.
"Zan ja ɗan uwana mu tafi, in ku bakwa sonshi bakwa da buƙatar shi, mu muna sonshi
munada buƙatar shi, a rayuwarmu domin mu dai shine farin cikinmu, shine silar
zamanmu cikin masarautarku, da tuni kun koramu tamkar karnuka, shine kuka haɗa Deel
a kashe mana shi, to kuji ku sani zamu bar muku masarautarku in dai ganinmu ne
bakwa tson yi."
Cikin faɗa Galadima yaja hannunshi yaje ya ajiyeshi gaban Lamiɗo.
Yana mai jin tausayin yaran.
Da ƙarfi Barmuji yace.
"Ashirin da biyar! Ashirin da shida!".
Zuwa wannan lokacin gaba ɗaya jikin Al'Sheykh Jabeer Habeebullah yayi ruɗu-ruɗu.
Tuni farin boxes dake jikinshi ya cika da jinin dake gangarowa ta bayansa da
cikinsa, inda bulalin suke taɓawa duka.
Babbar yatsarshi ta ƙafar damanshi da yatsun hannunshi kawai yake motsawa, wanda
suke nuna alamun yana nan da rai daram da kuma haiyacinsa.
Bayan wannan babu abinda yake motsawa a jikinshi,
Cake ƙasar garin yakeyi da yatsar kafar tashi.
yatsun hannunshi kuma, motsasu yake yana tasbihi dasu, wanda shima cikin
zuciyarshi yake ambaton Allah dayi mishi kirari da kyawawan sunayenshi.
Zafin da yakeji a jikinshi tabbas ya wuce zaton mai zato.
Taune lips ɗinshi na ƙasa yayi da fararen haƙoranshi tamkar zai hudasu, sai dai har
cikin ƙashin haƙoran nashi yake jin azabar dafin dake cikin wadannan bulalin masu
masifar siddabaru, sai dai babu wani siddabaru da yayi tasiri a kanshi ko a jikinsa
domin shi Allah ya riƙe, Ba'ana kuwa tsafi ya riƙe.
Wannan gasace tsakanin gsky da ƙarya, bawai gasar caɗi bane kamar yadda mutanen
wurin ke kallo.
Haka yasa duk da safin wannan bulalin sam basu kai zafin da yakeji a ranshi na
sashi ya tsaya gaban dubban al'ummar garin da ɗan guntun wonɗo a jikinshi ba.
Allah ya sani shi mai kunya ne, kuma shi mai suturce kanshine, shida kanshi yana
jin kunyar kanshi da kanshi.
Baya zama haka ko a ɗaki sabida yana tuna in mafa ya kaɗaice yana tare da Raƙib da
Atib Mala'iku makusantan ɗan adam, wanda in ka bar tsiraicinka ma su kauda ido
sukeyi daga gareka.
Shiyasa shima yake kauda ido daga kan kanshima bare wani.
Allah ya sani babu wani abu da aka taɓa yi mishi a duniya ya ƙona mishi rai sama da
wannan abun.
Tabbas da an barshi hakama, yafi jin zafin hakan sama da waɗanan bulalin.
A ranshi yake wani irin kuka mai cin rai yana mgnar zuciya.
"Anci min zarafi an wulaƙantani an tozarta ni a gaban waɗan mutanen da wasun
cikinsu zindigan kafuraine. An barni tamkar mara kima da galihu, wannan shine iya
maƙurar zalumcin da akayiwa rayuwata a karo na biyu".
Sam baya jin zuciyarshi tanada raunin da zai iya zubda hawaye kan bulalin nan
shiyasa ko zafinsu bai zame mishi abin zubda hawaye ko ihu da bakiba ko gudu ko
wani motsi.

Zuwa yanzu hankalin kafuran ƙabilar ɓachama ya yi masifar tashi domin wannan shine
karo na forko a rayuwar tarihin Ba'ana da ya zana mutun bulalin shaɗi har talatin
da takwas baiyi ihuba bai zubda hawayeba, bai sumaba, bai faɗi ba, bai guduba.
Kai wannan abun yayi tsamari wannan wanne irin mutum ne, anya kuwa mutun ne ko
al'jan.

Ya Salmanu kuwa, cikin tsanani kuka cur-cur da hawayenshi sabida yasan azabar da
Sheykh Jabeer yakeji.
Juyawa yayi ya fuskanci gabas, sujjada yayi tare da fashewa da wani masifeffen kuka
mai cike da rauni murya na rawa yake cewa.
"Ya Haiyu ya ƙaiyum, ya ziljalali wal ikram. Ya Allah ka ƙarawa wannan bawa naka
dauriya da jarumta, ya Allah ka bashi ikon jure wannan azabar, ya ubangiji ka
sanyaya mishi masifun dake jikin waɗanan bulalin, ya ubangijin taliƙai ka hana
wannan mugun mushirkin bawa naka samun nasara, ya Allah ka kare musulminka kan
wannan kafurin matsafin da baya salla".
Kuka sosai ne yaci ƙarfin Ya Salmanu.

Bappa ma wani irin raunine ya rufeshi tabbas kowa zaiyi tunanin Jabeer yana jin
azabar duniya.
Sai dai kasan cewarsa Jarumin namiji haka yasa babu wata alama da ya nuna na yana
jin zafi ko ciwo.
Sosai kuwa hakan ya tada hankalin kafuran.

Lamido da Galadima kuwa kallon juna sukayi tare da yin murmushi irin nasu na manyan
fada, murmushi ne mai manufofi.

Jalal kam kife kansa yayi a cinyar Lamiɗo ya saki kuka mai sauti.

Haroon ma hawaye yakeyi zuwa yanzu.


Hankalin duk tawagar Lamiɗo yayi masifar tashi, ganin yadda wani irin azabebben
zufa ya tsinkowa Jabeer tun daga tsakiyar kanshi, zufar nan take gangarowa har kan
jikinshi gaba ɗaya, saida ya jiƙe yayi jilak tamkar an kwaza mishi ruwa bokati
ɗaya.
Wani irin karkarwa jikin shi, ya farayi yana tsuma yana ɓari, gaba ɗaya jikinshi
karkarwa yakeyi.
wanda duk fulanin wurin suka fahimci cewa tabbas.
Zai iya cinye gasar zai kuma iya faɗuwa.

Shi kuwa Sheykh Jabeer daga can cikin naman jikinshi yake jin jikinshi na rawa
tamkar mazari.
Zuciyarshi kuwa wani irin duka takeyi, wanda muddin kana kusa dashi zakaji yadda
take bada sautin harbawa.

Hankalin Ba'ana yayi ƙololuwar tashi, ganin har yayi mishi bulala ta arba'in da
biyar.
Baiyi ɗaya daga cikin ababen da zai hanashi cin gasar ba.
Ganin hakane ya juya a fusashe, bulalin hannunshin ya wurgar kana ya sunkuyo kam
ranɗar bulalin tsafinshi, bulali biyar ya zaro, ya haɗa su ya damƙesu cikin
hannunshi.
Cikin azaban ƙarfi ya ɗagosu ya yarfawa Jabeer su a tsakiyar kanshi.
Wani irin azabane ya ziyarci ƙoƙon ranshi, wanda hakan yasa yaji wani irin fitsarin
azaba yana cika mishi mara.
Jinine ya tsinko ta kafaɗunshi, yana bin cikinshi,
bai gama jin azabar waɗannan ba ya kuma zarma mishi su a cinyoyinshi.
Da sauri Arɗo Bani ya miƙa tsaye daga sujjadar da yayi jin ihun mutane, suna cewa.
"Ka karya dokar gasa ba'a haɗa bulali biyuma bare biyar kasheshi zakayine.
Cikin wani irin isa ta jarumta da jinin sarauta Sheykh ya buɗe kwayar jajayen
idanunshi,
Barmuji da yayi kansu da nufin kama hannun Ba'ana ne,
Ya ɗagawa hannunsa alamun daka dakatarwa alamun ya tsaya kada ya iso ya bar Ba'ana
yayi komai ba komai.
Cikin tsananin mamaki duk al'ummar wurin suka zuba musu ido ganin jarumta ziraran
miraran tana tsaye da sawunta.
Shi kuwa Barmuji cikin rauni yaci gaba da nufosu yana cewa.
"A a Sheykh bazan barshi ba, ai ya karya ƙaida da dokan gasa".
Ya ƙarashe mgnar yana isowa inda suke.
Cikin tsananin takaici da firgicin ganin faɗuwa a karo na forko na rayuwarshi,
Ba'ana
Ya zargawa Barmuji bulalin da ƙarfi.
Wani azabebben ihu Barmuji ya narka tare da fara tsalle yana yarfa hannunshi yana
zagaya wurin hawaye na shatata mishi sabida azabar da yakeji, cikin ihun azaban
bulalin da aka yarfa mishi sau ɗaya, fitsari na tsiyaya a sawunshi yace.
"Arba'in da takwas!".
Ta gabanshi ya dawo ya shauɗa mishi na arba'in da tara, wanda yasa Jamil yin tsalle
yazo gabanshi cikin kuka yace.
"Kasheshi zakayi ne?". Cikin tsananin azabar da yakeji ne ya buɗe jajayen idanunshi
ya kalli ta inda yaji muryar Jamil.
Hannunshi yasa ya ture Jamil gefenshi.
Shi kuwa Ba'ana wani irin ihu yayi tare da buga tsalle yayi sama kana ya zabga
mishi bulala ta hamsin kuma ta ƙarshe.
Wani irin dogon numfashi Jabeer yaja tare da buɗe idonshi kan fuskar Lamiɗo daya
iso hango dishi-dishinsa yana nufo inda suke.
Wani irin ihu da karaji Ya Salmanu ya kurma da azaban ƙarfi,
Wanda ya haɗe ya gauraye da busar sarewa da al'gaita da dukan gamgar jami, aka saki
a tare.
Wani irin sowa da ihu da hargowane ya cika illahirin gaba ɗaya Rugar Bani,
Wanda mutane fulani suketa rawan farin cikin jarumtar Jabeer,
Arɗo Bani da sauran dattawan rugar kuwa gaba ɗaya sujjadar godiya sukayi wa
Ubangijinmu sarki gagara misali.
Gaba ɗaya an zagaye Sheykh Jabeer.
Wanda shi kuma ya juyawa Haroon baya alamun yasa mishi suturarsa.
Da tsananin rawan jiki.
Haroon ya wore al'kyabbar, ya zura mishi ita kan jikinshi daketa zubda jini.
Yana jin Haroon ya saka mishi Al'kyabbar ya ɗago kafaɗunshi ya gyara zaman
al'kyabbar.
Jiki na rawa yasa hannunshi ya kama gefe da gefen bakin al'kyabbar ya hadesu a
jikinshi ya suturce kanshi ya kare kanshi.
Barmuji na shirin kamo hannunshi yayi maza.
Ya ɗaga mishi hannunshin kana ya juya ya nufi inda motoncinsu ke jere.
Jalal da na ganin haka yayi maza yayi gabanshi.
Marfin motar ya buɗe mushi tun kafin ya iso.

Cikin taron kuwa, tuni Ba'ana da matasan ƙabilar ɓachama, sun ɗauki ranɗar bulalin
tsafinshi sun nufi Bonon da tarin baƙin ci dan ganin Sheykh Jabeer bai faɗi
gasarba, kuma ga mutanen fulani daketa yi musu dariya da ihun rashin nasarar su.
Hakan yasa suka tafi dan sun sani a ƙa'ida sai Jabeer yayi jinya ya worke da azabar
da Ba'ana ya shayar dashi kafin ya dawo ɗaukar fansa.

Cikin taron kuwa cikin kukan rauni Arɗo bani ya rusuna gaban Lamiɗo da tawagarsa
murya na rawa yace.
"Sauran ɗaukar fansar da zaiyi a duk sanda ya worke a duk sanda yaga dama, fatana
kuyi shirya bulalin tarihin masarautarku, domin ramuwa akan wancan taƙadirin da
baya jin koda harbin bindiga baya shigarsa.
Ina yakun farin cikin nasarar da Jabeer yayi a yau, ina kuma fatan yayi nasara a
ramuwar da zaiyi a wannan kuma in yayi nasarar mu zaku taya farin ciki, ko ba komai
zamu rabu da wancan taƙaɗirin."
Cikin wani irin tarin ƙuna Lamiɗo ya gyaɗa kanshi.
Kana ya juya yayi gaba Dogari na rike masa da laima ɗanzagi na cewa.
"Gyara kimtsi, a bada hanya, sarki ya barku lfy".
Waziri da Wambai Ɗan buram Ɗurɓi Da iya duk suka mara mishi baya.

Hakama Arɗo Bani da sauran dottawan wajen sukayo musu rakiya.


Sheykh Jabeer kuwa.
Yana tafe Galadima na biye dashi a baya. Haroon kuma na gefenshi.
Suna isa yasa kai ya shiga cikin motar,
kana Haroon da Hashim suka mara mishi baya, da sauri sarkin mota ya maida ƙofar ya
rufe.
Kana ya buɗewa Lamiɗo motar, gefen bayansu Jabeer ya shiga, kana Galadima ya shiga
kusa dashi, sannan aka rufe motar saura duk kowa ya shiga motar da yazo ciki.
Sannan duk suka rurrufe motocin.

Kana suma Fadawa da dogarai suka shiga nasu motoci biyun.


Ɗaya tayi gaba, sauran motocin suka bisu a baya, ta Lamiɗo na tsakiyarsu, kana ɗaya
ta fadawan ta biyo bayan uku da ke bin bayan ta Lamiɗo.

A haka suka ja motocin a jere a jere suka bar cikin Rugar Bani.

Cikin Rugar kuwa kowa ya tafi cikin al'ajabi da farin ciki.


Da yawa gani sukeyi kamar dai Jabeer ba mutun bane.

Sauran dottawan kuwa, zama sukayi cikin fadar bayan sunyi sallan la'asar ne, Bukar
yazo ya tsaya tsakiyarsu cikin rashin mutunci yace.
"Kuyi kuka da kanku akan duk abinda zai faru gaba".
Kafin ma su bashi amsa tuni ya juya ya tafi.

Su kuwa nan sukaci gaba da al'ajabi da tuanjidin Jarumtar Jabeer.

A cikin motocin kuwa, mutanen ko wacce mota da abinda kowa ke tunawa.


Wani irin azabebben gudu sukeyi tamkar zasu tashi sama, sabida bin umarnin Lamiɗo
wanda shi kuwa ya bada izinin gudun ne, dan ganin yadda Jabeer keta zubda jini, ga
wani irin masifeffen karkarwa da jikinshi keyi.

Gudu sukeyi a 360 musamman ma da suka samu suka hau kan babban titin Shikan wanda
zai sadasu da cikin babban birnin Ɓadamaya.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, wani irin karkarwa jikin shi keyi, idanunshi jinsu yakeyi
tamkar zasu zazzago su faɗo ƙasa, sabida wani irin masifeffen azaba da yakeji.
Ji yakeyi tamkar ya haɗiyi zuciyarshi sabida masifar fushi da harzuƙa da zafin rai,
babban abinda ya tsananta fushinsa shine yadda yaga lokacin sallan la'asar ya gota
musu,
akan shirmen banza da wofi da zalunci an hanashi yin salla kan lokacin ta.
Hannunshi yasa ya fizge rigarshi da ke hannun Haroon dake ta sa hiraminshi yana
tare jinin dake zubomishi ta ƙeyanshi.
Taune lips ɗinshi yayi tare da sa hannun shi, ya kama wuyan rigar cikin ƙarfi yaja
ji kakeyi,
Fasss sautin yagewar sabon saddan.

Ido suka zuba mishi gaba ɗayansu,


Ya Hashim kuwa jiki narawa ya kira Dr Aliyu wanda yake ƙanine ga mahaifinshi da
kuma Abbansu Jabeer ɗin.

A can baya kuwa inda Galadima dake zaune gefen Lamiɗo ne daya bashi umarnin ya kira
sarkin gida ya sanar mishi ayi tanadin jinyar Shaɗi cikin gaggawa.
Da sauri Galadima ya zaro wayarshi ya kira sarkin gida.
Cikin tashin hankali yake mgna a woya bisa alama duk da sarkin gida yake mgn.
"Ladodo, kayi maza yanzu ka sanarwa tsohon sarkin Shaɗin masarautar Joɗa yayi maza
ya haɗa tsumin igiyar bulalin shaɗi, ya kaiwa Jakadiyarsu Jabeer,
A shirya duk wani abun buƙata, domin Jabeer yana zubda jini sosai."

A can masarautar kuwa Sarkin gida yana jin haka ya miƙa ya nufi, sashin kananan
sarakuna kai tsaye gefen Sarkin Shaɗin ya nufa, ya sanar mishi umarnin da aka bada,
ai nan take Sarkin Shaɗin da sarkin Gida, suka shiga bayan sashin mai martaba
Lamiɗo,
inda bishiyoyin tarihi dana gargajiya da magunguna suke.
Forko bishiyar Goruba suka fara sassaƙan jikinshi.
Wanda shine babban makarin dukan shaɗun.
Sai kuma suka haɗa da wasu tsirran,. Koda suka gama kai tsaye gefen Jakadiya da
sauran ma biyanta suka nufa,
Nan suka bata dukkan abinda suka ɗebo, suka kuma yi mata bayani.
Kana sukace maza ta haɗa su ta dafa,
Sauran kuma sai sun dawo Lamiɗo ya shiga ɗakin sirri ya ɗebosu.

Cikin tsananin tashin hankali da rawan jiki Jakadiyarsu ta amshi magunguna, ta nufi
sashin Jabeer ɗin.
Cikin gaggawa ta shige kitchin ɗin shi, ta fara harhaɗa magunguna tana dafawa.

A can cikin motar kuwa cikin tashin hankali Ya Hashim yayiwa Dr Aliyu duk bayanin
abinda ya faru da halin da Jabeer ke ciki.
Ya ƙara da cewa, a shirya komai na bashi taimakon gaggawa.
Jin hakane yasa Dr Aliyu tada motar Ambulance wanda take nan cikin asibitin dake
cikin makarantar nasu, tazo bakin asalin babban gate ɗin masarautar nasu.
Kana ya kira babban abokinshi Dr Sanju wanda ba indiyene wani aikine ya kawoshi
ƙasar,
tuni suka iso bakin gate ɗin, cikin motar Ambulance ɗin suka shiga suka zauna tare
da haɗa duk wani abu na taimakon gaggawa da za'ayi mishi.

A cikin motar kuwa, gaba ɗaya ya gama yage rigarsa ya fizge wonɗonma ya yageshi
fata-fata.
Ganin wani irin kallo da yayi Haroon ne, yasa Haroon yin maza ya matsa tare da yin
mgnar zuci.
"Ka gani ko Lamiɗo hegen tsoho kai ka dace ka zauna kusa dashi.
Inma yagawarne ya yage ka".
A zahiri kuwa fuska ya ɗan haɗe tare da cewa.
"Kafa gama yaga kayanka yanzu nawane suka rage a jikina, naga ji kake kamar ka
yagamu, yaseen to bamu muka kar zomonba".
Dai-dai lokacin kuma, sarkin ƙofa ya buɗe musu ƙofar babban gate ɗin.
Kana suka kutsa kai. Suna shiga ko parking basu gama dai-dai tawa ba
Jabeer ya sa hannu ya buɗe marfin motar, ƙafarshi ya zuro woje,
wanda ganin haka yasa Dr Aliyu ya fito da sauri.
Sai dai kafinma ya fito tuni Jabeer ya fito cikin motar ya nufi asalin ƙaramin gate
ɗin da zai sadaka da asalin cikin farfajiyar.
Kusan a tare suka fito daga motocin gaba ɗayansu.
Cikin tsananin tashin hankali Ya Hashim ke ƙwalla mishi kira, amman ina bai ko juyo
inda sukeba.
Baya kuma jinsu sosai sabida duhu da jirin da yake gani.
Da gudu Haroon da Jalal Jamil suka biyoshi a baya cikin rauni Jamil ke cewa.
"Hamma Jabeer dan Allah ka tsaya Baba Aliyu zai dubaka, kaga fa har yanzu jinin
bai daina zuba ba."
Ina ai baya tare dasu tafiya kawai yakeyi, ba tare da yasan inda yake jefa ƙafarsa
ba.
Ganin hakane Dr Aliyu ya koma cikin Ambulance ɗin ya jata ya nufi inda yake, sai
dai tuni har ya shiga cikin asalin farfajiyar.
Haroon, Jalal, Jamil, Hashim, ɗan Barrister Kamal Sulaiman, da Imran, duk suna biye
dashi a baya da dudu-gudu da sassarfa.
Lamiɗo da tawagarsa kuwa, koma sukayi cikin motocin sukaja, suka nufi cikin gidan.

Shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya isa bakin side ɗinshi.


Cikin tsananin rawan jiki da duhu ya kusa kanshi ciki.
A babban falon ya samu Jakadiyarsu, tana ganinshi ta miƙe tsaye cikin tsananin
tashin hankali ta tsaya ganin ya ɗaga mata hannunshi ɗaya, kana yasa hannunshi ɗaya
kuma ya dafe kanshi.
Cikin wani irin kerma yake wani irin taku da jan wani irin dogon numfashi ya nufi
part ɗin shi.
Yana shiga falonshi na musamman, su Haroon na shiga babban falon.

A nan su Jamil kan suka tsaya, shi kuwa Haroon da sassarfa yabi bayanshi.
Yana shiga falon nashi ya hangoshi ya shiga bedroom ɗin shi.
Ya kuma maida ƙofar ya rufe, kai tsaye bathroom ya wuce yana shiga wani irin duhu
ya rufe idanunshi a hankali ya tafi...

A can Rugar Bani kuwa, kuwa Junainah har ta shiga kitchin ta sunkuyo zata ɗauki
akoshin naman gasassun zabbin, sai kuma ta fito a guje.
Kai tsaye inda ake gasar Shaɗi ta nufa, haka ta rinƙa kutsawa cikin taron, har ta
isa gaba-gaba kusa da ya Salmanu, ganin irin dukan da akeyiwa wannan kekyawan
mutumin data ganine yasata kuka da ihu.
Kukanta ne yasa Salmanu kuka, ya kuma ja hannunta ya fito baya da ita.
Hannunta ɗaya riƙene yaji yadda jikinta ke karkarwar kamar mazari, bayan yayi
sujjadar ya ɗagone.
Yace mata maza ta koma gida.

A haka ta koma tana kuka.

A inda ta bar Shatu dasu Rafi'a da Ummiy anan ta dawo ta samesu.


Kai tsaye kitchin ɗin ta nufa, da sauri ta ɗauko akoshin ta fito ta nufi inda suke,
cikin rawan jiki ta sunkuyo ta sauƙe musu akoshin ta ajiye a tsakiyarsu, kana itama
ta zauna a kusa da Ummiy dake jingine da jikin bishiyar mangoro.
Jiki na rawa tasa hannun ta janye fefeyin da aka rufe akoshin da shi.

Wani irin lumshe ido Rafi'a tayi, sabida wani irin ƙamshin daya buɗe hancinta,
Ummiy kuwa ido ta zubawa akoshin tana jin yawun bakinta na tsinkewa,
Shatu kuwa gyara zamanta tayi sabida wani irin azabebben ƙugin yunwa da cikinta
yayi.

Cikin sanyi suka gyara zamansu gaba ɗaya, a hankali Shatu ta riƙe hannun Junainah
cikin zubda hawaye tace.
"Jeki wonke hannunki sai kizo, da plet da ƙaramin akoshi mu ɗibawa Bappa mu sawa
Ummiy a plet ɗin".
Cikin sanyi ta tura baki kana ta miƙe tsaye, gindin randunarsu ta matso, yar
ƙaramar butarta ta ɗauka ta wonke hannunta, sannan ta nufi cikin madafarsu.

Tana shiga ta ɗauki ludeyi da ƙaramin akoshi kana da pilet sannan ta fito.
Tana fitowa tazo ta zauna gabansu, ta miƙa Shatu, cikin sanyin jiki tace.
"Bawa Rafi'a ta ɗiba musu, wlh jikina duka rawa yakeyi".
Amsar pilet ɗin Rafi'a tayi ta fara ɗibawa Ummiy rabin zabuwa.
Kana ta sawa Bappa gudar da romonta,
Tana cewa.
"Garkuwa yunwace fa, ace mutun ya wuni ya kuma kwana baici komaiba ya kuwa wuni ba
abinda yaci ai dole kiji jiri, gashi yawan kukan da kikeyi ne yasa miki zazzaɓi."
Ta ƙarishe mgnar tana rufewa Bappa nashi kana tace.
"To muci".
A tare suka saka hannunsu cikin akoshin.
Junainah ce ta fara yago tattausan farin tsokar ƙundun zabuwar cikin haɗiye min yau
ta kai hannunta bakin t....!

Dan Allah da Manzonsa kada ku fitarmin da littafina, in kinsan Zaki fitarne gaya
min in baki kuɗinki, dan Allah.

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: Ta kai hannun ta, kusa da bakinta kenan
Wani ƙaton gadamgare ya faɗo jikinta.
Wani irin tsalle tayi tare da rauza ihu, ta faɗa jikin Aysha tuni tayi fatali da
akoshin gasassun zabbin nan ya ɓare ƙasa kirib.
A firgeci Ummiy ta yunƙuro tare da nufar inda suke, wanda hakan yasa tayi fatali da
akoshin da akasawa Bappa zabbuwar da kuma take wanda aka zuba mata a plet ɗin ya
ɓare cikin lallausan yashin garin.

Ita kuwa Junainah gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi, fizge-fizge takeyi tana
ƙwaƙumar Shatu.
Sabida ita ji takeyi kamar dai har yanzu ƙadangaren yana jikinta.
Cikin kiɗima Shatu ta ruggume ta, tare da cewa.
"Ke Junainah ki bar ihun ƙadangaren ma ya razana da ihun da kika kurma ya sauƙa ya
tafi."
Jin hakane yasa ta tashi zaune tare da zazzaro ido,
Rafi'a kuwa dariya tasa tare da cewa.
"Kai Junainah yaseen kin cucemu, kallifa yadda kikayi fatali da akoshin nan".
Cikin sanyi Shatu tace.
"Haba wannan abu dai Allah yayi ba raban mu bane, Ni dama can haka nan in naga
naman sai inji zuciyata ya tsinke ashe ba rabanmu bane, da muncima da mun harar
dashi.

Ita kuwa Ummiy jan hannun Junainah tayi kana ta zauna kusa da Shatu.
A hankali ta jingina kanta da kafaɗan Shatu,
Rafi'a kuwa miƙewa tayi ta shiga kitchin ɗin su.
Abincin data dafa musu ta kawo musu.
Ta ajiye gefe, sannan ta ɗauko tsintsiyar kwakwa ta share ta kwashi naman kab ta
maidashi cikin babban akoshin, ta rufe, sannan taje ta wonke hannunta kana tazo
ta zauna suka fara cin abincin.

A can cikin fadar masarautar Joɗa kuwa.


Jin jiri na ɗibanshi ga duhu dake rufe mishi ganine ya sashi, tafiya a hankali tare
da dafa jikin gini.
A haka har ya isa bakin Jakuzin,
A hankali ya zare al'kyabbar jikinshi, ya wurgar dashi can gefe,
kana ya tura ƙofar ya Jakuzin ya shiga,
tsayuwa yayi tsakiyarshi, hannun na rawa ya buɗe shawan ruwan ɗumi.
Wani irin numfarfashi wahala ya sauke lokacin da yaji ruwan ɗumi yana ratsa raɗi-
raɗin azabobbun bulalin da yasha.
Wasu irin hawaye masu masifar zafine yaji suna tsastsafo mishi cikin jijiyoyin
kekyawan idanunshi, sai dai basu kai ga damar samun zobowa ba.
Wani irin tsuma duk illahirin sashin jikinshi ya fara,
zafin ruwan yakeji har cikin ƙoƙon ranshi,
wani irin karkarwa haƙoranshi sukeyi har suna dukan juna, kat-kat.
Kanshi ya sunkuyar tare da buɗe idanunshi a hankali, ruwan dake gangarowa daga
jikinshi yana bin ƙasa in da zai gangara yake kallo,
sabida zakace jinine ba ruwaba,
Sabida yana wonke mishi jinin jikinshi.
Haka ya tsaya a ƙasan ruwan ɗumin har saida yaga jinin ya daina zuba kamar da fari.
Sannan yasa hannunshi ya ɗauki daddaɗan sabulun wankan shi, ya fara murza sabulun
taki wani sashi na jikinsa, wani irin wahaltaccen ƙara yayi lokacin da sabulun ya
ratsa inda ya farfashe a jikinsa, cikin rauni yace.
"Wayyo Allah na! Wayyo Mamey na zan mutu, zafi zai kasheni tun kafin cikar burina."
Ci gaba yayi da murza sabulun tare daci gaba da cewa.
"Wayyo Umaymah wayyo Ummi".
Sai kuma ya taune lips ɗinshi kana ya rumtse idanunshi yayi ta murza sabulun tako
ina yanayi ruwan ɗumi na dukanshi.
A haka yayi wonka ya wonke duk wani jini dake jikinshi yayi fes.
Al'wala yayi, kana ya fito cikin Glass ɗin sannan ya ɗauki wanni tattausan baby
towel fari ƙal ya ɗaura a ƙirjinshi ya sauƙo har zuwa guiwansa.
Hannunshi yasa ya murza farin boxes dake jikinsa wanda ɗazu yake jiƙe da jini yanzu
kuma yayi fari tas.
Murza boxes ɗin yayi har ƙasa, kana ya ɗaurashi kan al'kyabbar jikinshi da ya cire,
Cikin Woshing mashine yasasu,
Kana ya fara yin taku a hankali ya iso gaban drower'n glass ɗin dake cikin bathroom
ɗin.
Wani tattausan gajeren wondo fari tas mai ratsin sky blue ya saka, gajeren wondon
yazo mishi har guiwarsa, kuma mai ɗan faɗine,
Wata tattaunawar riga mai guntun hannu wacce itama farace da ratsin Sky blue, ya
saka, kana ya zaro wata ɓakar tattausar jallabiya doguwa har ƙasa tazo mishi daya
zurata,
Wani hulan taɓa kaji Hadisi ya kifa kan suman kanshi dake da ɗan damshin ruwan
ɗumin.

A hankali yake taku sabida zuwa yanzu wani fitinenne zazzafan zazzaɓi yakeji.
Jiki na rawa ya fito, bisa sallayarshi dake shimfiɗe a wata ƴar kusurwa yaje ya
hau.
Yana hawa kan sallayar ya fuskanci gabas, yaji zuciyarshi tayi wasai, baya tuna
komai, baya kuma jin ciwon komai a jiki da zuciyarshi sabida kushi'i da tawakkali
da kyutata ibada baya jin komai sai hasken farin cikin ibada.
Kabbara ya tada tare da niyar sallan la'asar daya mannata bisa laruri ya makarar
dashi.

A falonshi kuwa, hankalin Haroon ya tashi yana nan tsaye bakin ƙofa yana ta
magiyar ya buɗe mishi,
bai saniba shi yana can har cikin bathroom ɗin shi.
Yana nan tsaye, mai Martaba Lamiɗo da Galadima suka iso tare da Sarkin Shaɗi.
Cikin sanyi yacewa Lamiɗo.
"Ya shiga ciki kuma ya rufe ƙodar ta ciki, inata kiranshi baya amsawa.

Murmushi Lamiɗo yayi kana, yacewa Galadima.


"Muje".
Kusan a tare suka fito falon.
Suka zauna, kana ya kira Abba, yace yazo yasa ɗanshi ya buɗe musu ƙofar.

Jin hakane yasa Abba tahowa da sauri.

A can babban falon kuma. Cikin damuwa Jamil ya labartawa Jakadiyarsu da Aunty
Juwairiyya abinda ya faru.
Ga mamakinsu sai sukaga Jakadiyarsu tayi wani ƙayataccen dariya cikin sakekkiyar
murya tace.
"Alhamdulillah wannan shine abinda muka daɗe muna jira tsowon shekaru da dama.
Kuma jinyarsa abune mai sauƙin".
Cikin ruɗani Jalal yace.
"Ummi kuka daɗe kuna jira kuma?".
Kai ta jinjina mishi, kana ta miƙe ta nufi kitchin dan harhaɗa aikin da akasata.

A nan Abba yazo ya samesu.


Jalal na ganinshi ya kauda kanshi.
Hakama Jamil Imran kuma bayanshi yabi suka nufi side ɗin Jabeer ɗin.

A falo ya samu iyayen nashi,


Cikin girmamawa ya rusuna yayi Lamiɗo Barka da yammaci kana ya matso kusa da baƙin
ƙofar Bedroom ɗin Jabeer cikin ɗaga sauti yace.
"Muhammad! Muhammad Jabeer! Jabeer!! Jabeeey!!! Ka taso maza kazo ka buɗe min ƙofar
nan ina jiran ka".

Jabeer kuma da yanzu yake raka'ar ƙarshe, sam hankalinshi baya ga jin kiran
Abbanshi domin a yanzu yana gaban Ubangijinmu ne.

Haroon kuwa wayar dake kunnenshi ya gyara riƙewa cikin shaƙiyancinsa yace.
"Uhumm Umaymah ke dai kicewa Sarki Jalaluddin da Sarki Abubakar baban Daddy na,
suyiwa masarauta Joɗo gudumowar suturu. Domin yau dai ran ƴan maza ya ɓaci, nasan
sai ya yayyage kab wani abu mai yaguwa a masarautarsu".
Cikin wani irin farin cikin wannan labarin da Umaymah taji tayi kekkyawan dariya
tare da cewa.
"Haroon yayan naka kakeyiwa tsiyako?".
Cikin tura baki yace.
"Allah ko Umaymah kecema kike sawa Jabeer yana rainani wai yayana".
Da sauri tace.
"To ba yayanka ɗin bane?".
Cikin yamutsa fuska yace.
"Yayan kwana arba'in, shiyasa yake min kallon kobo biyu da sisi, sabida yana jin
kuna ce mishi yayana, wani lokacin har cemin yaro yakeyi dan tsabar son girma da
manyance, Ni mamaki da yake bani kawai sai in zuba mishi ido in naga yana min faɗa
kamar wani ɗan cikinsa".
Murmushi Umaymah tayi kana, tace.
"Gobe zuwa jibi in sha Allah ina nan zuwa Masarauta Joɗo, sabida zanzo in lallashi
ɗana nasan yayi zazzafan fushi tunda yaƙi kula Dr Aliyu ma".
Daga nan sukayi sallama.

Shi kuwa Sheykh Jabeer saida ya isar da sallameshi yayi addu'o'in shi
Kafin ya tashi a hankali ya nufi bakin ƙofar sabida zuwa yanzu zanan bulalin sunyi
tsami ga zazzaɓi daya mishi rubdugu.
A hankali ya murɗa key ɗin ƙofar ya buɗe ta, kana ya juya ya koma kan gadonshi,
sabida rawa da jikinshi keyi na zazzafan zazzaɓi da wahala.

Yana konciya ya lumshe idonshi tare da fara karanta Suratul Khaf kasancewar yau
yammacin jumma'a ne.

Su kuwa a falo suna jin sautin buɗe ƙofar, suka zubawa ƙofar ido ganin shiru bai
fitobane yasa.

Galadima da Haroon suka nufi cikin ɗakin.


Jim kaɗan da shigarsu Galadima ya fito da sauri ya kira sarkin Shaɗi, da Lamiɗo
kana da Abba.

A tare suka nufi cikin ɗakin, suna shiga Haroon ya fito.


Babban Falon ya koma ya nufa yana kiran Jakadiyarsu da sunan da suke kiranta.
"Ummi! Ummi!!".
Da sauri ta fito kitchen ɗin riƙe da filas da kofuna, sai kuma wani ɗan kwarya mai
kyau ruwan ciki na tururi.

Da sauri ta miƙa mishi tare da cewa.


"Yauwa Haroona gashi kai musu da sauri".
To yace kana ya amsa ya juya ya koma, can cikin ɗakin Jabeer ɗin.

Zaune suke gaba ɗayansu, shi kuma yana konce ya duƙunƙune cikin wani jibgegen
blanket mai masifar kyau da taushi.
Sai karkarwa yakeyi tamkar mazari,
Cikin sanyi Lamiɗo ya ɗan janye borgon tare da cewa.
"Jabeer!".
Duk da azaban zafin da yake ciki, bai hanashi buɗe idonshi ba, wani irin mugun
kallo ya watsawa Lamiɗo,
murmushi sukayi baki ɗayansu kana cikin lallami Galadima yasa hannunshi ya kamo
nashi cikin sanyi yace.
"Jabeer tashi ko? Tashi kasha mgni".
A kufule yace.
"Bazan shaba ku barni in mutu tunda hakan shine fatanku".
Da sauri Abba ya kauda kai tare da yin wani faffaɗan murmushi kana, ya juyo ya
kalleshi cikin bada umarni yace.
"Muhammad tashi. Maza tashi kasha mgni".
Kanshi ya ɗan gyaɗa kana a hankali ya fara yunƙirin tashi zaune.
Ganin hakane Haroon yayi saurin taimaka mishi ya tashi zaune.
Idonshi ya rumtse sabida ji yake kamar har cikin ƙasusuwan jikinshi ake tsikara da
bakin allurai gashi duk inda hudar gashi yake a jikinsa sai ya ɗan tasa kamar wurin
da cinaka ya ciza.
Cikin tarin kula da wani mashahurin farin ciki, Lamiɗo da kanshi ya amshi haɗin
maganin da sarkin Shaɗi yayi mishi a wani ma dai-dai cin kofi.

Hannunshi yasa ya amshi kofin kana ya kaishi bakinshi,


fuska ya kwaɓe sabida gafin mgnin da yaji a jikinshi.
Cikin bada umarni Abba yace.
"Ka shanye duka".
Ido ya rumtse kana ya kafa kanshi ya shanye shi tas.
Miƙa musu kofin yayi, kana ya amshi wani kofin da Abbansu ke miƙa mishi,
Shima shanye shi yayi tas.
Yana miƙa wa Lamiɗo kofin.
Ya fara wani irin gyatsa mai ƙarfi, gyatsan a jere a jere.
Cikin sanyi Haroon yace.
"Sanno my broz".
Ina babu halin amsawa dan gyatsan ya tsananta, wani irin zufane ya keto mishi daga
tsakiyar kai har kan babbar yatsarshi.
Wani irin murɗane ya fara ɗibanshi tamkar zai tsinke mishi ƴaƴan hanji.
Cikin wani irin zabura ya fara wani irin yunƙiri.
Sai gashi yanata kela wani irin baƙin amai akan tattausan blanket ɗin nan.
Murmushi Sarkin Shaɗi yayi tare da kallon aman da kyau kana ya juya ya kalli Lamiɗo
da Abba yace.
"Da dafin kunamai yake tsuma bulalinshi, ga nan dafin yake amayarwa."
Murmushi Galadima yayi tare da cewa.
"Uhumm kaji mugun banza ko".
Shi kuwa Abba ido ya zubawa Jabeer ganin yadda yaketa kela amai, fuskarshi nan tayi
jazir, jijiyar kan goshinsa nan ta tashi ta miƙe samɓal.
Haroon kuwa tallafeshi yayi yanata ce mishi sannu.

Sai dai yayi kusan 30 minutes yana kwara amai kafin ya koma ya jingina da jikin
Haroon yanata wasu irin zafafan numfarfashi tare da lumshe idonsa.
Da sauri Lamiɗo yasa hannunshi ya tattare blanket ɗin ba tare da aman ya ɓata ko
maiba.
Ya dunƙuleshi ya miƙa wa sarkin Shaɗi.
Da sauri Sarkin Shaɗi ya miƙa Abba wani butan duma.
Sannan ya amshi borgon.
Shi kuwa Lamiɗo Haroon ya kalla tare da cewa.
"Cire mishi wannan rigar".
Da sauri Haroon yace to kana ya fara kiciniyar cirewa mishi jallabiyar.
Duk da yana galabaice saida ya ɗan ja tsaki tare da ture hannun Haroon cikin muryar
dake baiyana a wahalce yake yace.
"Bana so ku barmin rigata".
Hannunshi Abba ya buge tare da cewa.
"Bakinka bazai mutu bako".
Shiru yayi yana gani Haroon ya cire mishi rigar
cikin murmushin da ganin jarumta da ƙarfin hali irin na Jabeer Galadima yace.
"Cire wannan ta cikinma".
Ba musu ya bari Haroon ya cire mishi rigar,
Wani irin zaro ido Haroon yayi gani duk jikinshi yayi shatin zanen irin manyan
kunama nan".
Lamiɗo da Galadima da Sarkin Shaɗi kuwa murmushi sukayi tare da haɗa baki wurin
cewa.
"Uhum dafin ya gama fita, cikin jininshi."
Abba kuwa hannun ya haɗa ya miƙa wa Lamiɗo dake mishi alamun zai zuba mishi abu a
hannun.
Wani haɗin mgnin ya zuba mishi cikin tafin hannunshi.
Murzawa yayi kana, ya shafa a duk jikin Jabeer.

Wani irin sassanyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da lumshe idonshi.


sabida wani irin sanyin da yaji yana ratsashi har cikin ƙasusuwan jikinshi.
Tuni wani bacci mai fitinenne daɗi ya kwasheshi.

Nan suka gama yi mishi komai.


Kana suka fita,
Dr Aliyu kuwa da Ya Hashim suka shigo bisa umarni Lamiɗo.

Drip and injections Dr Aliyu ya ɗaura mishi tare dasa ruwan alluran a cikin ƙarin
ruwan da akeyi mishi.

Ganin sun gama yi mishi komai ne, suka fita suka tafi.
Suka bar Haroon kaɗai. Dan in ruwan ya ƙare ya cire mishi.

A falo kuwa Ya Hashim nayi musu bayanin ya samu bacci jikin da sauƙin duk sai suka
tashi suka nufi masallaci.
Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya aka bari a wurin.
Sum jin shiru ba motsin Haroon yasa suka tafi sashin Juwairiyya dan bawa hadimanta
umarnin shiga kitchen.

Bayan awa ɗaya kuwa ruwan ya ƙare ya cire mishi.


Ganin yana bacci ne yasa ya shiga wonka.

A can cikin gidan kuwa. Sashin Gimbiya Saudatu zaune take a bisa bakin gadonta ita
da Laminu ɗan ta na biyu video da yayi a Rugar Bani na zabgar Jabeer yake nuna
mata, cike da tsantsar jin daɗi, sai dariyar mugunta sukeyi.
Babban ɗan ta Ya Hashim ne, zaune can gefensu, ya zuba musu ido, yana nazartansu,
to sukuma me sukeji a zuƙatansu, akan Jabeer da sauran ƴan uwansa shin duk wannan
ƙiyeyyar ta mecece".
Muryar Baba Nasiru suka jiyo a falon yana sallama.
Da sauri Gimbiya Saudatu ta miƙa tsaye tare da kamo hannun Laminu tace.
"Zo taho muje gacan ƙaramin Babanku".
Da sauri suka nufi hanyar fita, wani irin kallo yayiwa Ya Hashim tare da jan tsaki
cikin faɗa tace.
"Banza mara zuciya, wanda bai san masoyansa da maƙiyansa, ai dai duk abinda nakeyi
a kankane".
Tana faɗin hakan suka fice.
Jiki a mace yabi bayansu, Allah ya sani baya son cutar da Jabeer da sukeyi.
A falon ya samesu zaune harda Baba Bashiru sunata sheƙa dariyar mugunta.
Gefe can ya zauna ya zuba musu ido. Bayan sun ɗan tsagaita dariyar ne,
Baba Nasira ya nisa tare da cewa.
"Allah kenan maji roƙon bawa, gashi ya amsa min addu'o'in da nai a safiyar yau ɗin
nan,
Yadda na wuni da baƙin ciki, shi kuma zai kwana da azaba".
Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace.
"Ai Ni nafi kowa farin cikin wannan dukan Kawo wuƙa da akayi wa wannan hegen yaro
mai jajayen kunnu, yaro sai hegen baki da rashin tsoro duk barazanar da akeyi mishi
baya kashe bakinsa.
Musamman ni kam ina mgna kafinma in sauƙe numfashin ya bani amsa ga shegen azanci.
Ɗan is abun buga cincim yau dai babu wannan bakin ai".
Cikin dariyar ƙeta Laminu yace.
"Ai wlh Umma ni so nayi a kashe hege a can, mu binneshi a waccar ƙaramar Rugar mu
dawo salum salum abinmu".
Cikin murtuke fuska Baba Basiru ya kallesu tare da cewa.
"Ai Ni yau ko mutuwa yayi ban huce baƙin cikin dana shaƙa ba lokacin da naga ya
fito ɗakin sirri da Lamiɗo har yanzu in na tuna zuciyata bugawa takeyi, to wai ma
meye hakan ke nufi.
Da farin ɗan uwanmu da aka bawa Galadima ya rasu dare ɗaya, ana biyu aka bawa
wancan hegen yaro mai nisan kwana Jafar ɗin sarautar.
Wannan abu shi yafi komai tada mana hankali, tunda dama duk cikinmu yaran Lamiɗo
babu wanda ya ba koda sarautar fadanci ce sai Yaya Muhammad, to kuma dan ya rasu
sai a maida sarautar kam jikoki a tsallake ƴaƴan duka."
Cikin tafasar zuciya Laminu yace.
"Yo waya ma sani ko sune suka kashe mana Babanmu dan mulkin ya koma hannunsu, ku
kuma kuka barsu".
Da sauri Baba Nasiru yace.
"Muka barsu kuma, ai Allah ne zai barshi ba mu in bamu ɗauki mataki ba, Allah
ya nuna ikonaa yanzu shi Jafar ɗin kallon me akeyi mishi?".
Da sauri Gimbiya Saudatu tace.
"Mahaukaci tuburan".
Dariya sukayi kana cikin rashin gamsuwa Laminu yace.
"To kuma duk da haka ai ba'a dawo da sarautar kanmu ba sai, aka bawa ɗan tsohon
sarkin wannan bappan naku mai farin gemu.
Bayan nan kuwa duk bawa kowa mulkin komai ba, dan sakacinku an ɗauki mulkin Garkuwa
an bashi."
Cikin sanyi Ya Hashim ya harari ƙanin nashi tare da cewa.
"Laminu kafa ji tsoron Allah ka tsarkake zuciyarka, ka raba kanka da wannan zalumci
da kafurar zuciya".
Cikin zafi Gimbiya Saudatu tace.
"Rufe min baki, samodaran banza sako tumaki ɓallo jakai,".
Cikin sanyi yace.
"Umma badake nakeyi ba da".
Cikin mgnar in-ina Baba Nasiru yace.
"Tafi daga nan damu kakeyi mana, ka fake da Laminu, maza tashi ka bamu wuri".
Miƙewa yayi ya fita ya bar musu wurin ya nufi sashinsa wurin iyalanshi.

Su kuwa nan sukaci gaba da sabgogin gabansu.


Nan Gimbiya Saudatu ke cewa.
"Sai gobe da sassafe zanje in salon hegen balaraben nan".
Dariya Laminu yayi tare da cewa.
"Yau da yaga haza, yaga zai zanu sai cewa yayi, wai shi ba bafulatani bane, a
kirashi dama duk ƙabilar da akaga dama".
Playing video yayi ya miƙa wa su Baba Basiru tare da cewa.
"Jaridar safi ta gobe da safe da wannan labarin zai fito a shafin forko nako wanne
kamfanin jarida,
Kana wannan abun shine hirar da BBC Hausa da kanshi zasuyi karin kumallo dashi.
Sai wannan lbri da video da hotuna sun bazu tako ina, dan ina jirane sai jaridu sun
fidda shi kafin in watsashi kafafen yaɗa labarai na duniyar gizo-gizo".
Cikin tsananin jin daɗi suka jinjina wa basirar Laminu.

A can sashin Gimbiya Aminatu kuwa, kekyawar tsohuwar bafullatana ƴar kimanin
shekaru 61 sosai hankalin ta ya tashi jin labarin abinda ya samu jikanta mafi
soyuwa a gareta. Cikin rawan jiki ta miƙe tare da juyawa zata nufi Side ɗin ta.
Da sauri Lamiɗo yayi gyaran muryar dake mata nunin ta zauna ta nitsu.
Cikin tashin hankali ta koma ta zauna tare da cewa.
"Allah Rane zanje in duba halin da yake cikine".
Cikin ƙasaita da bada umarni yace.
"Koma ki zauna ki nitsu kin ga magriba ta ƙara to. Bawai zan hanaki zuwa bane, ki
bari ayi sallan magriba da isha'i sai ki aika Jakadiya ta dubo miki in idonshi biyu
sai kije".
Ba don ta soba ta amince da hakan.

Hajia Mama kuwa, tana jin lbrin abinda ya faru daga bakin Abba, kai tsaye daga
sashinsa sashin Jabeer ɗin ta nufa.
A falo ta samu Haroon kadai zaune cikin shigar kakanan kaya. Cikin tashin hankali
da kiɗima da firgici ta nufi hanyar side ɗin. Jabeer ɗin ido na zubda hawaye.
Da sauri Haroon ya miƙa tsaye cikin sanyi yace.
"Mama ya samu bacci ne, kuma Dr Aliyu yace kada a tadashi, jikin da sauƙi ma sosai
ki kontar da hankalinki".
Ina hankalinta bai konta da hakanba, saima ƙara kutsa kai cikin falon side ɗin shi
takeyi.
Cikin sanyi ta tsaya jin Haroon na ce mata.
"Dan Allah Mama kiyi haƙuri, Allah kuwa jikin da sauƙin, Abba da Lamiɗo da kansu
suka kula dashi, yanzu haka bacci yakeyi."
Cikin tashin hankali murya na rawa tace.
"Haroon hankali na ya tashi sosai, ina tsoron kada a cutar min dashi kamar yadda
akayiwa Jafar."
Hannunta ya kamo kana yaja suka dawo falo, cikin sanyi yace.
"In Sha Allah babu wani abinda zai sameshi, in Allah ya yarda an gama samun nasara
a kansu, yanzu warakace ke kusantosu, in sha Allah duk sarƙaƙiyan dake sarƙafe
cikin masarautarku da mutanen cikinta zai worwore, za kuma ayi walƙiya kowa zai ga
kowa!".
Wani irin lumshe ido tayi tare da cewa.
"Allah yasa haka".
Cikin kontar mata da hankali yace.
"Amin Amin. Umaymah ma tace tana nan tafe".
Cikin tarin mamaki da baiyana tsantsar jin daɗin ta tace.
"Alhamdulillah kai naji daɗin wannan mgnar ko ba komai in tazo ai zan samu wacce
zan tattauna damuwar raina, sabida hirar waya bata wadatar wa".
Murmushi yayi tare da nuna mata hanyar fita cikin tsokana yace.
"Wato kun san ɗan naku ragone shiyasa duk kuka tashi hankulanku."
Cikin share hawayenta tace.
"Haroon yayanka nefa".
Tura baki yayi tare da cewa.
"To naji Hajia Mama je kiyi salla lokacin salla yayi, kinji an fara kiran salla".
Da haka ta fita.

Shi kuwa Haroon a hankali ya nufi cikin ɗakin, kamar yadda yabar Ya Jafar zaune a
tsakiyar gado yasa Jabeer a gaba, yana karatu tare da gyara mishi rufuwar shi.
Haka ya sameshi yanzuma,
Kuma har zuwa yanzu idonshi bai daina zubda hawaye ba.
Kana ganin fuskarshi zaka hango zazzafan so da ƙanan da tausayin ƙanin nashi cikin
ƙwayar idonshi.
A hankali Haroon ya matsosu.
Cikin sanyi yakai hannunshi ya kamo hannun Ya Jafar ɗin.
Kanshi ya ɗago ya zuba mishi ido.
Murya cike da rauni Haroon yace.
"Ya Jafar tashi kazo muje masallaci lokacin salla yayi. Muje muyi salla muyiwa
Sheykh Jabeer Addu'o'in samun lfy".
Kanshi ya gyaɗa sabida in dai abu na ibadane to bai kasance jiɓeɓɓe a kanshi ba.
Sunkuyo wa, yayi ya sumɓaci goshin Jabeer kana, ya sauƙo kan gadon.
ƙofar Bathroom Haroon ya nuna mishi da yatsa.
Shiga yayi bayan ya fitone, shima Haroon ya shiga ya sabunta al'wala kana, suka
fita.

A babban falon suka samu, Aunty Juwairiyya da Jakadiyarsu suna shirya musu abinci
bisa dinning table.

Cikin kula Aunty Juwairiyya ta kalli Haroon murya a sanyaye tace.


"Haroon ya jikin nashi dai?".
Ɗan tsayawa yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah gsky zama muce ya worke, sabida ya amayarda duk wani dafin dake
jikin bilalin yanzu naga shatin kunaman ma duk sun ɓace a jikinshi, ya zama sai
shatin bulalin".
Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa.
"Suma nanda kwana uku in sha Allah babu tabonsu a jikinshi. Na gaya muku ai jinyar
Shaɗi ba abu mai wuya bane a masarautar Joɗa, yanzu da asibiti aka kaishi, koda ko
ƙasar waje za'a fiddashi a ƙalla sai anyi watanni uku ana jinyarshi, in yanada
nisan kwana ya worke da kyar in kuma kwananshi sun ƙare ya cika a can. Amman yanzu
yana tashi bacci zaiji sauƙin sosai".
Cikin mamaki suka zuba mata ido.
Jalal da Jamil da yanzu suka shigone suka haɗa bakin wurin cewa.
"To wai Ummiy meyasa naga kamar farin cikin, abun kikeyi keda ko ruwan sama bakya
son ya taɓa lfyarmu mu bare ɗan gatanki".
Kanta ta ɗan jijjiga tare da cewa.
"Abune mai duhu shekarun ku baiyi yawan da zaku gane haskenba, su kansu magautan
Jabeer duk basu san ƙarfin iko da sani da shaharar wannan masarautar akan al'adun
Shaɗi bane,."
Jafar ne yayi gaba bayan ya duba agogon hannunshi ganin hakane duk suka bi
bayanshi.

A can Rugar Bani kuwa, bayan anyi sallan bamgrib, anyi Isha'i.

Shatu, Rafi'a, Ummey, da kuma Bappa sai Autar gidan Junainah dake konce gefen Ummey
duk sunyi shiru.
Suna jin Bappa yana basu lbrin yadda komai ya faru a wurin gasar cikin sanyi yaci
gaba da cewa.
"Tabbas akwai abinda Allah yake nufi da wannan bawan, haƙƙun nasan Allah bazai bari
a zalumceshi haka nan banzaba, inaji a jikina akwai wani babban al'amari mai
girgiza zuƙatan mutane da zai faru a nan gaba".
Cikin sanyin murya Rafi'a tace.
"Bappa meye sunan jikan sarkin ne?".
Cikin sanyi Bappa yace.
"An faɗa amman na mance sunan".
Sallamar da wani yaro yayine ya sasu maida hankalinsu kanshi, bayan ya rusuna ya
gaisa Bappa ne yace.
"Bappa ana sallama da Shatu wai tazo".
A hankali Shatu dake zubda hawaye ta juyo ta kalleshi. Bappa kuwa cikin girma yace.
"Waye ne?".
Wani irin azabebben ajiyan zuciya Shatu ta sauƙe jin yaron yace.
"...!

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:22 PM] +234 906 805 8984: "Ya Salmanu ne yake kirantan, yace tayi haƙuri
tayi sauri ta fito."
Cikin sanyin jiki Shatu ta manna kanta jikin kafaɗar Rafi'a.
Shi kuwa Bappa, gyaran murya yayi tare da cewa yaron.
"To je kace mishi tana zuwa."
Jin haka yasa yaron ya juya ya fita.

Miƙa Bappa yayi kana ya kalli Shatu murya a sake yace.


"Shatu tashi kije, kiji dame yake nemanki".
Cikin sanyi tace.
"To". Kana a hankali ta miƙe dan cika umarnin Bappa.
Rafi'a kuwa, miƙewa tayi ta shiga cikin ɗaki, gyara musu wurin konciya tayi, sannan
tazo ta shigar da Junainah kana ta cewa Ummey su shiga, jiki a saɓule Ummey ta miƙe
suka shiga.
Bappa kuwa turakanshi ya shiga.

A can ƙofar gidan kuwa.


Bisa ɗan dakalin ƙofar gidan nasu, suka zauna.
Tunda suka zauna tayi shiru, kanta na sunkuye tana wasa da ƴan yatsunta, kana
hawaye na ɗigowa kan tafin hannunta.
Shi ma Ya Salmanu shiru yayi, tamkar bazaiyi mgna ba.
Farin wata kuwa ya fito ras ya haska ko ina, alamun yau watan ya kai kwana tara ko
goma.
Kanshi ya ɗan juyo ya ɗan kalleta cikin tsananin tausayawa ya fidda numfashi mai
zafi tare da cewa.
"Shatu!". Shiru bata amsa mishiba sai dai ɗago kanta tayi tana kallonshi hawaye na
kwaranya, wani irin murmushi yayi cikin sanyi da harshen fillanci yace.
"Bazan hanaki kukaba, Shatu, sabida koni kaina nakan zubda zafafan hawaye a duk
sanda na tuna yayuna ƙannena makusantana, abo kaina da aka kashe, wanda basujiba
basu ganiba.
Nakanji zuciyata na tafasa, tafasar da nakejin bazai taɓa gushewa ba sai na ɗauki
fansa."
Cikin rawan murya tace.
"Ya Salmanu fansa kuma?".
Kanshi ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Uhum fansar dai, tunda hukuma da gwamnatin da masarautun gargajiya basu ɗauki
mataki kan abinda akeyi mana ba. To mu zamu ɗaukarwa kanmu."
A hankali tace.
"Ta yaya ɗin bayan duk an kashe matasa majiya ƙarfin. Cikin kaso goma na mutanen
Rugar Bani an kashe kaso 6 huɗune suka rage. Me amfanin ramuwa, wlh da zan faɗa aji
da mun bar musu garinsu kawai mu koma wani wurin".
Gyara zaman shi yayi ya fuskanceta da kyau cikin sanyi yace.
"Ko wani ɗan adam ina ya shiga dumuwa, ire iransa ke shige mishi ya magance
matsalar.
Yanzu da ɗan jarida ɗaya aka kashe zakiga zakiji yadda ƙungiyoyin yan jaridu zasu
magantu, sai ya zama babu wani rahoton da zasu buga sai na kashe ɗayansu da akayi.
Hakama da za'a kashe police officer ɗaya zakiji yadda hukumar zatayi ta bincike da
ɗaukar mataki har sai sun gano wayene sun kuma ɗauki mataki.
Da za'a ƙona kamfani ɗaya ire irensa kamfanoni sama da dubu zasu iya shiga fadan.
Hakama in da za'a taɓa ɗan kasuwa to zakiji yadda duk yan kasuwa zasuyi ta kumfar
baki.
Da za'a kashe manomi ɗaya to zakiji yadda gungun manoma zasuyi rubdugu kan mgnar.
Da za'a taɓa bafaden wata masarauta zakiji duk masarautun ƙasarnan sun amsa.

Haka abin yake. Duniyar ta zama waka sani? waya sanka? Mu kuwa Fulani bamu san kowa
ba bayan Allah da Manzonsa, bamu da wani namu a siyasance.
To tunda haka abin yake, muma da wannan salon zamuyi amfani.
Muna nan munata raba goron gaiyata wa duk al'ummar fulanin makiyaya a duk inda suke
a cikin duk faɗin duniyar nan, in dai sunada damar zuwa to su zo!.
Su kawo mana agaji, wlh in sha Allah da izinin ubangiji sai mun yaƙi kafuran Bonon
sai mun kashe dodon tsafinsu Bonon mun hallakashi a doron ƙasa,
Shatu mun kai matakin da wallahi babu mahaluƙin da zai dakatar damu.
Sai mun kauda Shirka da waɗannan mushirkan a wannan yankin."
Ido ta rumtse wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata.
Cikin muryar dake nuna ƙunar ranta tace.
"Ya Salmanu wane mataki ake ɗauka kan neman su ya Giɗi kuma?".
Kanshi ya jinjina tare da cewa.
"Yana cikin matakin shiga cikin ƙabilar mu yaƙesu, mu kuma bincika ko sun ɓoye su
Giɗi a cikin garin nasu".
Ajiyan zuciya taja tare da cewa.
"Allah ya taimaka".
Amin Amin.
Murmushi yayi kana yace.
"Kinji batun gasar da akayi ko da nasarar dake tinkarar rayuwarki ko?".
Cikin sanyi tace.
"Kaiya ya Salmanu ina kake da tabbacin nasara mutumin da bamu san irin fansar da
zai ɗaukaba, naso ace kaine kai wannan nasarar da nafi kowa farin ciki".
Murmushi mai ciwo yayi a ranshi kana yace.
"Nan ɗin ma muna zaton farin ciki, duk da akwai tarin ƙalubale, mu dai in mun samu
wani ya ci Ba'ana a gasar Shaɗi kin san yayi al'washin zai bar ƙasar nan gaba ɗaya
ko?".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Uhum in bai sauya salon ba dai".
Cikin jin daɗi yace.
"Ba zai sauya saloba, dole zai bar ƙasar sai dai shiri zaije ya ƙara, kafin ya dawo
kuma, an aura min ke, shi kuma jikan sarki.
Muyi musu mubaya'a, mun yarda su masarauta Joɗo fulani ne".
Cikin tsananin jin daɗi tace.
"Allah ya tabbatar da haka ya Salmanu yasa kuma a samo su Ya Gaini cikin Bonon don
Ni dai nafi zaton can suka kaisu.
In anyi gasar an cishi, ya bar kasar, a ɗaura aurenmu a ranar".
Da sauri tasa tafin hannunta ta rufe idanunta alamun jin kunya,
Shi kuwa Salmanu murmushi yayi tare da cewa.
"Iye yan Matana an girma, me ma za'ayi mana?".
Cikin kunya tace.
"Ban saniba".
Murmushi yayi kana yace.
"Ni ai bazan manceba tunda yanzu burin mu na kusa da cika, ayi mana aure, nima haka
ne tsarina ana watsewa gasar suna tafiya, za'a ɗaura mana aure.
Kinga gashi dama na samu aiki a babban birninmu.
Sai mu tafi can abinmu ko Wannan mugun saurayin naki ya dawo bazai samemu ba".
Murmushi tayi shi kuwa ido ya zuba mata yana jin tarin farin ciki.

*DAN ALLAH DA MANZONSA DA DARAJAR IYAYENKI DA SUKA HAIFEKI SUKA BAKI TARBIYYA, KADA
KI FITARMIN DA LITTAFINA DAN AL'FARMA ANNABI DA AL'ƘUR'ANI, KU DENA FITAR MIN DA
LITTAFI DAN ALLAH🙏🏻😭😭😭 Especially ku ƴan SPG na roƙeku da Allah🙏🏻😭😭

Da sauri ta gimtse dariyarta, cikin sanyi da tsoro ganinshi tamkar gilmawar walƙiya
sai gashi a gabansu.
Wani irin azabebben tsorone ya rufe Salmanu amman sai ya dake, cikin ƙarfin hali da
kalato jarumta ya kame jikinshi dake rawa.
Cikin ɗan rawan murya yace.
"Me haka, zuwa babu sallama?".
Wani mugun kallo ya watsa mishi tare da cewa.
"Kiyaye bakinka idan maza suna wuri."
Cikin dakiya Salmanu yace.
"Ina mazan!? Ai ni banga wani na miji a nanba sai mata maza. Ai namiji shi zai iya
sa namiji ɗan uwanshi zubda hawaye ko tsuma da faɗuwa, a dai yanzu ai babu wani
namiji a Rugar Bani da kewaye sama da Jarumin da bulalar SHAƊI bata sashi zubda
hawaye ba Sheykh nake nufi".
Wani irin zabura Ba'ana yayi ya nufi kansa alamun zai shaƙeshi.
Da sauri ya tsaya jin Shatu ta saki ihu tare da cewa.
"Bana so ya Ba'ana in dai kana son farin ciki na, to kada ka dakeshi ko ka cutar
dashi da komai".
Wani irin kallo ya mata mai cike da tuhuma da razana da kuma karaya,
Ita kuwa Shatu cikin rawan murya tace.
"Ya Salmanu ka tafi, bana so kaje ka bar koya min komai".
Cikin sauƙe ajiyan zuciya na tsoro.
Salmanu ya juya ya tafi.

Shi kuwa Ba'ana, zama yayi inda Salmanu ya tashi, cikin taraddadin ko dai Shatu
bata sonshi ne, ya nuna mata gefenshi.

A hankali ta zauna, shiru tayi tana sauƙe shessheƙan kuka.


Cikin ƙuna da baƙin cikin rashin sa wancan ɗan birni mai fata kamar ta jariri
kukanne ya sakar mishi fargaba,
cikin sanyi yace.
"Mata!".
Bata kalleshi ba kuma bata dena shessheƙan ba.
Kiranta ya kuma yi a karo na uku.
"Mata!".
Cikin disashewar muryar tace.
"Na'am".
Juyowa yayi ya fuskanceta da kyau a hankali yace.
"Mata bakya so nane!?".
A bazata tambayarshi tazo mata,
ta ina kuma ta yaya zatace mishi bata sonshi, bayan tasan abin da yayi mata
shekarun baya, dama fansar shi ta soshine kuma ta aureshi, da wanne bakin zatace
mishi bata sonshi.
wasu zafafan hawaye masu ɗumi ta zubda.
Haƙiƙa ya Ba'ana mugune amman a iya saninta a kanta ya zama mugun, tunda sai wanda
ya nuna baya sonta dashine yakewa mugunta,
Babbar matsalarshi mushirkine kuma baya salla.
Cikin rawan murya da kuka tace.
"A a Ya Ba'ana Ni bance bana sonka ba".
Da sauri yace.
"Uhhmmm to meyasa bakya ganin laifin Salmanu akan duk abinda yake min, ko dai shi
kikeso ne Mata!?".
Da sauri ta jujjuya mishi kai sabida sanin ko jinkirin bashi amsa tayi zai iya yiwa
Salmanu illa.
Cikin rawan murya tace.
"Bana son ka cutar da shine sabida, shi ya janye batun soyayyarsa gareni. Ka kuma
sani karatu yake koya min amatsayinshi na wanda ya samu karantarwa a wata jami'a,
Yana sona da al'khairi kai kuma kana ƙinshi, ko dai ka manta ka ce min zaka so duk
wanda yake sona da al'khairi yake kuma taimaka min".
Jiki a mace ya gyaɗa mata kai,
sai kuma ya rumtse idanunshi da yakejin suna cikowa da hawaye yace.
"Lokuta da dama sai inga kamar bakya farin cikin ganina, a madadin farin ciki sai
inga tsorona cikin ƙwayar idonki."
Juyowa tayi gareshi da kyau cikin kuka tace.
"Ba kai ke bani tsoroba, abinda kakeyi ne yake sani tsoronka, ya Ba'ana ka bar
wannan asirce-asircen babu kyau shirka ne, wanda yake ɗaya daga cikin manyan
zunuban da Ubangiji ya haramtawa mumini yin tsafi haramun ne".
Kanshi ya jingina da jikin gini yana kallonta tamkar yau ya fara ganinta,
A hankali ya fara mgna cikin muryar da bata taɓa jin rauninta a muryarsa ba yace.
"Mata ina sonki, wallahi Allah kenan rantsuwar musulmai, ina sonki, son da ni kaina
bansan adadinshi ba,
Duk abinda nakeyi a kanki nefa, Shatu ki min uzuri, na roƙeki kiyi min ɗa'ar riƙe
tukuicin abinda nai miki a baya,
Ki soni koda rabin yadda nake sonki ne.
Kiji tausayina Shatu ina jin tsoron kada ƙaddara ta rabamu,".
Kekkyawar fuskarshi ta zubawa ido, tana gani. Irin kyan da Allah yayi mishi sai dai
sam babu kyan hali ya zama kyan ɗan maciji.
Cikin sanyi tace.
"Ya Ba'ana tsoro kuma?".
Kai ya gyaɗa mata cikin sanyi yace.
"Eh sabida muddin aka rabamu, zan zamewa fulani babban ƙalubale a rayuwarsa, kuma
duk wanda yayi sanadin rabuwata da ke, wallahi zaiga toskun rayuwar duniya, zaiyi
dana sani, zan zama mugun zahiri. Na san ke Kum bakya son hakan.
Yau kuma fargaba na, yafi na baya yawaita da wannan jikan sarki ya iya daurewa
azabar bulalina baiyi ƙollaba."
Wani irin ajiyan zuciya taja tare da cewa.
"Babu komai ya Ba'ana Ni dai ina tayi mana addu'an ALLAH yayi mana zaɓi mafi
al'khairi a rayuwata, ya kuma shige min gaba a dukkan motsina".
Ido ya zuba mata babu ko ƙebtawa, cikin sanyi yace.
"Nine mafa al'khairinki Mata".
Da sauri tace.
"Baka saniba".
A zafafe yace.
"Na sani mana".
Cikin tsoro tace.
"Kai masanin gaibu ne kenan?".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Ehh kusan haka tunda nayi duba a kanki".
A hankali tace.
"Wa'iyazubillah. Duba ba gsky bane, zai iya maka ƙarya".
Hannu ya ɗaga mata da sauri kana ya nuna mata hanyar shiga gida.
A hankali ta tashi tsaye cikin sanyi tace.
"Allah ya baka haƙuri ya shiryeka".
Ta ƙarishe mgnar tana ƙoƙarin yin kuka.
Da sauri ya juyo cikin sanyi yace.
"Kada kiyi kukan mata, nayi haƙuri.
yanzu na fasa jiran Sai kin gama karatu ayi mana aure.
Duk randa wancan malamin ya dawo ya rama gasar Shaɗinsa. Za'a ɗaura auren mu a
ranar, domin
Koda duk bulalin duniyar nan zai zabgeni dasu wlh bazaici nasara a kainaba domin
idona ba idon da zai zubda hawaye a kanki bane bilali ɗaya nake tsoro kuma babu
wanda yasan inda suke.
In kuwa aka samu wani akasin dama bazai samuba, to zan bar ƙasar nan zan koma ƙasar
Cameroon can babban birnin Yahunde, inbi cikin Rugar wasu fulanin.
Sai dai ko bana nan duk wanda ya aureki ya auri ajalinsa."
Bata iya tanka mishiba, a haka ya juya ya tafi.

Kana ita kuma ta koma cikin gida.


A cikin masarautar Joɗa kuwa.

Sai da akayi sallan isha kafin.


Su Haroon suka dawo gida.
Suna tafe,
Abba da Lamiɗo da Galadima, da Dr Aliyu da kuma Sarkin Shaɗi.
Suna biye dasu a baya.

Kai tsaye wucewa sukayi har bedroom ɗin Jabeer har yanzu bacci yakeyi.
Sai dai tunda lokacin salla yayi yaketa jin baccin ba daɗi sai dai kuma Allah bai
bashi ikon farkawa ba.
Dubashi sukayi tare da ƙara shafa mishi wasu magunguna kana suka fita suka tafi.

Hakama Gimbiya Aminatu tazo itama har ɗaki sai dai samunshi yana bacci yasa ta
tafi.

Bayan fitanta ba daɗe Barrister Kamal da ɗan sa Sulaiman sukazo.


Suma har ciki suka shiga suka dubashi.
Kana suka tafi.

A ranan a daren gaba ɗaya mutanen masarautar kowa yaji lbrin abinda ya faru.

A falon su Jafar duk sukaci abinci.


Ganin dare ya tsalane yasa Juwairiyya jan hannun Jafar suka tafi.
Jalal, Jamil, Ya Hashim kuma sukayi musu saida safe kowa ya tafi side ɗin shi.

Jakadiyarsu kuwa itama ta nufi sashinta,


Ya zama dagashi sai Haroon.

Sha biyu da rabi dai-dai na dare.


Haroon zaune kan wata doguwar kujera irin ta sarakuna dake cikin ɗakin.
Waya yakeyi da Jannart,
yana konce ne dagashi sai boxes.
Waya sukeyi irin ta mosoyan da shaƙuwarsu tayi yawa,
Wani irin miƙa yayi wanda gaba ɗaya gabban jikinshi suka amsa.
Cikin tarin kasala da masifeffen shauƙi yace.
"Wash Allah na".
Cikin kashe murya da ta ingizo Bukatarsa tace.
"Ohhh sorry Ya Haroon meya faru gaya min me yasameka".
Cikin sakaliyar murya yace.
"Haroon yunwa yakeji".
Sam bata fahimci inda batunshi ya dosaba haka yasa cikin haɗa fuska tace,
"Ya Haroon ka dawo gida, shi Hamma Jabeer ba matace dashi ba, bare ya kula da
cikinku, na kuma san in kuna Side ɗinsa ba wani zuwa wurin Aunty Juwairiyya
zakuyiba, kuma itama fama takeyi da mijinta.
Ni gsky ka dawo Tsinako nasan Umaymah zata kular min da kai da kyau, ko kuma kazo
Masarautarmu Leddi julɓe, nida Sitti mu kula da kai".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Masarauta Joɗo fa masarautace mai daraja, da karrama baƙo baki san asalin tarihin
inda masarautar tasamu suna Joɗa bako.
Baby kada ki damu kular da muke samu ko sarki mai mata huɗu da kwarkawara biyar
baya samu.
Tako wani sashi na gidan abinci hadimai ke kawowa Side ɗin Sheykh a ƙalla wani
lokacin kusan abinci kala goma muke riska, kinsan fulani ba marowata bane.
Kawai matsalar wannan yunwar rashinki ne, a kusa yasa nake jina ina tashi sama
kamar doki".
Cikin kunya da kauda zancen tace.
"Ya jikin Hamma Jabeer shugaban tuzuran ƙasar mu?".
A hankali ya juyo kanshi ya kalli bisa makeken gadon da Jabeer ke kai.
Da sauri ya katse kiran bayan yace mata.
"Ina zuwa".
Kan gadon ya nufa, jabeer ɗin yana ƙoƙarin tashi zaune.
Hannunshi daya miƙa zai taimaka mishi, ya buge cikin haɗe fuska yace.
"Yanzu ƙarfe nawa?".
Wayarshi dake hannunshi ya duba cikin zuba mishi ido yace.
"Ƙarfe ɗaya dai-dai".
Cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi kuka yace.
"Shine ka barni ina bacci kamar kafurin da bashi da addini.
Anyi sallan bamgrib baka tasheniba, anyi Isha'i baka tasheniba, daga wannan
masifeffen bacci mara daɗi mai cike da mafarkai marasa daɗin da nasan rashin yin
salla a lokacin sane ya jazamin su.
Iya wunin yau duk so kuke kuyi min asarar lokuta masu muhimmanci da daraja, kun
sani na makara la'asar da magriba hakama isha."
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye,
Tare daci gaba da cewa.
"Da fari ansa ni na tsaya gaban jama'a da baiyana surata,
Aka ɗora min da duka kana, akasa na makara sallan la'asar,
Yanzu kuma mangriba da isha'inma kun barni ina baccin asara na makara, sabida baka
san darajar yin salla a cikin jam'i da kuma yin ta cikin lokacin ta ba ko?".
Cikin taɓe baki Haroon yace.
"Kasan ai ni ba musulmi bane, ban san komaiba".
Harara ya dannawa Haroon tare da cewa.
"Kai ka gayawa kanka, Ni bana kafurta mutum, abinda na sani dai kai tsarin yahudu
da nasarane,
To bari kaji, Ni bani da laifin komai sabida bacci nakeyi, mai bacci kuma al'ƙalami
ya sauƙa kansa har sai ya farka.
Kai dake ganina ina bacci lokacin salla yayi idonka biyu baka tasheniba haƙƙin a
kanka ya rataya."
Ya ƙarishe mgnar yana shiga bathroom tare da cewa.
"Ka cire idonka a kaina banza mai kallo kamar mayun wancan garin mugayen".
Murmushi Haroon yayi tare da komawa ya zauna bisa kujerar.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wonka ya kumayi da ruwan ɗumi,


kana ya kimtsa cikin irin suturun da yake ta'ammali dasu, in yana gida.
kana ya ɗaura wata farar jallabiya kai.
Sannan ya fito bayan ya shafa mai ya fesa turare.

Yana fita ya fara ramuwar sallan daya wuceshi yana bacci.

Haroon kuwa falo ya fita abincin da yasan zai iya ci ya kawo mishin

A ƙalla awa ɗaya yayi kafin ya tashi kan sallayan


Gaban gadonshin ya dawo ya zauna bisa tattausan carpet ɗin da ke shimfiɗe a wurin
mai kalar Sky blue and white.
Sosai yaji daɗin jikinshi, sai dai har yanzu yana jin raɗaɗin bulalin.
Tea kawai ya iya sha.
Kana a hankali yace wa Haroon.
"Canza min beshit ɗin nan da blanket ɗin."
Hararanshi Haroon yayi tare da cewa.
"Zan koma, yaseen na gaji da mulkinka da sarautar da kake ji dashi. Ji yadda ka
medani tamkar wani bawanka ko hadimin gidanku, kuma duk abinda zanyi maka sai ka
cini gyara, mutum ba'a iya mishi sai masifa kake min kamar dai nine nace a zaneka".
Ya ƙarishe mgnar yana miƙewa tsaye tare da gimtse dariyarshi, sabida ganin kallon
da Jabeer ke mishi.
A haka dai ya sauya komai na gadon kafin suka, hau suka konta.
Tsaki Jabeer yaja tare da cewa.
"Ni dama ka tafi wancan ɗakin sabida zancen gsky kasan ni bana son takura.
Sabida zaka hanani sakewa yadda nakeso".
Cikin gajiya Haroon yace.
"Allah babu inda zan fita inje".
Da haka dai Haroon yayi bacci.
Shi kuwa Sheykh Jabeer karatu yayi tayi har biyu da rabi tayi kana, ya buɗe tafin
hannunshi yayi addu'o'in bacci.
Falaƙi 3 Nasi 3 ƙulhuwa 3 Ayatulkursi'u 1 kana amarrasulu 1 tofa a tafin hannunshi
ya shafa a jikinshi.
Kana ya kuma yi. Haka ya tofa a tafin hannunshi ya shafa a jikin Haroon Wanda tuni
ya ɓingire,
Shi kuwa Jabeer wannan al'adar rayuwarsa ce daya saba, kan Jalal da Jamil sabida
suma haka suke bingirewa, shikeyi tofi ya shafa musu.

Washe gari Lamiɗo baiyi zaton Jabeer zai samu fitowa masallaci ba,
Shiyasa limamin dake jansu salla in baya nan ya fito ya jasu salla,
yayinda Jabeer ke cikin sahun forko.

Wannan yasa mutane sukayi zaton ciwon ne yayi tsamari bai samu ya fitoba.
Ana idar da salla kuma ya fito yayi cikin gida sabida.
Fushi yakeyi da wannan tsohon ya sani in ya tsaya kuma zai dameshi da wata
falsafarshi da zaici karo da addini.

Ƙarfe takwas dai-dai. Barrister Kamal da Ya Jafar, da kuma Baba Basiru ne zaune
dashi a falon shi.

Suna zaune anan Jalal ya shigo cikin yanayin damuwa yace.


"Hamma Jabeer, Umma na falo tazo dubaka da jiki."
Cikin yamutsa fuska yace.
"Wacece hakan?".
Cikin fusata Baba Basiru yace.
"Ashe uwarka ma bazaka santa ba, ina dai baka san wacece Umma ba".
Wani irin kallon ido cikin ido Sheykh yayiwa Baba Basiru,
sai kuma ya ɗora ƙafarshi ɗaya kan ɗaya, cikin ƙasaita ya kalli Jalal tare da
cewa.
"Mene Umman!?". Ya sani sarari Gimbiya Saudatu ake cewa Ummu .
Gyara tsayuwa Jalal yayi tare da gyara zaman belt ɗin ƙugunshi yace.
"Matar tsohon Galadima marigayi, Baba Muhammad ce Ummar Gimbiya Saudatu."
Da sauri Baba Basiru yayiwa Jalal daƙuwa tare da cewa.
"Kan uwarka hegen yaro ɗan shila".
Shi kuwa Jabeer ƙafarshi ya fara kaɗawa.
Barrister Kamal kuwa ido ya zubawa Fuskarta Jabeer da Jalal. Cikin sanyi da
tausasan laffuza yace.
"Jabeer tashi muje ka gaisa da ita tunda ta taso tazo har nan dubaka da jiki".
Kanshi ya gyaɗawa Barrister Kamal ɗin wanda suke cewa Baba Kamal wanda yake
mahaifin Sulaiman, sa'an Jabeer.
Da hannu yayiwa Jalal alamun yaje yace, yana zuwa.
Shi kam Baba Basiru bayan Jalal yabi.
A babban falon suka zauna shida Gimbiya Saudatu da Laminu da kuma Baba Nasiru.

Jalal, Jamil, Haroon, Jafar, kuwa duk suna can Dinning area kan dinning table
sunayin breakfast.

A jere suka fito falon shida Barrister Kamal.

Suna isowa tsakiyar falon.


Cikin wani irin taku mai cike da ƙasaita da rashin tsoro.
Ya kalli Gimbiya Saudatu dake zaune bisa kujerar zamanshi.
Yatsunshi biyu ya haɗa ya kaɗa mata tare da mata alamun tashi min kan kujera.
Cikin wani irin kallo mai nuna tsantsar fushi da tsana da zazzafan ƙiyayya ta fara
mgna cikin ɗaga sauti tace.
"Hegen yaro mai idanun mujiya, Ni kakeyiwa wannan iskancin dan kan uwar..!".
Kasa ƙarisa zagin da tayi nufin yi tayi jin yana cewa.
"Kan uwarki ko? Ki ƙara sa mana kikaga ikon wanda ya hana mata gemu ya baiwa maza!
Maza tashi min kan kujerar zama tunda ba wancan jiɓeɓɓen tsohon akun bane seyota".

Wani irin zabura Baba Nasiru yayi tare da ɗaga hannu zai kifeshi da mari, kamar a
mafarki yaji an riƙe mishi hannunshi da sauri ya juyo.
Ido ya zaro cike da mamakin ganin wanda ya riƙe mishi hannunshi cikin tafasar
zuciya da ƙuna yace.
"J....."

By
*GARKUWAR FULANI*
[2/22, 8:23 PM] +234 906 805 8984: Cikin wani zare ido na masifa yace.
"Jalal ni ka riƙe wa hannu".
Shima idon ya zare tare da cewa.
"Ba iya rikeshi kaɗai zanyi ba, in dai zai taɓa lfyar ɗan uwana a gaban idona,
datseshi zanyi gaba ɗaya in wurgar". Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da yarfa
hannunshi.
Wani irin asirtaccen murmushi Barrister Kamal, yayi tare da kallon ɗan shi Sulaiman
hannunshi ya dunƙule ya jinjina wa Sulaiman ɗin.
Kana suka koma suka zauna bisa kujera.
Shi kuwa Jabeer hannun ya nunawa Gimbiya Saudatu alamun ta tashi.
Mirtsitsi tayi tare da gyara zamanta.
Wani irin firgitacen tsawan da Jalal ya danna matane yasa, ta miƙe tsaye ba tare
datasan ta miƙa ɗin ba.

Cikin ƙasaita Jabeer ya baza tattausar al'kyabbar jikinshi,


Kana ya matso ya zauna bisa kujerar ƙafarshi ɗaya ya ɗora bisa ɗaya.
Gyara hiramin kanshi yayi tare dayin gyaran murya kana ya kalli ƙannen mahaifin
nashi kauda kanshi yayi ganin yadda suke wani irin cika da batse sun cika sunyi
tamtsan da fushi.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu zama tayi a kujerar dake kallon tashi
kujerar.
Itama ɗaura ƙafa ɗaya tayi kan ɗaya.
Cikin iya tijara ta watso sabbin jaridu gabanshi.
Jaridar bankaɗa da kuma kamfanin jaridar hantsi wato leƙa gidan kuwa.
Murmushin muguntan tayi tare da cewa.
"Ga sakamakon sa insa da kayi dani jiya, na yau kuma shima yana nan tafe.
Nayi maka murna darajar labarin ya kai matsayin da shine a shafin forko na
jaridun".
Da sauri Jalal ya sunkuyo yasa hannunshi ya ɗauki jaridar banƙaɗa.
Jiki na tsuma ya ɗago ya kalli Gimbiya Saudatu cikin tashin hankali yace.
"Wannan ƙarya ne, da babu jahilin da zai yarda dashi, wlh bazaku taɓa cin nasara
ba."
Hankali a tashe ya miƙawa Haroon jaridar tare da cewa.
"Ya Haroon gani zancen banzan da aka rubuta kan hotunan Hamma."
Da sauri Haroon dake sauƙowa kan stpes ɗin sauƙowa falon daga dinning area,
ya ƙaraso. Hannuyasa ya amshi jaridar.
Wani irin azabebben zufane ya fara keto mishin ganin abinda aka rubuta a jikin
jaridar.
Jin jikinshi na rawane ya sashi zama kusa da Sulaiman.

Ummi kuwa dake tsaye a dinning area tana haɗawa.


Jafar abin da zaici, gaba ɗaya ido ta zubo musu cikin taraddadin me aka rubuta.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu wata iriyar shaƙiyiyar dariya tayi tare da cewa.
"Ya haka dai ƴan kanzagi, ku bawa shi uban gidan naku, jaridar yage me aka rubuta,
daga nan sai inga bakinshi da baya mutuwa da bada amsa ko zai iya cewa wani abu."
Baba Nasiru da Baba Basiru, ma fuska cike da farin ciki suka zauna.
Laminu kuwa miƙewa tsaye yayi tsakiyar faffaɗan falon cikin ɗaga sauti yace.
"To tunda bazaka iya bashi ba, bani ni in karanta mishi."
Yana ƙarishe mgnar yasa hannunshi ya amshi jaridar.
Cikin ɗaga sauti ya fara karanta rubutun dake rubuce a ƙasan hoton da gefe da
gefenshi.

"Abun kunya, ya baiyana jikan sarki Nuruddeen Bubayero ɗaga Habibullah,


Yayiwa ɗiyar Fulani fyaɗen da yasa.
Hanun Sarki Lamiɗo ya kama hannun Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero
wanda yake limamin masalacin ƙofar sarki ya miƙa shi ga hukumar addini musulunci.
Gashi anayi mishi bulalin haddi kamar dai yadda Musulunci ya wajabta.

Wani irin murmushi Jabeer yayi, hannunshi yasa ya shafa tattausan gemunshi.
Cikin rashin karaya ya kalli Haroon cikin nitsuwa yace.
"Ɗan wannan abun ne kuke zaton zai kashe wannan bakin nawa da yake rayuwa da
ambaton Allah!?
Shin ko kun mance tsawon shekaru da dama ana fataucin rufe bakin Ya Jafar, shima
har yau baku samu nasarar hanashi ambaton Allah ba,
Duk sharrinku ya zame mushi al'khairi, tunda baya wani motsi ba tare daya kira
sunan Allah ba, ikirarin ku na ya zauce, ya tabbata kune zautattun".
Sai kuma ya ɗan kalli Gimbiya Saudatu, murmusawa yayi tare da cewa.
"Baki nafa bazai mutuba sai in nufashina ya bar jikina, batun shiga ɗakin sirri
kuma, nifa wannan abin da kuketa haƙilo a kai ba wani baƙon abun bane a wurina.
sarauta a cikin jin jikina yake."
Sai ya kuma juyo ya kalli Haroon da jikinsa yayi la'asar da lamarin su, miƙewa
tsaye yayi tare da cewa.
"Haroon wai ɗan wannan makircin nasune ya kashema jiki.
To kontar da hankalinka. Ni nan Muhammad Jabeer ƙi gudune sa gudu.
Tun kan suyi tunanin yin abu a kaina na nazarci abun."
Juyowa yayi ya kalli Baba Nasiru cikin tsareshi da ido yace.
"Kaje duk inda ake saida jarudu ka bada farashin one million akan ko wanne jarida
kaga in za'a fito maka da wannan jaridar, in bada wannan ƙwaya ɗayar kaga dai itama
kuma gata a gabana."
Cikin tarin mamaki suka zuba mishi ido.
Shi kuwa gaban Laminu ya isa cikin isa ya miƙa mishi hannunshi tare da cewa.
"Bani shi nan".
Cikin tsananin tsoro da firgici ƙarara. Jiki na rawa Laminu ya miƙa mishi. Sabida
kwarjin Jabeer ya mishi nauyi a idonshi ya kuma san artabu dashi ba daɗi.

Ita kuwa Gimbiya Saudatu wani murmushi tayi mai cike da taraddadi da al'hini da
nazarin yadda zataga bayan wannan yaron mai bakin tsiya.
Jaridar gabanta ta miƙa mishi.
Kanshi ya girgiza tare da kaɗa mata yatsarshi manuniya cikin rashin tsoro da
ƙasaita yace.
"Ba kifa kai matsayin da zaki nuna min wani abin da idanuna basu rigaya sun ganiba
ko basu san dashiba domin ke a makance kike rayuwarki, Ni kuwa nan da kike gani
idona buɗe suke ras.
Ita wannan itace tayi bayanin abinda ya faru na gsky a Rugar itace tai bayanin cewa
bulalin shaɗi akayi min bana Haddiba to sai me kuma!?".
Shiru sukayi gaba ɗayansu.
Kowa da abinda yake nazarta a ranshi sai bugawar da zuciyoyinsu keyi.
Buɗa al'kyabbar jikinshi yayi tare da kuma haɗe ta cikin fillanci yace.
"In kun gama ihun ku ficemin daga Side ɗina Dan ba haɗamu akayi ba. Kuma ku sani
(MOH ALLAH WUJI FURƊATA)."
Yana faɗin haka ya juya ya nufi falonshi.

Ita kam Gimbiya Saudatu ta cika tayi maƙil.


Baba Nasiru da Baba Basiru kuwa,
A kufule suma suka fita.
Haroon kuwa ido ya zuba musu.
Barrister Kamal kuwa murmushi yayi mai tarin ma'anoni kana shima ya fita Sulaiman
na biye dashi.

A hanyarsu ta komawa side ɗinsu ne, Gimbiya Saudatu ta kalli Laminu cikin takaici
tace
"Banza kawai me tsoron zuci me dan ya matso kusa dakaii ka wani firgita ka razana
har ɓari jikinka keyi ka miƙa mishi jaridar, da zamu iya kaita a tallata".
Wani irin wawan ajiyan zuciya Laminu yayi tare da cewa.
"Uhummmm Umma kenan wato, fa duk wannan kumfar bakin da kikeyi abinda yasa kike
yinta da jin daɗin yinta, dan wancan Jabeer ɗin bai taɓa kifa miki bari bane
shiyasa.
Wallahi Allah da ya taɓa marinki da waɗannan hannayenshi da kike ganin taushinsu
kamar na jarirai shakka babu, wlh suma zakiyi sai an yayyafa miki ruwa".
Cikin kufula Baba Basiru yace.
"Kai tafi daga nan banza mai zuciyar mata, ji abinda kake cewa kan mari ɗaya tak
daya taɓa yi maka".
Wani irin kallo Laminu yayi musu kab lokacin da suka shiga falon Gimbiya Saudatu.
Cikin rumtse idonshi sabida tuno marin da Jabeer ya kifa mishi randa yayi gangancin
zai zageshi.
Da sauri ya buɗe idanunshi cikin kara yace.
"Yesss sabida baku ya shararawa mari ɗayanba shiyasa.
Kuna sanefa mari ɗayan da yayi min. A take kunnena ya rinƙa zubda jinin da Ni dai
har yau bansan ta inda ya ɓulɓuloba, wlh Allah lokacin daya mareni kusan suma nayi,
har yau in na tuno marin sai inji kunnena yayi gummmmm".
Cikin zafi Gimbiya Saudatu ta yunƙuro zata surfawa ɗan nata masifa, sai ta kuma
komawa ta zauna jin Baba Nasiru na cewa.
"Uhummm Dafa gskyar Laminu, in dai Jabeer ya ɗauki hannun mahaifinshi to tabbas,
suna da zafin hannu mai ban tsoro,
In dai ya gado hannun Ya Habibullah to fa duk abinda suka mara wlh in dai dabbace
sai dai a matso mata da wuƙa, in kuwa mutum ne to, tabbas zai sha azaba mai raraɗi.
In jifa ne ma sukayi ma basa saɓawa saiti sai sun samu abin harinsu, in kuma
tsuntsune ko ƙananan halittu tofa in suka harba sai lahira."
Sai kuma ya ɗan tsaya ya kallesu cikin dakiya yace.
"Munada buƙatar sabon shiri, akanshi, zamuyi mgnin bakinshin nan da baya mutuwa".
Cikin takaici Gimbiya Saudatu tace.
"A duk cikin ababen da ake dangantawa dasu babu, abinda yafi cimin rai kamar meda,
zoo ɗin masarautar sade ɗin Jabeer.
Wlh duk sanda najiyo kukan Ɗawisun Masarautar da sauran tsuntsaye nakiji kamar in
je in samisu shinkafar tsuntsaye suci su mace kab ɗinsu kowa ma ya huta."
Barrister Kamal dne dake,
Jinsu ta window ɗin falon.
Ya jinjina kai tare da jan hannun Sulaiman suka tafi yana mai cewa.
"Uhum naku burin dai baza taɓa cikaba in sha Allah".
Su kuwa nan sukaci gaba da tattaunawa yadda shirunsu a kanshi zai kaya.

Jakadiyarsu kuwa saida taga fitansu ta sauƙe ajiyan zuciya.


Jafar kuwa saida yaga Barrister Kamal ya fita kafin jikinsa ya dena rawa da
karkarwa.
Shi kuwa Haroon da sauri yabi bayan Jabeer cikin sauƙe nannauyan numfashi yace.
"Wato kai bakinka bazai mutu bako."
Cikin kufula ya juyo ya kalli Haroon jin ya yace mishi irin
Abinda kullum Abba yake cemishi.
A hatsale yace.
"Eh bakina bazai mutuba ba kuma zan bar ko wanne taƙadirinba, duk wanda yace dani
tak zai samu amsa dai-dai da zancensa.
Wannan zarerriyar matarfa ta kiyayeni, kadafa ta fusatani, tam!".
Ya ƙarishe mgnar da taune lips ɗinshi.
Cikin sanyi Haroon yace.
"Nifa tsorona ɗaya Jabeer kada su cutar da kai, so dan Allah duk abinda zasuyi maka
kosu Jalal da ya Jafar kada ka tanka musu.
Yanzu wannan sharrin ya zamuyi dashi?".
Wani irin kallo yayiwa Haroon cikin sauƙe numfashin yace.
"Tuni na magance ta, na saye jaridun, tun kafin a fiddasu, shima dan ya ɗauka ne
tun kafin inji inje wurin.
Kuma gashi shima a hannun yanzu sai dai su nemo wani sharrin. Kuma batun basu
amsa, da sun gane sun dena sako Mahaifiyata a duk abinda zasuyi min da Ni dai ko
kallo basu isheni ba."
Cikin sauƙe numfashin Haroon yace.
"To Alhamdulillah Allah ya kare gaba".
Amin yace tare da zama bisa kujerarshi ta musamman wacce take kyautace ga Sheikh
Abdulkarim. Tab ɗin shi ya ɗauka ya fara wasu yan dube-duben.

Anan falonshi suka zauna, shida Haroon.


Jin muryar Gimbiya Aminatu na ratso falon ne yasa Haroon yin murmushi cikin sabo da
tsohuwar yace.
"Yauwa Gimbiyar Lamiɗo kizo kiyiwa wannan jikan naki faɗa".
Murmushi tayi mai ƙayatarwa,
a hankali ta ƙara so cikin falon ita ɗaya hadimanta suka tsaya a can babban falo da
abincin data kawo mishi.
A hankali tayi taku zuwa gabanshi gefenshi ta zauna,
cikin sanyi ya kalleta.
Ita kuwa cikin kulawa tace.
"Jabeer, ya jikin naka".
Cikin harshen fillanci yace.
"Da sauƙi".
Yadda ya bata amsa a taƙaicene yasa ta kalli Haroon tace.
"Yaci wani abu kuwa?".
Da sauri yace mata ehh.
Cikin kula tace.
"Me yaci!?."
Murmushi yayi cikin tsokana yace.
"To da sanyin safiyar nan dai an sanshi magantuwa".
Dariya ta ɗan yi tare da cewa.
"Taso kuzo kaci abinci".
Kanshi ya girgiza mata tare da cewa.
"Bana buƙatar komai, kawai ki gayawa wannan dottijon mijin naki da sufanshi baya
gaya mishi dai-dai ya gargaɗi Gimbiya Saudatu ta dena zuwa min side ɗina.
In kuwa taƙi wata ran zan bar Jalal yayi mata ɗan karen duka".
Murmushi tayi tare da cewa
"To naji taso muje kaci wani abun".
Dai-dai lokacin Lamiɗo da Galadima suka shigo.
Ɗanzagi da dogari kuma suka tsaya a can bakin ƙofar shigowa falon.

Bayan sun zauna ne Lamiɗo yace.


"Ya ƙarfin jikin?".
Rai a ɓace yace.
"Ai baka da case da raina da lfyata, ko in samu sauƙi ko kada in samu ba matsalarka
bace, tun da gani kake iyayena sun haifa maka nine dan ka bawa wasu ƙattin daji su
dakani".
Murmushi Lamiɗo yayi cikin tsokana yace.
"To wai in ban basu kaiba wa kake son in basu?".
A hatsale yace.
"Ka basu kanka mana, me zai hana kai ka tuɓe gwanjinka a zaneka, dan masifar rainin
wayo sai ka nunani, duk da tarin jikokinka da suke wurin."
Murmushi Galadima yayi tare da cewa.
"Yanzu dai jikin da sauƙi gashi, har zanar ta maidaka mataɗaci, ka fara shiri nan
bada dadewa ba za mu koma ka rama".
Da sauri ya ɗago kanshi daga kallon Tab ɗinshi ya zuba musu tare da nuna kanshi.
Ido suka zuba mishi. Shi kuwa cikin tsuke fuskarsa tamkar zaiyi ruwan jini yace.
"Ni! Ni!! Ni!!! Muhammad Jabeer Kuma a wancan garin, me zanje inyi a can, wannan
garin ko a mafarki bana fatan Allah ya gwada minshi, dan Wallahi Allah kenan duk
duniya babu garin da na tsana sama da wannan garin.
Na tsani garin bana ko son jin makamacin sunan garin. Da garin da mutanen garin
gaba ɗaya basa cikin jadawalin jerin mutanen da zuciyata zata sosu har gaban abadan
me na samu a wannan garin banda tozarci da ɓaƙar azaba."
Murmushi Lamido yayi kana cikin son jikan nashi ya dafa kafaɗarshi tare da cewa.
"A makon-nan ma kuwa zaka koma wannan garin da izinin Allah".
Mgnar Lamiɗo ta ƙarshe da yace da izinin Allah ne yasashi yin shiru.
Haka suka ƙaraci mgnarsu bai kuma ɗago kanshi ya kallesu bama bare ya kulasu.

Bayan sun tafine.


Ummi da Gimbiya Aminatu suka samu suka sashi ya ɗanci abinci.

Zuwa azahar kuwa sai ga Sarkin Musulmi Jalaluddin da Sitti.

A sashin Gimbiya Aminatu Sitti ta sauƙa shi kuwa Jalaluddin a sashin amininshi
Lamiɗo ya sauƙa.
Saida akayi sallan la'asar kafin suka isa sashin, Jabeer.
Sosai suka nuna mishi kulawa da gata,
Inda yaketa son huce haushin da yakeji a kansu tunda sune dai suka sashi yin wannan
abun a bisa dole.
Hajia Mama kuwa daɗi kamar ta goya Sittin dan kulawa da so.

Sai washe gari. Suka koma Laddi julɓe sunan jihar da nanne asalin tushen masarautar
sarkin Musulmai yake.

Mama kam hankalinta ya konta ganin jikin Jabeer yayi sauƙin sosai.

Batul kuwa babu nacin da batayiba ta samu ta ganshi ido da ido abin yaci tura.

A haka kwanaki sukayi ta tafiya, ana bawa Jabeer kula tamusamman.

Yayinda Sarkin Shaɗi kuwa yake ta tsuma bilalin Shaɗin masarautar Joɗa wanda a
ƙalla tsawon kusan shekaru ɗari biyu da wani abu. Suna binne cikin ramin tsuminsu
Wanda da dafin macijin gadin masarautar ake tsumashi.

Umaymah kuwa tana shirin zuwa duba jikin ɗan ƴar uwar tata ɗa mafi soyuwa a gareta
sama da ƴaƴan data haifa a cikinta ma.

Yau kwana biyar da faruwan abun.


Sosai jikinshi yayi ras.

Yaune kuma Umaymah ke tahowa jirgin yamma zata biyo.

Shi kuwa Jabeer zuwa yanzu ko mgnar kowarshi wannan garin ba'ayi sabida irin ɓacin
rai da yake baiyana a fuskar shi, in an mishi mgnar zuwa garin.

Allah ya sani yana jin ya tsani wannan gari tsana mai tsanani.
Yana masifar jin kunyar komawa na wannan garin da a tsakiyarshi akashi cire
suturarshi ya zauna dagashi sai boxes.

Yakanji kamar ya faɗi ya mutu in ya tuna garin.

Ƙarfe biyar dai-dai motocin da suka ɗauko Umaymah suka iso cikin harabar
masarautar.

Dai-dai lokacin kuma Hajia Mama da Batul suna gab da shiga sashin Jabeer,
A tsakiyar falon sukayi kiciɓis dashi. Yana sanye cikin tufafin da sune suturarshi,
al'kyabbar ruwan madarace, sai kayan dake cikin al'kyabbar su kuwa ruwan bonbitane,
yayi wani irin masifar kyau, sai ƙamshi yake bazawa tako ina.
Fuskarshi ta fito ras cikin hiraminshi ruwan madara,
Wani irin ƙyalli da sheƙin kyau yakeyi.
Duk da ba murmushi a kan fuskarsa amman ana iya gano tsantsar farin cikin da yake
ciki.
A hankali yake taku, Ya Jafar na biye dashi a baya,
Cikin tarin kula da nuna soyayyarsa Hajia Mama tace.
"Masha Allah, Ɗan Umaymah yayi kyau, ga farin ciki ya wadaci kekyawan fuskarnan
taka".
Kanshi ya ɗan kauda ya kalli Ya Jafar daketa jan hannunshi su fita, cikin nitsuwa
yace.
"Sun isoma".
Cikin jin daɗi tace.
"Eh haka dai Jamil ya gaya min".
Ta ƙarishe mgnar tana juya baya tare da Batul da cikin sanyi tace.
"Ya Jabeer ya jikin?".
Cikin jan gajeren tsaki yace.
"Lfyata lau".
Murmushi tayi sabida jin zazzaƙar muryar shi.

A tare suka fito su Mama na gaba shida Jafar suna baya.

Suna fitowa harabar Side ɗin shi.


Motarshi da Sheykh Abdulkareem yasa aka taho mishi da ita wacce bai taɓa
hawantaba, asalima gani yake tamkar almozzaranci ne,
sai yau ya bawa Haroon key ɗin ta yace a ɗauko mishi Umaymahnshi, shi bazai je
ɗaukotaba sabida.
Lamiɗo yace bazai fitaba.
A hankali ya tsaya ganin hancin motarshi ƙirar Mercendes benz maybach Exelero wacce
ta kai kimanin $8 million dollars.

Da sauri ya ƙarasa jikin motor. Hajia Mama na biye dashi.


Yana isa inda suke yasa tattausan hannunshi ya buɗe marfin motar.
Karo na forko da naga murmushi a fuskarshi, cikin tarin shaƙuwa da kulawa yace.
"Marhababuki ya Umaymah, ta faddal".
Wani irin murmushi Umaymah tayi cikin tsantsar so tasa hannu ta kamo hannunshi daya
nuna mata alamun ta fito.
Wani irin yalwataccen murmushi mai nuna tsantsar jin daɗi ya kumayi lokacin da yaji
tasa hannunta tsakiyar kanshi.
Da sauri ya rusuna a bakin motar cikin sanyi ya manna kanshi da guiwowinta dake
zuro woje,
kanshi ta shafa tare da cewa.
"Allah yayi maka al'barka ya kare mana kai da kariyarsa mai tarin yawa ya iya
maka abinda idonka baya gani".
Amin Amin, su Haroon da Jalal, Jamil, Hibba, ƙanwar Haroon, da kuma Imran,
Sulaiman, Aunty Juwairiyya dake kusa da Umaymah.
suka amsa tare da murmushi a fuskokinsu.
Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya tashi kana ya buta hanya ta fito.
Tana fitowa Hajia Mama ta ƙara so gareta cikin tarin baiyana jin daɗi ta ruggume
Umaymah tare da cewa.
"Ta ɗanki kawai kikeyi, mu har mun kusa mu bushe a tsaye".
Murmushi Umaymah tayi tare da cewa.
"Afwan ya Aunty kin san in Jabeer na yana wuri bana ji da ganin kowa sai shi".
Haroon ne ya taɓe baki tare da cewa.
"Uhumm ai mun saba ganin wariyar launin fata".
Hannunta tasa ta ɗan zunguri Haroon tare da cewa.
"Kishi".
Jamil ne ya ɗan kallesu lokacin da suka ɗunguma suka nufi Sade ɗin Jabeer cikin
tura baki yace.
"Allah ko Mama kada ki bari Umaymah ta sauƙa a sade ɗin Hamma in dai ba sade ɗinmu
zata sauƙaba Muda muke ƙanana sai ta sharemu saishi.
Tunda hakane ta sauƙa side ɗinkin".
Cikin dariya Umaymah ta juyo da sauri ta kalleshi tare da cewa.
"To Jamil harda kai, wato kaima ɗan team ɗin Haroon ne ko?
To sha kuriminka Aunty bazata shiga tsakanin uwa da ɗaba, ko Hajia Mama?".
Ta ƙarishe mgnar tana kallon Hajia Mama daketa murmushi cikin jin daɗin tace.
"Haka kuma ɗa bazai shiga tsakanin ya da ƙanwaba,
Gaba ɗaya Jabeer ya kwace mana ke".
Murmushi mai kama da dariya sukayi gaba ɗayansu lokacin da suka shiga cikin falon.

Shi dai Jabeer sai murmushi yakeyi.


Ya Jafar kuwa in yaga Jabeer na murmushi sai shima ya ɗanyi murmushi.
Aunty Juwairiyya ce ta ɗan kalli Batul dake gaida Umaymah sakin fuska tace.
"Matar ƙani yau tun safe ban jikiba".
Wani irin murmushin jin daɗi tayi Allah yasani in Aunty Juwairiyya tace mata matar
ƙani tana jin daɗi.
Cikin happy tace.
"Yau a kitchen na wuni inayiwa Umaymah girkinsu na larabawa".
Murmushi Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Yo ai na rigaki, dama girkin bare bari kikayi mata".
Kanta ta ɗan juya takalli Sheykh Jabeer dake zaune kusa da Umaymah, in zaiyi mata
mgna sai ya juya harce zuwa larabci.
A ranta take addu'o'in Allah ya nuna mata ranar da zata zauna kusa dashi haka a
matsayin abar sonshi.
Tattausan Lips ɗin shi masu kama da kunnen fure ta kalla.
sunan jazir sai sheƙi sukeyi a cikin tattausan sajenshi da gemun tamkar an shafa
musu mai.
Allah ya sani randa ta samu lips ɗin nan a matsayin mallakinta, tabbas sai ta kusan
haɗiyesu.

Hajia Mama da kanta da ita da Aunty Juwairiyya ne suka rinƙa kawowa Umaymah
abubuwan motsa baki yaran yar uwarta na zagaye da ita, Hibba ce yar autarta ta ƴar
kimanin shekaru 16 kalli Jabeer cikin cikin sanyi tace.
"Hamma Jabeer Aunty Jazrah tace in gausheka, wai yaushe zamuje".
Kanshi ya juyo ya ɗan kalli Hibba cikin son yarinyar yace.
"Hibba auta yaushe kikeso muje".
Da sauri tace, sai na tambayi Aunty Jazrah".
Murmushi yayi kana ya kalli Aunty Juwairiyya yace.
"A shigar mata da kayanta, a ƙara gyara mata masauƙinta, yafi fadar Jalaluddin
kyau".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Shi kuwa Sheykh Jabeer kamar ba shi yayi mgmar ba.
Ita kuwa Umaymah da Hajia Mama hararanshi suka ɗanyi tare da cewa.
"Ai babu fadar da zatafi fadar shi kam, shinefa gatanka".
Murmushi ya ɗanyi tare da cewa.
"A a kam Allah ne gatana, shi kuma da yake son ayi ta ɗimata".
Juwairiyya kanta tayi mamakin sakewar Jabeer sosai
Duk wanda ya ganshi zaiga tarin farin ciki tare dashi.

Nan dai suka zauna akayi ta hira.

Saida aka kira magriba ne, duk suka miƙe sukaje sukayi al'wala.

Batul kuwa tafi kowa farin cikin, zuwan Umaymah ko ba komai ta samu ganin Jabeer
yadda take so.

Bayan an idar da sallan isha'i ne suka dawo masalacin.


A nan bisa dinnin area. Suka zauna nan sukaci abinci.

Koda suka gama ne, sunata hira a falon harda Jakadiyarsu.


Jabeer ne da yanzu ya fito falonshi cikin nitsuwa yace.
"Kai dan Allah ku barta ta huta mana".
Sai ya kuma ɗan kalli Umaymah tare da cewa.
"Umaymah muje ki gaisa da Lamiɗo, ya kirani yanzu yanata min ihu a kunne wai yaji
kin iso tunda yamma kuma ban kai mishi keba".
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
"To muje".
Hibba ce ta tashi da nufin binsu sai kuma ta zauna, jin Jabeer nace mata.
"Zauna Hibba saida safe kuje da Jalal."
Sai ya kuma kalli Jakadiyarsu cikin taushin murya yace.
"Ummi muje".
Itama da sauri ta miƙa.

A tare suka fito yana gaba Umaymah na binshi,


Jakadiyarsu na bayansu.
Suna tafe cikin jin daɗi ko ina yayi lib sai sanyin korayen ciyawi da furannin da
dogayen bishiyoyin gwanda da ayaba da sukayiwa ko ina ƙawanya.

Suna isa ƙofar Gimbiya Aminatu da sauri.


Sallama ya basu hanya, wanda a ƙa'ida sai ya shiga ya nemawa mutun izinin shiga
kafin ka shigo.
So amman Jabeer baida hijabi da sashin kakanin nashi,
shiyasa kai tsaye suka wuce.
Shiru babban falon babu kowa.
Haka yasa suka wuce sashin Lamiɗo, a hankali yayi sallama,
Cikin murmushin Lamiɗo ya amsa sallamar tare da cewa.
"Bismillah, ku shigo".
Kusan a tare suka kutsa kai cikin tamfatsen falon nashi.

Wani irin kallo sukayiwa juna,


Ganin...!

By
*GARKUWAR FULANI**MEVYASA? ME YAYI ZAFI SHI BA WUTABA? ME RIBARKU A
CIKIN FIDDA LITTAFINA WOJE KU WATSASHI WA DUBBAN MUTANE? ME FA'IDAR HAKAN? NIYARKU
KO TUNANIN KI, KADA WASU SUZO SU SAYA NE? A ZATONKI DANKU DAN KU ƁATA MIN RAINE? KO
KUNA ZATON ZAKU HANANI SAMUN BINDA ALLAH YA RIGADA YA ƘADDARA YA RUBUTA RABO NANE?
Nayi matuƙar mamakin al'ummar Annabi, Ni a zatona a iya hasashena, idan mace dan
Allah da Manzonsa da darajar iyayen na kai ƙololuwar makurar roƙonda duk musulmi
zai yi min al'farmar abinda na roƙa! Sai dai abin tsoro ashe abin ba haka bane, to
wannan abun shine kadai ya bani tsoro, lallai kam tabbas muna akiruzzaman. Ai na
sani kuma kuma mutanen kirki waɗanda kuka sai littafina da zuciya ɗaya kun sani
dole za'a fitar da littafi. Sabida ba kaina farauba kuma ba kaina ƙarauba. Sabida
haka kuyi haƙuri, dan Allah kuyi haƙuri, kuyi haƙuri da abinda wasu daga cikinku
keyi. Alhamdulillah tunda na'annabi basa ƙare wa, tunda har gobe saya akeyi, wasu
suna ganin gana satan a gabansu, amman sai su kauda ido suzo gareni su biya kuɗinsu
a sasu a group ina godiya gareku*

Bayan Allah da Manzonsa da darajar iyayen dana haɗa mutane dasu bani da wani tsumi
ko dabarar tsira daga sharrin masu zuciyar da basu san girman Allah da Manzonsa da
darajar iyayensu ba. Domin duniya gaba ɗaya tana fama da gubar irin waɗannan. Iya
tsaro dai kamar na bankuna, to amman me ana samun masuyin kutse a ciki har suyi
sata. Manyan kampanunnuka na duniya ma suna fuskantar ɓarayj yan kutse, hakama ƴan
Film suke fama da wannan matsalar, to mu ma rubuta suwaye mu da zamu tsira dasu,
Roƙona anan dan Allah da Manzonsa abar maimaita mgnar a cikin groups ɗin GARKUWA.
Su masu fitarwa dai na fita haƙƙinsu tunda inai musu posting sau biyu a rana kamar
yadda na faɗa, su sukaji suka gani suka fitar, to wannan can musu. Ina da mutanen
da nake matuƙar ganin kimarsu da darajar su a SPG shiyasa, bazan tanka musuba.

*Fatan al'khairi VIP groups ƴan dari uku ina al'fahari daku, kun bawa maras ɗa
kunya, shiyasa tun forko nace Ni kune VIP na, duk da nasan kuma ɗin a cikinku
tabbas akwai masu fiddawar, to amman dai naku baya zama illa kamar na SPG. Ina
yinku ɗari bisa ɗari.*

Wlh rubutu yafi sauƙi akan mu'amalat da wasu taƙadiran da yake jarabtan marubuta da
mgna dasu, ya ilahi ya mujibadda'awati, kai ina jinjina muku marubuta fama da wasu
mutanen, wato da a haɗaka mgn da wasu gwara kawai a baka renon shanu garke guda na
wuni ɗaya, domin shi dabba yasan abinda ake kira da makiyayinsa, amman wasu mutanen
basu san darajar Allah da Manzonsa ba bare iyayensu. Allah ya kyau. Allah ka haɗamu
da mutanen kirki.

*Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan layin
09097853276, ko ki turo dubu ɗaya ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu
Garkuwa, sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276.*

*Zan ƙara roƙo ba domin irinku kangararruba a a sai dan masoyan Allah da Manzonsa,
dan Allah kada ku fitarmin da littafina. In kin san kin sayane dan ki fitar min da
littafina to dan Allah da Manzonsa kizo kimin mgn ta pc kice kawai GARKUWA bani
kuɗina bazan iya saya ban fitarba, wlh Salim alim zan meda miki kuɗinki in biki da
godiya, in kuma baki sayaba zaki saya dan ki fiddane dan Allah kada ki saya. Dan
Allah in kin rigada kin saya kuma Please turo ac no ɗinki kawai kadama kiyi mgnar
kamai a take zan meda miki kuɗinki in cireki in miki godiya🙏🏻*

Lamiɗo da Galadima da Sarkin Shaɗi. Bisa alamu wata mgna mai mahimmanci suke
tattaunawa.
Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Umaymah cikin kulawa yace.
"Khadijah lale da zuwa Masarautar Joɗa."
Da sauri Umaymah ta ƙarasa gabansu, cikin ladab ta zauna gabanshi tare da duƙar da
kai tace.
"Allah rene Barka da dare".
Kanshi ya jinjina irin na sarakuna kana yace.
"Barka dai Khadijah kinzo lfy, ya Sarki Aliyu?".
kakan Haroon kenan wanda ya haifi baban shi.
Cikin girmamawa tace. "Yana lfy yace yana gaidaka".
Kanshi ya jinjina, kana ya ɗan kalli Jabeer dake danne-danne a wayarshi.
Ya hakimce ya ɗaura ƙafa ɗaya kan ɗaya.
Jakadiyarsu kuwa tayi shiru a gefe kusa dashi.
Galadima da Sarkin Shaɗi kuwa, murmushi sukeyi suna kallon Jabeer.

Gyaran murya Lamiɗo yayi kana cikin dattaku yaci gaba da cewa.
"Ina amsawa, ya kika samu jikin ɗan naki?".
Cikin murmushi ta juyo ta kalli Jabeer kai ta rusunar ganin samfa hankalinshi baya
kansu cikin yin ƙasa da murya tace.
"Alhamdulillah na samu jiki ya worke!".
Galadima ne wanda yake ƙanine ga baban Lamiɗo ya amshi zan da cewa.
"To sai ki sanar mishi batun komawa Rugar Bani, dan ramuwa bisa cika ƙaidar..".
Shiru yayi bai ƙarisaba jin muryar Jabeer yana cewa.
"Ƙa'idar Allah da Manzonsa ne da zai zama dole sai an cika, ba ƙa'idar wani zalumci
da tozarcinba".
Kanshi ya ɗan tanƙwara a wuyanshi.
Kana ya zamo kaɗan ya zauna gaban Umaymah cikin nuna rauninshi yace.
"Ayyah Umaymah kada kice min inje, Please Umaymah ki fahimci wannan abunfa al'adace
ba addini ba, kuma abune da kai tsaye zamu iya ce mishi makaruhi in ma bamu
haramtashi ba, ya za'ayi inje in sake tuɓe kayan jikina a gaban duniya wai dan in
daki wani. Ni bana so.
Ba dai sune suka kainiba, suka kuma ce a dakeni, to dan me zasu buwayeni da sai
munje na rama".
Haɗe fuska Umaymah tayi cikin kafeshi da ido tace.
"Ni bana iya yiwa iyayena musu. Jabeer tabbas na sani al'adace ba addiniba, amman
ka sani duk wani abun da zakaga ya faru a duniya to akwai dalilin faruwarshi, kada
kace zaka tsananta bincike tabbas lokacin zai baiya mana dalilin.
Bana son gardama kawai kaje Dan ALLAH".
Hannunshi yasa ya dafe kanshi,
kana yayi shiru Umaymah ta gama dashi da tace dan Allah, ya sani tabbas da a
madadinsa Ayyah ɗin da yace forkon mgnar da ya mata da ya rigata cewa Dan Allah da
shike nan yasan zatayi shiru.
Shi kuwa Lamiɗo murmushi yayi tare da kallon Umaymah cikin jin daɗi yace.
"Allah ya miki al'barka".
Da sauri tace.
"Amin ya Allah".
Galadima kuwa, murmushi yayi tare da jinjina kai.
Jakadiyarsu ma cikin jin daɗin tasirin mgnar Umaymah akan Jabeer take murmushi
sabida ta sani.
Shi mutunne mai kaifi ɗaya, in yace eh tofa eh ɗince inko yace a a to a'ance.
Especially baya son duk wani abu da zaici karo da addininshi.
Kanshi ya jinjina Umaymah alamar shikenan idonshi yayi jazir alamun dole akasashi
yin abinda baya so.
Kana ya kalli kakarsa dake murmushi tsuke fuskarsa yayi tare da cewa.
"Gimbiya Aminatu muje ki bani gashin da kikayiwa Lamiɗo".
Cikin dariya Gimbiya Aminatu tace.
"Iye gashinsama zan baka?".
Da ƙarfi yace.
"Eh shi zaki bani, ai in dukane kam ya iya zille kanshi ya turani.
Shine dan gashinsa zakice iye".
Murmushi tayi tare da bin bayanshi,
ganin Lamiɗo na mata alamun taje ta bashin.

Nan sukaci gaba da hira, suna tattauna wasu mahimman al'amuran da sirrine garesu
iya su biyar.
Wato Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, Umaymah, Jakadiyarsu.
Bayan su babu wanda suke yarda da sanin sirrin Jabeer.
A hakanma kuma a suɗinma akwai wani sirrin da babu wanda ya sanshi sai Lamiɗo da
Umaymah.

Suna zuwa har falonta suka wuce.


Wani kekyawan akoshi mai masifar kyau ta ɗauko mishi.
Ta ajiye a gabanshi.
Inda yake zaune a ƙasa bisa carpet ya naɗe sawunshi.
fork ɗin dake saman fefeyin ya ɗauka.
Daddageggen gaseshen jan namane wanda yaji wuta ya gasu gashin tukunyar ƙasa yayi
tiɓis.
Sai wani irin ƙamshi na musamman yakeyi,

A hankali yake sa Fork ɗin yana yagan tattausan tsokokin yana sawa a baki.
Ita kuma tana zaune gefenshi.
Tafashesshen madaran shanu mai ɗan ɗumi ta miƙa mishi a wata ƴar ƙwarya mai kyau.
Taune naman yayi tare da haɗiyewa kana cikin zuba mata ido yace.
"Dole sai na karɓa da hannun nane? Ki ajiye mana.
Da wanne hannun zan amsa tunda inacin abinci dana daman".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Dole sai ka amsa, bazan baka shi a ƙasa".
Kanshi ya ɗan rausayar tare da cewa.
"Allah ya nuna min ranar da za'a bar.
Wannan tsare-tsaren shamfi na masarautar Joɗa. Komai da ƙaida da yadda ake
yinshi".
Ita dai miƙa mishi ƙwaryar takeyi dole ya ajiye spoon ɗin yasa hannunshi ya amsa.

Nan suma sukaci gaba da hira.


Sai kusan sha ɗaya Umaymah da Jakadiyarsu suna fito.
A nan Gimbiya Aminatu ta ajiyesu suma saida sukaci gashin nata kafin suka tafi.

Kafin su isa Side ɗinsa dai sha biyun dare tayi.

Haka yasa suna isa suka samu ba kowa a falon.

Sai Haroon da suke jiyo muryar sa, a falon Jabeer.

Cikin nitsuwa ya matso kusa da Umaymah a hankali yace.


"Sai da safe Umaymah kiyi bacci ki huta."
To tace har ta juya zata tafi sukaji Muryar Haroon yana cewa.
"Abba yazo wurinki zaku gaisa bai samekiba, nace mishi kun tafi wurin Lamiɗo yace,
to saida safe ya gaidaki da hanya Hajia Mama ma yanzu ta fita, tace Lamiɗo ya riƙe
mata ƙanwa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"To Allah ya bamu al'khairi saida safen".
Amin Amin suka ce.
Kana shida Haroon suka wuce Side ɗinsa.

It's kuma Umaymah da Jakadiyarsu suka wuce.


Side ɗin da kullum in dai Umaymah tazo nan take sauƙa.

Suna shiga suka samu, tuni Hibba tayi bacci, wannane ya basu damar tattauna wasu
mahimman sirrukansu.

Nisawa Umaymah tayi bayan ta saurari jawaban Jakadiyarsu Jabeer cikin tsantsar
tafasar zuciya da tarin baƙin ciki tace.
"Uhummm suyi dai Ni nan ina dai-dai- da ƙugun ko wanne shege da shegiya,
In sha Allahu zasusha mamaki.
Zasuga yadda Ubangiji ke ikonsa, ban cire raina ƴar uwarta zata sake rayuwar enci
da salama, da izinin Ubangiji zataga sakayar waɗanda suka cutar da ita da yaranta a
gaban idonta.

Cikin zubda hawaye Jakidaya tace.


"In sha Allah, sai farin ciki ya dawo, a sashinta, inata addu'a a kullum a cikin
dukkan sallolina, Allah ya kare ahlinta, ya kuma baiya gsky tayi halinta kowa ya
gani".

Amin Amin Umaymah tace tare da share hawayenta.

Washe gari ranar Alhamis. Ta kama yau kwana shida da faruwar gasar Shaɗi, kana
gobene za'a koma dan ramuwa,
A goben kuma zai cika kwana goma da kisan gilla da kafurai ƙabulun Ɓachama sukawa
Fulanin Rugar Bani.

Misalin ƙarfe sha biyu na safe.


Fadar Sarkin Nuruddeen Bubayero Joɗa, cike take maƙil da tawagarsa kama daga.
Galadima, Waziri, Wambai, Dan buram, Dan iya, Ɗan isa, Ɗan Kade, Sarkin fada,
Sarkin yaƙi, Sarkin Dowaki, Sarkin Gabas, Sarkin Kudu, magayaƙi, Jarma uban doma,
Makawa Ɗurɓi, Turaki, Da dai sauran members ɗin masarautar baki ɗayansu, an cika
anyi maƙil.
Sallama na tsaye can bakin ƙofar shigowa.
Dogari kuma suna tsaye gefen hagu da daman Lamiɗo.
Suna rike da mafici sunayi mushi fifita, ɗanzagi kuma yana gefe,
Kana wasu fadawan duk suna gefen.
Gyaran murya Lamiɗo yayi tare da gyara zaman shi cikin shugarsa ta sarakuna masu
al'farma, a hankali yace.
"To da farko dai fatan duk kowa na lfy".
Da sauri Ɗanzagi yace.
"Sarki ya gaisu yana yi muku fatan alkhaiy".
Sai ya kuma juyo ya kalli Lamiɗo tare da cewa.
"Godiya suke."
Kanshi ya ɗan jingina da tattausar kujerarsa da masu son gadonta sunfi a ƙirga,
cikin ƙasaita yace.
"Kamar dai yadda muka tattauna, kwanakin baya akan sarkin Garin Shikan,
to yanzu zan zantar da hukunci.
Sarkin aike na bada umarni kaje garin Shikan ka karɓo min sandar sarautar Shikan ka
kawo min shi, yau ɗin nan.
Kaje da jagorancin Galadima, da Matawalle da Makawa, sai sarkin yaƙi".
Da sauri duk suka runsunar da kayu kansu tare da cewa.
"An gama".
Nan take kuwa suka miƙa suka tafi.

A cikin gida kuwa. Tunda asuba da Jabeer da tawagar ahlinshin suka dawo masallaci.
Kai tsaye ɗakin Umaymah ya nufa, suna biye dashi a baya.
Bisa sallaya suka sameta riƙe da al'ƙurani mai girma tana karatu cikin tsananin
nitsuwa.

Ganin hakane duk suka fito falo.


Nan Aunty Juwairiyya taja Ummi suka tafi side ɗin ta da Hibba da ƴar aikinta suka
shiga kitchen.

Jalal kuwa shine yaje wurin Ya Jafar, don bashi mgni kamar yadda Jabeer ya
umarceshi.

Jamil kuwa waya yakeyi da sabuwar budurwarsa da ya samu.


Wacce yake masifar sonta,
Ko yaushe suna liƙe da juna a waya.
Haroon kuwa a falon Jabeer ya zauna yana kallon lbrin CNN.

Shi kuwa Sheykh Jabeer.


A hankali ya wuce ta gaban Haroon.

Gefen gabas ya fuskanta, inda labulaye sukayiwa wurin ƙawanya.


A hankali yasa hannunshin ya yaye labulen.
Wani ƙofa ya buɗe a .
Sai ga wani ɗan siririn corridor.
Shiga yayi, kana ya saki ƙofar ta koma ta mannu da ƙofar sai dai bata rufuba.

A hankali yake taku cikin nitsuwa,


Lips ɗin shi na ɗan motsawa alamun tasbihi yakeyi.
Tafiya mai ɗan tsawo yayi sai gashi ya kuma riski wata ƙofar.
Hannunshi yasa ya murɗa key ɗin ya buɗe, ƙofar.
Sai ga kuma wata ƙofa irin ta ƙarafuna kana dai iya hango woje.
Buɗe wannan ƙofarma yayi.
A hankali ya kutsa kai.

Wani irin sassanyan ajiyan zuciya mai tsawo yaja ya sauƙe a hankali.
Idonshi ya lumshe sabida wani irin sanyi mai masifar daɗi daya ratsa mishi jiki da
zuciya.

Wani irin ɗan madaidaicin Garden Park ne mai masifar kyau.da sanyi da tsaruwa.

Daga nan bakin ƙofar daya fito ɗin.


Tayis ne fari tas a malale iya ganinka, sai gefen damanshi da bishiyoyin ayaba masu
masifar duhu da sanyi dake jere reras.
Gefen hagunshi kuma bishiyoyi mangoro ne irin yan duƙus-duƙus ɗin nan ke jere,
Reras.
A hankali yake taku yana tafe yana tasbihi.
Yana jin kukan tsuntsaye mai daɗin ji yana ratsashi.

Tafiya kaɗan yayi sai gashi ya baiyana a wani irin wurin mai masifar kyau.
Wasu yan zagayen gini dakalin bulok bibbiyu akayi a ƙalla sunfi hamsin.
A ciki ko wanne zagayen akwai bishiyar dabino. Na gabanta inabi na gaban inabi
tuppa, kana sai Yazawa, sai kuma na tsada, daga tsada sai na kanya, sai goruba da
na giginya.
Cikin ko wanne zageyen kuma ƙasanshi koriyar ciyawa ce mai sanyi.

Can tsakiyar filin kuma wata iriyar ƙoramace mai masifar sanyi,
Ruwanshi na kwance fari ƙal-ƙal bakin wurin kuma jeren bishiyoyi goibane wanda
sukayiwa kwaramar inuwa.

Gaban ƙoramar kuma wasu irin kujerun silver ne masu masifar kyau da sansi a jere a
ƙalla sun kai goma zuwa ashirin.

Can gefenshi kaɗan kuma wani shingene aka zagaye da waya.


Shuke-shuken gargajiya akeyi a wurin.

Nan kusa da ƙoramar kuma shingen farar waya akayi a cikin ta wanda akayi ƴan
ɗakuna-ɗakuna a cikin.

Tsuntsaye ne a ciki iya ganinka ko wanne da muhalli shin.

Kama daga Tattabaru farare ƙal-ƙal.


Sai kuma tsuntsu carki jajaye masu kyan launi ga kuma kanari da suke blue.
Sai kuma zabbi da suke yawo a ƙasa tako ina.
Can bakin ruwan kuma agwagin ruwa ne sunfi ɗari ƙwa-ƙwa.

Sai kuma zabbin daji.


dangin tsuntsaye dai babu irin wanda babu.

Ido ya zubawa tsuntsaye tamkar mai son yin magana dasu.

A hankali ya sunkuyar da kanshi jin tattausan gashin Ɗawisun Masarautar Joɗa da ya


kai shekaru masu tarin yawa.
A hankali ya rusuna tare dasa tafin hannunshi ya shafa dai-dai ƙunɗun Ɗawisun inda
wurin yake mai kalar blue mai kyau sabida Sheykh blue ne kalar da yafi so.
A hankali ta fara taku, ta juya mishi baya kana ta ɗaga bindinta sama samɓal har
yana iya taɓo geminshi.
Wani irin takun ƙasaita tayi kana ta buɗa fikafikinta ta bazasu, ta fara tafiya a
hankali.
Wannan itace suntsuwar da muddin mutun ba jinin Masarautar Joɗa bace, in ka shigo
mata gaba gaɗi ba tare da an gabatar mata kai ba, zatayi ta yagune mutun tana
caccakarshi.
Amman muddin dai kai jinin Masarautar Joɗa ne, kana shiga zata zo gabanka.
Tayi maka hakan.

Sai dai kuma bayan yin hakan in mutun nada wata zazzafar nasaba a masarautar misali
shine sarki maici to in tayi wannan baza fikafikinta takanyi ta zagaya sarki sau
bakwai kafin ta tsaya a gabanshi sai sarkin ya umarceta data tafi kafin zata tafi.

To babban abinda ya ƙara jazawa Jabeer matsala a rayuwarsa shine,


Duk sanda yazo gaban tsuntsuwar Ɗawisun nan sai tayi mishi wannan abin da zagaya
sau bakwai abinda a tarihin masarautar sarki kawai yakeyiwa abin.

Matsalar abin a gaban Barrister Kamal da kuma Baba Bashiru da Abba sai Lamiɗo ne ta
fara yimishi wannan abun.
Tofa ta bakin Baba Basiru ne mgnar ta zaga kunnen mazauna masarautar Joɗa.

Babban tashin hankalin masu son gadar wannan kujerar, shine yadda side ɗin Jabeer
ke kusanci da Garden ɗin da take ciki.
Tashin hankalinsu ya ƙara tsananta ne tun randa Suka ga Lamiɗo yasa an buɗawa
Jabeer hanyar shiga wurin ta cikin falonshi ba sai ya zagaya yabi hanyar da kowa ke
bi ba,
Ya zama shida Lamiɗo sune masu hanya kowa daga falonshi zai shiga wurin.

A hankali Jabeer yayi murmushi tare da kallon yadda tsuntsuwar ta gama zagayashi
kana tazo ta tsaya gabanshi tare da baza fikafikinta.
Cikin harcen Larabci yace mata.
"Fatana dai ba bauta min kikeyi ba! Domin babu wani abin bautawa da gsky sai Allah,
wanda shine ya halicce ni ya halicceki.
Ni kuma ba kowa bane face halittarsa, sai dai na kasance cikin halittarsa mai girma
da karrama fiye da komai, dan shi da kanshi yace.
Walaƙad karramna bani Adam."
Wani irin juya kai tsuntsuwar tayi kana ta meda fiffigefa ta rufe, kafin ta juya ta
nufi wani kekyawan wurin da aka ware mata, inda take tare da yayanta da mijinta.

Juyawa yayi can gefe ya hango wasu yan kyawawan tsuntsaye farare
A bakin ruwan.

Ga tattabarun sun zagaye wurin da sauran tsuntsayen.

A hankali ya zauna a wata kujera mai kamar gado.


Kishinƙiɗa yayi kana ya lumshe idonshi yana maijin yadda sassanyan iskar wurin ke
ratsashi.
Karatun al'ƙur'ani ya fara cikin sassanyan murya mai daɗin sauraro.

Umaymah kuwa tunda ta fito, sai ta nufi sashin Hajia Mama, hira sukayi sosai cikin
shaƙuwa irin ta yan uwa.

Suna zaune a nan Abba ya shigo.


Tana ganinshi tai murmushi,
shima murmushin yayi tare da cewa.
"Maman yara".
Cikin sakin fuska tace.
"Na'am Yaya".
Murmushi mai cike da zafi da ƙuna wanda ya baiyana har kan fuskarshi yayi kana ya
zauna gefenta.
Gaisawa sukayi cikin danne ababen dake cin ransu.
Hajia Mama kuwa, tuni sai hawaye take zubdawa.
A hankali Umaymah ta miƙa mata handkin dake hannunta alamun ta share hawayenta.

Bayan ta share hawayenta ne,


Abba ya miƙa tare da cewa.
"Kin gaisa da Mom Imran kuwa? Da Salma".
Fuska a ɗan haɗe tace.
"A a".
Miƙewa yayi tare da cewa.
"To muje ku gaisa."

Binshi tayi a baya suka nufi inda yace ɗin.

A falo suka samu Mom Imaran tana ganin.


Sun shigo tare da Hajia Mama tayi wani irin haɗe fuska, cikin nuna ko in kula
tacewa Umaymah.
"Yaushe kikazo?".
A daƙile tace.
"Jiya".
Kanta ta ɗan kauda tare da cewa.
"Ya hanya".
Alhamdulillah tace a taƙaice.
Cikin kufula Hajia Mama tace.
"Mu tafi".
Miƙewa Umaymah tayi kana Abba ma ya miƙa sashin Amaryarshi Salma ya nufa da ita.

Suna shiga tana jin muryarshi ta fito, da sauri ta nufe shi da nufin zata
ruggumeshi da sauri yace.
"Ga Umaymah tazo".
A take taja birki ta tsaya cikin gyatsine tace.
"Ya kike kinzo lfy, ki gaida mutan gida".
Cikin wani irin kallo Umaymah tace.
"Uhummmm kema ki gaida mutan gidanku".
Tana faɗin haka ta juya ta tafi abinta.

Hajia Mama na biye da ita.


Ita kuwa Salma tana ganin fitansu ta ruggume mijinta.

Koda suka koma Side ɗin Hajia Mama bata daɗe a nanba ta nufi sashin Gimbiya
Aminatu.

To bata fito nan ɗinba sai shabiyu saura.


Koda ta dawo Haroon da Jakadiyarsu da Aunty Juwairiyya kawai ta samu a falon.
Sai kuma Jalal da Hibba da suke dinning area suna zaune bisa kujerun Dinning table
ɗin.
Sun sa plet a tsakiyarsu da kofunan tea a hannunsu, alamun sai yanzu sukeyin
breakfast.

Cikin kula Aunty Juwairiyya tacewa Ƙanwar mahaifinta ɗin.


"Umaymah muje kuci abinci rana tayi fa".
Murmushi tayi tare da son danne ɓacin ranta tace.
"Alhamdulillah Juwairiyya Ni kuma da nakeda Hajia Mama ga Gimbiya Aminatu, ai naci
nayi nak."
Cikin sauri Jakadiyarsu ta e.
"Ga kuma Matar Barrister Kamal ma ta aiko miki abin kari.
Gimbiya Saudatu ma ta aiko miki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"A ajiye minshi sai anjima, kinga Juwairiyya kada ki shiga kitchen yau kizo mu wuni
hira abinmu, abinci tako ina zaizo".
Cikin sanyi Juwairiyya tace.
"Uhummm Umaymah ke har zaki iya cin abinci waɗanan mutane ai Gimbiya Saudatu ba
abin wuya bane tasa mana guba muci duk mu mutu.
Sai dai muci na gidan Barrister".
Kai Jakadiyarsu ta jinjina alamun eh.

Cikin ɗan ɗaga murya Umaymah tace.


"Haroon!."
Da sauri ya amsa tare da tahowa inda take.
Gefenta ya zauna tare da cewa.
"Umaymah gani".
Ba tare da ta kalleshiba tace.
"Ina Jazlaan?".
Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Y shiga Garden".
Kai ta ɗan jinjina mishi tare da zubawa Jalal ido.
Ita Hibba sai murmushi takeyi shi kuma fuskarshi kamar boss.

A hankali ta miƙa ta nufi falon Jabeer ɗin.

Da sauri ta kalli Haroon tare da cewa.


"Ina zakaje".
Baki ya ɗan tura tare da cewa.
"Umaymah inda zakije mana".
Cikin tsokana tace
"Sirri zanyi da ɗan".
Tana faɗin haka ta juya ta nufi can. Shima Haroon yana biye da ita a baya.

A hankali take taku har ta isa inda yake.


Gefenshi ta zauna tare da zuba mishi ido.
Cikin kula tace.
"Jazlaan".
Cikim nitsuwa ya buɗe idonshi tare da kallon inda tarin tsuntsayen nan suke,
Lokaci ɗaya idanunshi suka kaɗa sukayi jazir.
lips ɗinshi ya fara motsawa da nufin yin mgna amman ya gagara,
sai wani irin kuka mai ƙarfi da yake son ƙawance mishi daga can ƙasan zuciyarsa.
Hakan yasa lips ɗinshi karkarwa tamkar mai jin sanyi.
Umaymah kuwa. Tuni hawaye sun wonke mata fuskarta tana mai kallon tsuntsayen.

Ganin Haroon yasa tayi mishi alamun ya kawo mata ruwa.


Ba musu ya juya ba tare da yayi mgn ba jim kaɗan ya dawo da goran ruwa da glass
cup. Ruwan ya tsiyaya a kofin ya miƙa Umaymah.
Cikin sanyin murya tace.
"Ga ruwan sanyi kasha, nasan zakaji sanyin ƙunan da kakeji a ranka".
Ta ƙare shi mgnar tana miƙa mishi cup ɗin.
Amsa yayi yayinda gaba ɗaya jikinshi karkarwa yakeyi alamun tsananin tarin baƙin
ciki duniya.

Da kyar ya iya shan rabin kofin.


Nan ta gyara zamanta tare da kamo hannunshi ta fara tausar zuciyarshi kan abinda
tasan shine babban matsalarshi.

A garin Bani kuwa zuwa yanzu hankali ƙabilar ɓachama yayi matsifar tashi, tsoro mai
tsanani ya rufesu.
Tsoron da yasa da yawansu suka rinƙa guduwa suna koma cikin babban birnin Ɓadamaya,
Wasu kuma su tafi wasu jihohin.
Sabida sun gama tsinkewa da goron gaiyata da fulani keta raɓawa babu dare babu rana
birni da ƙauye duk inda suka san fulani na nan sai da suka aika musu goro
Wannan ne yasa mafiya yawan kafuran aran na kare.

Inda hakan ya fusata Habban Ɓacama.


Har ta kaishi ga cewa, duk ba ɓacamen da yasan tsoron fulanine ya sashi guduwa to
kada ya kuskura ya sake dawo mishi garinshi garin Shikan.
To wannan abun shiyasa wasu suka fasa guduwa, wasu da basuyi nisaba suka dawo.

To kuma kwatsam sai gashi yau an aiko an karɓin sandar sarautar Shikan dake
hannunshi
Wannan abun yasa da yawa mutanen cikin Shikan Maza da mata hausa fulani da Ɓacamawa
da sauran ƙabilu suka kuma rinƙa fecewa sabida, suna ganin yanzu dai shi kanshi
Sarki Shikan bashi da madafa bashi da ƙarfi tunda an karɓe sandar sarautar shi.

To hakane yasa, ya rinka bin ƙauyuka Especially mutanen Bonon da kewaye ya rinƙa
zugasu da ingiza su cewa, nanfa garinsu ne ya zasuyi su gudu kan Fulani.
Kuma ma suda sukeda dodon tsafinsu Bonon ai shi kadai ya ishi fulanin.
Da haka yasa duk ƙabilun Ɓacamawa na ƙauyukan basu guduba.
Sunata shirin faɗa yayinda cikin garin Shikan kuma yayi shal ko ina shiru babu
mutane.

Cikin garin Bani kuwa, iya tsoronsu da suka gani a cikin kafuran ya sasu jin daɗi
tunda gashi har suna guduwa subar garin da suke musu gadara da gori a kanshi da
cika bakin sai sun kori Fulani a garuruwansu.
To tabbas sunada nasara akan fansar da zasu ɗauka, zasu ramane dan nemawa kansu
enci.
Sun san iya sau ɗaya in sun nunawa arnatakun nan zasu iya gwabzawa dasu zasu barsu
su sarara.

Haka yasa suke jin ƙarfin guiwar yin abun.

Ba'ana kuwa yanata ƙara shirya kanshi, sabida ramuwar gasar da za'ayi.

Ya Salmanu kuwa yanzu ya fara jajir cewa, yana fakewa da jarumtar Jabeer yana
gasawa Ba'ana maganganu.

Sosai ya ƙara shigewa Shatu a mako ɗayan nan.


Kuma tana jin daɗin hakan.
Ta sake sosai.
Zuwa yanzu kuma jikin Ummey yayi sauƙi garawau sai dai har yau bata taɓa yin mgna
ba ta zama tamkar kurma.

Da dare bayan sallan isha'i,


tana zsune ita da ya Salmanu suna hira cikin nitsuwa tace.
"Ya Salmanu gobene zamuje asibiti mu dubo su Junaidu da sauran marasa lfy dake
cikin Genaral Hospital Ɓadawaya, dan naji ƙishin-kishin ɗin wai har yanzu babu
likitan daya dubasu."
Cikin gamsuwa da hakan yace.
"Eh hakan yana da kyau, kuje in sha Allah muma jibi asabar zamuyi gamgami muje,
danma goben jumma'a ne da munje tare".
Sai kuma ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Da yaushe zakuje?".
Cikin sanyi tace.
"Da safe zamuje, in anyi sallan azahar zan dawo, amman Rafi'a zata wuce
makaranta".
yace.
"To ke sai yaushe zaki koma?".
"Sai Ummey ta ɗan ƙara samun sauƙi. Ni da na so mu kaita asibiti kan batun rashin
mgnar tata.
Gyara zaman shi yayi tare da cewa.
"Wannan ba matsala bace, wlh firgici da tsoro ne yasata hakan".
Haka dai sukaci gaba da hirarsu.

Washe gari ranar jumma'a, misalin karfe sha biyu dai-dai suka fito zasu tafi
asibitin.

A bakin lambun garinsu sukayi kiciɓis da Ba'ana nan ya tsaidata dole suka zauna.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa,


Lamiɗo, Galadima, Sarkin Shaɗi, da Jabeer ne tafe a hankali suka shiga cikin Garden
ɗin nan.
Ta gefen Lamiɗo, suna shiga suka nufi inda katon curin dake wurin shekara da
shekaru.
Shi dai Jabeer binsu yakeyi baiyi magana ba,
Koda suka isa wurin zama sukayi dabas a ƙasa.
Dole shima ya zauna, cikin sanyi Lamiɗo yace.
"Assalamu alaikum Jaimi".
Da mamaki Jabeer ya kalleshi,
Hiraminshi ya gyara tare da cewa.
"To yau kuma".
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya rufe mishi bakinshi.
Hannunshi yasa ya janye hannun Galadima tare da cewa.
"Yo ai ba sai ka rufe min bakiba, in kace nayi shiruma zanyi, sai dai ina naga abin
saɓon Allah ko tsireni za'ayi sai na faɗa".
Dafe kai Galadima yayi tare da tsuke fuskarsa.
Ganin haka ya taɓe baki tare da ɗaga kafaɗunshi ya ɗan buɗasu alamar, ban damuba.

Sarkin Shaɗi kuwa bai kallesu bama.

Wani irin zabura Jabeer yayi cikin tsananin firgici da kaɗuwa lokacin da yaga wani
irin h ....!

By
*GARKUWAR FULANI*Ganin wani irin hayaƙi fari tas yana fitowa, tako
wacce ƙofa na jikin curin.
Da sauri Galadima yasa hannunshi ya kamo hannun Jabeer yaja da ƙarfi.
Alamun ya nitsu ya zauna, cikin mamaki ya zubawa tarin hayaƙin dake bulbulowa daga
ƙofofin ramin shirgegen curin.
Su kuwa ga ɗayansu hankali konce suke zaune.
Ido ya zuba musu tare da cewa.
"Me hakan?".
Da sauri Lamiɗo ya girgiza mishi kai hakanne ya sashi jan gajeren tsaki tare da
cewa.
"Nifa ba son wannan soki burusun naku da surkunlenku nakeyi ba. Me gamina da ku da
tsare-tsaren naku. Fisabilillahi me wannan?".
Cikin faɗa Lamiɗo ya sa hannu zai bugi bakinshi da sauri ya kauce.
Cikin hatsala Lamiɗo yace.
"Wannan bakin naka da baya mutuwa, komai sai kayi inkarin a kai tabbas sai na kashe
bakin nan".
Wani kallo yayi mishi tare da cewa.
"Uhumm ai babu mai kashe bakin Muhammad Jabeer sai Allah".
Ganin zaija suma suyi surutune ya sasu kauda idonsu kanshi.

Bayan kusan mitinu goma, sai ga hayaƙin nan ya bar fitowa,


Sai wani irin huci.
Da sauri Jabeer yace.
"Nifa zan tafi, inma kun mance in tuna muku yau jumma'a ace, inada abinda yafi
wannan abun naku mahimmanci a rayuwata ta duniya da ƙiyama, yanzu gashi har kusan
sha biyu."
Murmushi sukayi baki ɗayansu ba tare da sunce mishi komaiba.
Sabida dama sun san za'ayi haka kam.
Sabida kowa ya sani shi Jabeer yana barranta da duk irin waɗannan ababen gado na
sarauta shiyasa sarautar kanta shi bata ɗaɗashi da ƙasa ba.

Da sauri ya buɗe siraran idanunshi da kyau.


Sabida ganin wani irin ƙaton maciji ya sako kanshi cikin babban ramin da yafi
girma.

Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun!."
Sai kuma ya zubawa maciyar nan idanu.
Tana fitowa cikin ramin ta, zuɗuɗuɗuɗuɗu. Haka yake zaro jikinshi.
Haƙiƙa dole duk wanda bai taɓa ganin macijinba bai kuma san da zamanshi ba, dole ya
razana.
Dan ma shi zuciyarshi na cike da tsoron Allah so irin wadannan ababen ba kasafai
suke firgitashiba.
tashinsa fahimtar ko wani ɗan abin sihirin za'ayi mishi ne.
Wani dagon numfashi yaja mai ƙarfi ya sauƙe ganin. Yadda macijiyarna taketa keta
fitowa taƙi ƙarewa.
Su dai su Lamiɗo shiru sukayi a zaune.
Saida ta gama fitowane, ya rage iya bindinta sai gashi ta fito bindinta na
kananmaɗe da wasu irin kitsastsun bulalin da ka gansu kasan tsoffine.
A hankali ya turo bindinshi gaban Lamiɗo,
Ya ajiyesu, sai kuma ya sumkuyo da kanshi ya zaro harshensa ya rinƙa lasar bulalin
nan saida suka fito ras kamar an wonkesu.
Kana ta juya ta nufi cikin curin zuɗuɗuɗuɗuɗu ta koma,
Kamar forko sai ga hayaƙin.

Wani nannauyan numfashi Jabeer ya sauƙe tare da cewa.


"Uhum inda ranka kasha kallo. Oh ni Muhammad Jabeer an ɗauramin jakar tsaba za'a
jazamin kaji su bini su tsastsageni.
Du wai wadannan abubuwan na menene wai dan Allah".
Ya ƙarishe mgnar yana kallonsu baki ɗayansu,
fuskarshi cike da alamun fargaban gudun saɓawa ubamgijinshi.
Su kuwa saida hayaƙin ya gama ɓacewa baki ɗaya sannan Lamiɗo ya fara miƙewa kana
suma duk suka miƙa.
Sarkin Shaɗi ruggume da bulalin.

Juyawa sukayi zasu nufi hanyar da zata ɓullo ta falon Lamiɗo,


da sauri ya ɗan motsosu tare da cewa.
"Dan Allah shi wannan abun me amfanin zamanshi a nan? Wurinda Kum san duk baƙin da
suke zuwa tako wani sashi na duniya ganin abin tarihin masarautar Joɗa muna kawosu
nan.
Yanzu in wata ran yunwa ta koroshi ya fito ya cutar da mutane fa me zakuce?".
Cikin ƙosawa da mgnar Galadima ya gyara riƙon da yayiwa sandarsa cikin sanyi yace.
"Bata tare da yunwa, macijiyar da duk wata sai an ajiye mata motar ƙwai a cikashi
da kiret-kiret na ƙwai shine abincinsa".
Da sauri Galadima ya nufi hanyar fita.
Lamiɗo kuwa tuni sun tafi.

Ganin sun tafi sun barshi a nan a tsayene. Yasashi sauƙe numfashin tare da juyawa
ya nufi, ƙofar da zata sadashi da falonshi.

A hankali yake taku, cikin kasala da mutuwar jiki, da mgnar zuci.


"Wai ya zanyine? Wanna wacce irinyar masifeffiyar rayuwace? Yaushe zamu samu Allah
ya gama tsarkake mana wannan masarautar Joɗa ya rabata da wadannan tsarabe-tsaraben
gargaji.
Wannan wacce iriyar fitinace?".
Dogon numfashi yaja lokacin da ya shigo falonshi,
babu kowa, can babban falo ma babu kowa bisa dukkan alamu duk sunje shirin sallan
jumma'a ne.

A hankali ya kutsa kai cikin bedroom ɗin shi.


Kai tsaye bathroom ya wuce.
Jallabiyar jikinshi da hirami da vest ɗin ya cire,
Cillasu yayi cikin injin wonki.
A hankali yake taku kanshi a sunkuye dagashi sai boxes Sky blue.
A hankali ya shiga cikin wurin wonkan.
Kamar yadda ya saba haka yayi wonkan jumma'a anshi.

Bayan ya fitone ya nufi drower'n glass ɗin dake cikin bathroom ɗin.
Wani tattausan Baby towel ya ɗauka bisa saman kafaɗunshi ya ɗauri ya fara gogewa,
yana tsane ruwan jikinshi.
Kana a hankali ya ɗauki wanni babban towel ɗin ya ɗaura daga saman ƙirjinshi.
Wanda ya sauƙo har guiwa shi, a hankali yasa hannun ta ciki ya fara murza boxes ɗin
yayi ƙasa, dashi yana zuwa sharabanshi ya riƙe shi ya zare ƙafa ɗaya, kana ya zare
ɗayar ma.
Lallaɓeshi yayi ya matse kana ya shanyashi kan ƙarfin silver da yake na shanya.
Farar jallabiya ya zura a jikinshi, kana ya kwance towel ɗin. Dashi ya goge suman
kanshi.

Cikin hamzari ya fito bedroom,


Kai tsaye gaban dreesing mirror ya nufa, mai ya shafa a dukkan sashin jikinshi.
Kana ya taje tattausan suman kanshi tare da shafa mishi manshi, wani Duaol jannah
mai masifar daɗi ya shafawa jikinsa, kana ya ɗauki wani ƙaramin kum ya tace
tattausan sajenshi ya kontar dashi lib-lib hakama gemunshi.

Saida ya gama komai na gaban Mirror kana ya nufi babban drower'nshi da sauri-sauri
yakeyin komai.
Wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da taushi fari ƙal ya zaro.
Kana ya ɗan yi sama da kanshi ya kalli cikin tsep ɗin ƙarshe na drower'n inda
al'kyabbanshi suke jere a kimtse tamkar shagon saidasu.
Hannu yasa ya zaro wata sabuwa dal tana cikin ledanta tana haɗe da hiramin ta da
komai.
Rufe wannan wurin yayi kana, ya buɗe wani sashin inda ƙananan kayan shi ke jere,
boxes and singlet ya zaro farara ƙal suma sabbi ne.
Da sauri ya rufe drower'n kana yazo ya ajiyesu bakin gadonshi.
Ba tare da ya cire jallabiyar jikinshi ba, ya saka boxes ɗinshi saida ya dai-dai-ta
zamanta a jikinshi da kyau ya kimtsa komai nashi yadda zaiji daɗi tafiya, kana ya
zare jallabiyar ya ajiyeta bakin gadon
Singlet ɗin ya yasa, sannan ya ɗauki farar tattausar jallabiya mai dogon hannun ya
saka, jallabiyar daya cire ya ɗauka ya gaban ƙaton drower'n nashi ya nufa, wani
side ɗin ya buɗe nan ya saƙalata.
Kana ya dawo bakin gadon.
Ledan al'kyabbar ya farka da ƙarfi da kuma sauri sabida ganin tuni ƙarfe ɗaya da
rabi tayi, yasan yanzu masallacin ya cika maƙil da mutane.
Ɗan gajeren tsaki yaja, tare da ci gaba da warware al'kyabbar.
Yana gamawa ya zurata a jikinshi, al'kyabbar baƙace, sai gefen bakinta da akayiwa
kolliya da wani zare mai masifar kyau Golding color irin mai sheƙi da ɗaukar ido,
hakama, kan kafaɗunsa har zuwa hannunta anja zirin irin wannan kolliyar.
da sauri ya dai-dai-ta zamanta a jikinshi, kana
Ya juya ya nufi, gaban dreesing mirror da hiraminshi a hannunshi,
Yana isa ya ajiye baƙin abin, kana ya ware farin hiramin shima da kolliyar Golding
color a jikinshi, ya ninkeshi kamar yadda muke ninke dankwali, bayan ya gama ne.
Ya ɗaurashi a kanshi ya dai-dai-ta zamanshi kana, ya ɗauki baƙin abin wanda shima
an zagayeshi da Golding color ya sakashi a akanshi, ya fito ras tamkar a Saudia.
Allah ya sani yana masifar son wannan shigar da jin daɗinta a jikinshi babu takura
babu matsi gashi ka suturtu da kyau mayu masu kallon tsiya irinsu Jazrahda Batool
duk basa iya ganin komai a jikinshi ba.

Da sauri ya nufi wurin aje takalma shi wanda yake na glass ne marfin ya buɗe kana,
ya ɗauki wasu takalma irin nasu na sarauta Golding color ne kuma half cover ne,
zura jajayen sawunshi yayi a ciki, kana ya koma gaban mirror, wani kolba turaren
OudKareem mai masifar ƙamshi mai sanyi, ya fesa a duk sashin jikinsa.
Kana yasa hannunshi ya ɗauki carbinshi. Farin galashi ɗan siriri ya manna a
idonshi.
Kana ya juyo da sauri zai fita, sai kuma ya tsaya cike da mamakin ganin. Haroon
tsaye ya zuba mishi ido.
Ya buɗi baki zaiyi faɗa sai kuma yayi shiru jin Haroon na cewa.
"Kada kace zakayi faɗa Lamiɗo ne yace inzo in kiraka, lokaci na tafiya fa."
Bai kulashi ba kawai yayi gaba, da sauri Haroon ya bishi tare da cewa.
"Wannan baza ƙamshi haka sai kace wurin amarya zakaje, gsky kayi kyau sosai masha
Allah".
Bai kula Haroon ba sabida addu'o'in da yakeyi.
Amman duk da haka saida ya bawa Haroon amsa a zuciyarshi, yake cewa.
"Akwai wani wuri da yafi cancanta da ɗan adam yayi shiga ta tsabta da kyan shiga
da ƙamshi sama da masallacin ne? Innal masajida lillafa, duk duniya da babu wurin
da Allah ya keɓanta yace dakinshine sai masallatai. Nan zamu gana dashi. Domin idan
mu bama ganinshi ai shi yana ganin mu".
Murmushi Haroon yayi, dan Jabeer bai san mgnar da yakeyi a zuci ta fito filiba.

A haka dai suka shiga Masallaci.

Dole yau a gaggauce yayi Kudbar jumma'a dududu 15 minutes yayi yana kudbar kan
halaccin mace ta kalli mijin da yakeson aurenta, kamar dai yadda yayi al-ƙawari a
wancan satin.
Daga nan aka kabbarta sallah.

A can Rugar Bani kuwa.


A hankali Shatu ta ɗago kanta ta kalli Ba'ana jin tunda suka tsaya baice mata
komaiba, ganin yadda ya zuba mata idone yasata, saurin yin ƙasa da kanta,
cikin sanyi muryar tace.
"Ya Ba'ana zamu tafi rana tanayi fa!".
Wani dogon numfashi ya ja ya sauƙe da ƙarfi, kana a hankali ya ƙara matsowa kusa
da ita da sauri tayi baya cikin tsoro, hannunshi ya ɗaga mata alamun karta gudu,
kai ta jujjuya tare da ƙara matsawa cikin rawan murya tace.
"Ba kyau ina tsoro".
Kanshi ya jingina da jikin bishiyar gamjin da suke ƙasanta, ido a rufe yace.
"Da dai inada niyar cutar dake, da bamu kawo zuwa yau ban cutar dakeba Shatu,
kadafa ki mance tun kina ƴar tatsitsiyarki nake sonki kuma nake tare dake, dare da
rana, kada ki mance kullum sai kinje gidanmu da dare da asuban fari kin amsowa
Ummey mgninta, da har ina son cutar dake da tun wancan lokacin zan cutar dake.
To amman bani da niyar cutarki, ina sonki ne sabida Allah, da kuma gsky da zuciya
ɗaya, Shatu koda zaki ƙi yarda dani a kan komai dan Allah ki yarda dani cewa ina
sonki, na kuma soki a baya zan soki har gaban abadan, wlh babu ƙarya a cikin
soyayyarki a zuciyata, Shatu sonki shine babban raunina a duniya.
Har yau babu wani abu dake firgitani da bani tsoro sai rasaki.
Babu wani abu na duniya daya taɓa sani zubda hawaye sai soyayyarki, dan Allah ki
dena zaton dan na matso kusa dake zan cutar dake, ki amince dani in baki abinda
idonki zai buɗu da gane sihiri duk ƙanƙantarshi".
A hankali take juya mishi kai cikin sanyi tace.
"Na sani Ya Ba'ana wlh na yarda da kai akan soyayyata, na sani bazaka cutar daniba,
tunda baka cutar dani a bayaba, nasan kana sona, na kuma yarda da son gsky kakemin,
to amman ni bana son wadannan abubuwa asirce-asircen sabida haramun ne.
A hankali ya zame jikinshi ya zauna kan jijiyan bishiyar.
Ganin haka itama tayi sauri ta zauna bisa guiwowinta ta durƙushe a ƙasa.
Cikin mamaki tace.
"Dan Allah ya Ba'ana meyasa kwanan nan duka sai kayi ta zubda hawaye a gabana,
hankalina yana tashi."
Kanshi ya ɗan ɗaga ya kalli sama, a hankali yace.
"Shatu ina sonki zan kuma soki har iya numfashin na, bazan bari wani abu ya rabani
da keba, in kuma akasamu wani ya zama ƙaddarar rabani dake, to shi kuwa tabbas zan
rabashi da rayuwarshi, kiyi haƙuri in dai a kanki ne zan iya yin komai, na kuwa san
duk duniya babu wanda yasan hanyar da za'abi a kamani ko aci galaba a kaina, sai ke
ranki ke ɗaya tak ce kikasan duk wani sirrina ban saniba ko zaki iya min halacci ki
sirranta min rayuwata".
Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
"Ya Ba'ana ai rayuwa a hannun Allah take, wata ƙilma in rigaka mutuwa, kuma in dai
nice in sha Allah bazan baiyana sirrinka dan a cutar da kaiba, ko ba komai kana
soma kuma kace dan zaka nemo su ya Gaini ne kayi wannan tsarin gudun kada mugaye su
cutar da kai, Ni na sani Ya Ba'ana waɗannan layun bazasu kareka ba, sabida ba
hanyar Allah ka biba amman ni zanyi ta maka addu'a".
Ido ya zuba mata a zahiri da baɗininta gsky ta faɗi dan yaga hakan cikin ƙwayar
idanunta.
A hankali ya jawo tandun duma dake rataye a kafaɗunshi, cikin sanyi yace.
"Ga ruwa kisha".
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"Bana jin ƙishi".
Tura mata tandun yayi gabanta tare da cewa.
"Eh ba mgnin ƙishi bane, kishi dan kiji sanyi a zuciyarki naga kina kuka".
Cikin share hawayenta tace.
"Ba kai bane ka sani kukan kana ta barmin amanar sirrikanka bayan kuma shi amana
rikeshi nada girma da nauyi da wuya".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Zaiyi wuya ki riƙe kenan?".
Da sauri tace.
"In sha Allah zan riƙe".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"Bazaki sha bako?".
Kanta ta gyaɗa mishi alamar eh.
Kana ta miƙa tsaye, gaba ta ɗan yi kusa da Rafi'a, tace.
"Rafi'a mu tafi".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Rafi'a ku tsaya".
Cikin tsoronshi Rafi'a tace.
"To Ya Ba'ana".
Da sauri ya ƙara so gabansu, tare da cewa.
"Mata ɗago hannunki mu gani kinada zobene?".
Kai ta girgiza alamar a a babu.
kana ta ɗaga hannunta na dama,
Yatsarshi ya karkaɗa mata tare da cewa.
"Lalala ɗago hannun hagu mu gani".
Cikin gajiya ta ɗago hannunta, fararen tausasan zara-zaran yatsunta suka zubawa ido
gaba ɗayansu.

Babu zobe ko ɗaya a yatsunta,


Murmushi yayi kana yace.
"To bari in baki zoben ziyara, koda bakya tare dani, duk lokacin da na nake kusa
dake kawai zakiga zoben a yatsunki".
Da sauri ta buɗe baki da nufin cewa a a.
Kawai sai tayi shiru ganin wani irin zoben azurfa mai masifar ƙyalli da sheƙi sai
ɗauke ido yakeyi.
Ta juyo zata ce mishi a a Ya cire sai kuma tayi shiru ganin ya ɓace daga gabansu.
Yatsunta tasa da nufin cire zoben da sauri ta barshi jin tamkar yatsunta zasu
tsinke.
Rafi'a kam tuni tayi gaba, haka yasa itama tabi bayanta.

Suna zuwa bakin titin suka samu motar zuwa cikin Ɓadamaya.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa,


Bayan an idar da salla, kamar kullum Lamiɗo ya gaggaisa da mutane, talakawan
garinshi.
Shi kuwa Jabeer dashi da tawagarsa duk sun nufi cikin gida.
Sabida Galadima nata ce mishi su tafi cikin gida su fara shirin tafiya.

Haka yasa duk suka nufi cikin gidan masarauta.


A nan babban farfajiyar suka ɗan tsaya.
Ido Jabeer ya ɗan zubawa jerin motocin da a ƙalla sun kai ashirin da biyar zuwa
talatin an bisa alamu anyi manyan baƙi ne ko kuma za'ayi fita mai mahimmanci.

Cikin suka wuce a falo suka samu Umaymah, Hajia Mama, Aunty Juwairiyya, da Ummi,
duk suna zaune suna ɗan hira.
Hibba kuwa tana kitchen.

Suna isowa ta fito da sauri jin muryarsu.


A hankali ta isa gefen Jalal cikin yin ƙasa da murya tace.
"Ya Jalal kazo kaci abinci karku tafi bakaci komaiba".
Kanshi ya ɗan gyaɗa mata,
Jamil ne ya hararesu tare da cewa.
"Allah shi ƙara, ai in dai Jalal ne kaɗan kika gani da gwatsalel, mutumin da ba'a
iya masa bare a masa gwaninta".
Haroon ne ya ɗanyi dariya tare da cewa.
"Haka suke shida Jabeer yadda suke kamanninsu iri ɗaya hakama halinsu".
Da sauri Jamil ya zare ido tare da ɗan ja da baya yace.
"Tab a a Ni dai wlh bance hakaba".
Jabeer kanshi Jamil ya bashi dariyar da dole ya ɗan murmusa, tuni sukuma sauran
dariya sukeyi.
Ya Jafar kuwa shi ganin murmushin Jabeer shine ke sashi murmusawa.

Ita kuwa Hibba tura baki tayi ta koma gefe ta zauna alamun tayi fushi, baibi ta
kantaba, sai Jamil ɗin ne ya ɗan lallasheta, haka dai sukayi ta yar raha, saida
Lamiɗo ya aiko su fito kafin.
Suka miƙa duk suka fita, shi kuwa Sheykh Jabeer gefensu Hajia Mama da Umaymah ya
ɗan rusuna kusa da Umaymah a hankali yace.
"To Umaymah bari inje bisa umarnku ba don raina yaso ba".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Allah ya bada Sa'a ya kaiku lfy ya kuma dawo daku lfy, Allah ya tabbatar mana da
al'khairan dake cikin wannan tafiyar, al'farma Annabi da Alqur'ani".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu, Hajia Mama dasu Ummi ma duk sukayi mishi addu'a,
kafin ya fito.

Yauma kamar ranar mota ɗaya suka shiga da Haroon da Lamiɗo da Ya Hashim da Laminu.

Kana sauran tawagar sarki.


Daga nan suka nufi hanyar fita gari su nufi garin Shikan.
A cikin motocinsu kamar na ranan.

A tsakiyar garin Ɓadamaya ne suke tafiya sun zo dai-dai bakin Genaral Hospital
Ɓadawaya.
Lamiɗo ya bada umarnin cewa su shiga cikin asibitin zai kai ziyarar dubiya wa
marasa lfya.

Nan take kuwa suka jujjuya akalan motocin.


Suka fara kutsa kai cikin asibitin.
Da ƙarfi Jabeer ya rumtse idanunshi tare da furta.
"Lahaulawalaqutailla billah".
A hankali sabida wani irin masifeffen bugu da zuciyarshi tayi da ƙarfin masifa.
Wani irin taraddadi ya diro masa.
Ya ilahi shine abinda ya ambata a saman lips ɗin shi.
Dip dab dip dab dip dab dip dab haka zuciyarshi ke harbawa da bugawa a tare a
tare,
addu'o'in ya fara karantowa a zuciyarshi da harshenshi, yadda suke ƙara kutsawa
cikin asibitin haka bugun zuciyarshin ke ƙaruwa.

Anan cikin asibitin kuwa, A maraba da baƙi Shatu take tun zuwanta sabida, anan aka
juye duk fulanin da suka samu rauni sanadin wannan faɗan,
an zubesu a wurin gwamnatin jiha kuma tayi burus da batunsu sam bata bawa likitoci
damar dubasuba,
Sai ma cewa sukayi sai fulanin sun nemo polices kafin a karɓesu.
Su kuma dama ƴan agaji ne ma suka taimaka suka kawosu nan ɗin ma.

Zuwan Shatu ne da Rafi'a da ta samesu a yashe hankalinta ya tashi.


Ranta yayi matuƙar ɓaci nan ta haura gidan sama inda can jerin jadawalin officer's
ɗin DOCTOR'S suke.
Rafi'a na biye da ita tana rabka mata kira.
"Garkuwa! Garkuwa!! Ke GARKUWA!!! Ina zakije ne wai?".
Sam bata kula Rafi'a ba sabida abin da akayiwa ƴan uwanta yayi masifar ci mata rai.

Ganin yadda take gudu-gudu da sassarfa ne yasa itama Rafi'a ta fara Binta da gudu-
gudu da sassarfa.

Yayinda kuma dai-dai lokacin Lamiɗo da tawagarsa ma ke tafe suna shiga cikin gidan
saman.
Lamiɗo ne a gaba sai Jabeer da Galadima dake gefenshi da Sarkin Shaɗi.
Kana su Waziri da Wambai Matawalle da Makawa Ɗurɓi Turaki Tafida da dai sauransu,
kana Dogari na rike da laima wa Lamiɗo,
Ɗanzagi kuwa ya kware murya yanata.
"Gyara kimtsi sarki ya gaisheku".
Kana sauran fadawa masu red and blue ɗin Uniform kuwa da tabka-tabkan rawuna babu
kunne ko ɗaya suna biye dasu a baya da gefe gefe, suna tafe babu takalma, ga dogin
bulali masu masifar tsawo da kauri suna jansu a ƙasa.

Lamiɗo, Galadima, duk shigar manyan kaya na sarakuna, masu al'farma sukayi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer shigarsa ta al'farma na limamai yayi, wannan yasa kwarjinshi
ya fi nasu.
Daga nesa zakace yafi shekarunshi in ka hangoshi sabida kamala da haibarsa da suka
baiyana a fili.

Laminu kuwa tuni yayi gaba yana ɗaukar shigowarsu.


Sabida aikinshi na jarida dama neman rohotone aikinshi.

Sanadin saurin da suke ɗanyi ne yakesa al'kyabbar jikinshi ɗan buɗewa tana bazuwa
hakan sai ya zama kamar ƙasaitace tasa yake wannan abun a wurin mai kallonshi.

Gaba daya duk ta inda suka zo wucewa, sai ya ɗaga hannunshi duka biyu, yayi musu
sallama tare da cewa.
"Ya mai jiki?".
In sunce da sauƙi. Sai yace.
"Laah Ba'as ɗuhhuru in sha Allah".
Duk inda suka gilma sai an bisu da ido. Especially Jabeer da babu wanda zai
kalleshi bai ƙaraba

Tuni labari ya kai ga kunnen Dim din asibitin.

Lokaci ɗaya ya kikkira DOCTOR'S ɗin ta wayar salulu ya sanar musu su kimtsa komai
su kula da kowa yadda ya dace.
Mai martaba Lamiɗo na cikin asibitin.

Ita kuwa Shatu tana haurawa sama.


Ido take ɗagawa ta duba sunan Office da mai Office ɗin Office na forko taga
musulmine haka yasa ta kutsa kai ciki.
Zaune yake babu kowa sabida duk majinyatan sun tafi.
Wasu an duba su, wasu kuma korarsu akayi da cewa yau half day ne, sabida haka su
tafi.
Da mamaki ya ɗago kanshi jin an shigo mishi Office babu sallama. Da sauri yace.
"Waye?".
Sabida cikin shigar yan matan larabawa take.
Arabian gawd ne mai masifar kyau da taushi a jikinta wanda samanshi yake a dai-dai
jikinta ƙasa shi kuma yake a buɗe, wasu irin duwatsune a jikin rigar tun daga sama
har ƙasa sai wal-wali sukeyi suna ɗaukar ido.
Tayi rolling kanta da ɗan kwalin rigar fuskarta ta fito ras a ciki.
Wasu takalmi Golding color ne masu ɗan tudu dai-dai misali sai Ƴar ma dai-daiciyar
hand bang mai masifar kyau shima Golding color ne, sai wayarta ƙirar iPhone 11.
Fuskarta babu kolliya sai dai duk da haka bai hanata yin kyau ba gashin girarta ya
konta lib-lib. Sai dai kuma ta rufe fuskar da tattausan Niƙab sai dai bashi da duhu
sosai.
To wannane ya hana Dr Salim ganin fuskanta, ita kuwa Shatu cikin tsananin ɓacin
rai da zafin tozarcin da akayi wa yan uwanta tace.
"Dr Salim".
Cikin Mamaki yace.
"Na'am". Yatsarta tasa tana nuna mishi maraba da baƙi ta wondon shi, cikin rauni
tace.
"Dr Salim na tabbatar kai musulmine, kuma nasan kasan cew manzon Allah yace shi
musulmi ɗan uwan musulmine! Shin ko ka mance hakane, da ka kasa taimakawa yan
uwanka musulmai da kafurai sukayi musu rauni akazo aka watsar dasu a nan kuma kuka
ƙi dubasu meyasa, ko dan kawai sun kasance fulanin dajine laifinsu?".
Cikin sanyi Dr Salim yace.
"Wallahi umarni ne ba'a bamuba daga sama".
Cikin tafasar zuciya tace.
"Umarni wanne irin umarni kuma zaku jira bayan Allah da Manzonsa sun baku dukkan
dama da umarnin taimakawa ɗan uwanku musulmi muddin kunada dama".
Miƙewa tsaye yayi tare da cewa.
"Dim ɗinmu ne ya hanamu dubasu".
Cikin kufula tace.
"Kan kafurar uwarshi! wato a cikin asibitima sai an mana ƙabilan ci, dan Allah Dr
kuje ku taimakawa bayin Allancan".

Cikin jin ƙarfin guiwa ya juya, ya fita, ya nufi can.


Ita kuma haka ta rinƙa bin duk Office ɗin da taga na musulmi ne tana shiga.

Tawagar Lamiɗo kuwa suna isa baƙin wani tamfatsetsen Office Sheykh Jabeer, ya ɗan
kalli Lamiɗo tare da cewa.
"Ni bari in shiga office na, ko mutun biyar in duba kafin ku gama zagayawa".
Cikin gamsuwa da hakan Lamiɗo yace.
"To bisimilla".
Nan ya nufi babban barandar da Nurses suke tare a wurin maza da mata.
Jamil kuma na biye dashi da System ɗinshi a hannunshi. Hakama Haroon ya biyoshi.

Nurses ɗin kuwa suna hangoshi duk suka mimmiƙe tare da cewa.
"Sir barka da zuwa".
Barka dai yake ce musu tare da ratsawa yana wucewa.
Su kuwa sun taru a wurin ne dan tawagar Lamiɗo na wucewa su sauƙa ƙasa su duba
Fulanin nan kamar yadda Dim ɗinsu ya basu umarni sabida kada Lamiɗo ya gansu a
yashe a ƙasa yasan abun bazai mishi daɗi ba.
Suna ganin ya shiga Office ɗin suka juya da nufin zasu tafin sai kuma suka tsaya
jiyo muryar Shatu na cewa.
"Ku tsaya ina kuma zakuje? Baku da aikin yi ko? Amman da yake ba taimako ne a
zuƙatankuba kun bar bayin Allah a wulaƙance ko?".
Cikin masifar Nurses da su ba komaiba sai iya ciwa mutane zarafi a hatsale tace.
"Ke kuma waye".
Kallonta Shatu tayi sama da ƙasa tare da kallon rubutun dake saman aljihun rigarta
ganin sunan arniyace ga kai da gashin doki ga uban faratu kamar na jaki yasa taja
tsaki tare da cewa.
"Banyi da keba, da masu hijabi nake mgn".
Yadda tayi mgnar da ƙarfi ne yasa, su Jabeer ma jiyo muryarta,
wanda shi kuwa zuwa yanzu yana jin zuciyarshi zata iya faɗowa ƙasa dan bugawar da
takeyi.
Jin muryar wata nurse ɗin tana cewa.
"Wannan ma ai iskanci ne".
Cikin taɓe fuska ya nunawa Jalal yatsa alamun ya buɗe mushi ƙofar yaga meke faruwa
da suka cika mishi kunne da hayaniya.
Da sauri Haroon yabiyo bayan Jalal suka fito.

Shi kuma Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar shi.
Tare da rage girman idonshi ya zubawa bayan Shatu ido.

Ita kuwa Shatu cikin zafi ta kalli arniyar nan da tace mata wannan ma ai iskanci ne
tace.
"A kul kada ki kuskura ki sake kira min iskanci a gabana, ke kika sanshi ba niba,
ke kika taso cikinsa".
Sai kuma ta juya harce cikin fillanci tace.
"Shegu masu wari".
Sai kuma ta juyo ta fuskancesu da kyau, Haroon kuwa da Jalal ido suka zuba mata
cikin mamaki.
Shima Jabeer idon ya zuba mata so yake yaji meyasata ihun nan.
Ita kuwa Shatu cikin sanyi ta fuskanci musulman ciki murya a ɗan tashe tace.
"Kada dai ku manta nace daku nakeyi masu hijabi sabida nasan kun san ma'anar
Al'muslim akul muslim. Kun kuma san girma da daraja da kuma wanda ya faɗi hakan".
Cikin gamsuwa duk suka ɗaga mata kai, rai a ƙuntace tace.
"To meyasa kuka bar waɗanan can bayin Allah'n a tozarce a yashe a maraba da baƙi
koda dreesing na raunuka su bakuyi musuba, menene laifinsu, kawai dan sun kasance
fulanin daji, shiyasa DOCTOR'S da Nurse's kab bazaku jiƙansu ba".
Cikin sanyi ɗaya daga cikinsu tace.
"Ayyah yanzuma can zamu tafi. Sabida sai yanzu Dim ya bamu umarni".
Wani dogon tsaki taja tare da cewa.
"Daga baya kenan yau kwanansu goma cib babu wanda daya dubasu, sai da suka gama
jigata".
Tsaki arnan ciki sukaja tare da juyawa suka tafi.

A hankali Jalal ya juyo ya kalli Hammanshi da yake cewa.


"Rufe min ƙofa wannan ta cika min kunne da ihu".
Da sauri yace to.
Haroon kuwa murmushi yayi tare da juyowa zai shiga ciki kafin Jalal ya rufe ƙofar.
Da sauri ta juyo jin takun mutun a bayanta,
Cikin muryar umarni tace wa Jalal.
"Kai mai kamar larabawa tsaya kada ka rufe ƙofar, Office ɗin na arne ne ko
musulmi?".
Cikin dariya Haroon yace.
"Na musulmi ne".
Taku ta fara tare da nufo cikin Office ɗin.
Wani irin sunkuyawa Jabeer yayi ya kifa ƙirjinshi kan babban Glass table dake
gabanshi, sabida ji yakeyi tamkar kan zuciyarshi take taku. Ji yakeyi zuciyarshi
zata fashe tsabar yadda take bugawa da azaban ƙarfi yadda take ƙara matsoshi haka
bugawa zuciyarshi ke ƙara tsananta.
Cikin mamaki ta zubawa Office ɗin ido. Office ne mai matukar girma da kyau da
tsaruwa, kai bakace Dr Office bane in ba ɗan wannan gadon da labulanshi da sauran
kayan aiyukansu ka ganiba.
Duk da sai sati-sati yake zuwa nan Office ɗin tsab-tsab sai wani irin sanyi da
ƙamshi yakeyi, cikin taɓe fuska tace.
"Me hakan shima DOCTOR baida lfy ne? Kodai tsabar wulaƙanci ne?".
Murmushi mai kama da dariya Haroon yayi sabida yasan babu abinda Jabeer ya tsana
yake kuma tsoro kamar a tsaya a kanshi ana mgna da ƙarfi, yo shi ko a hankali kake
mgna sai yace kana mishi ihu a kai bare kuma wannan da take tsaye a kusa dashi
kuma tana mgna da ƙarfi cewa zaiyi haushi takeyi."
Shi kuwa Sheykh Jabeer hannunshi yasa yana dafe ƙahon zuciyarshi da yakejin yana
tsalle.

Rafi'a kuwa tsaye tayi a bakin ƙofar tana kallon ikon Allah.

Sauran Nurses ɗin kuwa suma, tuni sun tafi, maraba da baƙin.

Ita ko Shatu a hankali ta ƙara motsowa gaban table ɗin hannunta tasa ta bug...

😂😂😂😂tsawon shekaru labarin littafin GARKUWA yana kimtse a kaina da zuciyata. Ni


kaina in na tunoshi sai nayi murmushi nayi shauƙi sarƙaƙiyarsa kan hanani baccin
dare inyi ta nazartan lmrin lbrin GARKUWA, nakanji murmushi da daɗi in na tuna
lbrin nakan zubda hawaye wasu lokutan wasu lokutan nakanji jikina yayi sanyi da
rayuwar duniya, labarin Garkuwa bazaka ganeshi ba, sai in ka karantashi duk iya
lbrin mai labartawa bazai labarta maka yadda komai yakeba, Uhummm Allah ya nuna
mana ƙarshensa, salon soyayyar Sheykh ta musamman ce..
Masoyan Parvina kuna sani dariya.

Masoyan Shatu kuna burgeni.


Ina masoyan Boleru jinjinan girma gareku.

Masoyan Sheykh ina sonku,


Sheykh yana gaidaku.

Masoyan Jalal yace ku dena kallonshi.

Masoyan Umaymah tace ku tayata da addu'a Allah ya yaye musu matsalarsu.

Wai Ya Ba'ana baida masoya ne?


Allah sarki Ba'ana ina sonshi dan al'khairin da yayiwa Aysha a baya. To wai wane
al'khairi yayi mata ne?

Littafin GARKUWA na kuɗine in kina buƙatan Normal group turo katin mtn na ɗari uku
kacal ta wannan number 09097853276. In kuma special Group kikeso kiyi min TRANSFER
ɗin dubu ɗaya rak ta asusun na 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki
turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853276. Masu turo katin mtn numbers
ɗin zaki turo ba hotonba.

By
*GARKUWAR FULANI*Ta ɗan buga table ɗin, tare da cewa.
"Malam ka tashi kaje ka taimakawa yan uwanka musulmai! in kuma baka da lfy ne ka
nemi bokaye irinka su duba lfyarka".
Zuwa yanzu gaba ɗaya jikinshi tsuma yakeyi ta ciki. Kanshi ne yakeji yana jujjuya
mishi sabida yadda ta konkotsa glass table ɗin da kanshi ke kife a kai. Ga kuma
sautin muryarta da yake jinshi har tsakiyar kanshi.
Da sauri ya ɗago kanshi tare da ware matsakaita kyawawan idanunshi na zaiba.
Cikin sauri Haroon ya matsoshi ganin idanunshi sun cika tab da ƙwalla sai sheƙi
sukeyi alamun suna iya zubda ƙollan a ko wanne lokacin.
Cikin harɗewar murya ta larabci yacewa Haroon.
"Please ka fitar da ita a nan, ta matsa kaina zata fasa min dodon kunne".

Ita kuwa Shatu cikin tarin mamaki da al'ajabi ta zaro manyan idanunta tare da cewa.
"Laaah!". Sai kuma ta fara ɗan ja da baya tare da cewa.
"Afwan baka da lfy ne!?." Wani irin fitinenne murmushi Haroon yayi tare da cewa.
"Eh baya jin daɗi ne, ɗan fita zamu kira wasu bokayen suzo su dubashi".
Cikin sauri tace.
"Subahanallahi bokaye kuma?".
Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.
"Yesss ba haka kikace ba, ya nemi bokaye ƴan uwanshi su dubashi".
Kanta ta ɗan dafe tare da cewa.
"No kada ka munana min zato, ina nufin likita bokan turai ka gane ko?".
Da sauri taja da baya ganin Jabeer ya miƙa tsaye da ƙarfi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer tsayuwanta kusa dashi barazana ce ga zuciyarshi tabbas zata
iya faso ƙirjinshi ta fito.
Ganin yadda ya haɗe fuska ya nuna mata hanyar fitane, yasa ta juya ta fita.

Shi kuwa Jabeer komawa yayi ya zauna tare da sauƙe wasu tagwayen ajiyan zuciya a
jere a jere.
A hankali yake jin bugun zuciyarshin na ɗan dai-dai-ta kamar dai yadda yaji kafin
ta shigo.

Sai kuma ya fara jin zuciyarshi na tsinkewa ras-ras kamar dai tana tsoron kada wani
abu yayi nesa da itane.
"Ya ilahi ya mujibadda'awati ya hayyu ya ƙayyum".
Sune kalaman da Jabeer yaketa maimatawa a saman lips ɗinshi.

Haroon kuwa wani irin kallo yakeyi ma Jabeer mai cike da nazari.

Jalal ma kallonshin yake cike da tarin mamaki duk da sun san baya son akeyin mgn da
ƙarfi a kanshi, to amman idonshi bai taɓa ciko da hawaye ba, sai yau.

Ita kuwa Shatu, ido ta zubawa Rafi'a da ta tsareta da ido, cikin yin ƙasa da murya
tace.
"Rafi'a dama, wannan shugaban tuzuran ƙasar nan, yana aiki anan asibitin gwamnatin
jihar nema?".
Kamo hannunta Rafi'a tayi tajata sukayi gaba.
Haroon kuwa dariya yayi sabida, duk da rage muryarta da tayi sunji abinda tace,
sabida wurin da suke ɗin yanada amsa kuwar amo.

Cikin yin ƙasa da murya sosai Rafi'a tace.


"Garkuwa ki nitsufa ki rufa mana asiri, kin ko san waye wannan?!".
Shiru sukayi dukansu lokacin da suka juyo wata kekyawar mata tana bawa wasu ƴan
mata Nurses a ƙalla sun kai goma lbri.
Ido Rafi'a da Shatu suka zubama wannan matar cewa.
"Shi wannan Dr Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa, ba kamar sauran mutane
bane, shi mutunne da Allah yayi masa wasu baiwa da nasabobi masu tarin yawa".
Wata ƴar kekyawar cikinsu ne ta ɗan lumshe ido tare da cewa.
"Allah ya sani Aunty ina sonshi, ina son wa'azin shi, muryarshi kawai in naji yana
zuba larabci sai inji bani da sauran damuwa a duniya, sai dai shi kuma yana nan
kamar dutse!".
Da sauri Matar nan tace.
"Ai bazai yiwuba, wlh bazai taɓa kulakiba, duk nacinki da korkosarki, shiyasa wasu
ke raɗe-raɗin shi waliyi ne!".
Numfashin ta sauƙe tare da ci gaba da cewa.
"Duk matsayinki, kyanki, mulki, sarauta, gata, ilimi!. ko da meye kike taƙama dashi
a duniya ya fiki abin".
Kusan a tare suka haɗa baki wurin cewa.
"Kawai dan shi jikan sarkine sai yafi mu komi?".
Kanta ta jinjina tare da gyara zaman ta cikin sanyi tace.
"Ba haka bane. Bari kuji kaɗan daga cikin nasabarsa.
Kunga forko dai shi mutum ne wanda ubangijin yayi mishi baiwar ilimin addini dana
zamani.
Yana ɗaya daga cikin manyan malam da Afirka gaba ɗaya take ji dashi.
Sabida a ƙiyasin malamai babu yaro matashi mai jini a jiki da tarin ilimin addini
kamarshi.
Tun yanada shekaru takwas a duniya ya haddaci al'ƙur'ani mai girma.
Sannan ya fara karatun littafai shine matashin da yakeda haddar hadisai
zunzurutunsu a kanshi sama da dubu ashirin.
Kunji wannan darajeta da tasa ko manyan mutane suke girmama shi.
Sannan shi jinin Masarautar Joɗa ne ta wurin mahaifinshi.
Ta wurin mahaifiyarshi kuwa shi jinin sarki Jalaluddin ne, masarautar sarkin
Musulmai.
Kana ta wurin kakarshi data haifi mamanshi. Asalin balarabiyar saudiya ce, wacce
zuriyarta ne limamen Harami.
Kunga nasaba kan nasaba kenan.
In kyau ne na halitta, babu irin kyan da bai ganiba,
In kuwa kuɗine, ku leka ƙasan gidan saman nan zakuga ayarin motocin da sukayi mishi
rakiya, to ko kakan nashi Lamiɗo motar da yake hawa bata kai ta Jabeer ba.
Uwa uba shi mutun ne da ya ƙoshi da sunna, baya son bidi'a.
Shi mutun ne wanda ya samu kekyawan zato a wurin mutanen duniya ake mishi shaidar
salihi, mumini, mai tausayi."
Da sauri suka ƙatseta da cewa.
"To Aunty meya hanashi yin aure har yanzu?".
Cikin maida numfashi tace.
"Allahu alamu, sai dai ance kamar shi bana miji bane!".
Cikin sauri wata tace.
"Kai mgnar. Duniya dan Allah kiji zancen ƴan shashi faɗi. Bita da ƙulli har an
samo sharrin da aka liƙa mishi bawan Allah."
Rafi'a kuwa kai ta jinjinawa Shatu alamun kinji ko, ita kuwa Shatu zuru tayi kamar
makahon daya tsinka garaya".
Cikin sauri wacce tace tana sonshin tace.
"Wlh ni dai ko shi bana miji bane zan iya zama dashi a hakan in da zai yarda muyi
aure".
A hankali Shatu ta gyara riƙon da tayiwa wayarta tana ɗaukar su video.

A hankali matar nan ta nisa tare da cewa.


"Uhum Nafeesat kenan ai kuwa da wuya ya aureki duk abinda zakiyi.
Sabida kin ga Dr sugzana yar India ce ƙabilar buramin bautar wuta takeyi.
Tace tana sonshin, tace in dai zai aureta zata musulunta, amman yaƙi".
Da sauri ɗaya dake cinsu tace.
"Sabida me yaƙi duk da tayinta na shiga addinin Allah?".
Cikin sanyi matar tace.
"Yayi bayani kuma manyan malamai sun gamsu da hujjarsa, inda yace, tace dole sai
in zai aureta zata musulunta, kenan badon Allah zata musulunta ba sai dan sonshi.
Ta kuma ce in sunyi aure duk yaransu rabasu zasuyi rabi suyi addininshi rabi suyi
addininta bi ma'ana wasu suyi bautar wuta wa iyazubillah.
Yace wannan dalilin yasa bazai aureta ba, kuma shi baya sonta, ya kuma gargaɗi mata
su dena cewa suna sonshi.
Dan shi yanzu al'majiri ne sai ya girma zaiyi aure".
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Jin hakane yasa Rafi'a yana Shatu suka ci gaba da tafi.

Su kuma waɗancan sukaci gaba da hirarsu.

Tafiya kaɗan sukayi suka samu wasu yan mata da samari suna hira ɗaya daga cikinsu
na cewa
"Ni tsarin Sheykh Jabeer yana masifar burgeni a rayuwata.
Shifa tunda yake a duniya babu wani mahaluƙin da zaice yaga koda singalalin
hannunshi ne a waje.
Mutum ne da Allah yayi mishi sutura, yake kuma suturce kanshi."
Cikin dariya wani yace.
"Kai nima yana burgeni sai dai tsarinshi na wai mata su dena yafa gyale, su rinƙa
yin shigar zurmuƙa-zurmuƙan hija baine bai minba, to mu matasa taya zamuyi ta
kallonsu munajin daɗi.
Ni wlh wani lokacin a kallonma nake biyan buƙatar damuwata sai dai inje inyi
wonka".
Cikin tashin hankali ɗaya daga cikinsu yace.
"Ouzubilla, ka nemi gafar Allah wlh zina kakeyi".
Cikin zaro ido yace.
"Kai malam dakata ni banyi zinaba".
Cikin sanyi babban nasu yace.
"Wlh kayi sabida ita zina ai kashi-kashi ce akwai ta ido akwai ta kunne haka kuma
akwai ta zahiriya, fisabilillahi ka kalli yar mutane na tafiya har kaji ka biya
buƙatar ka?".
Kai ya gyaɗa musu cikin sanyin jiki.
Nan sukayi ta mishi nasi daya kame idanunshi
Da sauri suka wuce su.
Ita kuwa Rafi'a cikin murmushi tace.
"To bari in baki amsar tambayar ki.
Yana zuwa nan asibitin sau ɗaya cikin ko wanne sati. In yazo kuma ranan duk wanda
ya duba magani kyautane, in kuma aikine kyautane.
Kinga Hospital ɗin school ɗinmu shi kuma a wata yake zuwa sau ɗaya,
Nanam da kyar ya yarda, yanada asibitinshi mai zaman kanshi can yafi maida
hankali".
Ajiyan zuciya Shatu tayi tare da cewa.
"Uhum can yake tara kuɗin bayin Allah ya ƙwamushewa dai".
Kai Rafi'a ta jujjuya tare da cewa.
"No ba haka bane, duk abinda zan ce miki bazaki gamsuba in sha Allah sai Next
month in ciwon mararki ya tashi, zan kaiki can zakiga zahiri.
Amman dai daga sunan asibitin zaki iya fahimtar manufarsa".
Kallonta ta ɗanyi tare da cewa.
"Menene sunan asibitin?".
Ƙara saurin tafiyarsu sukayi tare da cewa.
"Ballitai Hospital". Kanta ta gyaɗa alamun gamsuwa da sunan asibitin kana taja
hannun Rafi'a suka tafi can maraba da baƙi.

Abin mamaki suna isa suka samu.


Kusan rabin DOCTOR'S din asibitin duk suna wurin.
Duk DOCTOR'S ɗin da Shatu tayiwa mgna sunzo nan sunata basu taimakon gaggawa.
Kana ga Nurses tako Ina, sunata tura marasa lfyan ana basu gadaje.
Cikin abinda bai gaza awa ɗaya da rabi ba.
Komai yayi dai-dai hatta waɗanda za'ayiwa aikin anyi musu.

Bisa umarnin Lamiɗo kana ya rinƙa bin gadajensu yana ajiye musu kuɗi dubu biyar-
biyar.

Sosai wannan abun yayi masifar yiwa Shatu daɗi, tana kallon dattijon tamkar wani
nata,
Godiya sosai sukayi musu da zasu tafi, suna fita nan sukayi kiciɓis da Jabeer da
yanzu ya fito ɗakin tiyata.

Ita kuwa Shatu Junaidun Junainah ta kalla lokacin da aka dawo dashi daga ɗakin
tiyata,
Inda aka ɗinke mishi inda aka sareshi.
Cikin murmushin yace. "Adda Shatu zamu kwana ko?".
Murmushin jin daɗi tayi tare da cewa.
"A a Junaidun yanzuma zan tafi, kasan Ummey ba lfy, amman jibi ma zanzo gobe su ya
Salmanu zasu zo, yanzu dai hankalinmu ya konta tunda kun samu kulawar likitocin
yanzu sai matsalar abinci".
Cikin sanyi Sumaye matar marigayi Sarkin bakansu, tace.
"La abinci kam bamu da matsalarshi, tako ina zakiga musulmai na dafo abinci suna
kawo mana sadaka, harda kayan zaƙi da kuɗi wasu ke bamu".
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
"Alhamdulillah yau kam mutanen Rugar Bani zasuji lbri mai daɗi".
Cikin kula tace.
"Toni yanzu zan tafi in Sha Allah gobe akwai masu zuwa, Allah ya baku lfy".
Ta faɗi tana kallon sauran mutanen nasu.
Haka Rafi'a ma tayi musu fatan lfy kana suka fita tare.
Adaidaita suka shiga, saida ya kai Shatu tasha kafin.
Ya wuce da Rafi'a school ɗin su.

A can wurinsu Lamiɗo kuwa ganin lokacin sallan la'asar yayine yasa Jabeer cewa,
suyi salla a masallacin asibitin kafin su tafi.
Haka kuwa akayi, sai gashi masallaci ya cika maƙil da bani adam,
saida suka idarne kana suka kama hanyar tafiya garin Rugar Bani.

A cikin motocin kuwa kowa da abinda yakeyi.


Shi kuwa Sheykh Jabeer tsuratul Khaf yake karantawa a hankali.
Hakama Lamiɗo.

Su Jalal kuwa kowa na ruggume da waya.


Haroon ma waya yakeyi da Umaymah tana tambayarshi sun isane.
Nan yake gaya mata inda suke da abinda sukayi.

A cikin Rugar Bani kuwa, kamar ko wacce ranar jumma'a yauma hakane.
Tunda aka taso sallan jumma'a suka dawo tsakar garinsu suka zauna suna ƙara jadda
mitin ɗin su na ɗaukar fansa.
Zuwa yanzu garin yana amsar baƙoncin Fulanin da suka gaiyata tako wani sashi na
Afirka. Sunata shirye-shiryen su.

Suna cikin masallaci suna sallan la'asar ne suka rinƙa jiyo, shigowar motoci cikin
Rugarsu kamar bazasu ƙare ba.

Cikin nitsuwa sukaci gaba da sallan su.

Su Lamiɗo kuwa suna shiga garin ganin tsit kuma alamun ana salla, sai yace su
tsagaita gudun.

Jabeer kuwa zuwa yanzu tuni zuciyarshi ta fara luguden dukan ƙirjinshi ya rasa
wannan abu na menene?
Yanzu wannan karo na huɗu kenan yana jin wannan abun a rayuwarsa, ya kuma gwada
kanshi yaga bashi da BP dan sani BP nayin hakane ya sashi godawa.

A jere a jere sukayi parking motocinsu cikin nitsuwa,


Dogarai da fadawa suka fito suka zagaya motocin.

Bayan sun idar da salla sunyi addu'o'insu ne kana suka fito.


Gani fadawa da dogarai ma kaɗai ya ganar dasu waye yazo.
Dan haka cikin karrama da mutun-tawa Arɗo Bani ya nufi inda suke.
Sosai dogarai sukayi mamakin yadda wannan karon kuma yakeyi kamar ya haɗiyesu dan
farin cikin zuwansu saɓanin wancan karon da yayi ta aunawa Lamiɗo boma-boman
baƙaƙen maganganu.
Jiki na rawa ya juyo ya kalli matasan tare da cewa.
"Maza ku shiga cikin gidan ku fito da dardumai da kilisai kuzo ki shimfiɗa.
Ina sarkin kiɗa maza a fito da gangaguna a fara sanarwa.
Mabusa ku fito."

Ai kuwa cikin abinda bai gaza 21 minutes ba aka gama shirya komai.
Tuni mutane sun cika sunyi maƙil ko ina ya cika da bani adam.
Kiɗe-kiɗen da bushe-bushen sarewa da al'gaita kuwa tuni ya cika illahirin garin
tako ina mutane ke shigowa.

Ba'ana da tun jiya yake cikin ɗakin dodon tsafinsu Bonon.


Jin al'gaita Shaɗi ne, ya sashi fitowa bayan ya gama shafe magunguna.
Dama yayi zaton wannan hegen mai jajayen kunnuwan zaizo shiyasa tun jiya ya shiga
ɗakin sirri dan a dafashi da kyau.

Jinsu ne yasa ya fito dashi da tawagarsa suka nufi Rugar Bani.


Lamiɗo kuwa da tawagarsa a hankali cikin ƙasaita da kwarjini suke taku har i zuwa
cikin rumfar karan da aka malale musu kujeru da kilisai.

Bayan sun zaunane duk dattawan wurin sukazo suka gaida Lamiɗo da tawagarsa.
Jabeer kuwa ji yake tamkar ya kira Sojoji su zo su zazzane mishi mutanen garin gaba
ɗayansu ko zaiji ya huce da abinda sukayi mishi.
Sam baya son ganin fuskokinsu, ga toshe mishi kunne da sukayi da wannan bushe-
bushen sarewa.
Ga bugun zuciyarshin dake neman zautar dashi.
Allah ya sani baya son ganin ko ƙasar garinne.

Cikin kula da nitsuwa da kamala Bappa ya kalli Jabeer ɗin tare da cewa.
"Yaro ya ƙarfin jikin naka".
Ba tare daya ɗago kanshiba ya amsa, sabida jin muryar tanada kamala.
A hankali yace.
"Alhamdulillah".
Gaba ɗayansu suna farin cikin ganin Jabeer yazo cikin ƙoshin lfy.
Sunyi masifar mamaki ganinshi garau ya worke cikin mako ɗaya tak.
Wannane ya ƙara sawa Ya Salmanu wani farin ciki na ban mamaki.

A hankali Bappa yace.


"Masha Allah, Allah ya ƙara sauƙi".
Idonshi ya ɗan ɗago ya kalleshi, haka nan yaji dottijon ya cika mishi ido a hankali
yace.
"Amin ya Allah".
Bukar ne ya ɗan kalleshi tare da cewa.
"Yanzu yaron nan kaine? Ka sake zuwa garin nan lallai baka son ranka".
A daƙile Jabeer yace.
"Inuwa tace".
Galadima ne ya ɗan kalleshi tare da mishi alamun kada yayi mgna.
Kwaffa yayi tare da murtuke fuska.

A hankali su Arɗo bani suka koma wurin zamansu.


Kana Barmuji ya fara sanarwan ana son ganin Ba'ana a tsakiyar fili.

Wannan abu shine na forko a tarihin shi a nemeshi yazo tsakiyar fili dan a rama
gasar da yayi.
Haka yasa cikin karsashi da buɗa ƙwanji yayi wani irin tsalle ya faɗo tsakiyar
taron.
Juyi ya farayi da ihu da ɗaga hannunshi sama, saida yayi kusan sau goma kafin
yacewa Barmuji.
"Ka gayawa yan kallo in dai an cini gasa zan tafi in bar ƙasar nan, zan koma ƙasar
Cameroon nida ƙasar nan sai dai ziyara,
Dan ba'a yin jarumai biyu a gari ɗaya kamar yadda ba'a sarakuna biyu a gari ɗaya."
Wani irin ihu da shewa gaba ɗaya mutanen suka ruɗe dashi lokacin da Barmuji ya
sanar da ikirarin Ba'ana.

Kana dattawan garin kuma kowa da abinda ke cikin ransa Arɗo Bani dasu Bappa kamar
su haɗiye haƙorinsu dan daɗi.

Arɗo Bani ne ya ronƙofo kusa da Lamiɗo cikin nitsuwar datattaku yace.


"Allah rene, bisimilla GARKUWA ya fito fage shi ake jira."
Kai ya gyaɗa mushi kana ya juyo ya kalli gefen damanshi inda Jabeer ke zaune cikin
shigarsa ta al'farma, yayi masifar kyau, yana zaune cikin kamala sai lips ɗinshi ke
ɗan motsawa a hankali alamun tasbihi yakeyi.
Cikin yanayi girma da bada umarni da tsare fuska Lamiɗo yace.
"Jabeer kai ake jira tashi kaje muyi abinda ya kawomu."
Fuskarshi ya tsuke tare da lumshe idonshi, muryar Galadima da yajune yasashi buɗe
idonshi.
Shi kuwa Galadima hannu ya miƙa ya kamo hannun Jabeer, tare da fara ja alamun zai
miƙar dashi tsaye.
Cikin mamaki Jabeer ya zubawa tsohon ido wanda yake Bappa ne ga Lamiɗo, in banda
ƙarfin hali inashi ina iya ɗaga Jabeer.
Muryar Lamiɗo yaji yana kuma cewa.
"Jabeer DAN ALLAH KA TASHI".
Tsaki ya ɗan ja kana ya yunƙura ya miƙa a hankali.
Cikin jin daɗi Galadima ya kama hannunshi yaja suka fara taku, zuwa cikin taron.
A hankali yake bin bayan Galadima kana fadawa na biye dasu.
Al'kyabbar shi ya ɗan gyara mahaɗinta.

Suna isa tsakiyar taron. Mabusa da makaɗa duk suka kaceme wurin da bushe-bushen
sarewa da al'gaita kana da kaɗe-kaɗen.

Barmuji ne ya matso bayanshi da alamun zai cire mishi Al'kyabbar shi.


Da sauri Barmuji ya dakata sabida ganin wani irin lallo da Jabeer ya watsa mishi
cikin tabbatarwa yace.
"Kada ka sake gangancin ciremin suturar da Allah yayi min har abadan. In kuwa ka
gwada tabbas zakaji yadda raɗaɗin marin tafin hannuna yake, in kunnenka ya kuramce
ansan kuramtane yasa bazakaji gargaɗi da kashedi na ba!".
Ya ƙarishe mgnar da tafasar zuciya,
cikin tsuma Barmuji ya rusuna tare da cewa.
"Duk da dokar gasa ce, anyi maka wannan lamunin tunda kaine mai duka ba kai za'a
dakaba".
Ba'ana kuwa wani murmushi jin daɗi yayi sabida yasan yin duka da ƙatuwar riga haka,
zai takurashi bazai samu damar zage ƙarfin shi ya zabga mishi bulaliyar ba.
(Allah sarki Ba'ana bai san zafin hannun Sheykh bane.
Sarkin Shaɗi ne, ya miƙe tsaye tare da tanɗun shantun da a ciki suka zuro bulalin
nasu.
Ya nufi wurinsu Jabeer yana zuwa.
Yasa hannunshi ya zaro bulala ɗaya daga cikin bulalin ya miƙa mishi.
Hannun yasa ya amshi bulalar.
Kana ya gyara al'kyabbar jikinshi.
Shi kuwa ba'ana gabanshi ya matso ya tsaya ya buɗa sawunshi, kana, yasa hannunshi
duka biyu ya riƙe ƙugunshi, ya buɗa ƙwanjinshi da kyau.

Sheykh kuwa ƙasar garin ya zubawa ido, yana tuno irin zafi da ƙunar sashi cire
kayanshi da sukayi satin daya gabata, yana tuna raɗaɗin da zuciyarsa ta masa a
wannan lokacin.
Busar sarewa da akayi azaban ƙarfi ne, tabbacin an bada dama a farane.
Yasa Jabeer gyara riƙon da yayiwa bulalar, yana maiji cikin ransa da jikinsa zai
rama dukan azaba da wannan ya mishi.
Yanajin zai ramane kuma dan tsorotar dashi kan sake dukan wani.
Yasani in sha Allah daga kanshi baza'a sake wannan gasar daba adadin bane, yayi
niyar yin ramuwar ne dan tare wannan ɓarakar zai ramane ko zai samu ya huce tsanar
da yayi mutanen garin, sabida kasan cewarsu Musulmai ƴan uwansa baya son yayi musu
irin wannan tsabar lokacin ɗaya fushinsa na ranar ya dawo.
Shiyasa ya murza yatsunshi da kyau tare da matsawa gefe kaɗan, Rumtse bubalar yayi
a tafin hannunsa da kyau, kana ɗagata tare kuma da cewa Bismillah, ya fara da
sunan Allah kana ya ɗaura da fara karanto ayatul shifa sannan ya zabgawa Ba'ana ita
a tsakiyar bayanshi.

Gaba ɗaya hankali da idon kowa bisa fuskar ba'ana yake.


Shi kuwa ba'ana wani irin murmushi yayi tare da kallon gefe da gefenshi kana, yayi
fito alamun babu wani abu da yaji dai yaji tsikar jikinshi yana tashi yar-yar.

Arɗo Bani da sauran dattawan kuwa har ji sukeyi tamkar su kamo hannun Jabeer suyi
ta zabgar Ba'ana babu ƙaƙƙautawa.
Shi kuwa Jabeer wani bulalan ya kuma shimfiɗa mishi a tsakiyar bayanshi tare da
sunan Allah.
Still murmushi yayi sai dai wani irin masifeffen bugawa da zuciyarsa tayi ya tsinke
ras.
A karo na uku ya tabka mishi bulalar a tsakiyan kafaɗunshi wannan karon baiyi
murmushi ba, ƙebta idonsa yayi, tare da gyara tsayuwa sai kace dutse ake tabkawa
bulalin.
Fargabane ya fara dukan ƙirazan dattawan Fulani, yayinda ƙabilar ɓachama kuwa,
suketa ihu da tsalle da fito da kiran ba'ana suna ƙara mishi ƙarsashi.
Bulala ta biyar Jabeer ya kuma tsula mishi, still babu sauyi.
Cikin sauri Arɗo Bani ya juyo ya kalli Lamiɗo dake zaune.
Ko ajikinshi dashi da tawagarsa, Sarkin Shaɗi kuwa murmushi ma yakeyi.

Cikin fargaba, Arɗo Bani yace.


"Allah rene Lamiɗo wannan yaron bai iya duka da ƙarfi bane? Ko dai ba bulalin
masarautarku bace!?".
Wani irin kallo mai cike da mamaki da kuma tuhuma Lamiɗo yayi mishi.
Sai kuma dai ya kauda kanshi.
Ɗanzagi ne yace.
"Hattara dai Arɗo , Masarauta Joɗa sun wuce aro, zuba ido kaga ikon Allah".
Bulala ta bakwai ne, Jabeer ya ɗago ya tsulala mishi ita a gadon bayanshi.
Da sauri Ba'ana ya rufe ƙwayar idanunshi sabida wani irin tashi da yaji tsikar
jikinshi yayi.
Tsikar jikinshi bai gama konciya ba, yakuma jin Jabeer ya rausa mushi wata
bulaliyar, da sauri ya buɗe idonshi sabida.
Wani irin Yar-yar da yaji tsikar jikinshi tana zubawa duk gashin jikinshi ya miƙe
tsaye.
Bai gama dawowa nazarin meyasa yakejin hakaba ya kuma jin wata bulaliyar.
A hankali yaji zufa ya fara keto mishi duk ta inda hudan gashin jiki yake a
fatarsa.
Murmushi yakeyi har yanzu sabida bawai zafi yakeji ba, sai dai fargaba ta rufeshi,
sabida jin alamun sihirurrukan jikinshine ke fecewa.
A haka Jabeer yayi ta tsula mishi bulala har zuwa bulala ta goma sha ɗaya.
Ata goma sha biyu ne, da ya tsula mishi yayi wani irin gantsarewa sabida wani irin
azabebben ƙaiƙayi da yaji wurin yanayi mishi.
Da sauri yasa hannunshin a bayanshi alamun zai sosa.
Ife-ife da sowan da matasa suka farayi ne da Muryar Barmuji na cewa.
"Dokar gasa banda susa".
Da sauri ya dawo da hannunshin tare da cewa.
"To ya dane karatun da yakeyi, bana so, ya dena kira min sunan Allah".
Wata bulalar Sheykh ya zabgawa shege tare da cewa.
"Sunan uwarka zan kira maka in ban kira sunan Allah ba?".
Arɗo Bani kuwa wani irin ajiyan zuciya mai ƙarfi yaja.
Shi kuwa Ba'ana wani irin masifeffen ƙaiƙayi ne yakeji a duk inda Jabeer ya zuba
mushi bulala, a bulala ta goma sha biyar ne, da aka zuba mushi.
Yayi wani irin gantsarewan da yafi na ɗazu.
Wani irin azabebben zafi da raɗadine yakeji yana tsarga mishi jiki da zuciya.
Zuface ta ketomishi tako wanne sashi na jikinshi.
Cikin sauri Jabeer ya juya bulalar ya amshi ta biyu ya haɗa data forkon.
Ya damƙesu a hannun hagunshi.
Wanda dama shi badamene kuma bahagone duk abinda hannun damanshi kan iya yi to na
hagun yana fi iyawa.
Sai dai kasamcewarshi mutun mai ilimi da sanin addini shiyasa yake amfani da
hadinsin nan da Manzon Allah ke cewa.
A cikin dukkan abinda zamuyi mu wakilta dama a forko, har dai sai in shiga bayan
gidane aka ware shiga da ƙafar hagu.
To juya hannun yayi da hannun hagunshi, kana ya riƙe mahaɗin al'kyabbar jikinshi da
hannun damanshi.
Gyara tsayuwarshi yayi kana ya ɗaga bulalar da ƙarfi ya zubawa Ba'ana a tsakiyar
bayanshi.

Wani irin azabebben ihu mai ƙarfin amo da karaji Ba'ana ya kurma tare da fara
karkarwa kar-kar tamkar mai farfaɗiya.
Ihun da ya kurmane yayi masifar tada hankalin dukkan kafurai magoya mayanshi.
Arɗo Bani kuwa a gabansu Lamiɗo ya tashi tsaye ya juya ya fuskanci al'ƙibila yayi
sujjada.
Bappa ma da kanshi wani irin murmushin jin daɗi yakeyi.

Hakama duk sauran dottawan.


Shi kuwa Ba'ana wani irin azabebben kuma masifeffen zafi yakeji a dukkan sashin
jikinshi.
Wani irin tsalle ya buga da ƙarfi lokacin da aka kumayi mishi bulala ta ashirin.
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi keyi hatta Ba'anansa miƙewa tayi tana
karkarwa, wata tafasashiyar zuface ta sinƙo mishi, zafi yakeji har cikin ƙoƙon
kanshi da zuciyarshi.
Bulala ta ashirin da biyu akayi mishine yasashi fashewa da wani irin kuka mai
azaban ƙarfi wani irin masifeffen fitinenne fitsarin azaba ya fara kwaranyo mishi,
ihu mai cike da azaba yayi.
Wanda gaba ɗaya rugar saida kowa ya jiyoshi.
Ƙabilar ɓachama kuwa gaba ɗaya suma kuka suka saka.
Shi kuwa Ba'ana da ƙarfi ya faɗi ƙasa yana burbuwa, tamkar wanda yayi al'janu.
faɗuwanshi ƙasane yasa Jabeer rusunowa ya rinƙa tabka mishi bulalar, ihu da burbuwa
da rarrafe alamun guduwa Ba'ana yakeyi cikin azaba da karaɗi da kuka yake cewa.
"Wayyo! Wayyo!! Wayyo Bonon!!! Ka ceceni zan mutu zai kasheni.
Wayyo Bononnnnnn! Yau bakayi min ranaba, ga bulalin karin sihirina sun iso gareni
wayyoooooooo Bonon meyasa baka gaya minba na hudu tun kan wannan malamin ya kasheni
ya karya min komai na jikina da sunan Allah."
Ya ƙarishe mgnar da ƙarfi tare da miƙewa tsaye ya fuskanci kudu. Ya ɗiba a guje ya
ari ta kare ya nausa a guje.
Wani irin taku Jabeer yayi tare da biyoshi baya da sassarfa abunka da dogon mutun
sai gashi ya isoshi a gigice ya fara kai mishi bulalin hagu da dama,
Jin azabar ta zarce azabar da yake zatone, yasa Ba'ana kurma ihu da kururuwan da
yasa kab mutane suka nufosu.
Gudu yakeyi Jabeer na binshi yana zaneshi har ya fiddashi cikin taron gaba ɗaya.
Barmuji ne ya riƙe hannun Jabeer tare da cewa.
"A dokar gasa Shaɗi in dai ya gudu ka bishi ka korashi cikin farfajiyar shike nan
ya faɗi a gasa kaci.
Kuma bazai sake samun damar shiga gasarba bazai kuma sake zama a garinba."
Wani irin busar sarewa da al'gaita kana da kiɗe-kiɗen tsantsar farin ciki, al'ummar
Rugar Bani suka farayi.
Sunayi suna zagaye Jabeer. Haroon kuwa da Arɗo Bani da Galadima miƙewa sukayi cikin
farin ciki suka ruggumeshi.
Jamil, Jalal, Imran, Hashim, Sulaiman. Suma kab farin cikine ya cika musu zuƙata.
Laminu kuwa ji yakeyi tamkar ya shaƙo Jabeer ya karshi sai dai tabbas dama ya zaci
aha dan shi mari ɗaya nema Sheykh ya masa ya kusan suma, shiyasa ya tausayawa
Ba'ana.
Lamiɗo kuwa jinjina kai yakeyi yana tattausan murmushi.

Koda su Galadima suka ruggumeshi, Arɗo Bani kuwa kama hannunshi yayi ya ɗaga sama
alamun yaci gasar Shaɗin.

A haka suka iso gaban Lamiɗo hannunshi yasa ya dafa kan Jabeer tare da sanya mushi
al'barka.

Mutane kuwa duk an kacame da farin ciki.


Ya Salmanu kuwa kusan suma yayi tsabar masifar jin daɗi.
Alhamdulillah yau dai burinshi ya cika ya samu konciyar hankalin duniya an ɗauka
musu fansa, shida masoyan Shatu na baya, harma da yayanshi.
Jan gefe makaɗan suka sabi, da sauran zugar jamar gari.

Jabeer kuwa mamaki yakeyi yadda yaga.


Fulani nata shigowa garin tako ina wasu bisa dawakai wasuma ƙan raƙuma.
Lamiɗo kuwa waya yakeyi da amalun a sirrance yake mgnar sabida ko Jabeer ɗin dake
kusa dashi baya jinshi.

Bisa umarnin Arɗo Bani ne aka rinƙa fito da ƙwaran nono da fura da dambu da ƙwaran
zuma,
Ana kawowa su Lamiɗo.

Wanda fadawa da dogarai ne sukasha.

A hankali Jabeer ya kalli Lamiɗo cikin gajiya yace.


"To ai sai ku tashi mu tafi ko!".
Shiru Lamiɗo yayi mishi, ganin hakane, ya gyara hiramin kanshi kana ya kuma cewa.
"Mu tafi ko".
Galadima ne yace.
"Ai bamu gamaba".
Cikin sauri Haroon yace.
"To meya rage kuma?".
Galadima ya buɗe bakin zai bashi amsa kenan. Sai kuma duk suka juyo suna kallon
wasu tsala-tsalan motocine masu masifar kyau da tsada, suna shigowa Rugar Bani a
jere-a jere. Cikin fidda numfashi Haroon ya ɗan kalli motocine da mamaki yace.
"Ha Jabeer kalli wannan kamar tawagar motocin Uncle Abdulkarim da Abudulfata kalli
kamarfa harda Jadda". (Sarki Jalaluddin suke cewa Jadda)
Sai kuwa ya juyo ya kalli Lamiɗo cikin nitsuwa yace.
"Lamiɗo lfy kuwa?".
Kanshi ya gyaɗa mishi alamar eh Lfy kau.
Shi kuwa Sheykh Jabeer cikin nitsuwa yake kallon ayarin motocin a fakaice tabbas.
Su Jalaluddin ne da yaranshi. Kana ga kuma Baban Haroon, ga kuma su Dr Aliyu da
Barrister Kamal da su Baba Basiru Baba Nasiru dama duk sauran manyan masarautarsu.
Da sauri ya juyo ya kalli Lamiɗo da nufin yin tambaya sai kuma yayi shiru ganin
Lamiɗo na mgna da Galadima da kuma wani amintaccen bafadanshi.
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
"To wannan ƙus-ƙus du na menene, ku duk abinda babu kyau kuna jin daɗin yinshi."
Shiru yayi ganin motoci sama da talatin ne suka shigo Rugar.
Kana duk manyan mutanene kuma sun fito cikin motocin sun nufo inda suke zazzaune.
Wanda tuni Arɗo Bani yasa an kuma firfito da taburman cikin masallacin su.
Kana yasa an fito da sauran dardumai da kilisai anzo an shimfiɗa.

Suna isowa sarki Jalaluddin da Abba suka dafa kafaɗun Jabeer tare da sanya mushi
al'barka kana suka zauna gefenshi ya zama sun sakashi a tsakiya.
Kusa dashi Abbanshi ya zauna,
Kana Jalaluddin ya zauna kusa da Abban.
Lamiɗo kuwa na kusa dashi shida Galadima.

Da sauri Haroon dasu Jamil kan sukabi bayan fadawan da suka nufi motocin da sukazo
yanzu da ido.

Shi kuwa Sheykh Jabeer ido kawai ya zubawa wayarshi.


Yana wasu aiyukanshi a ciki.

A hankali ya ɗago kanshi ya kalli Haroon dake taɓashi.


Da yatsa Haroon ya nuna mishi gabanshi.
A hankali ya juya kanshi ya kalli inda Haroon ke nuna mishi.
Fadawane da hadimansu keta jido katon-katon ɗin sweet ga kuma fufun goro shima
sunata jidowa suna ajiyewa a gabansu Arɗo Bani.
Cikin mamaki ya kalli Lamiɗo tare da cewa.
"Me za'ayi da wannan kuma? Kamar wanda suka zo ɗaurin aure!".
Da sauri Galadima yace.
"Eh ashe ka gane ai ɗaurkin auren ne".
Cikin mamaki Haroon yace.
"Aure kuma? To auren waye?".
Lamiɗo ne ya kalleshi cikin isa yace.
"Auren Muhammad Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero Joɗa!".
Wani irin yunƙura Jabeer yayi zai miƙe, cikin tsananin haɗe fuskarnan tamkar zatayi
aman jini ya kalli Lamiɗo tare da yunƙurin miƙewa yace.
"Zancen banza kenan a wurin banza, ai wlh baka isaba, wlh Lamiɗo kafa kiyayeni
kanafa shigemin rayuwa, ka fita hanyata ka fice min a ido kar in rintsa da kai fa
kadafa ka bari in juyo kanka".
Ya ƙarishe mgnar da miƙewa tsaye. Sai kuma ya juyo jin an kamo hannunshi an medashi
zaune, a fusace ya kalli inda yaji anja hannun nashi ganin Sarki Jalaluddin ne ya
riƙo hannunshi ya sashi kuma tsuke fuskarsa cikin faɗa yace.
"Jadda sakarmin hannu bana so! Bana son abinda kuke min da rayuwata, wlh gwarama
kun tashi mun tafi, dan babu ruwana dan Ni bazanyi aure ba".
Da sauri ya juyo jin muryar Abbanshi yana cewa.
"...!

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number
09097853276, sai in saki cikin Normal group wanda a kwana talatin za'a gama
littafin. Ko kuma kiyi min TRANSFER ɗin dubu ɗaya ta asusuna na Jaiz 0005388578
Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai
09097853276. Sai in saki a Special Group inda cikin mako biyu kacal za'a gama Part
1 da izinin ubangiji.

By
*GARKUWAR FULANI*"Muhammad!". Ya kira babban sunanshi tare da jawo
hannunshi, ya zaunar dashi bisa kujerar da ya tashi a kai.
Cikin wani irin yanayi mai cike da tashin hankali da tsoron abinda suke shirin
aikatawa, ya kalli Mahaifin nashi, kana ya juyo ya kalli Lamiɗo da Galadima gefen
damanshi ya juyo ya kalli Jadda cikin rauni ya kuma kalli mahaifin nashi tare dayin
ƙasa da murya yace.
"Abba kada ka bari su ɗaura auren nan, dan Allah kace musu su bari, kada su ɗaura".
Ya ƙarishe mgnar cikin tashin hankali da ɓacin rai da tarin rauni a fuskarshi.
Cikin zuba mishi ido Abbanshi yace.
"Meyasa? Sabida me za'a bari!? Meyasa baka so!?."
Kanshi ya jujjuya tare da haɗe hannayenshi wuri ɗaya ya fuskanci mahaifin nashi
cikin sanyi yace.
"Ni dai bana so. Abba dan Allah kada ka bari suyi.
Bana son garin nan bare mutanen cikinsa, kuma bawai haka banza naƙi auren nan ba,
Abba inada matsala, Please Abba na tuba dan Allah kace su bari. In yaso a ɗaura da
wani amman banda ni kam".
Lamiɗo ne ya kamo hannunshi cikin isa yace.
"Auren' nanfa, kamar ma an ɗaurashi an gama, domin babu wani abu ko wani mahaluƙin
da ya isa ya hana wannan ɗaurin auren, gwarama ka kontar da hankalinka. Tunda ka
iya jure bulalin aiko tabbas dole ka aureta, babu shakka dole sai ka aureta, bazai
yiwu a dakeka a kantaba sannan ka barmusu itaba."
Cikin jin haushin wannan fitinenne tsohon ya kwace hannunshi daya riƙe tare da
cewa.
"Haka kenan kullum zanyi ta wahala a bisa wasu dalilanka da bana addiniba, me
ruwanka da dukan da akayi min, ba dai kai-kasa dole aka dakeni ba".
A hankali Galadima yace.
"Eh da kuma bakayi kukaba, baka guduba, yau kuma kasa yayi kuka ya gudu ai dole ka
aure matar da a kanta aka haɗaku gasar, tunda mu dai ba sakarkaru bane, bare ace
bamu san dokar gasar Shaɗi ba."
Wayyo Jabeer ji yakeyi tamkar ya mammake tsoffin nan dan tarin baƙin ciki. Rai a
ɓace yace.
"Bakufa fini sanin kainaba, tunda nace muku bana son aure, bazan kuma yi aureba, to
ku barni mana, rayuwata ce ko taku, ko dole ne duk wata matsalata da sirrin
rayuwata sai kun sani! Nace muku bana son wannan garin na tsani garin bana son
mutanen garin karankatab ɗinsu.
Bani babu su, in kuma kukayi gangancin cusa min wata muguwar yarsu, tabbas! lallai
ilaihin! A kanta zan rama sauran bulali ashirin da wancan ƙaton gardin ya min,
hamsin, ni a talatin ya gudu".
Kai Jadda ya girgiza tare da cewa.
"Ka rama mana kaida matarka, ka rama ka kuma jinyace ta".
Shiru sukayi sabida jin muryar Dr Aliyu da kuma Galadima da Arɗo Bani da Bappa suna
tabbar wa juna lfyar yaransu, cikin Mamaki ya kalli Galadima dake cewa.
"Muma ɗanmu lfyarshi lau, Namiji ne".
Cikin sanyi Jabeer yace.
"Ji maƙaryacin tsoho, wai lafiyata lau, ko yaushe ya zama likita ya gwadani. Harda
wani karkacewa yana zuba ƙarya ko farin gemunshi bai martaba-ba".
Jin Abbanshi ya daki gefen ƙafarshi ne yasashi yin shiru.

A nan a gabanshi a gaban mahaifinshi. A gaban dubban al'ummar fulani makiyaya


daketa tsastsafo tako wani sashi na duniya, a kuma gaban Lamiɗo da tawagarsa hakama
Jalaluddin da tawagarsa.

Aka ɗaura auren Muhammad Jabeer da Aysha. Bisa koyarwan addinin Musulunci.

Sosai su Jalal, Jamil, Hashim, Haroon, Sulaiman. Sukayi mamakin wannan aure na ba
zata. Ba zato ba tsammani.
Bayan an gama dai-dai-ta komai an ɗaura auren ne, kuma.
Lamiɗo ya kalli Arɗo Bani, cikin girma da ƙasaita yace.
"Yanzu zai tafi da matarshi."
Cikin sanyi da al'hini Bappa yace.
"Allah rene yanzu kuma!?".
Galadima ne ya amshi zancen da cewa.
"Haƙƙun yanzu zamu tafi da ita!".
Arɗo Bani ne yayi murmushi mai cike da jin daɗin yace.
"To ba laifi ai, muje a fito muku da ita".
Shi kuwa Bappa ido ya zuba musu.
Dan shi a zatonshi ba yau zasu tafin mishi da Shatunsa ba.

Nan duk suka ɗunguzuma, suka shiga motocin. suka nufi ƙofar gidansu Shatu.

Ya Salmanu kuwa, tuni ya shiga cikin gidan su.


Ya shiga ɗakinshi yana ta kuka kamar yaro. Bai tsamci haka abin kan iya juyewa ba,
Ba'ana ya rasa Shatu shima ya rasata.

Suna isa ƙofar gidansu, duk motocin suka tsaya.


A hankali Bappa da Arɗo Bani suka kutsa kansu cikin gidan.

A tsakar gidan suka samu.


Shatu na zaune dan dawowarta kenan, hannunta tasa ta tallabe haɓarta ta zubawa su
Junainah ido, shigowarta gida kenan daga dawowarta.
Cikin Ɓadamaya su Binto suka shigo gidan a guje suna ce mata wai an ɗaura aurenta
da ɗan sarkin da akayi gasar Shaɗi dashi.
Jin hakane yasata yin murmushi tare sauƙe dogon ajiyan zuciya na gajiyar tafiyar
da tayi, ido ta lumshe tare da cewa.
"Auren kuma wasane, da zai zama an aura min wani wanda ba'a san halinshi ba, ko ƴar
tsana ma ai ba'a aurar da ita a hakaba bare ni".
Ta faɗi mgnar cikin fargaban ganin yadda suketa rantse mata. Duk da bawai ta yarda
da zancensu bane. Junainah kuwa dariya takeyi tare da ɗan tsalle-tsallenta tana
cewa.
"Yeeh Auren Addana yazo, zanyi gayyan fati muyi gaɗa".

Cikin zuba musu ido, ta zauna gefen, Ummey dake ta Binta da ido, cikin sanyi tace.
"Ummey na dawo! Ya jikin naki!?."
Da sauri ta gyara zamanta tare da zubawa Ummey ido, cikin mamaki take kallonta
ganin idanunta nata zubda hawaye ne, yasata cikin ruɗani da tashin hankali da
fargabar abinda ke shirin faruwa da ita da rayuwarta.
A kiɗime tace.
"Ummey meya sameki? meya saki kuka? Jikin ne yake miki ciwo?."
Sam Ummey bata iya mgna ba, sai kukan da takeyi,
hakanne yasa zuciyar Shatu karaya, cikin rauni wasu hawaye masu ɗumi suka fara
tsiyayo mata.
Hakan ya ƙara ingiza kukan Ummey hakama,
Junainah sai ta raɓa gefensu tayi, zurui a zatonta aure abun daɗi ne ba kukaba to
gashi taga su kuma kuka sukeyi.
Sosai Shatu takeyin kuka mai tarin dalilai.
Suna isa Bappa yasa hannunshi ya kamo nata, cikin sanyi yace.
"Taso kizo".
Ido cike da hawaye ta mike tsaye bisa umarnin Bappa.
Shi kuwa Bappa cikin sanyi ya kalli Ummey da Junainah yace.
"Kada kuyi kuka, kuyi mata addu'o'in samun nasara a cikin wannan al'amari, muyi
mata fatan aurenta ya zamo haske ne a rayuwarsa shi mijin da ahlinshin baki daya,
fatanmu aurenta ya zamo ƙungiyar da zata jawo gskya cikin raminda aka binneta ya
fito da ita kowa ya gani."
Shiru Ummey tayi sai hawayen da suke kwaranya.
Hakama Shatu hawayenta wani na korar wani.
Ita kuwa Junainah faɗawa jikin Ummey tayi sukaci gaba da zubda hawaye.

Bappa kuwa hannunta yaja suka juya suna nufi hanyar fita.
Da kayanta na ɗazu wanda taje Genaral Hospital Ɓadawaya dasu, hatta hand bag ɗinta
na rataye a kafaɗarta wayarta na ciki.

Cikin mamaki take bin bayan Bappa, tare da yin taku a hankali tana bin bayanshi
yadda yake jan hannunta.
Arɗo Bani kuma na biye dasu a baya.

Suna fitowa ƙofar gidan, Haroon da Jalal suka juyo suka kalli juna,
Cikin tarin mamakin ganin kamar yarinyar ɗazuce.

Shi kuwa Sheykh Jabeer yana zaune cikin motar, shi ɗaya dan duk sun fita.
Da sauri ya dafe saitin ƙahon zuciyarshi jin ta tsananta bugawar da yakeyi.
A hankali ya maida bayanshi ya jingina da sit ɗin tare da rufe idonshi.
Yana mai jin sanyin A/C na ratsa mishi jiki da jini da zuciya.
Amman duk da haka zuface ke tsastsafo mishi a jikinshi sabida bugun da Zuciyarshi
keyi ya wuce misalin.

A hankali ya juya kanshi ya kalli gefen hagunshi inda yaga motar Jadda da kuma Dr
Aliyu ne da Barrister Kamal ke jere a wurin.

Bappa kuwa a hankali yake taku, yana nufo inda Lamiɗo ke tsaye Dogari na riƙe masa
da laima, Ɗanzagi da fadawa na zube a kasa.
Ita kuwa Shatu cikin rawan jikin jin idanun mutane na yawo a jikinta dan ma Allah
yasa akwai niƙab a fuskarta.
Take bin bayanshi. Shi kuwa Sheykh Jabeer yadda suke ƙara matso inda yake haka
bugun zuciyarshin keta tsananta.
Suna isa gaban Lamiɗo Bappa ya miƙawa Lamiɗo hannunta cikin sanyi da nitsuwa da
taushin lafazi yace.
"Allah rene, ga Aishatu matar Muhammad Jabeer.
Gata amana bisa jagoranci ka, nasabarka da yardarka.
Da kamala da nitsuwa da na gani a fuskar yaron yasa naji ƙarfin guiwar baku
aurenta.
Ba tare da fargaba ba, yanzu kaine kaka kuma jagora a gareta".
Sai ya kuma nuna Barrister Kamal da shima yana cikin wakilai, shi a zatonsa ma
shine mahaifin Jabeer cikin sanyi yace.
"Kai kuma kaine matsayin mahaifi a gareta ku zame mata dangin ta data rasa, naso
ace da mata a masu ɗaukanta, dan in danƙa amanarta a hannun macce yar uwarta.
Amman ba komai, na baku amanarta dan Allah kada a cutar da ita, domin nima ta
kasance amanace a uwurina, domin ƴaƴan mu da muka haifama amanace Allah ya bamu
kuma abun kiyayewa, bare kuma ɗiya irin Shatu ɗiyace da take da nasabobi masu yawa
a gareni".
Cikin gamsuwa Lamiɗo yasa hannunshi ya amshi hannunta daketa karkarwa, tuni niƙab
ɗin fuskarta ya jiƙe jilak da ruwan hawaye.

Cikin Dattaku Lamiɗo yace.


"In sha Allah zan kula da dukkan lamuranta tamkar yadda nake kula dashi Jabeer,
kuma kada ka damu akwai masu meye mata gurbin uwa ƙanwa yaya dama duk danginta a
cikin masarauta Joɗo, baƙoma baya kukan maraici bare kuma, matar sashin jinina".
Cikin sanyi da wasu hawaye Bappa yace.
"To Ngd matuƙa".
Arɗo Bani ne ya dafashi tare da cewa.
"Ka sanya mata al'barka a cikin aurenta ba zubda hawaye ba."
Sosai Haroon ya zuba mata ido.
Shi kuwa Sheykh Jabeer da mamaki yake kallon Bappa dake zubda hawaye.

A hankali su Bappa suka ɗan ja da baya.

Shi kuwa Lamiɗo ya juya ya nufi motar riƙe da hannunta.


Haroon ne yayi saurin buɗe musu marfin motar, suka nufoshi gadan-gadan.
Jalal kuwa ido ya zubawa yatsun hannunta da Lamiɗo ke riƙe dashi.

Shi kuwa Jabeer idonshi ya rufe da ƙarfi. Sai kuma ya buɗesu, dai-dai lokacin
Lamiɗo ya kawota bakin ƙofar motar tare da cewa.
"Mamana kiyi bismillah ki shiga da ƙafar dama".
Cikin shessheƙan kuka ta gyaɗa kai tare da yin bisimilla kana ta ɗan sunkuyo, sai
kuma kukan ya kubce mata.
Shi kuwa Jabeer da sauri ya buɗe marfin motar ta gefen hagunshi. Kamar gilmawar
walƙiya ya fita cikin motar.
Dai-dai lokacin da Shatu tasa ƙafarta ciki.
da sauri yasa hannunshi ya buɗe motar Jadda tare da shigewa ciki yaja marfin ya
rufe sabida ji yayi zuciyarshi zatayi bindiga, wani irin dogon ajiyan zuciya ya
sauƙe mai ƙarfi.

Ita kuwa Shatu, a hankali ta shiga ta zauna, don batama lura da shi bane tabbas dai
taga mutun ya fita cikin motar.
Tana shiga Haroon ya maida marfin ya rufe
Shida Lamiɗo suka koma sit ɗin bayan wannan sabida su a zatonsu Jabeer na ciki.

Ganin Lamiɗo ya shigane yasa duk kowa ya shiga motarshi.


Hakama Jadda ya shiga ya zauna hankalinshi na woje.
Sai da akaja motocin suka fara tafiya ne, ya juyo da sauri jin Jabeer na jan wani
ja'irin tsaki mai tare da ajiyan zuciya.
Cikin mamaki Jadda yace.
"Haaahh kai kuma Meya kawoka nan? Yaushe ka shigo min mota!?".
Bai kula Jadda ba, asalima yi yayi tamkar bai jishiba.

Haroon kuwa cikin dariya ya ɗan bugi sit ɗin da yake zaton yana wurin cikin juya
harcen Larabci yace.
"Masha ALLAH, gasar Shaɗi tayi mana rana mun rabaka da gwauranci".
Murmushi Lamiɗo yayi tare da kallon Haroon yace.
"Saura kai". Murmushi yayi tare da cewa.
"Ni ai nan kusa za'ayi".
Jin shirune, yasa Haroon yayi shiru,
Azotonshi ya ƙin mgna da shariyar ne suka zowa Jabeer bare, yasan yanzu a cike
yake.

Su Jalal kuwa kab da al'hini suke tafeyi.

Jadda kuwa yayi iya mgnarshi yayi shiru ganin bai kulashi ba.

A haka suka isa cikin Masarauta Joɗo.

Suna isa kuwa Jabeer ya fito ya nufi Side ɗinsa, fitowarsa cikin motar Jadda ne
yayi matuƙar bawa Haroon da Lamiɗo mamaki.

Haroon kuwa bayanshi yabi da sauri.

Suna shiga Side ɗinsa kuwa suka samu babu kowa.

Suna gama tsayuwa Sallama ya nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu bisa umarni Lamiɗo.

Yana shiga a babban Falon ya samu. Umaymah, Ummi, Aunty Juwairiyya, Hibba, Adda
Rumana wacce take yayarsu Jabeer yar farin Abba kenan, sai mai bin mata Rumaisa.
Kana sai Gimbiya Aminatu dake tsakiyarsu, sai hadimanta.

Koda ya sanar musu, sun iso.


Kusan duk a tare suka miƙe sai Gimbiya Aminatu ce bata tashiba da hadimanta.

Su kuwa da sauri suka nufi woje, Umaymah ce gaba sai Aunty Juwairiyya dake biye da
ita a baya riƙe da wani tire wanda samanshi ke ɗauke da al'kyabbar irin tasu ta
matan masarauta da kuma wasu sauran tarkace.
Suna fitowa motar na isowa har bakin wurin. Da sauri suka nufi jikin motar.
Ita kuwa Zuwa yanzu ta tsagaita da kukanta, sabida ababen da take gani a cikin
masarautar ya shallake tunanin mai tunani,
gaba ɗaya jikinta tsuma yakeyi, sabida idonta na gane mata ababe na ban tsoro.
Cikin ranta take mgnar zuci.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, wannan wanne irin gidane? Me yake faruwa da
mutanen masarautar? Sunko san gskyar junansu?".
Da sauri ta rumtse idanunta sabida wasu irin hayaƙi da take gani yana tashi tako
ina na gidan yayiwa gidan rumfa gaba ɗayansa.

A da sauri ta buɗe idonta jin an kamo tafin hannunta,


Umaymah kuwa cikin tsantsar jin daɗin da farin ciki maras misaltuwa tace.
"Marhababiki ya binti". Wani irin azabebben tsinkewar zuciya da firgici da razanine
ya daki zuciyar Shatu a lokaci ɗaya.
Da sauri ta ƙara ware idanunta, dan son kallon matar da take jawota tare da cewa.
"Kiyi bismillah ki fito da ƙafar dama, ki riƙe hannuna da kyau ɗiyata, ki kalleni
nan nice jagorarki ki taka ƙafarki a inda zakiga na taka tawa".
Ido ta zuba mata, tare da fitowa a hankali.
Tana fitowa bakin ƙofar Umaymah tasa hannu ta amshi al'kyabbar da Aunty Juwairiyya
take miƙa mata.
Kangeta tayi kana tasa mata al'kyabbar, sannan ta gyara mata rufuwarshi da kyau ta
rufa mata hularshi. Yadda sam mutun bazai samu damar ganinta ba.

Ga niƙab ga kuma hular al'kyabbar da lu'ulu'u danke reto a fuskarta.


Da sauri Aunty Juwairiyya ta matso tare da cewa.
"Marhabin yar uwarta, Alhamdulillah yau kam na samu yar uwa".
Adda Rumana ce ta matso kusa da ita tare da yin mgna da fillanci tace.
"Sannu da zuwa Masarautar Joɗa ƙanwata".
Adda Rumaisa kuwa murmushi yaketayi tare da matsowa, haka suka sata a tsakiya.
Jakadiyarsu kuwa sai bin takun ƙafar Shatu takeyin da ido.

A haka suka zagayeta, kana hadimai suka mara musu baya.

A haka suka isa babban falon Gimbiya Aminatu.


Suna isa Umaymah ta kaita har gabanta ta ajiyeta,
Cikin tsantsar jin daɗi tace.
"Alhamdulillah Gimbiya yau dai ga sabuwar Gimbiya dan yanzu itace amarya ba keba".
Cikin dariyar jin daɗi Gimbiya Aminatu tasa hannu ta kamo hannun Shatu da Umaymah
ke miƙa mata tare da cewa.
"Kishiya ban haushi, ta isa ta zama Gimbiya zakisa yanzu in korata woje".
Dariya sukayi baki ɗayansu.

Yayinda tuni hadimai mata suketa jere ababen maƙulashe a gaban Shatu.
Danginsu, Zuma, Madarar shanu, Da ƴaƴan itatuwa masu sanyi.
Ita dai Shatu ƙasa tayi da kanta,
tana jin fargaba da kuma tsoron wannan bahagon gidan data shigo.

Su kuwa nan sukayi ta mata hidima da nuna mata so.

Ganin magriba ta ƙara to ne yasa,


Umaymah ta jawo hannunta ta kaita wani ɗaki dake nan kusa dana Gimbiya Aminatu.

Tare da cewa.
"Yauwa ɗiyata kiyi salla. Za'a kawo miki abinci, kada kici komai sai nazo".
Cikin sanyi ta gyaɗa mata kai.
Ita kuwa Umaymah hannu tasa ta fara zare mata al'kyabbar, koda ta cire mata shi,
cikin kula tace.
"Cire niƙab ɗin, babu mai shigowa nan yanzu sai nida Gimbiya Aminatu da Juwairiyya
sai Jakadiyarsu".
A hankali tace.
"To".
Haka nan taji duk wani yarda na duniya ta sauƙeshi kan wannan kekyawar mata mai
fara'ar nan.

A hankali tasa yatsunta ta kamo niƙab ɗin ta ɗin ta yayeshi.

Wasu irin tagwayen numfarfashi Umaymah ta sauƙe tare da cewa.


"Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!!".
Da sauri ta juyo ta ruggume Jakadiyarsu a hankali tace.
"Alhamdulillah Ummin Jabeer itace. Wlh itace".
Cikin wani irin tarin jin daɗi Jakadiyarsu ta ɗan kalli Shatu, tare da yin murmushi
mai cike da ma'anoni.

Jakukkunan dake hannunta ta ajiye, kana ta iso kusa da ita ido ta zubawa fuskarta
kana tace.
"Ɗiyata menene sunanki?".
Cikin yin ƙasa da ido Shatu tace.
"Aysha".
Kusan a tare sukace masha ALLAH.
Nan Umaymah kam ta juya da sauri ta fita.

Ita kuwa Jakadiyarsu Jabeer shirya mata kayan data shigo dasu takeyi a drower'n.
Tare da bata umurnin taje tayi al'wala.

Umaymah kuwa tana fita kai tsaye Side ɗin Jabeer ta nufa.

Shiru ba kowa, da kamar duk sun tafi masallaci ne.

Aunty Juwairiyya da Hibba kuwa suna sashin Juwairiyyan.


Ummi kuwa na can wurin Shatu.

Kai tsaye ɗakin da nanne masaukin ta, ta nufa.


Bathroom ta faɗa ruwa ta ɗan watsa tare da yin al'wala kana tafito tazo ta kabbarta
sallah.

Ita kuwa Shatu zaune take bisa sallayan.


Tunda ta idar da sallan bata tashiba.
Sai kanta data jingina jikin gadon da take gefenshi.
A hankali ta rumtse idanunta tare da motsa laɓɓanta tana karatun al'ƙur'ani cikin
sanyin murya, Ummey da Junainah ne suka faɗo mata a rai shine ya sata zubda hawaye
wasu na korar wasu.
Kewarsu da begensu, ya tuno mata su Ya Gaini da marigayi ya Lado.
Ummi kuwa itama bisa sallayan take tana lazumi.

A haka har lokacin sallan isha'i yayi.

Jin wata zazzaƙar murya mai matsifar daɗi na karatun.


Hannun tasa ta share hawayenta dan jin karatun takeyi yana ratsa mata zuciya ya
tsananta zubar hawayenta.

A hankali ta miƙe itama ta kabbarta sallan isha'i.


Hakama Ummi.

Bayan an idarne. Ummi ta miƙe tsaye ta ninke abin sallan, kana a hankali take taku
har kusa da ita.
Cikin sanyi ta zauna bakin gadon tare dasa hannunta tsakiyar kanta a hankali tace.
"AYSHA kuka kikeyi!?."
Da sauri ta jujjuya kai alamar a a tana mai share hawayenta.
Cikin kula Ummi tace.
"Kuka mana kikeyi, gashi kinata zubda hawaye! Kiyi haƙuri kinji ko Aysha ki bar
kuka, in kinji kewan mamanki ki kalleni a matsayinta, in kinji kewar yayarki ki
kalli Juwairiyya a matsayinta, in kuma yayu maza kikaji kewarsu ki kalli Jalal da
Jamil a matsayinsu.
In wani abu na damunki ki gayawa Sheykh, shine mijinki kuma majiɓancin lamuranki in
kinji kewar ƙanwa mace ki kalli Hibba a matsayinta,".
Bata hafimtar kalaman wannan matar,
bare tasan me take nufi saboda babu mutun ɗaya da ta sani cikin mutanen data kira
mata.
Abu ɗaya ta fahimta Sheykh shine wanda wai tace shine mijine ko majiɓancin
lamurane, bata sanshiba bai kuma santaba ta ina zai jiɓanci lamuranta,
Shin ta yaya zata zauna a wannan gidan da tun shigowarta take ganin ababe masu ban
tsoro."
Jin tayi shirune yasa.
Ummi shafa bayanta tare da cewa.
"Jikinki na rawa zazzaɓi kikeyi ne?."
Cikin sanyin murya tace.
"A a sanyi nakeji".
Da sauri ta ɗan miƙe tare da cewa.
"To bari in rage gudun A/C'n".
Ragewa tayi kana tazo ta zauna kusa da ita.

Umaymah kuwa tana idar da sallan isha'i, ta miƙe ta dawo sashin Gimbiya Aminatu.
Tayi matuƙar mamaki ganin batun auren Jabeer ya karaɗe masarautarsu gaba ɗaya,
taki wani sashi kawo abincin amarya akeyi.

Ita da kanta da Gimbiya Aminatu sukayi ta shigar da Foodflaks ɗin abincin cikin
ɗakin da take suna jerawa a gabanta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer bayan an salla.


Ya fito kamar koda yaushe su Jalal na biye dasu a baya.
Haroon kuwa suna tafiya a jere,
suna cikin tafiya duk suka tsaya fuska a haɗe Jabeer ya juyo ya kalli gefen
hagunshi da yaji an dafa kafaɗarshi, Jadda ne ya ɗan kalleshi kana ya kauda
fuskarshi ba tare da yace mushi komaiba.
Murmushi Jadda yayi cikin sakin fuska yace.
"Ƙarfe tara dai-dai jirginmu zai tashi. Zamu koma da kawunan naku duka".
Cikin muryar dake nuna cewa yana cikin tsananin ɓacin rai yace.
"Allah kiyaye hanya". Ya ƙarishe mgnar tare da juyawa yaci gaba da tafiyarshi.

Shi kuwa Jadda murmushi ya kumayi, fahimtar Sheykh yana tsananin fushi da baƙin
cikin abinda sukayi mishi.

Lamiɗo ne ya kalli Aminin nashi tare dayi mishi alamun ya barshi.


Su tafi.

Daga nan suka juya duk suka nufi, sashin Lamiɗo, inda aka gama shirya manya-manyan
Foodflaks a tsakiyar falonshi bisa wani tattausan Turkey carpet mai masifar kyau da
taushi.

Nan suka zauna sukayi Dinner sunayi suna hira,


Tare da yaransu.

Bayan sun gamane, suka miƙe dan tafiya Airport sabinda lokacin tafiyarsu ya kusa.
Kusan a tare suke fito zuwa babban falon dake tsakanin side ɗin Lamiɗo dana Gimbiya
Aminatu.

Bayan sun zaunane, Sallama yaje ya sanarwa Gimbiya Aminatu cewa Sarki Jalaluddin
yana neman Umaymah da Amaryar Sheykh.

Jin saƙon Sarki Jalaluddin daga bakin hadimanta da Sallama ya isarwa saƙon ne yasa
ta miƙe ta nufi ɗakin da Umaymah take.

A cikin ɗakin kuwa, cikin kula Umaymah take gabatarwa Aysha da abin ci dana taɓa ka
lashe dana motsa baki.
Adda Rumana kuwa kamar tasa mata abinci har bakinta,
Itako Aysha kanta a sunkuye, ta zubawa kulolin abincin ido tana ganin ikon Allah
dake wanzuwa cikin kayayyakin cimar, da sai dai gidan wane da wanen.
Fahimtar kunya ne ya hanata cin komai yasa suka fito falo suka barta, da Umaymah
kawai wacce taketa janta a jiki ganin hakane yasa, ta ɗan yarda taci abincin kaɗan.

Suna zaune a nanne Gimbiya Aminatu ta shigo ta sanar musu saƙon sarki Jalaluddin
nan, Umaymah ta sake saka mata wata al'kyabbar cikin jin daɗi tace.
"Aysha ki saki jikinki dani, ki gaya min dukkan abinda kikeso, yanzu kinga wurin
kakanunki zan kaiki.
Sarki Jalaluddin mahaifina ne, wanda kuma shine mahaifin maman mijinki, ɗaurin
auren sukazo shida yayunmu da ƙannenmu maza yanzu zasu koma jiharmu ne.
Kinga wannan kuma Gimbiya Aminatu itace ta haifi mahaifin mijinki.
Kana Sarki Nuruddeen ɗan Sarki Bubayero jikan sarki Joɗa, shine kakan mijinki.
Mu ma mahaifiyarmu na Raye mijinki ne yasa mata suna Sitti, tana jiharmu ita bata
samu zuwaba sai daga baya zata zo".
Ajiyan zuciya tayi tare da kamo hannunta kana taci gaba da cewa.
"Mijinki ɗan babban family ne gaba da bayanshi.
A ƙalla zai ɗaukeki shekaru goma cikin masarautar Joɗa data musulmai baki gama
sanin adadin dangi da yawan yan uwan mijinki ta gefen mahaifiyarshi da mahaifinshi
ba.
Yanzu muje su ganki ki gansu."
Cikin sanyi tace.
"To Aunty".
Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
"Ba Aunty ku bace, Mijinki Malam Jabeer yafi yarda da ita fiye da kowa a dangin
mahaifiyarshi, Umaymah yake kiranta".
Kai ta gyaɗa tare da mgnar zuciya.
"Ikon Allah".
Ita kuwa Umaymah murmushi tayi kana tana hannunta suka fita.
A falo suka samu Jakadiyarsu, da sauri Umaymah tace.
"Yauwa kinga wannan itace Jakadiyarsu, itace ta rainesu tun suna yara, bayan
mahaifiyarsu babu wanda yasan halin Jazlaan sama da ita a cikin wannan masarautar,
ki kasance mai bin umarnin ta, domin itace idonki cikin wannan masarautar, Jazlaan
a matsayin uwa mahaifiya yake kallonta ba baiwar gidansu ba".
Cikin nitsuwa Aysha ta gyaɗa kai tare da cewa.
"Nagode".
Ita kuwa Ummi murmushi tayi tare da bin bayansu.

Suna isa bakin ƙofar tayi musu iso bayan ta shiga ta sanar musu da isowarsu.

A hankali suka shiga, cikin nitsuwa take bin takun Umaymah.


Ita kuwa Umaymah har gaban Sarki Jalaluddin da Sarki Nuruddeen taje da ita,
cikin shaƙuwarta dasu, ta ajiyeta a gabansu tare da cewa.
"Jadda ga amaryar Sheykh Jabeer a sanya musu al'barka".
Murmushi yayi tare da kallon Aysha. Wani nannauyan ajiyan zuciya ya sauƙe tare da
cewa.
"Allah ya sanya al'khairi ya basu zaman lafiya. Allah yasa tazo mana da hasken da
zai kore duhun daya meye hasken idanunmu".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Uncle Abdulkareem ne ya ɗan kalleta cikin sanyi yace.
"Allah yayi miki al'barka dake da mijinki ya baku zaman lfy mai ɗorewa".
Kanta ta ƙara sunkuyawa,
Ita kuwa Umaymah matsota tayi tare da cewa.
"Kinga ɗan ɗago kanki ki kallesu.
Kinga ga Mahaifina. Ga Sarki Lamiɗo".
Sai kuma ta nuna Abba dake zaune cikin murmushi tace.
"Ga wannan shine mahaifin Jabeer mamanshi kuwa sai gobe a bisa ƙaidar masarautar
keda shi Jakadiyarsu da Sallama zasuyi muki jagora ku zagaya cikin masarautarsu
baki ɗayansu a nuna miki ahlinsu to da ɗakin mamanshi za'a fara kaiki".
Kinga wannan shine babban Yayanmu sarki mai jiran gado.
Ga kuma wa ƙaninmu Abdulmumin."
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
"A a Khadijah a rana ɗaya kikeso ɗiyar taki tasan komaine? Ai abun da wuya, dole
sai a hankali zata gane mu".
Murmushi Jakadiyarsu tayi tare da cewa.
"Hakane kam. Amman gwara an gabatar mata da manya".
Sarki Jalaluddin ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"To Khadijah mu yanzu zamu wuce, ke kuma sai yaushe?".
Murmushi tayi tare da kallon gefen damanta inda Haroon ke zaune da wani kekkyawa
mutun mai matsakaici shikara.
Mi kama dashi wanda bisa dukkan alamu babanshi ne.
Kauda kanshi yayi daga kallon da Umaymah keyi mishi, cikin ƙasaita alamun shima
jinin sarauta ne, yace.
"Ni kada ki wani kalleni, bance komaiba".
Murmushi dattawan sukayi baki ɗayansu, Haroon ma murmushin yakeyi.
Ita kuwa Umaymah kauda zance tayi da cewa.
"Yauwa Aysha kinga wannan shine Haroon ɗan uwa kuma aboki amini abokin faɗan
Jabeer.
Akwai kuma ɗan yayanmu Ibrahim shine shaƙiƙin Jabeer shi yana Cairo, amman kwanan
zai dawo ki ganshi."
Jadda ne ya kuma tsareta da cewa.
"Khadijah yaushe zaki koma?".
Cikin sanyi tace.
"Jadda in Abban Haroon ya amince zanyi wata ɗaya rak, sabida ganin yadda lamuran
zasu tafi.
tsakanin yaran, ita kanta Aysha tana buƙatar makusanci tare da ita, sabida baƙonci
a irin gidajenmu abune mai wuya ga wanda ba irin gidajen ya taso ba".
Murmushi Abban Haroon yayi tare da cewa.
"Ba laifi na Amince, Amman bazaki ɗauki azumi a nan bada".
Da sauri tace.
"Na yarda".
Haroon ne ya ɗan juya idonshi alum lissafi kana yace.
"Ke nan sati uku zakiyi tunda azumin saura wata ɗaya".
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa,
Jadda ne ya kalli Jakadiya tare da bata umarnin su tafi ita da Aysha.
Gane abinda yake nufine yasa ta kamo hannun Aysha suka fita. Gimbiya Aminatu na
biye dasu a baya.

Gyaran murya Jadda yayi bayan sun fita, cikin nitsuwa da girma ya kalli Umaymah
tare da cewa.
"Alhamdulillah Khadijah, aure dai an ɗaura, duk da tarin tsana da ƙin abin da ɗan
naki keyi.
Haƙiƙa baya son wannan abun da akayi mishi. Naga fushi da tashin hankali mai tarin
yawa a ƙwayar idanunshi da fuskarshi.
Ina da yaƙini bisa halin Jabeer in ya tsani abu tofa ya tsaneshi kenan har gaban
abadan, wannan shine babban tashin hankali na,
Sabida yanada lafiya da tsayuwa kan kaifi ɗaya. Ya gayawa kakarshi Sitti babu wani
gari na duniya da yakejin ya tsana sama da wannan garin. Yace baya son garin da
mutanen garin. Sabida anci mishi zarafi a garin a gaban kafurai an tozarta shiga ta
addinin Musulunci".
Shiru sukayi baki ɗayansu, tabbas sun san hakane mgnar Jadda.
shi kuwa Jadda a hankali yaci gaba da cewa.
"Yanzu kubar Yarinyar a ta kwana a nan.
Kana a ɗan ɗaga kafa har sai an gyara mata inda zata zauna, kamar ko wacce amarya.
Sannan kada kuyi mishi mgnar auren bare ita yarinyar,
in anyi haka fushinsa bazai tsanantaba, zaici gaba da al'amuran rayuwarshi, tunda
shi mutum ne mai ibada da kuma aiyuka".
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
"In dai baza'ayi mishi mgnarta ba, to wallahi mancewa zaiyi da ita da babinta ma
gaba ɗaya".
Lamiɗo ne ya gyara zama tare da cewa.
"Ya isa".
Murmushi Umaymah tayi sabida ta lura har yau su Lamiɗo basu gama sanin Jabeer da
halaiyarsa ba.

Shi dai Jadda nan ya jadadda musu cewa, kada suyiwa Sheykh Jabeer mgnar sai an gama
gyara komai na sashinta.
Ko gaisuwar su bari sai bayan kwana uku a zagaya da ita cikin Masarautar.

Nan dai sukayi sallama suka, tafi baki ɗayansu.

Suna tafiya, Umaymah ta koma ɗakin da Aysha take, nan ta samu Ummi na zaune da ita.
Nan ta zauna ta suka ɗan yi hira ganin alamun gajiya da bacci a tattare da itane
yasa, sukayi mata saida safe suka fita suka tafi.

Ratsawa sukayi wurin Gimbiya Aminatu suka mata saida safe kana suka fita suka tafi.

Cikin tsananin jin daɗi suke tafiya, har suka iso bakin.
Mashigar sashinsa, cikin nitsuwa sukaci gaba da tafiya.
Shiru ba motsin komai suna gab da isa bakin ƙofar, suka tsaya cikin zaro ido, suka
kalli Laminu da Gimbiya Saudatu, cikin haɗe fuska da zafi Umaymah tace.
"Aoozubikalimatillahi taaa'ammati minshirin makalaƙa!."
Cikin tsantsar tsanarta Gimbiya Saudatu tace.
"A kanki hegu masu jajayen kunnuwa".
Tana faɗin haka taja hannun Laminu suka fita.
Su kuwa Umaymah da sauri sukayi ciki.

A falo suka tsaya. Ba kowa a falon haka yasa tayi sauri ta nufi arear'n Side ɗin
Jabeer, a falo ta samu Haroon konce bisa kujera.
Yana ganinta ya tashi zaune.
Cikin gimtse dariyarshi murya a hankali yace.
"Yau duk kayan ahlin masarautar Joɗa sai an yagesu baki ɗayansu."
Ya ƙarishe mgnar yana nuna mata ƙofar ɗakinshi.

A hankali ta kutsa kai cikin ɗakin tare da yin sallama.


Can ta hangoshi kan gadon yana konce rigingine, idonshi a lumshe,
a hankali takeyin taku tana nufo inda yake.
tare da mgnar zuci.
"Wato harda sharrin Haroon zayiwa ɗan Umaymah".
A hankali ta zauna bisa bedside drower'n. Idonta ta sauƙe bisa goshinsa, cikin
mamaki ta juyo ta fuskanceshi da kyau ganin yadda Goshinsa ke....!

By
*GARKUWAR FULANI*Wata iriyar zuface ke tsastsafo mishi bisa
goshinsa,
Kamar an watsa mishi ruwa.
Ya kamo lip ɗin shi na ƙasa yana taunewa.
Hannunshi dake cikin blanket ta zubawa ido.
Dan son gano abinda yakeyi,
shiru tayi sawon 5 minute kana, a hankali ta ɗaura tafin hannunta kan goshinta,
tare goge mishi zufar, daketa tsastsafowa duk da sanyin A/C dake ratsa ɗakin.
Idonshi ya saisaita lumshe su da yayi, ya sani Umaymah ce.
sabida babu mai shigar masa ɗaki kai tsaye sai ita.
Babu kuma mai taɓa mishi goshi haka sai ita.
Cikin kula tace. "Jazlaan!".
A hankali ya gama buɗe idanunshi da sukayi jazir alamun tarin ƙuna da yakeji a
ransa.
A hankali tace.
"Jazlaan!." Ta kuma kiranshi a karo na biyu.
A hankali ya motsa lips ɗin shi alamun zai amsa mata.
Amman Ina zafin da zuciyarshi keyi ya danne harshensa hafimtar hakane yasata, nuna
damuwarta a hankali tace.
"Kaci abinci?". Ƙarya ba ɗabi'arsa bace ba kuma halittarsa bace, duk ɗacin gsky zai
faɗeta, bare a kan kashi.
Kanshi ya girgiza alamun baiciba.
Cikin sanyi tace.
"To Muje kaci koda abu mara nauyi ne!."
Da ƙarfin ya fizgo mgnar.
"Bazan ci ba".
Ta sani yadda yayi mgnar, ta kubce masane, dan in ransa a ɓace yake baya mgna,
ɓacin ran mai limini kenan babu faɗe-faɗe bare hargowa ko buge-buge.
Sanin ko ya zatayi bazai cin bane, kamar yadda ya faɗa mata yasa,
ta miƙe a hankali kanshi ta shafa tare da cewa.
"Saida safe".
Kai kawai ya iya gyaɗa mata,
Haka ta fara tafiya, tana kallon yadda yake motsa hannunshi cikin blanket tabbacin.
Wani abun yake yagewa.

Yadda ta bar Haroon haka ta sameshi saida safe tayi mishi kana ta wuce ta tafi.

A can Rugar Bani kuwa. Kamar yadda Ba'ana ya ɗaukarwa kanshi al'ƙawari haka ya bar
ƙasar ya nufi ƙasar Cameroon Kai tsaye Yahunde ya nufa, cikin rugagen Fulani, yana
tafiyarne da ɗan sauran tsafi da sihirin dake jikinsa.

A haka ya nausa cikin ƙasar Cameroon da yake jihar Ɓadamaya tana bakin bodar ƙasar
ne.

Fulanin Rugar Bani kuwa, a daren wannan ranar sukayi gangamin ramuwa, suka faɗawa
ƙauyukan kafuran ƙabilun ɓacamawa dake cikin Shikan da kewayenta.
Allah ya basu nasarar yaƙan kafuran nan.
Har suka samu damar ƙona ƙauyem Bonon wanda shine zuciyar ƙabilar ɓachama, kamar
yadda Abuja take zuciyar Nigeria.
Cikin daren suka ƙona ƙauye dama dodon tsafinsu Bonon da suka ɗauka a matsayin
Ubangiji su sun ƙonashi sun ɓadda shi a doron duniya sai dai tarihinsa.

Wannan labarin shine labarin.


Da gidajen rediyo dana tv da jaridu sukayi.
Breakfast dashi yayinda akayita kuzuzuta cewar Fulani sun zama ƴan ta'adda sun
farma garuwa da yaƙi.
Uhummm wannan shine halin da Fulani ke rayuwa a ciki. A zalimcesu, kaji cib duniya
babu mai yin mgn su kai ƙorafinsu a koresu. Gwamnatin kasar data jiha suyi kamar
basujiba. In fulanin sun rama na lokaci ɗaya sai asa musu sunan ƴan ta'adda ko yan
tada zaune tsaye, har ana ikirarin korarmu.😭😭😭

Hankalin ƙabilun Ɓacamawa dake cikin Shikan duk suka ari ta kare.
Hausawa da Fulani kuwa kowa ya koma, cikin gidansa.
Domin Allah ne yabi kadunsu.

Sarkin Shikan da kanshi yayi masifar girgiza da yawan da Fulani sukayi cikin
garinshi da kewaye.
Gashi an ƙone dodon tsafinsu nasu kuma babu abinda ya samu fulanin.
Hakane yasa shi kanshi ya arce, sai abu ya lafa ya dawo.

Su kuwa Fulani bayan sun gama.


Suka tsaya suka bawa yaransu da tsoffinsu mafaka, domin su basu kashe yara da
tsoffi da mataba.
Anyi an gama, kafin hukuma tazo, ta ƙara sai saita Komai.
A cikin masarautar Joɗa kuwa. Washe gari da safe.
Lbrin ya rinski Sarki Nuruddeen, shine ya bada umarnin kada a kama bafulatani ko
ɗaya.

Aysha ce zaune gaban Umaymah Aunty Juwairiyya na gefenta ita da Hibba, cikin kula
Umaymah tace.
"Yauwa Aysha kinga wannan ki ɗauke ta matsayin yayarki ita ɗin yar babban Yayanmu
ne wanda na nuna miki jiya.
Mijinta kuma ya'yan Jabeer ne, Side ɗinta na kusa da naku.
In kinga duk wani abun da baki fahimta ba ki tambayeta, in kin gaji da zaman
kaɗaici zaki iya shiga wurinta, da wurin Mamanku, da kuma nan wurin Gimbiya
Aminatu".
A hankali ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya, tare da cewa.
"Ina kwana Aunty". Cikin jin daɗi Aunty Juwairiyya tace.
"Lfy lau ya baƙunta". A hankali tace.
"Alhamdulillah!".Hibba ce ta ɗan tsuke baki cikin sanyi tace.
"Shike nan ai, an gabatar mata da kowa sai ni aka ware".
Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa.
"To Aysha ga Hibba wutar Umaymah, duk family itace auta a jikokin Sitti na nan
ƙasar".
Murmushi ta ɗan yi sabida ganin yadda Hibba tayi sai Junainah ta faɗo mata a rai.
Ita kuwa Hibba motsata tayi tare da cewa.
"My happiness".
Cikin murmushi Aysha ta nuna kanta, alamun "Nice my happiness?".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Yes haka Umaymah tace wai kece farin cikin ahlimu da izinin ubangiji".
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta.
Haka nan taji tana jin sonsu a ranta, Especially Umaymah da Hibba.
Aunty Juwairiyya kuwa da Ummi breakfast Suka gabatar mata, kana suka fita.
Umaymah da kantane ta haɗa mata tea mai kauri ita da Hibba kana ta zuba musu
abincin da Aunty Juwairiyya ta kawo musu tare da cewa.
"Bismillah kuci abinci".
tana faɗin haka ta miƙa ta fita,
Ita kuwa Hibba da tsauri ta gyara zamanta tare da ɗaukan Fork ta matso gaban plate
ɗin da aka zuba mata soyyyan dankali da kwai, hannun tasa ta soki guda biyu tare da
ɗagowa zata kai bakinta, sai kuma ta tsaya tare da zubawa Aysha ido ganin ta riƙe
mata hannunta.
Cikin sanyi da ɗan sakin jiki da Hibba ta girgiza mata kai tare da cewa.
"Kada kici wannan abincin".
Cikin juya ido Hibba tace.
"Meyasa!?".
Kai ta jujjuya mata kana ta gyara zamanta, tare da ɗan kallon ƙofar shigowa ta
gefen idonta.
Wani kekyawan Foodflaks da aka kawo daga sashin Gimbiya Saudatu ta jawo tare da
cewa.
"Ki ɗiba a nan kici". Cikin mamaki.
Hibba tace.
"Aunty Aysha, ai Bama cin abincin gidan Gimbiya Saudatu, kuma naga Hadimanta ne
suka kawoshi".
Cikin rashin gane manufar zancen Hibba tace.
"Meyasa bakwa ci?".
Juyawa Hibba tayi ta kalli bayanta kana ta juyo ta kalleta da kyau kana a hankali
tace.
"Bata son Hamma Jabeer dama duk ƴan uwanshi, cewa take zata kasheshi in ta samu
dama, shiyasa Umaymah take hanamu cin abinci ta".
Wani irin nannauyan ajiyan zuciya ta sauƙe tare da kallon Hibba cikin cushewar
tunani ta kalli jerin kulolin da a ƙalla sun kusa takwas a gabansu.
Cikin sanyi tace.
"Buɗe su mu gani".
Jin hakane yasa Hibba buɗe su ɗaya bayan ɗaya.
ita kuwa ido take zubawa duk kular da Hibba ta buɗe.
Kular ƙarshe wacce ke ɗauke da Chicken Ball's mai zafi sai turiri yakeyi da ƙamshi.
ta nunawa Hibba tare da cewa.
"Kici wannan".
Murmushi Hibba tayi kana tace.
"Yauwa shinema na Gimbiya Aminatu kuma ta iya girki tsohuwar hakana hadimanta, a
plate ta zu musu. Kana suka faraci suna ɗan korawa da ruwan tea mai zafi da kauri.
Sunaci Hibba nata janta da hira duk da ita Aysha zuciyarta a cushe yake.

Bayan sun gamane, Hadiman Gimbiya Aminatu suka shigo suka tattare komai suka gyara
wurin bisa umarni Jakadiya.

Ganin Aysha ta ɗan saki jiki da Hibba ne yasa, Umaymah ta wuce Side ɗinsa ita da
Umminshi.

A falo suka samu Jafar, Jalal, Jamil, Haroon. Suna bisa kujerun Dinning area, Aunty
Juwairiyya tana zuzzuba musu abincin.

Murmushi Umaymah tayi cikin jin daɗin ganin su, da wal-wala hatta Jalal fuskarshi a
sake take.
Jamil ne ya kalleta lokacin data ƙara so kusa dasu, cikin murmushi yace.
"Umaymah mu sai yaushe za'a nuna mana Amaryar a gabatar mata damu, ta sanmu da
kyau".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Ai ku tun daren jiya nagabatar da sunayenku da matsayinku gareta".
Haroon ne ya ɗan kurɓi tea tare da cewa.
"Yo ai Ni dai ba sai an gabatar daniba, domin nasanta tun safiyar jiya kafinma a
ɗaura auren ko Jalal?".
Taɓe baki Jalal yayi tare da cewa.
"To ni mamaki nakeyi, ko dai dama ita tazone dan taga wanda za'a aura mata".
Umaymah ce ta ɗan zauna kusa da Jafar tare da kallonsu kana tace.
"Babu sam ita kanta bata saniba bata zata ba bata tsammaci aurenta a jiyaba.
Sai dai arashi kukayi, Ni tun jiya da kuka gayamin nasan arashi ne kawai ya haɗaku
a asibitin. Bata san komaiba akan auren nan hakama iyayenta, basu da zaɓine kawai
dan sun san ƙa'idar gasar Shaɗi ne hakan yasa sukayi haƙuri."
Kai Jalal ya jinjina tare da cewa.
"Uhummm mu dai yanzu yan kallone. Dan na sani tabbas yanzu za'a fara buga Game ɗin
yanzu wasan zai soma".
Cikin yin ƙasa da murya Jamil yace.
"Sosai ma, dan kuwa akwai kitimurmurar da za'ayi a masarautar Joɗa, wannan Ustaz
Sheykh Malam akarmakallahu Hamma Jabeer ɗin, salonshi na dabanne a dukkan lamuran
yauda kullum wannan auren dai zamuga ya zai kasance!". Ya ƙarishe mgnar da yin ƙasa
da murya sosai, yanayi kuma yana kallon hanyar falon Sheykh Jabeer.
Cikin haɗe fuska na wasa Umaymah tace.
"Al'khairi shine zai wanzu".
Murmushi Haroon yayi tare da cewa.
"Inafa al'khairi a wannan abun da bashi da tushe, ni kaina naji baƙin cikin wannan
al'amari, auren Muhammad Jabeer ya zama kamar a munafuce a ɓoye babu wani shiri
bare kimtsi kun bari an auro mishi mace kamar auren ƴar tsana".
Jafar kam abincinsa yakeci, ba tare da ya kulasuba.
Jamil kuwa sai murmushi yakeyi.
Jalal kuwa shiru yayi alamun nazari.

Ummi kuwa ware wasu kyawawan Foodflaks takeyi gefe.


Tare da abinci a cikinsu.
Bayan ta gamane ta ajiyesu gefe.
Tare da cewa Umaymah.
"Ga breakfast ɗin Sheykh".
Kai Umaymah ta gyaɗa mata.

Nan sukaci gaba da hira.

A can Side ɗin Mama kuwa,


Tunda batun auren Jabeer ya basu ya riski kunnuwan ahlin masarautar Joɗa,
kowa da abinda ke ransa.

Batool kuwa hankalin Mama in yayi dubu ya tashi, bisa irin kukan da Batool ketayi
har cewa takeyi ta gane ai dama Mama bata son ya aureta.
Da kyar ta samu tasha kanta,

Gimbiya Saudatu kuwa, da Baba Nasiru da Baba Basiru da Laminu.


Zaman gaggawa suka tanada.

Suna tattauwana wannan baƙin lbrin da bai musu daɗi ba.

Zaune yake gaban wani ƙasurƙumin boka matsafi.


Cikin tsantsar tashin hankali da kiɗima yace.
"Boka Tsitaka haka mukayi da kai? Yaushe ka fara min ƙarya kan aiyukan da nake
baka? Ya za'ayi kwatsam rana tsaka ace wannan shegen yaron da nakeji tamkar in
kasheshi yayi aure? Da kai mukayi mgna a nan tsawon shekaru kace min ka, kashe min
wutsiyar ɗan iska mai jajayen kunnuwa, babushi ba mace har yaumal ta ƙunun nadi.
Ka bani tabbacin. Har gobe sihirin na bibiyarshi, kace min duk sanda zanen kan
macijin ya isa kan tsaitin ƙahon zuciyarshi zai mutu kowama ya huta. Sai kuma jiya
kamar sauƙan aradu ace yayi aure!".
Wata iriyar razanenniyar dariya mara daɗin amo boka Tsitaka ya kece da ita, wanda
har saida tsaunuka da kwazazzaban dake wurin suka amsa amonta.
Dariyar mugunta yakeyi babu ƙaƙƙautawa, har saida baƙon nashi ya fara hatsala cikin
tashin hankali yace.
"Wannan ai insakanci ne, in bazaka iyaba ina nemo wasu matsafan. Ya zan zo da
matsalata da sanyin safiyar nan kai kuma ka kama min dariya, Ni mahaukacin gidanku
ne?".
Cikin dariyar boka Tsitaka yace.
"To ai tashin hankali na banzane, kana kokonto kan aikin da shekaru goma sha biyu
yana cinsa yana bin jikinshi. Kana zaton ya karye ne? To bari kaji wannan sihiri
yana nan a jikinshi, har kwanan gobe wutsiyarsa bata harbawa, baya jin kanshi a
namiji.
Ba kuma zaiji yadda maza kejiba har abadan.
Iya bincikena banga mai mgnin da zai gani aikin da mukayi mushiba.
Auren da akayi mishi, da ya sani tabbas da zai watsa abun. In kuwa kana zaton
sihirin yana sauƙa kaje ka dubu, zanen bindin maciciyar da yake tun daga kan ƴar
babbar ƴatsar ƙafarshi ta dama, zaka samu kan macijiyar ya ƙetare ƙugunshi.
Na kuma gaya maka duk sanda kan macijiyar ya isa kan ƙirjinshi, saman nononshi, zai
mutu, kuma yadda zai bar duniya haka ƙannenshi da wanshi zasubar masarautar Joɗa
har abada yadda ba'a tambayi yaushe matacce zai dawo duniyaba haka suma baza'a
tambaya ba."
Cikin ɗan jin daɗi baƙon bokan yace.
"To ai dole hankalina ya tashi, kaida kace min bazai wuce shekaru biyar ba zai rasu
gashi yanzu shekaru goma sha biyu bai mutuba".
Cikin zare ido boka Tsitaka yace.
"Kai ai mun ma yi dacen yin asirin da wurine, tun kafin ya gama girma da yanzune
sam bazai kamashiba, mutumin da baya rabuwa da sunan Allah a bakinshi. Yaronda ko
yaushe da al'wala yake zama, ai badan hakaba da tuni mun hallakashi".
Cikin ɗan samun nitsuwa baƙon ya direwa Boka Tsitaka kuɗi kana ya miƙa ya fice.

A can wurinsu Umaymah kuwa.


Suna cikin hira, Umaymah ta ɗan juyo a hankali ta kalli hanyar fitowa falon Sheykh
Jabeer, sabida jin ƙamshin turaren shi.
Murmushi mai cike da jin daɗi tayi ganinsa cikin shiga ta al'farma, kamar yadda ya
saba.
Wata jallabiya blue color ce mai taushi a jikinshi.
Sai al'kyabbar da ya ɗauka samanta shi kuma peach brawn mai ɗan karen kyau sai
sheƙi yakeyi,
kana sai hira minshi shima Peach brown da ɗigo-ɗigon white.
Sai takalmansa sau ciki masu kyau, baƙaƙe kana sai ɗan abun saman hiramin shima
baƙi.
Taku yakeyi cikin nitsuwa da haiba da kamala, fuskarshi cike da kwarjini da
ƙasaita.
Hannunshi na riƙe da Tab ɗinshi.
Idonshi na kanta yana sarrafata da hannun damanshi yayinda hagunshi ke riƙe da ita.
Sai wani irin ƙamshi yake bazawa a duk inda ya wulga.
A hankali yake taku amman da alamun sauri yakeyi.
A tsakiyar falon ya tsaya, tare da kallon inda suke zaune.
Ganin Umaymah ta nufoshi ne yasashi gyara tsayuwarshi.
Tare da ɗan kallon ta, kana yana mai amsa gaisuwar su. Jalal da Jamil.
Tana isowa inda yake ya ɗan kalleta, cikin yanayin rauninshi dake baiyana in yana
gabata, a hankali yace.
"Umaymah ina kwana".
Cikin kula tace.
"Lfy lau Alhamdulillah Jazlaan ya gajiya da jikin!".
A taƙaice yace.
"Alhamdulillah". Sai kuma ya ɗan juya yayi taku uku zuwa biyar ya isa Dinning area,
kana Umaymah na biye dashi.
Dafa kujerar da ya Jafar yake a kanshi yayi tare da sunkuyowa ya kalli fuskarshi da
kyau, sai kuma ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin kauda kanshi a kanta yace.
"Ya jikin nashi?". Cikin sanyi tace.
"Alhamdulillah jiki kam da sauƙi sosai, dan tunda ka dawo zaiyi baccinsa lfy ba
tashin hankali in lokacin tashinsa yayi kuwa ba hargowa zai tashi yayi al'wala yayi
ta nafilfilinshi".
Cikin yanayin jin daɗin zance yace.
"Alhamdulillah. In sha Allah komai zai dai-dai-ta domin babu cutar da bata da
waraka sai dai ina ba'a gano mgninshi ba".
Hannunshi ya gyara da kyau yadda Jafar zaiji daɗin riƙon da yayi mishi.

Umaymah kuwa cikin daƙile fuska tace.


"Zauna kaci abinci".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalleta, cikin tonƙoshe kai bisa kafaɗunshi ya ɗan taɓe baki
kana a hankali yace.
"Sai na dawo".
Shiru tayi sabida ta lura sauri yakeyi.
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Jakadiya cikin sanyi yace.
"Ummi lfy kuwa na ganki haka ba walwala".
Nisawa tayi tare da cewa.
"Ina fa zanyi wal-wala bayan Sheykh na cikin yanayin fushi, da rashin jin daɗi
alamun na gaza riƙe amanar da uwar ɗakina ta danƙamin kenan".
Wani ɗan guntun tsaki yaja tare da kallonta da kyau cikin sanyi yace.
"Ba komai Ummi kin riƙe duk amanar da aka baki, ba matsalar komai fa".
Cikin ɗan sakin fuska tace.
"To Alhamdulillah, yanzu ina zuwa?".
Bayan Jalal ya ɗan matso tare da cewa.
"Vallai zan je inada zama na musamman da sauran likitocin, domin jaddada musu kula
da marasa lfyan da aka kai jiya".
Kusan a tare sukace to Allah ya taimaka".
Amin yace a taƙaice kana ya tsare Jalal da ido cikin tuhuma yace.
"Jamil jiya ina ka kwana?."
Cikin mamakin ya akayi Hammanshi ya gane bai kwana a gidaba ya ɗan sunkuyar da
kanshi cikin sanyi yace.
"Club naje to bamu taso da wuriba ne, sai na biya gidansu a bokina Hayatuddeen na
kwana a can".
A hankali yasa hannunshin ya kamo kunnenshi tare da matseshi da yatsu sa biyu.
Da ƙarfi Jamil ya saki ƙara tare da cewa.
"Wayyo Hamma Jabeer bazan sakeba, na tuba".
Bai sakeba sai ma kauda kanshi da yayi yana kallon Umaymah cikin rauni yace.
"Kinji ba, shi kullum yana Club music sai kace ɗan ma kaɗa ko maroƙa, yaje ya kwana
cikin yan iska azo ayi ta musu video ana yaɗawa duniya, ana liƙa sunana a ƙarshen
sunayensu a social media kamar nine uban daya haifesu.
Haka kenan zanyi ta fuskar ƙalubale ina rasa yadda zan karesu ko in zagesu."
Ya ƙarishe mgnar rai a ɓace.
Ita kuwa Umaymah faɗa ta fara yiwa Jamil.
Shi kuwa gaban Jalal ya tsaya tare da kafeshi da ido.
Cikin tura baki Jalal ya fara bayani ba tare da an tambayeshi ba yace.
"Shiya shiga sabgata Ni kuma na dakeshi".
Cikin nuna ɓacin rai yace.
"Da yake kaine sarkin duka, ko kunyan Baba Kamal bakaji ba, ka kama Salis da duka
kawai dan ka wuce da MP kana danna waƙe-waƙe da suɓale wonɗo shine tsokanar?".
Cikin yin ƙasa da kai yace.
"To ai zaginka yayi wai ilimi ka na banza tunda gamu a lalace bakayi mana wa'azi
mun shiryuba, shiyasa Ni kuma na mishi aikin wanda ba shiryayyu ba".
Kwaffa yayi tare da cewa.
"Zagi kuma na nawa? Ba kune ke jazamin zaginba, kada ka yarda in sake jin ka taɓa
shi Uhummm!".
Ya ƙarishe mgnar da kwaffa.
A hankali Jalal yace.
"Kayi haƙuri in sha Allah bazan sakeba".
Nan duk suka nufo cikin falon.
Suna isowa Hajia Mama na shigowa Batool na biye da ita a gefe.
Jafar kuwa da sauri ya koma bayan Sheykh tare da riƙe hannunshi ya fara ja alamun
su tafi.

Shi kuwa Sheykh ƙara tsuke fuskarsa yayi ganin Batool cikin sauri ya gaida Mama, ta
amsa fuska a sake tare da sanya masa al'barka.

Kana ya nufi hanyar fita, da sauri Jafar yabi bayanshi.

Umaymah kuwa da Ummi da Juwairiyya da Batool nan suka zauna suna ɗan hirarsu.

Jalal kuwa da Jamil a tare suka fita, shi kuwa Haroon falon Jabeer ya koma.

Yana shiga ya kira Jannart bayan sun gaisa take tambayarshi yaushe zai je
masarautarsu nan yake ce mata.
Yana nan tafe a satin nan.

Shi kuwa Sheykh Jabeer yana fita kai tsaye Valli Hospital ya nufa.

Asibitinshi mai zaman kanshi.


Asibitin da duk nahiyar Ɓadamaya babu kamarshi.
Asibitin da in kana cikinsa zakayi zaton a ƙasashen turawa kake.

Haka lamarin yaci gaba da tafiya.


Babu mai yiwa Sheykh Jabeer batun Aysha.
Itama Aysha gani take kamar ziyara tazo ba aureba.
Tunda ita dai da idonta bata taɓa ganin mijinba, sai dai taji sunanshi.

Sosai ta shaƙu da Hibba da Umaymah, hakama Gimbiya Aminatu da Ummi.

Lokuta da dama takan shiga Bathroom tai ta kuka sabida begen ƴan uwanta.

Yau kwananta uku cur a gidan.


Idonta ma baiga ranaba.

Umaymah kuwa a sashin Jabeer yana fita.


Wata tirela ta iso har bakin Side ɗin shi.
Nan aka fara sauƙo da kayayyakin ɗaki na amare.
Ana shigarwa ciki. Kana masu aiki na ɗaure komai suna kimtsashi.

Sai kusan la'asar suka gama komai kafin.


Suka tafi kana su Umaymah suka taho.

Suna shiga asalin babban falon, Aunty Juwairiyya da Hibba suka haɗa baki wurin
cewa.
"Wow masha Allah, Kai Umaymah ƙara so da sauri kiga falon nan yadda ya zama fadar
masarauta".
Da sauri Umaymah da Ummi suka ƙara so.
Masha Allah! Masha Allah!! Masha Allah!!! Shine abinda kawai Umaymah keta mai-mai
tawa, sabida kyau da tsaruwan falon yayi masifar kyau.

Kasan cewar falon irin ƙaton nanne mai faɗi da tsawo.


Wasu irin kujeru ne Daimond set masu masifar kyau da tsada, a shirya a cikin
tamfatsen falon.masu Golding color mai ɗan karen sheƙi sai surkin Brown color mai
sheƙin gaske da ratsin ruwan madara..
Kana haka ma kalan labuyen falon masu tsawo da faɗi da taushin gaske.sai wani table
na glass mai Golding color da aka ajiye a tsakiyar falon bisa wani tattausan carpet
mai azabar kyau.
Sai wani babban Tv dake liƙe a jikin bongon, kana gefen dama kuwa wani babban
majigine manne wanda yake baiyana rubutun Kur'ani reras daki daki.

Can gefen kuwa steps ɗin hawa Dinning area ne,


wanda aka canza Dinning table and chairs ɗin,
Aka zuba wasu masu masifar kyau da tsadan gaske.

Ba'a wani cika falon da tarkace ba, amman yayi matuƙar kyau.

Tafiya kaɗan zakayi ta gefen hakun zaka ratsa cikin wani madaidaicin falo.
Yayinda na Jabeer yake hannun dama.
falon ɗakin da Umaymah ke tsauƙa in tazo kenan.
2 bedroom ne wannan falon yake dashi ko wanne da bathroom a ciki.
Kana sai Dinning area matsakaici daga nan gefen Dinning area kuma akwai ɗan ƙaramin
corridor wanda zai sadaka da kitchen da store.
wasu irin datsa-datsan kujeru masu masifar kyau da ɗaukar hankali aka kimtsa a
falon wanda komai na ciki.
Peach and white coffee ne mai ɗan karen kyau.
Hakama Dinning table and chairs ɗin.
Still labulayen ma hakane.

Sai kuma cikin bedroom ɗin wanda duk girmansu ɗaya, haka yasa aka shirya wasu
tagwayen gadaje masu masifar kyau suma Golding color ne mai sheƙi da ɗaukar ido.

Saɓanin side ɗin Jabeer komai Sky blue and white ne, wanda hakan yasa kana shiga
sashinsa sai kayi zaton a sararin samaniya kake rayuwa.

Komai yayi kyau.


Especially kitchen ɗin dake matsakaicin falon.

Domin wancan kitchen ɗin dake babban falon ba'a taɓa shi ba, hakama Side ɗin
Sheykh.

Sai kuma sama wanda shi a rufe yakema, sam babu kowa a ciki.

Sosai fa su Umaymah suka yaba da kyan shirin da akayiwa wurin.

Nan suka zauna a falon.


Umaymah ce ta kalli Jakadiya cikin sauƙe numfashin tace.
"Alhamdulillah, gobe kuma zakiyi musu jagora shida matarshi su zaga ta gaida ahlin
masarautar Joɗa, ta gansu su ganta su san juna, gudun kada a haɗu a wani wurin ba'a
san junaba".
Wani gwauron numfashin Ummi ta sauke tare da cewa.
"A nan gizo ke tsakar ko ta ya zamu samu, Sheykh yayi wannan al'adar yadda ya dace
ake kuma yinta, kinsanshi mutunne mai kunya, koda yana son abunma bare ba wani son
abun yakeyi ba".
Cikin yarda da kai Umaymah tace.
"Kada ki damu yana ɗaya daga cikin dalilin da yasani, na zauna sai naga kamun
ludeyin zaman nasu."

Haka dai suketa tattaunawa,


Suna nan zaune Gimbiya Saudatu ta shigo tare da hadimanta, kana da Laminu da Baba
Basiru da Baba Nasiru.
Cikin isa da ƙasaita ta nufi kujerar da duk canjin da akayiwa falon ba'a canzashi
ba sabida kujerace ta masarautar Jalaluddin, cikin isa take taku yayinda ta bawa
ƙofar shiga baya.
Cikin gatsali ta kalli Umaymah data tsareta da ido. Kallon uku saura tayi mata kana
tace.
"Duk mutun muna fuki abin tsorone. Amman munafurcin balaraben Mutun yafi na kowa
muni da bada tsoro.
In banda salon munafurci ayi aure yau kwana uku a gaza fito da amarya a nunata ga
mutanen masarauta, bare a fanshi idonta."
Ta ƙarishe mgnar tana kai mazaunanta bisa, Kujerar.
Sai kuma tayi maza ta miƙa, jin muryar Jabeer da yanzu ya shigo, ko mgnar ta, ta
ƙarshe baijiba.
Cikin isa da ƙasaita da rashin tsoronta, da kuma tsare fuska alamun Ni bani da
lokacin ki, kuma ni ba sa'an yinki bane ya nuna mata hanyar fita da yatsarshi tare
da yamutsa fuska cike da ƙarfin zuciya ya kalleta ita da ƙannen Mahaifin nashi
yace.
"Fice min daga gida, bacci na dawo zanyi so banda lokacin jin ihunku na kar...!

By
*GARKUWAR FULANI*"Kamar tsoffin karnuka". Cikin fusata Gimbiya Saudatu
ta miƙe tsaye tare da nufo inda yake.
Shi kuwa kanshi ya jinjina tare da cewa.
"Kinyiwa kanki Garkuwa da kika tashi daga kan kujerata".
A hatsale tace.
"Wai kai a zatonka tsoronka nake jine ko meye?".
Da sauri ya jujjuya mata kai tare da tsuke fuskarsa alamun baison sautin amon
muryanta da take ɗaga mishi, a daƙile yace.
"A a, na isa inyi zaton tsorona kikeji. Ke da bakinji tsoron Allah'n daya halicce
ki bama, ina zakiji tsoron wani bawa nashi, ai masu tattausan zuciya suke tsoro".
Hannu Baba Nasiru ya ɗago da alamun zai kifeshi da mari.
Ba zato yaji ya kama hannunshi, kana ya ɗan juyo fuskarshi gareshi, cikin
sakekkiyar murya yace.
"Wai ku meyasa bakwa gane, yare da harshenmu na bani adam ne? Meyasa kukafi son
Yaren dabobbin marasa hankali, a zatonka ka kai matsayin da zaka ɗago hannunka ka
mari fuskanta?".
A hatsale ya fuzge hannunshi tare da cewa.
"Da uwarka kakeyi, kasan wacece dabbar ai!. Ɗan hegiya mai jajayen kunnuw..!".
Shiru yayi bai ƙarisa mgnarba ganin wani irin kallo da Jabeer ke mishi, ido cikin
ido.
Kana ya ɗaga hannunshi na dama, yana ɗan buga bayan tafin hannun damanshi cikin
tafin hannunshi na hagu.
Still idonshi na kan fuskar ƙanin Mahaifinshi, miƙar da tafin hannunshi yayi, tare
da mishi alamun datsa a cikin tafin hannunshi, kana cikin danne fushinsa, dan baya
son su gane abinda ke masifar ci mishi rai, sai dai duk danniyarsa ya rigada, sun
gane babu abinda ya tsana a duniya sama da azagar mishi mahaifiyarshi bare a
suffantata da ƙaddararta, da binta da kalaman bita da ƙulli.
Baba Basiru ne, yayi wani irin dariyar mugunta kana ya ɗan matsa baya kaɗan cikin
izza yace.
"Datse mana wuya zakayi, dan a zagi waccar munafukar da Allah ya nuna mata ishara
tun a duniya".
Murmushi mai rauni yayi kana yace.
"Mahaukaciyar tsohuwar ku ko! Eh na gane lallai kam, batunka haka yake".
Cikin fiffiƙewa suka fara kumfar baki ina dalilin zaicewa uwarsu mahaukaciyar
tsohuwa".
Daga nesa za'a iya jiyosu.
Shi kuwa ko Aunty Juwairiyya dake Dinning area bata jiyo abinda yake faɗa.
Domin cikin nitsuwarsa yake zaro musu, duk amsar mgnar da sukayi mishi tunma kafin
harshensu ya huta.
Gimbiya Saudatu kuwa, a masifance tace.
"Ai asirinku zai tonu nan bada dadewa ba, munafukar kakar takace, tayiwa
mahaifiyarsu asiri ta haukatata dan baƙin kishi irin nata".
Murmushi yayi ganin yadda ƙannnen mahaifinshi keta ihu uwa karnuka.
Allah ya sani lamarinsu yana bashi mmki har yau ya rasa me yayi musu mai zafi a
duniya da suke gaza danne tsanarshi a aransu.
Me Mahaifiyarshi tayi musu da suke masifar tsanarta?.
Kanshi ya juya ya kalli Umaymah daketa murmushi mai cike da jin daɗin yadda yake
komai a nitse.
Juyawa yayi zai nufi gefen hanyan falonshi.
Sai kuma ya ɗan tsaya ganin Gimbiya Saudatu tasha gabanshi.
Cikin danne shakkarsa tace.
"A haka zaku ƙare. Komai na muna furci, anje anyi aure a muna furce a ɓoye, sannan
an kawota yau kwana uku kenan an kasa fito da ita a nunawa mutane ita, dan masifar
rashin gsky.
Ko dai cikin shegene da ita yasa kuke ɓoyeta."
Da sauri Umaymah ta ƙara so inda suke, cikin tsuke fuska tace.
"A kanki shege zai samu, in sha Allah bazai samu a tsatson yar uwata ba, kin kuma
yi gaggawa, da yake dama aikin shaiɗan ne dole zakiyi ta aikatashi.
Ki koma ki wanke idonki zai kawo miki Amaryarshi matarshi kuma uwar ƴaƴan shi, har
Side ɗin ki, cikin falonki, har gaban ki.
Kinaji zai gabatar mata ke da munanan ɗabi'unki dan tasan irin zaman da zatayi
dake".
Laminu ne yace.
"Ke kuma waya kasa dake, ki bari ƴan gida suyi mg...!".
Wani irin tsalle yayi ya koma baya, jin marin da Jalal wanda yanzu ya shigo ya kifa
mishi ta bayanshi.
Da sauri Baba Nasiru da Baba Basiru suka juyo kan Jalal, alamun wai zasu dakeshi.
Karkata kai yayi ya kallesu da gefen ido.
Kana a hankali yasa hannunshin ya ɗaga rigarshi, wata ƴar madai-daiciyar bindiga AK
47 ya zaro a ƙugunshi .
Wani irin wawan birki sukaja, tare da cewa.
"Eh lallai babu shakka masarautar Joɗa ta raini tantirin ɗan ta'adda bindiga, wato
abin har yakai ka matakin riƙe bindiga".
Kanshi ya tankwashe tare dasa bakin bindigar yana sosai tattausan sajenshi irin na
Hamma Jabeer ɗin shi.
Kana da bakin bindigar ya nuna musu hanyar fita.
Ai a jere suka juya suna fita.
Gimbiya Saudatu na cewa.
"Duk wanda yaci tuwo dani, tabbas miya zaisha.
Amaryar munafurcin a fito da ita mu ganta in an taki gsky".
Laminu ne ya amshi zancen da cewa.
"Menene ma abin gani a Bororiyar daji".
Da haka dai suka fita.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo na tuhuma, da tarin mamaki yakeyiwa Jalal.
Bindiga a hannunshi, shi kuwa Jalal ganin yadda duk suka zubawa bindigar idone
yasashi.
Meda ita cikin rigarsa.
Kana ya juya da sauri ya nufi hanyar fita.
Jabeer bai ce mishi komaiba.
Yana ganin ya fitane shi kuma ya juya, ya nufi falonshi.
Bedroom ya wuce, a hankali ya zauna bakin gado,
tare dasa hannunshi yana buɗa bakin al'kyabbar jikinshin sai kuma yasa hannu shi na
dama ya dafe kanshi, kalmar amarya mata ya maimaita a fili.
Wani irin rumtse idanunshi yayi da ƙarfi Allah ya sani shi yama mance, batun wannan
jagulellen auren da akayi kamar na wasan yara.
kanshi ya ɗago a hankali ya kalli Umaymah dake shigowa da sallama a bakinta.
Gefenshi tazo ta zauna bisa bedside drower'n tana fuskantarshi.
hannunshi yasa, ya fara cire hiramin kanshi.
ita kuwa Umaymah cikin hikima tace.
"Idan mutun yana yi maka fatan ci baya to kayi mishi nuni da nasarorin rayuwarka,
ban cika son takura maka akan baka umarnin yin abubuwan da baka soba, to amman bani
da zaɓi akan duk wata al'ada ta masarautar Joɗa, da cikin masarautarmu ne, tabbas
inada damar hana wani abun da saka wani abun."
Cikin rauni ya kalleta da idonshi da sukayi jazir a hankali yace.
"Me Mahaifiyata tayi musu mai zafi da suka sata a gaba ita da ah'linta.
Duk abinda sukeyi Mata bata kulasu, bare ta kai ga ramawa, tana haƙuri akan komai,
haka yasa suke zaton tsoronsu takeji.
Ita kullum yanayi musu uzuri.
su kuma kullum fatansu su cutar da ita har dai suka samu nasarar cutar da rayuwarta
sannan muma basu barmu ba.
Ni na gaji da zama cikin masarautar Joɗa, zan bar musu garin gaba ɗaya".
Sauƙe numfashin tayi tare da cewa.
"Basu da nasara a rayuwarsu.
Nasara ɗaya ce garesu kuma sun yi ta.
Ta ƙare musu".
Sai kuma ta ɗan kalleshi cikin sanyi tace.
"Jazlaan!". A hankali ya amsa mata.
Fuska ta ɗan raunata kana a hankali tace.
"Yau kwanan matarka uku a gidan nan!".
Da sauri ya kauda fuskarshi a kanta wani irin haɗe fuska yayi tare da taune lip ɗin
shi na ƙasa ta ciki.
Shi ya mance da wannan batun yana rayuwarshi hankali konce. Wannan kariyar matar
Gimbiya Saudatu tazo ta tono zancen.
Ita kuwa Umaymah a hankali taci gaba da cewa.
"Baka gantaba! Baka nemeta ba! Baka san halin da take cikiba! Baka nunata wa
ah'linku ta masarautar Joɗa, a matsayin ta, na matarka.
Lamiɗo yayi mgna har ya turo Umminka taxo ta sanar maka, sai tace bata so ɓacin
ranka. Abbanka yace shi bazai ce maka komaiba, sabida babu abinda baka saniba kan
al'adar masarauta.
Yace kada wanda yayi maka mgna akan matarka sabida.
kai ba jahili bane, duk ka fimu sanin haƙƙin mace akan mijinta. Yace kunya tashi
kake son yi a idon mutane!".
Kanshi ya fara jujjuyawa a hankali yace.
"Me kukeso inyi! Umaymah ya kuke son inyi? Bazan iya juya kaina in dawo yadda
kukeso bafa, daga yadda Allah ya halicce ni".
Cikin hikima da sanyi tace.
"Ka shirya gobe, ka gabatar da matarka ga ƴan uwanka da iyayenka".
Hannunshi biyu yasa ya dafe kanshi.
Tare da rufe idonshi, sabida sarawar da yaji kanshi nayi.
sai kuma ya ɗan kalli Umaymah jin tana shessheƙan kuka.
Cikin sanyi yace.
"To!".
Murmushi tayi tare da shafa kanshi kana ta juya ta fita da sauri.

Kai tsaye sashin Gimbiya Aminatu ta wuce, ta sanar mata yadda sukayi da ɗan nata.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, a hankali ya miƙe al'kyabbar jikinshi ya zare, kana ya nufi
bathroom da jallabiyar.

Yana shiga ya zare jallabiyar da snglet ɗin. Kana ya shiga wurin wonkan.
Ruwan sanyi ya sakarwa kanshi.
sabida sarawar da kanshi keyi,
tun ihun dasu Baba Basiru sukayi mishi a kanshi.
Ga kuma wani sabon zance na zagaye idanun mayu da kulullukan masu konciyar ɗaukan
rai na masarautarsu.
A ƙalla yayi mituna biyar ruwan sanyin na zubo mishi a tsakiyar kai, kafin ya fara
sauƙe ajiyan zuciya alamun kan ya fara lafawa.
Al'wala yayi kana ya fito.
A nan drower'n glass dake bathroom ɗin nashi ya kimtsa kanshi cikin wasu datsastsen
yadi mai masifar kyau Super Nour, Noble blue mai ɗan karen kyau, tattausan yadine
mara nauyi, kana yanada ɗan shara-shara kaɗan, riga da wonɗo ne dai-dai jikinshi
rigar half jomfa ne wanda aka watsa mishi aiki da da baƙin surfani.
in ka tsura mishi ido sosai zaka iya hango shatin snglet and white boxes jikinshi.
Wani Oud mai daɗin gaske ya fesa.
Kana ya fito.

Baƙar fula ya kafa a kanshi wanda ya bawa tattausan gashin kanshi damar baiyana ta
gefe da gefen kanshi da kuma ƙeyanshi.

Fararen kyawawan Ƙafafunshi, ya zura cikin. Wasu tattausan takalma baƙi.


Sai kuma yasa hannu ya ɗauki carbinshi.
Agogon dake liƙe saman mirror ya kalla,
Lokacin sallan la'asar yayi, dan haka dole babu baccin tsakanin azahar da la'asar
ɗin da ya dawo yi.

A masallaci ya samu su Haroon da Jamil.

Bayan anyi sallan ne kowa ya kama sabgogin gabanshi.


Shi Jabeer komawa gida yayi.
Ya saka garen kayan jikinshin kana.
Ya fito, Ummi ya samu tsaye a tsakiyar falon, cikin kula tace.
"Zaka fitane?". Kai ya gyaɗa mata alamar eh.
ba tare da damuwar rashin bata amsarba tace.
"Da yan rakiya ko kai ɗaya?".
Yana gyara zaman hular kanshi yace.
"Ni kaɗai. Zanje gidan Malama Abubakar ne!".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ka gaida minshi".
"In sha Allah zaiji. Umaymah fa?".
Gane abinda yake nufine yasata cewa.
"Tana can sashin Gimbiya Aminatu, wurin ɗiyarta Amarya Aysha".
Kanshi ya ɗan sunkuyar ba tare da yace mata komai ba,
ya fita.
Malam Abubakar shine, malamin da ya fara ɗiga mishi harafin Ba''un a allon shi,
wato Be a fillance, Basinmi'arra a hausance ko?.
A wurin shi yayi sauƙan forko, sai dai zuwa yanzu, shi Jabeer shike ƙara wa Malam
Abubakar sani, akan Nahawu da Tajwid sabida shi da karatun zaure yayi.

Umaymah kuwa, ita da kanta ta sanarwa Lamiɗo cewa, gobe Sheykh zai gabatar da
amaryarshi.

Haka yasa, ta fara shirya Aysha, shiri na musamman.


Cikin Hadiman Juwairiyya ɗaya daga cikinsu.
Mai suna saratu, itace Umaymah tasa ta yarfawa Aysha zanen lalle mai ɗan karen
kyau.
Kana Ummi da kanta ta wonke mata kai sabida ita keyiwa Juwairiyya ma.
Sosai ta fito ras.
Ita kuwa Shatu duk abinda sukeyi Mata.
Tunanin Hibba al'hinin da tun randa tazo bata kuma ganinta ba.
tana son ta tambayesu ta rasa ta ina zata fara, dole dai haka ta haƙura tai shiru.

Washe gari ranar talata. Da hantsi, ko ina na sashin Gimbiya Aminatu sai ƙashi
yakeyi, sabida shiri da kimtsa amarya.
Umaymah da kanta take kimtsata, wani irin dakekken wagambarine mai matukar kyau
Royal blue, tasaka doguwar rigace. Tayi cib-cib da jikinta.
wani irin ɗauri ɗan kwali Aunty Juwairiyya ta murza mata a kanta, irin mai stpes
ɗin nan.
Kana sai wata farar al'kyabbar masarauta fara ƙal mai kolliyar zaren aiki da ulunta
Royal blue.
da surkin Golding color mai sheƙi.
Wasu fararen takalma masu ratsin Sky blue ne a kekyawan kafarta da yasha jan lalle,
takalman basu cika tsini da tuduba, sai dai kuma ba dab da ƙasa bane.
Tayi kyau iya kyau, sai ƙamshi da sheƙi take zubawa.
Umaymah ce ta kama hannunta har zuwa falon Lamiɗo, wanda bai rigaya ya fita fadaba.

Gefen Gimbiya Aminatu ta ajiyeta, kana tace.


"Bari inje inzo da Angon."
Murmushi Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
"To kuyi sauri dai".
To tace kana ta fita.

A can sashin Sheykh Jabeer, kuwa.


Da alamun wonka ya fito, a nitse yake kimtsawa, cikin wani fitinenne yadi mai
taushin gaske.
yadin Royal blue ne mai masifar kyau.
rigar half jomfa yar tsukekkiya,
tsaki ya ɗan ja lokacin daya gama dai-dai-ta zaman rigar a jikinshi sabida tayi
kib-kib a jikinshi har kamar ta ɗan matseshi.
Wondon kuma irin mai iya kuibin sawune, irin sakun wondunan ahlul sunna.
a hankali ya iso gaban drower'n da hulunanshi da hirami da baƙin abun saman hiramin
ke jere a ciki.
Har yasa hannunshi bisa wani farin hula, sai kuma ya sunkuya ya ɗan kalli. Kanshi.
Fuskarshi ya ɗan tsuke, sai kuma ya ɗan juyo jin muryar Haroon yana cewa.
"Wow masha Allah, gsky kayi kyau, Please ka fita haka mana, ka ganka ɗan saurayi
mai jini a jika, amman in kasa al'kyabbar nan, sai kwarjininka yayi yawa yaseen.
Ni kaina sai inji ina shakkarka,".
Kai ya ɗan shafa kana yasa hannunshi ya zaro hiraminshi fari da baƙin zagayen.
ɗaya marfin drower'n ya buɗe tare da zaro wata dakekkiyar al'kyabbar fara mai
ratsin blue na zaren aiki gaba da bayanshi.
Gaban gado ya dawo yana warware al'kyabbar tare da cewa Haroon.
"In na fita a haka ai ji zanyi kamar babu tufafi a jikina, sabida sunyi min kaɗan."
Ya ƙarishe mgnar yana zura al'kyabbar a jikinshi.
Masha Allah, Haroon yace.
Kana ya matsoshi yana tayashi gyara zaman al'kyabbar yana cewa.
"Duk shigar da kayi tana maka kyau, in na ganka ba al'kyabbar sai inga kamar kafi
kyau.
In kuma kasa al'kyabbar sai inga kafi kyau".
Baice dashi komaiba yaci gaba da gyara sakun hiraminshi,
saida ya gama dai-dai-ta hiramin sai ya juya ya nufi, wannan drower'n da
hulunanshi ke jere a steps biyu na sama.
Biyu na ƙasan kuma jerin takalmanshi ne.

Fararen takalma masu taushi ya saka ƙirar Gucci,


Zara-zaran yatsunshi sarari sabida ba sau ciki bane ba kuma half cover bane.
turare ya fesa, tare da sa hannunshin ya shafa sajenshi.
Kana ya kalli Haroon daketa ɗaukar shi hoto.
Cikin tura baki Haroon yace.
"Na bari, nasan yanzu zakayi ƙorafi, yanzu ina zakaje?".
Yana fita yace.
"Valli Hospital, akwai yaron da zan duba aikin da akayi mishi".
Bayanshi ya biyo tare da cewa.
"To sai ka dawo".
Ni zamuje wurin Budurwar Jamil taga babban yayanshi.
Wani kallo ya mushi tare da cewa.
"Allah ya shiryeka babban kobo".
Dariya Haroon yayi tare da cewa.
"Eh naji na yarda, zanje yaro ya samu matsala da ita tanata wahal dashi ba dole
inje in dai-dai-ta musu matsalar ba".
Juyowa yayi jin abinda Haroon yace cikin sakin gajeren murmushi yace.
"Uhumm yaushe ka zama luwali, bani da lbri, to kai taka matsalarma yaushe ka
warware ta, kun iya cikamu da zancen ku ƴan soyayya ne, kuma bakuma san yadda ake
soyayya da magance matsalolin ta da tattalinta gudun ta lalaceba".
Wani irin dariya mai sauti Haroon yayi tare sara mishi.
Da sauri ya juya, da nufin tafiya,
sai kuma yaga Umaymah na tsaye a gabanshi.
Hannunta tasa ta kamo nashi tare da janshi suka fara tafiya.
Cikin sanyi yace.
"Oh Umaymah ina zamuje?".
Haroon kuwa baki ya taɓe tare da cewa.
"Wlh gobe zan koma in sha Allah, komai sai an nunawa mana ƴan ubanci".
Dariya Umaymah tayi tare da cewa.
"Allah kiyaye hanya".
Da sauri yace.
"To na fasa tafiya".
Suna gab da fitane yace.
"Umaymah sakeni karmu fita a haka".
Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa.
"To taho".
To yace mata kana yabi bayanta.
Suna tafiya cikin ƴar faffaɗan hanyar da bishiyoyin namijin gwanda yayi musu
ƙawanya,
shiyasa wurin yayi sanyi.

A hankali ya kalleta lokacin da suka iso.


Bakin ƙofar Gimbiya Aminatu.
tare da cewa.
"Umaymah me zanyi a ciki?".
Hannunta tasa ta kamo nashi.
Kawai ta kutsa kai ciki. Dole ya bita a baya.
Yana saka ƙafarsa cikin falon yaji zuciyarshi ta buga,
da ƙarfi, lokaci ɗaya ta fara harbawa da sauri-sauri.
Cikin sanyi yace.
"Umaymah barni a nan".
Bata kulashi ba taci gaba da janshi tayi har bakin ƙofar falon Lamiɗo.
wani irin rumtse idanunshi yayi yin yadda zuciyarshi ke barazar fashewa.
Da sallama a bakinta, suka shiga.
Yayinda Lamiɗo da Abbanshi suka amsa mata.
Cikin wani irin azabebben bugun da zuciyarshi keyi, yasa ƙafarshi cikin falon.
yayinda Umaymah ke riƙe da hannunshi tana mishi jagora har zuwa gaban Lamiɗo da
Galadima da Abbanshi da kuma Malaminshi Malam Abubakar.
Kana ta tsaya dashi kusa da Aysha tare da rusunawa.
Yayinda shi kuma cikin fargabar yadda ƙirjinshi keyi ya rusa a hankali ya zauna
bisa tattausan carpet ɗin dake shimfiɗe a wurin.
Dib, dab, dib, dab, dib, dab. Haka zuciyarshi keyi.
yayinda itama Aysha da bai lura da ita Bama haka zuciyarta keyi,
sabida jin an mutun ya zauna kusa da ita.

A hankali ya lumshe idonshi, sabida bugawar da zuciyoyinsu keyi a tare yasa, ƙarfin
nashi bugun ya ɗan ragu kaɗan.

Cikin nitsuwa ya kalli Abbanshi kanshi a sunkuye yace.


"Barka da safiya Abba".
Cikin kula yace.
"Barka dai".
Sai ya kuma kalli Malamin nashi cikin kamala yace.
"Allah hokke sabbugo, Malam Barka da zuwa ya gida?".
Cikin nitsuwa Dattijan yayi murmushi tare da cewa.
"Alhamdulillah Sheykh Jabeer ya hidima".
Alhamdulillah yace, kana ya kalli Lamiɗo da Galadima.
sai kuma ya kauda kanshi.
murmushi Galadima yayi tare da cewa.
"Mu bazaka gaishemu ba kenan?".
Ɗan tsuke fuskarsa yayi tare da cewa.
"Gaggawa dai aikin shaiɗan ne".
Murmushi Lamiɗo yayi sabida ya fahimci duk abinda zasuyi,
sai ya cisu gyara ta kuma fuskar gsky.
Galadima ne yace.
"To ni bari in gaisheka Ina kwana".
Kanshi ya jinina mishi tare da cewa.
"Kayiwa kanka tanadin lada ashirin, a madadin kaɗan da zaka samu in ni na ɗaga maka
gaisuwar.
Lfyta lau Alhamdulillah."
Ya ƙarishe mgnar da amsa gaisuwar.
Dariya sukayi kana, ya kalli Lamiɗo a daƙile yace.
"Ina sauri dan inada aikin yi, menene kasa aka jawoni nan".
Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda Abbanshi da Malaminshi bazasu jiba.
Kana ya ɗan muskuta ya matsa gefe yayi nesa da Aysha sabida wani tsalle da yakeji
zuciyarshi nayi, a madadin bugun da takeyi kafin ya zauna kusa da ita.
Cikin zuba musu ido.
Lamiɗo yayi murmushi sabida sunyi masifar dacewa da juna, shigarsu da ta zamo iri
ɗaya tayi matuƙar yi musu kyau.
Cikin wasa irin na kaka da jika yace.
"Ga amaryar taka baku gaisaba, ku gaisa sai ka kaita kuje ka gabatar da ita".
Fuskarshi a haɗe yace.
"Hakan addinine ko al'ada?".
Da sauri Galadima yace.
"Al'adace kuma sai kayi ta".
Ta gefen ido ya kalli Galadima tare da cewa.
"Da ba Galadima za'a bakaba, da sarkin raya al'adu za'a baka".
Shiru yayi jin Abbanshi na cewa.
"Allah ya bamu nisan kwana, kaima watan watarana a gabanka yaranka zasuyi min haka
Muhammad".
Cikin yin ƙasa da kai cikin girmamawa da karrama mgnar mahaifin nashi yace.
"Sun isa! Suyi maka haka in barsu".
Murmushi Malam Abubakar yayi tare da cewa.
"Kamar yadda ka isaba".
Shiru yayi gane manufarsu.
Jin duk sunyi shiru ne, yasashi ɗago kai ya kallesu.
Suma shi suka zubawa ido, da sauri yayi ƙasa da kanshi.
Ita kuwa Aysha shiru tayi tamkar ruwa ya cinyeta, tanajin yadda suke musayan
kalamai. Sai dai bata fahimtarsu domin, tuno nata ahlin.

Gyaran muryan da Abbansa yayine yasashi ɗago kai ya kalleshi.

Cikin bada umarni Abba ya nuna mishi Aysha tare da cewa.


"Kama hannunta kuje, ka gabatar da ita, ka fara daga sashin ƙannen Lamiɗo, sai na
Mamanku, daga nan kuje wurin Gimbiya Saudatu,
dama sauran matansu Babanku Nasiru".
Bisa dole yace.
"To kana ya yunƙa ya miƙa,
da sauri Umaymah ta miƙe tazo ta miƙar da Aysha.
kana ta kamo hannunta ta miƙa mishi alamun ya riƙe hannunta.
Cikin tsuke fuskarsa da kwaɓeta tamkar zai ɗaura hannunshi a ka ya kurma ihu.
Ya zuba mata ido. Muryar Abbanshi ce ta katse tsayuwar da yayi kamar an dashi.
"Riƙe hannunta ku je". A hankali ya ware tafin hannunshi da Umaymah ta kamo
kana lokacin guda yaji zuciyarshi tana tsalle da harbawa, kamar dai tana mararin
wani abu.
Hannun Aysha Umaymah tasa mishi cikin nashi tare da meda yatsunshi ta rumtsesu.
Dam-daradam-dam haka zuciyarshi tayi wani masifeffen bugun mai kama da na aradu
kana tafara wani irin tsalle.
Ita kuwa Aysha, wani irin tsuma jikinta ya fara lokacin da taji tattausan yatsun
hannunshi da fatar tafin hannunshi ya rumtse nata.
Hannun wani irin masifeffen tsoro da kunyane suka diro mata, a lokaci guda.
Shi kuwa Sheykh wani irin asirtace kuma ɓoyeyyen dogon ajiyan zuciya ya sauƙe mai
sanyi, jin gaba ɗaya zuciyarshi ta koma ta nitsu tabar wannan tsinkewar da bugawar
da tsalle tayi lib a cikin ƙirjinsa.
Jin muryar Jakadiya ne yasa, Sheykh Jabeer, yin ƙarfin halin ɗaga ƙafarshi ta dama.
Jin ya ɗan yi gabane yasa itama, ta ɗaga ƙafarta ta hagu, sai hakan ya bada wata
dama ta musamman, ya zama suna ɗaga ƙafafuwan su, a tare kana suna taku a jere.
Sai dai shi ɗin ya ɗan kereta kaɗan.

"Masha Allah. Tabarakallah,". Sune kalaman da Umaymah ke Maimaitawa, lokacin da


take biye dasu a baya.

Lamiɗo da kanshi da Galadima sunga wani irin dacewa na musamman a tsakin Muhammad
Jabeer da Aysha.
Abba kuwa murmushi yakeyi mai baiyana jin daɗi.
Malam kuwa, Addu'o'in yaketa jero musu na fatan al'khairi da zaman lafiya da
nitsuwa da samun zuriya ɗayyiba.

A hankali suke taku yayinda kowa zuciyarshi ke bin takun sawunsa,


A haka suka fito babban falon Gimbiya Aminatu nan suka samu Ummi. Tana ganinsu ta
miƙe da tsauri tayi gabansu, hadimai hudu cikin na Gimbiya Aminatu kuwa, sukayi
bayan Umaymah dake bayansu.

Shi kuwa Sheykh Jabeer suna fitowa yayi wani irin saurin sake hannunta tare da
janye nashi,
Sabida shi ji yake tsikar jikinsa na tashi tamkar ya riƙe wutan lantarki ne sabida
masifar tsuma da yaki naman jikinsa nayi.
Murmushi Umaymah tayi ganin still dai suna tafiya a jere a jere suna wani irin taku
mai ƙayatarwa.

Suna fitowa, suka samu sallama a bakin mashigar wurin.


Nan ya shaida musu, duk sashukan gidajen anje anyi sallama dasu an kuma basu daman
shiga.

Tafiya kaɗan sukayi daga sashin Gimbiya Aminatu, ta gefen hagunshi,


suka ɓullo farfajiyar wani babban part,
Jakadiyarsu na gaba suna biye da ita a baya, Umaymah na biye dasu.
A hankali suke taku cikin ƙasaita hadimai da fadawa na mara musu baya.
Suna shiga ciki, suka samuwa wata dattijuwar tsohuwa mai tarin shekaru.
Cikin murmushin da muryar tsufa tace.
"Malamai magada annabawa, lallai yau inada babban baƙo da babbar baƙuwa."
A hankali suke tafiya har zuwa gabanta, inda take zaune bisa tattausan carpet
hadimanta na kewaye da ita.
wanda biyu daga cikinsu, suka tashi da sauri suka kawo ababen motsa baki suka jera
a gabansu.

Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya kalli tsohuwar da take matar ga Galadima.
Cikin kula yace.
"Barka da safiya Innano". Cike da kula tace.
"Barka dai Malam Muhammad, mun samu ƙaruwa ko".
Kanshi ya gyaɗa mata a hankali haka yasa duk basu ganiba sai ita da yake gabanta.
"Cikin muryar tsufa tace.
"Allah ya sanya al'khairi. Ya baku zaman lafiya. Yasa matarkace iya rai da mutuwa.
Ya azurtaku da zuriya ɗayyiba."
Da Sauri Umaymah ta amsa da Amin Amin hakama sauran baki ɗayansu.
Ita kuwa Shatu, cikin saisaita nitsuwarta ta ɗan kalli tsohuwar tare da cewa.
"Ina kwana".
Murmushi tayi tare da kai hannunta ta kamo hannun Shatu, tafin hannunta ta buɗe ta
zuba musu ido, na yan wasu ɗakiƙu kana tace.
"Lafiya lau, ya baƙu ta?".
A hankali tace.
"Alhamdulillah". Jakadiyarsu ce ta ɗan rusuna tare da cewa.
"Mun barki lfy".
Kai ta gyaɗa kana tayiwa hadimanta umarni su miƙo kyautar da take gadon
masarautarsun ce farin gyale ne mai kyau da taushi.
Umaymah ce ta amsa ta miƙa hadiman dake bayanta.

Kana suka miƙe suka fita.

Daga nan sashin wani sashin na kusa dashi suka shiga.


Wanda yake sashin ƙannen Lamiɗo ne.
Saida suka gama da sashukan manyan masarautar.
Kana suka nufi sashin Hajia Mama.
Tuni tasan da zuwansu.
haka yasa ta kimtsa ta tsara komai na tarban surkar tata.
A matsayinta na uwar ango.
Har can cikin bedroom Ummi ta wuce, su kuma suna biye da ita a baya.
Suna shiga suka sameta, zaune bisa kilishi,
Batool na gefenta, wacce son ganin amaryar ne, ya hanata tafiya.
Hadimanta kuma na zagaye da ita.
Suna shigowa ta tashi zaune daga kishingiɗar da tayi.
Cikin tsananin baiyana farin cikin ta, ta nunawa Jabeer kusa da ita.
a hankali suka iso suka zauna gabanta.
Umaymah kuwa gefenta ta zauna.
Ummi ko na bayansu hadiman kuma suna can falo.
Hannunta tasa ta kamo hannun Jabeer.
Cikin fara'a tace.
"Alhamdulillah Muhammad Jabeer, Allah ya sanya al'khairi ya baku zaman lfy".
To shifa suna ɗaure mishi kai, da tarin addu'o'insu na al'khairi, shi dai ba sonta
yakeba ba kuma zama da ita zaiba,
to me zai wahal dashi da zaice Amin Amin.

Umaymah da Jakadiyarsu ne suka amsa da Amin Amin kamar dai yadda sukayi a sauran
wuraren.

Batool ce ta kalli Shatu cikin isa tace.


"Amarya ki ɗago kanki mana kinga gaban uwar mijine kike".
Duk da taji mgnar Batool sai tayi kamar batajiba,
Abubuwan ci da sha dake gabansu ne,
Hajia Mama ta jawo wani ɗan ƙaramin tray da cups biyu ke kanshi.
Gyara zama tayi da kyau, tana murmushi ta kalli Shatu dake mgna a hankali.
"Ina kwana Mama".
Cikin kula tace.
"Lfy lau ɗiyata ya baƙun ta".
Alhamdulillah tace, tare da tsurawa madara da zumar da Hajia Mama ta zuba musu
cikin kofu nan ido.
a hankali ta ɗan muskuta kaɗan tayi baya, tare da ƙara yin ƙasa da kanta.
ita kuwa Hajia Mama, kofin ta ɗauka ta miƙa mata.
Tare da cewa.
"Gashi ɗiyata amshi kisha."
Cikin sanyi murya can ƙasa ta girgiza kanta tare da cewa.
"Alhamdulillah".
cikin nuna kulawa da so Hajia Mama ta ƙara miƙo mata kofin tare da cewa.
"A a ɗiyata, amshi kisha, wannan al'adace ta masarautar Joɗa, dole in marabceki
dashi."
Kai ta kuma girgiza alamun ya isheta.
da sauri Umaymah ta matso kusa da ita tare da cewa.
"A a Shatu amshi kisha kinji ko?".
Cike da mamaki ta ɗan kalli Umaymah ta gefen idonta.
jin Umaymah na ƙoƙarin matso da kofin kusa da itane yasa tayi mgna cikin ɗan ɗaga
murya tace.
"Bana shan madarar".
wani irin kallo mai cike da damuwa Hajia Mama tayi mata tare da cewa.
"Subahanallahi, bakya sha, kuma, amai yake sakine? Ƙa'idane da dole kishi".
Ta ƙarishe mgnar cikin damuwa.
Ita dai Shatu shiru tayi idonta na bisa kofunan madarar.
Ummi ce ta matsota tare da cewa.
"Shatu amshi kisha koda kurɓa ɗaya ne".
Cikin rawan murya tace.
"Bana sha".
Jin alamun rawan murya irinta an takura mutum ne, yasa duk sukayi cirko-cirko suna
kallon Madarar.
Zuwa can Hajja Mama ta sauƙe wani bahagon ajiyan zuciya, kana ta ɗauki ɗaya kofin
ta miƙa Jabeer tare da cewa.
"To gashi kai kam kasha naka".
Zamanshi ya ɗan gyara tare dasa hannun damansa ya amshi kofin.
Wani irin zaro ido Shatu tayi.
Kallon kofin takeyi tamkar zata maida kwayar idanunta cikin kofin.
duk jikinta tsuma yakeyi, wani irin masifeffen bugawa ƙirjinta yakeyi da ƙarfi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer zaune yake riƙe da kofin, ya fuskanci Hajia Mama da kyau.
Ita kuwa Hajia Mama hannunta tasa ta kamo ɗaya hannun Jabeer da baya riƙe da
kofin.
Kana ta miƙowa Shatu hannun alamun ta miƙo mata hannunta.
Ƙara runsunar da kanta tayi tamkar bata gane me take nufiba.
Cikin murmushin Hajia Mama tace.
"Kawo hannunki ko ɗiyata".
A hankali ta ƙara maida hannunta baya,
dai-dai lokacin kuma Jabeer ya ɗago kofin ya kai saitin bakinshi da niyar zai sha.
cikin hikima ta muskuta ta ƙara matsowa jikinshi da sauri ta ɗago hannunta kamar
zata miƙawa Hajia Mama hannun.
sai kuma ta ɗan kaikaice, ta buge c...!

Ƙaƙa tsara ƙaƙa

By
*GARKUWAR FULANI*Ta bugi kofin madarar, ba zato ba tsammani, Jabeer
yaji kofin ya tsumbce mishi.
ya faɗi gefenshi.
Tass ya fashe madarar ta kwaranye a ƙasa.
Cikin sauri da tsuƙe fuskarshi ya juyo ya kalleta.
Itama ɗin shi take kallo.
Ido cikin ido sukayi da ita a karo na forko a rayuwarsa duk da yasan sun taɓa
haɗuwa.
Kallon kwaɗayye mai irin bakin Junainah, tayi mishi.
Sai kuma ta janye ƙwayar idanunta cikin nashi da sauri.
Sabida wani irin kallon da taga yanayi manata.

Umaymah da Ummi kuwa, kallon junansu sukayi, cikin yanayin son gane ya akayi kofin
ya faɗi dan basuga sanda ta ta ɗan buge mishi hannunta.

Hajia Mama kuwa cikin tashin hankali da kiɗima ta kalli Umaymah tare da cewa.
"Akwai matsala, ita batasha, shi nashi ya kwaɓe."
Sai kuma ta maida dubanta ga Shatu cikin alamun damuwa tace kawo hannunki na dama."
Still maida hannun nata tayi baya, ba tare da tace komaiba.
Ummi ce ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa.
"Miƙa mata hannunki ku gaisa".
Murya can ƙasa tace.
"Yana ciwo". Ta ƙarishe mgnar da jin haushin kanta da ƙaryar da suka satayi.

Batool ce ta kalleta sama da ƙasa kana cikin gyatsine tace.


"Umaymah ai wannan ba irin matar Sheykh bac."
Sai kuma ta haɗiye ragowar mgnar dan ganin wani irin kallon daya watsa mata na
alamun.
Ki kama kanki da kiran sunana a bakinki.
Wani dogon ajiyan zuciya Hajia Mama ta sauƙe cikin fargaba tace.
"Tashi Kuje ku gaida sauran. Allah yayi muku al'barka ya baku zaman lafiya.
In sha Allah babu komai".
Kamar jira Shatu takeyi a basu izinin tashi tayi fit ta miƙe.

Da tarin mamaki Umaymah da Ummi suka miƙe, dan abubuwan da suka faru da yanayin
Shatu, ya tsaya musu a rai.
Shima Sheykh Jabeer miƙewa,
yayi kana suka jere suka fita.
Sai dai Shatu na ɗan sassarfa.

Cike da mamakin wannan abun suka nufi Side ɗin Gimbiya Saudatu.

A falonta suka sameta tana hakimce bisa kujerar ikonta,


ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya tana karkaɗa ƙafar cike da izza.

Ummi na gabansu suna bayanta Umaymah na bayansu.


Cikin rusunar da kai Jakadiyarsu ta durƙusa gefenta tare da cewa.
"Barka da safiya Gimbiya Saudatu, ga Sheykh Jabeer ya kawo miki da amaryarsa!".
Cike da izza ta ɗan kallesu sama da ƙasa, kana ta nuna musu gabanta.
Alamun su zauna, cikin sanyi Shatu ta rusuna tare da sunkuyar da kai ta zauna
gabanta.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo yayi mata, mai cike da ma'anoni,
gefen ta ya kalla inda wata kujerar ke kusa da tata komansu iri ɗaya.
Taku yayi cike da ƙasaita ya isa gaban kujerar, kana ya juyo ya zauna kan kujerar.
Hakan yasa ya fuskanci Shatu da Umaymah.
zaman ƙasaita da isa yayi.
wani mugun kallo take binshi dashi har ya zauna.
Ita kuwa Shatu kanta a duƙe tana murzam ƴan yatsunta.

Umaymah ce ta ɗan taho zata zauna kusa da ita, a hankali ya jujjuyawa Umaymah kai,
alamun. A a kada ta zauna a ƙasa.
gane manufarsa ne, yasa ta zauna bisa kujera.

Shiru kakejin falon, sai takun sawun hadimanta dake kawo ababen motsa baki, suna
ajiyewa gaban Shatu.

Suna gama jerawa suka koma can gefen.

Jin shiru-shirun yayi yawane yasa Shatu ɗan ɗago kwayar idanunta, ta kallesu.
A ranta take mgnar zuci.
"Ikon Allah, ohoho ni Shatu wannan wanne irin bahagon gidane, mai cike da sarƙaƙiya
da tubkar baƙin zare,
To ko dai ita wannan ɗin kurmace."
Muryar Gimbiya Saudatu ce ta ƙatse mata tunani ta,
cikin isa da izza ta kalli Sheykh Jabeer, kana ta juyo ta kalli Shatu, murya a
daƙike tace.
"Bakiyi sa'an mijiba, yarinya duk da gashi kamar kinada nitsuwa".
Ido Shatu ta jujjuya cikin hular al'kyabbar jikinta.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko ta kan mgnar ta bai biba,
sabida ai dama ya tsammaci, hakan
kai ta juyo ta kalli Umaymah cikin ɗagawa tace.
"A buɗe min fuskar amaryar in ganta da kyau, inga wanne irin idone da ita".
Bata rufe bakintaba taji yana cewa.
"Baza'a buɗe ba!."
Murmushi Umaymah tayi sabida tsamar Sheykh Jabeer da Gimbiya Saudatu wani lokacin
yadda kasan shi ubanta ne, haka yake mata mgna da yanke hukunci kai tsaye a karan
kanta ma bare akan abinda ya shafeshi.
ita kuwa Shatu a hankali take juya ƙwayar idanunta, tana kallon sawun Gimbiya
Saudatu.
cikin al'kyabbar ta ɗan juya idonta da kyau ta maidasu, kan kyawawan fararen sawun
Sheykh, wanda suke tamkar ka taɓa jini yayi yo tsalle ya fito, sabida taushi da
laushin fatar
Wanda duk mutun mai zama da al'wala da yawan karatun al'ƙur'ani tafin hannunshi da
ƙafarshi sukanyi wani kala mai masifar kyau da ɗaukar hankali koda baƙin mutun ne
sai fatar hannunshi dana ƙafarshi sunyi kyau na musamman, hakama kuma fatar
jikinshi wannan shine baiyanennen darajar zama da al'wala da yawan ambaton Allah
kenan.

Da ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗe su.


kan babbar yatsar kafarshi ta zubawa ido, sosai da sosai.
wani ɗan zane baƙi mai suffar tafiyar maciji ta gani.
sai dai bata samu ganinshi ras yadda take soba, shiyasa taketa zare ido,
shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya ɗan turo ƙafar damanshi gaba.
Dan ya gyara zaman ɗayan a kanta.
Hakanne ya bawa Shatu damar zubawa yatsun nashi ido, suna nan zara-zara alamun
mutum ne mai matsakaici tsawo.
Ras zanen bindin maciciyar nan yake kan babbar yatsarshi.
har zuwa bisa rumfar ƙafar kamar zanen dayis,
cikin tarin mamaki da al'ajabi take bin zanen da idanunta.
har inda igiyar takalminshi ya tsare zanen.
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali.
sabida rashin ganin ƙarshen wannan zanen, da kuma inda ya nufa, da kuma ganin ya
saman zanen yake.
Hankalinta kab ya tafi ga zanen shiyasa bata jin ta ƙaddamar da Gimbiya Saudatu ke
zubawa ba.
Muryar ta taji da ɗan ƙarfi tana cewa.
"Bata da sunane? Ke me sunanki".
Ta ɗago kai da nufin yin mgna kenan sai kuma tayi shiru.
jin Umaymah na cewa.
"Sai kisa mata naki sunan, ba sai kiji namu ba".
A gyatsine ta kalli Umaymah kana, ta ɗan matso bakin kujerar,
hannu tasa ta ɗauki tupa cikin jerin ƴaƴan itatuwan da aka jera a gaban Shatu.
miƙa wa Shatu tayi tare da cewa.
"Kici kada ki tafi bakici komaiba,".
A hankali tace.
"Alhamdulillah!". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace.
"A ni ba'a zuwa sashina a tafi ba abinda akaci".
Hannu ta miƙa ta amshi tupan kana ta riƙe shi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer miƙewa tsaye yayi alamun tafiya hakane yasa.
Suma suka miƙa suka fita.

Daga nan kai tsaye Side ɗin.


Baba Nasiru suka nufa.
A falo suka samu matarshi da yaranshi dama shi kanshi.
Bayan sun zaunane.
ya kallesu sama da ƙasa yace.
"Dama baku zauna ba, a hakama na ganku.
ba sai kun zauna ba".
Cikin sanyi ƴarshi Jamila ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa.
"Ayyah Baba ka barsu mu gaisa".
Haɗe fuskarshi yayi sabida yasan irin masifeffen son da Jamila keyiwa Jabeer lokuta
da dama, takanyi ta kuka in taji abubuwan da mahaifinta yakeyi mishi.
shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya zauna ya harɗe ƙafa,
Jamila kuwa cikin nitsuwa ta gaidasu kana.
Ta kawo musu abin sha,
Ummanta ku ko kallo Bata ishesuba yadda itama bata lallesu ba.

Haka dai suka fita suka tafi.


gidan Baba Basiru kuwa suna shiga ya tashi ya bar musu wojen.

Daga nan suka shiga gidan Barrister Kamal


Baba Kamal kenan.

Yana ganinsu ya tashi ya ruggume Sheykh tare da cewa.


"Masha Allah, Alhamdulillah yau dai Allah ya nuna min ɗana da matarsa".
Zama sukayi bayan sun gaisane yayi musu addu'o'in al'khairi.
Daga gidanshi gidan Dr Aliyu sukaje,
wanda yake mutun mai mutunci da kamar Barrister Kamal.
Sosai suka jima a sashinsa,
yayi musu addu'o'in da sanya al'khairi da al'barka.

Daga nan kuma sai Sashin Mom tsakar gidan Abbanshi.


Maman Imran, ba yabo ba fallasa ta amsa musu.
Daga nan wurin Amryar Abbansu sukaje, wanda suka sameshi a can.

Daga nan sukaje gidan Ya Hashim da sauran ƴan bappanunsu.


Gida na ƙarshe dai gidan Aunty Juwairiyya ne, can suka samu Hibba da Ya Jafar.
Bayan sun gaisane,
Umaymah ta ɗan matso kusa da ita cikin sauƙe numfashin gajiya tace.
"Ɗago kanki Shatu kinga nan ƙofar Aunty Juwairiyya ce, ga mijinta shine babban
yayan Jabeer, kuma yanada matsalar ƙwoƙolwa.
Yanzu daga nan Side ɗinkin zamu wuce, wanda yana nan kusa da nasun. Sai gefen nakun
kuma nasu Jalal ne."
A hankali ta ɗago kanta ta kalli Ya Jafar, yana riƙe da hannun Jabeer yana karatun
shi a hankali.
Cikin sanyi tace.
"Ina kwana yaya!".
Kafaɗarta Umaymah ta dafa tare da cewa.
"Baya mgnar komai a duniya inba karatuba, sai dai yanajin komai kuma yana gane
komai in an gaya mishi amman fa baya mgna kam in ba karatuba."
Cikin tsananin rauni da tausayawa,
idonta cike da ƙwalla tace.
"Allah sarki, Allah ya bashi lfy".
Karon forko kenan tunda suko fito dashi taji ya amsa addu'a duk da tarin addu'o'in
da akayi ta musu sai yanzu taji yace.
"Amin ya Allah". Hakama Umaymah da Jakadiyarsu da Hibba sai dai duk ya riga su
amsawa.
A hankali take ɗan satan kallonshi a fakaice.

Hibba ce ta janye mata hankali da cewa.


"Aunty Shatu kin gaji kam. muje ki huta, gashi azahar ta kusa ma."
Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa.
"Uhum".
Umaymah ce ta miƙe ita da Ummi kana sukace.
Taso mu tafi, yanzu Hibba zata cikaki dan zance."
Cikin murmushi Aunty Juwairiyya tace.
"Ayyah Umaymah ku bar mana ita mana".
Ummi ce tace.
"Lokacin sallafa ya ƙara to".
"Hakane kam". Juwairiyya tace tare da ɗaukar Foodflaks dake kan dinning table, tabi
bayansu tana cewa.
"Hibba ɗauko sauran!".
To tace kana ta suggumi sauran tabi bayansu.
Nan suka bar Jabeer da Ya Jafar ɗin.

A babban falon suka zauna.


Aunty Juwairiyya da Hibba suka ajiye Foodflaks ɗin bisa Dinning table,
kana suka dawo tsakiyar falon.
Umaymah ce ta miƙe tare da kallon Shatu, tace.
"Taso mushiga ciki, kiga tsarin wurin naku".
Miƙewa tayi cikin alamun gajiya, domin zagaye masarautar Joɗa babban aikine mai
zaman kanshi. Donma su sun saba, ita kuma bafulatanar dajine tafiya baya bamu
tsoro.
Bayan Umaymah tabi, ta gefen Dinning area ta ɗan ratsa da ita,
Suka shiga cikin kitchen, juyowa tayi ta kallesu Ita da Hibba,
"Nan shine babban kitchen ɗin ki, dake babban falonki.
Shine wanda in kinada aiki mai yawa, kamar na salla ko azumi, ko zakiyi ki aikawa
surakanki.
Hadimai zasu iya shigowa su tayaki."
cikin fahimta tace.
"Toh". Hibba ce ta ɗan ƙara so shigowa ciki tare da cewa.
"Kai wanga kitchen badai girmaba, gashi komai a tsare gonin kyau. Kalarsa green and
white komai na ciki gwanin kyau".
Murmushi suka ɗan yi kana, Umaymah ta juya dasu.
Daga nan cikin kitchen ɗin ta gefen dama akwai wata ƙofar da sai ka hau stpes huɗu.
A gefen ƙofarne wani datsetstsen Fridge mai girma yake kwance.
Haurawa sukayi kana Umaymah ta tura ƙofar ta shiga.
Store ne mai zaman kanshi.
akwai komai na buƙatar rayuwa, sai dai ba mai yawa bane.
Shatu ta ɗan kalla tare da cewa.
"Ga kuma store ɗinki. Nan za'a ke aje miki duk wani abun buƙata".
Kai ta gyaɗa, kana suka fito.
Wata ƙofar daketa hannun hagu ta nuna mata suna buɗe wa suka fito.
Sai gasu bisa wata baranɗa mai girma, kana can ƙasan barandar fulawine da kuma
pompona ke jere iya ganinka,
Daga sama kuma igiyoyin shanya ne da a ƙalla sun kai huɗu.
sai saman barandar kuwa, injin wanki ne.
Nan dai ta nuna mata komai na wurin kana suka dawo cikin gida.

Suna shigowa falo. Sheykh na shigowa.


A nitse yake taku, kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi da yake lallatsawa.
Umaymah ce ta ɗan bi bayanshi tare da cewa.
"Zo nan Shatu".
Cikin zuba bayansu ido. Ta ɗan gyaɗa kai, tare da taka sawunta a hankali tabisu.
Hibba kuwa gefen Aunty Juwairiyya ta zauna.
Shi kuwa yana shiga falon nashi, ya juyo ya ɗan kalli Umaymah cikin kwaɓe fuska
yace.
"Umaymah, Dan Allah ni bana son ana shigomin da wasu ababen cikin Side na, bare
rayuwata, me wancan abun da kika kira zaizo yi anan?".
Ido ta kafeshi dasu hakane, yasa yayi ƙasa da kanshi.
tare da shigewa bedroom yana cewa.
"Dan Allah iya kar abun can falo".
Ƙeyanshi Umaymah ta zubawa ido.
"Wato ma wai wancan abun, lallai ma Jazlaan".
Juyawa tayi ta ɗan leƙo a corridor ta hangota, murmushi tayi tare da cewa.
"Taho mana".
Kai ta kuma gyaɗawa tare da ƙara saurinta tafiyarta a hankali.

Suna shiga falon, tayi wani irin ɓoyeyyen ajiyan zuciya mai sanyi,
sabida wani irin masifeffen sanyi mai gauraye da ƙamshi mai ɗan karen daɗi da taji
ya bugu jiki da zuciyarta.
lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su a hankali jin Umaymah na ce mata.
"Nan falonshi ne, namusamman ba kowa ke shigo mishi wurin kai tsaye ba.
dan ko Juwairiyya bata shigo mishi nan, kana akwai ƙannenshi ƴan uba maza da kuma
Jalal basa shigo mishi nan.
Jamil kan shiga in baya nan in zai dawo shikeyi mishi shara da gyaran wurin.
Jalal kuwa yakan iya shekara ƙafarshi bata tako nanba.
Sai kuma Ya Jafar ɗin sa, shi kam bashi da hijabi da Side ɗin Jabeer, yakan shiga
har cikin Bedroom nashi wani zubin har bathroom.
Sai kuma Haroon da Ibrahim su dama, dan su yasa aka gina sama wai masauƙinsu in
sunxo.
To ammanfa in sunzo a ɗakinshi suke ko motsi zasuyi tare zasuyishi.

Sai kuma yayan Hibba, Hibbab shi na hannun damanshi ne.

Dan haka daga yanzu in dai yayi tafiya kece, zakiyi aikin da Jamil keyi".
A hankali tace "to".
Haura step ɗin Dinning area ɗin shi dake falon wanda akayiwa ƙawanya da wani irin
labule mai masifar kyau.
Labulen ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu kama dana Daimond.
wasu farare wasu Sky blue wasu Royal blue. suna da wani irin haske mai wal-wal.
Cikinsa kuma.
Wani badaidaicin Dinning table ne mai kujeru shida nan uku nanma uku sai wani
fridge ma daidaici. Gefensa show glass ne mai kyau wanda yake ɗauke da cups and
plates and spoons and forks Mug. Da dai sauran ƙananan abeben buƙata.
sai woshing hand Baby, dake liƙe a can gefe.

sosai tsaruwan wurin yayi kyau, komai Sky blue and white. Abun sai ya zama kamar a
duniyar taurarin yake yadda walwalin ke haska ko ina.
Falon kuma yanada ɗan karen duhu, domin saida Umaymah ta kunna musu wuta.

Bedroom nashi ta nuna mata da yatsa.


"Ga makwancinsa, sai kuma wancan ɗakin shi ba mai kwana a cikin ɗakine na musamman
babu mai shiga ciki sai shi ni Lamiɗo Galadima, domin ɗakin aikinshi ne".
Ita dai da to take bin Umaymah, sabida sanyin falon yana gab da sata kuka.
Allah ya sani bata son sanyi ko kaɗan. Ta kuma lura su kuma mayun sanyi ne.

Falon suka fito. Nan dai suka samu su Hibba nata hira da Ummi.
Side ɗin ta suka nufa.
Cikin kula tace.
"Ga Side ɗinki ga falonki ga kitchen ɗinki."
Ta ƙarishe mgnar suna shiga kitchen ɗin. A hankali take kallon komai na Kitchen ɗin
kalarsa Pink and white. Sosai tsarin wurin yayi kyau.
daga nan Dinning area Suka shiga ta nuna mata kana suka fito falon.
Suka shiga bedroom ɗinta komai ya tsaru.
Kuma komai sabone fil gwanin burgewa.
juyawa Umaymah tayi tare da cewa.
"Wancan ɗakin kuma masauƙi nane in nazo."
Cikin ɗan murmushi tace.
"Ayyah". Ƙofar Bathroom Umaymah ta nuna mata tare da cewa.
"Azahar tayi shiga kiyi al'wala kiyi salla sai kizo muyi Lunch".
to tace kana Umaymah ta juya ta fita.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, yana shiga ya maida ƙofar Bedroom ɗin ya rufe shiyasa
Umaymah bata gwada shiga da itaba.

Shi kuwa bathroom ya wuce wonka da al'wala yayi, ya sauya kaya. Kana ya fito cikin
shigarsa ta musamman ya nufi. Masallaci.
Koda sukayi salla suka fito.
Falon ganin bata fito bane yasa, Umaymah cewa Hibba.
"Jeki kiramin ɗiyata". Da sauri Hibba ta juya ta nufi ɗakinta.
Kwance ta sameta bisa sallayar da tayi salla, ta kife kanta cikin hijabin jikin
nata,
bisa dukkan alamu kuka takeyi.
jin shigowar Hibba ne yasa tayi saurin share hawayenta,
tare da juyowa,
cikin mamaki Hibba ta zuba mata ido.
A hankali tace.
"Aunty Shatu meya sameki kike kuka".
Murmushin ƙarfin hali ta ƙaƙalo tare da cewa.
"Kuka kuma Hibba".
Cikin sauri tace.
"Eh mana gashi idonki yayi ja".
Miƙewa zaune tayi da kyau cikin sanyi tace.
"No bacci na fara, shiyasa kikaga hakan".
Kai Hibba ta gyaɗa kana tace.
"To taso mu tafi falo Umaymah tace kizo muyi Lunch".
Hannu tasa ta ɗan shafa cikinta tare da cewa.
"Kamar na ƙoshi fa".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Tab ai Wlh taso kawai mu tafi, dan Umsymah bazata barki bakici abinci ba".
To tace kana ta miƙe ta ninke sallayan. Sabida gajiya ne da bege da kewar yan
uwanta ne ya sata kuka da kuma jin yunwar ta mutu a cikinta.

Suna fitowa su Umaymah duk suka miƙa, Dinning area suka nufa.

Bayan duk sun zaunane, Ummi, ta miƙe da nufin saka musu abincin.
Da sauri Aunty Juwairiyya ta miƙe tare da cewa.
"A a Ummi ki huta bari in saka mana".
Foodflaks ɗin dake kusa da ita ta ture tare da jawo wanda suka shigo dasu.
Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ya kika ture wancan?".
Baki ta ɗan taɓe tare da cewa.
"Uhummm wai fa Gimbiya Saudatu ce, ta turowa amarya abinci dan salon munafurci".
Wani irin kallon ƙasa-ƙasa Shatu tayi mata tare da zuwa abincin data buɗe ido,
cikin mgnar zuciya take cewa.
"Uhumm wai zata cewa wata muna fuka, muguwa Itan ko meye sunanta!?".
Sai kuma ta kalli Umaymah jin tana cewa Juwairiyya.
"Ni zubo min na gidan Hajia Mama naga tuƙeƙƙen tuwone da biyar zogale".
To Aunty Juwairiyya tace kana ta zuba mata.
da sauri Shatu ta ɗan kalli Umaymah lokacin da aka saka mata mal-malan tuwon farar
ɗanyar shinkafa,
tare da miyar a side sup.

Sai kuma ta juyo ta kalli Hibba da Ummi da tuni sun ja plate ɗin da Aunty
Juwairiyya ta saka musu. Couscous and vegetables sup, mai ɗan karen kyau da ƙamshi.

Da sauri ta jujjuya kanta lokacin da Aunty Juwairiyya ta turo mata na plate ɗin
gabanta, cikin sanyi tace.
"La da baki saminba". Da mamaki Umaymah tace.
"Sabida me?". Sunkuyar da kanta tayi tana tunanin.
suma ta yaya zata hanasu cin abincin. jin Ummi ta kuma mata tambayar da Umaymah
tayi matane yasa ta ɗan kallesu.
Ta buɗe baki zatayi mgnar kenan.
Sheykh ya shigo da sallama, a bakisa.
kusan a tare, suka amsa masa.
A fakaice ya ɗan kalli Aunty Juwairiyya kana yace.
"Kije ki bawa Ya Jafar mgninshi".
To tace tare da miƙewa da sauri ta fita.
Ita kuwa Shatu, wata nannauyan ajiyar zuciya ta sauƙe.
Kana tasa hannunta ta ture plate ɗin gaban Umaymah tare da jawo na gaban Ummi da
Hibba,
Ido suka zuba mata cike da mamaki.
Ita kuwa cikin sanyi ta kallesu tare da cewa.
"Dan Allah kada kuci wannan abincin.
Kuci wancan ne".
Jabeer dake ƙoƙarin shigewa falonshi ne, a ranshi yace.
"Uhumm lallai kam wannan abun wato itace ma zata zaɓa musu abinda zasuci".

Hibba kuwa da sauri tace.


"Aunty Shatu abincin gidan Gimbiya Saudatu fa kike cewa muci."
Ganin kallon mamaki da tuhuma da Umaymah da Ummi keyi matane yasata yin ƙasa da
kanta cikin jin tausayinsu a ranta tace.
"To in bazaku cishiba, Umaymah bari ni in shiga kitchen nida Hibba yanzu zan girka
muku duk abinda kukeso".
Ko inda suke Sheykh Jabeer da yanzu ya fito zai wuce baiba, yacewa Umaymah.
"Zan fita".
Juyowa tayi ta kalleshi tare da cewa.
"Allah kiyaye hanya, ya bada Sa'a".
Amin Amin yace, hakama Ummi tai mishi addu'a.

Ita kuwa Shatu kanta na sunkuye,


Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin nazartan yanayin ta, da yin tunani hakafa ɗazuma
taƙi shan madarar Barka da shigowa masarautar Joɗa da Hajia Mama ta bata,
ta kuma amshi tuppar da Gimbiya Saudatu ta bata,
yanzu kuma tace kada suci abinci Juwairiyya.
Wannan abun shi yafi komai tsayawa Umaymah a rai.
Yaya daga shigowarta zata kasabto wasu hasashen a ƙwaƙwalensu.

Kai ta jinjina tare da cewa.


"Hibba sa mana abincin Gimbiya Saudatu, muci".
Jin hajane yasa Shatu jawo Foodflaks ɗin ta fara saka musu.
Ita kuwa Hibba ta kwashe plate ɗin da Juwairiyya tasa musu ta kaisu kitchen.

Nan sukaci abincin kowa da abinda ke ransa.

Ita Shatu bataci na kirki bama.


Sabida ta lura da kallon da Umaymah keyi mata kamar da tuhuma.

Suna gamawa suka tattare wurin ita da Hibba.


tuni su Umaymah kuwa suna falon.

Suna gamawa suka fito falo.


da sauri ta kamo hannun Hibba suka wuce falonta har bedroom ɗinta.

Suna shiga Haroon, Jamil, suka shigo.


Shigarsu ba jimawa Jalal ma ya shigo.
Nan sukayi ta hira.
to ganin yanzu ta shigane yasa Umaymah bata kirata dan tazo taga ƙannen mijin
mataba.

Suko. Suna cin abinci suka fita sabida kiran sallan la'asar,
daga nan kuma basu kuma shigowa falonba sai kusa goma na dare kafin nan kuwa tuni
Shatu da Hibba sunyi bacci ma.
Washe gari ranar Laraba, da safe.
Aunty Juwairiyya ta shirya musu breakfast kamar yadda ta saba, koda su Umaymah basa
nan, abincin Sheykh a sashinta yake duk da ma, yakan iya wata biyar baisa abincin
nata a bakinshi ba.
sai dai Ummi Jakadiyarsu ta ɗan dafa mishi irin ababen da yafi so yaci lokuta da
dama kuma na rayuwarshi da Lamiɗo yake cin abinci a Side ɗin kakarsa Gimbiya
Aminatu shiyasa bai fiye cin wanda ake kawowa sashinsa ba.
Jalal Jamil Ummin suke cin wannan abincin.
To sashin Hajia Mama kullum za'a kawo Side ɗin shi.
Hakama gidan Barrister Kamal da Dr Aliyu yawanci suma sunasa ana kawo mishi.
kana gidan Baba Nasiru ma,
yawanci ana kawowa.
Especially kamar yanzu da su Umaymah ke nan.

To yauma haka abin yake tako ina an kawo musu breakfast, na maraba da zuwan amarya.

Koda suka zauna cin abinci.


Kamar jiya da dare, haka yauma Shatu ta ɗan kalli Aunty Juwairiyya cikin hikima
tace.
"Aunty Juwairiyya asaka mana na gidan Gimbiya Aminatu".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Wato kema irin mijin nakine, kuna son girkin Gimbiya, kunsan nata yafi naku na
zamani daɗi da lfy".
Murmushi Shatu tayi cikin jin sanyi da daɗin basu fahimci manufarta ba.

Sun fara ci kenan.


Jalal Jamil suka shigo.

Dama Haroon, Ya Jafar, oga Sheykh Jabeer suna falonshi.


can Ummi ta kai musu nasu karin.

Cikin murmushin Umaymah tace.


"Yauwa Jalal kuzo nan, kuga Aunty Amaryankun."
Matsowa gefenta Jalal yayi tare da kallon Shatu a fakaice kana yace.
"Uhumm aini na santa, taje ta tasa min ɗan uwa gaba har cikin Office dinshi tana
mishi ihu a kai".
Cikin sauri ta ɗan kalleshi tabbas ta ganeshi ta kuma tunashi Umaymah ta ɗan kalla
tare da cewa.
"Sherri ne, Umaymah ni banyi ihuba".
Murmushi Jamil yayi tare da cewa.
"Eh ai ba ihun kukaba, shi da mijin naki duk bauɗaɗɗun mutanene, da zaran kin ɗan
yi musu mgna da murya a sama to cewa sukeyi, wai kayi musu ihu".
Ya ƙarishe mgnar yana kallon corridor fitowa falonshi.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Ga baki ga tsoro".
Aunty Juwairiyya ce ta nuna musu wurin zama tare da fara zuba musu abincin.
Ita kuwa Shatu murmushi kawai ta ɗan yi, sai taji hawaye na neman cika mata ido.
Zamansu hakan ya tuna mata yayunta, ko ina suke? Wani hali suke ciki? Ko ya jikin
Ummeynta? Ya Junainah keyi da kewarsu.
Ba ya Lado, Babu Ya Gaini, Babu Ya Seyo, babu Ya Giɗi, sannan nima an kawoni nan an
cusani cikin wani irin bahagon gida mai wuyar ganewa".
A hankali tasa tafin hannunta tana share hawayenta cikin hikima.
Ɗan juyowa tayi ta kalli. Umaymah dake cemata.
"Shatu, ga Jalal da Jamil tagwaye ne, sune ƙannen Sheykh Jabeer da suke binshi
yanada wasu ƙannen Affan baya ƙasar.
Sai Imran ɗan amaryar Hajia Mama mom.
sai kuma yayunsu mata, kin san su ai ko? Rumaisa da Rumana".
A hankali ta gyaɗa kai alamar eh.
Ita kuwa Umaymah su Jalal ta kalla tare da cewa.
"Ga Auntyn ku, matar Hammanku".
Jamil ne ya ɗan yi dariya tare da cewa.
"Allah ya ɗaiyiba".
Murmushi sukayi tare da cewa.
"Amin Amin."

Nan dai sukaci sukasha kana suka dawo falon.

Kamar jiya haka yauma suka wuni.

Umaymah da Ummi na yawan yi mata dukkan bayanin komai na Side ɗinta.

Washe gari ranar. Al'hamis, da yamma taja Hibba suka koma falonta.
Cikin yin ƙasa da murya tace.
"Yauwa Hibba sammin wayarki.
Wallahi na nemi tawa har na gaji ban ganiba tun a Side ɗin Gimbiya Aminatu".
Da sauri Hibba tace.
"Dama kinada wayane? Kuma ya ɓata baki faɗawa Umaymah".
Da sauri ta jawo hannun Hibba tare da cewa.
"Ina zakije?."
"Zanje in gayawa Umaymah mana".
Ta bata amsa tana cire code ɗin wayarta-ta tare da miƙa matashi, da sauri tace.
"A a ki bari ke dai bani aron taki bari in kira Bappa na".
Ajiye mata wayar tayi bisa cinyarta kana ta wuce ta fita.
Ita kuwa Shatu, da ido ta rakata, jin tana ta rabkawa Umaymah Kira tun kafin ta
fita.
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare dasa hannun ta ɗauki wayar.

Jujjuya wayar tayi tare da miƙewa ta nufi bedroom ɗinta.


Number Bappa ta saka, kana kirashi.
tare da kara wayar a kunne mugu ɗaya ana biyu, aka amsa kiran.
Wani irin murmushi tayi jin muryar Junainah tana cewa.
"Bappa! Bappa ga wayarka ana kiranka".
Da sauri tace.
"Ƙanwaliya".
Cikin wani irin mamaki da jin daɗin Junainah tace.
"Laaaaah Adda Shatu, kece? Ina kike? Adda Rafi'a tazo jiya wai tana neman wayarki
baya shiga, Bappa yace mata ai anyi miki aure, taita kuka tace to ya batun
karatunki,
Bappa ma ya nemi number ki baya shiga.
Ina kika ajiye wayar ne to Adda Shatu".
Cikin sanyi tace.
"Wayar ta ɓata ne Junainah".
Cikin tura baki tace.
"To mijinki ya saya miki mana".
Ido ta lumshe tare da cewa.
"Ina Ummey na? Ya jikinta?".
Cikin sauri tace.
"Ummey tana na Kitchen, yanzu jikinta da sauƙi tana mgna kaɗan-kaɗan, ko ɗazuma
itace tace.
"Bappa ya kira mata ke!."
Cikin tsananin jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, kai mata wayar".
Da sauri ya juya ta nufi kitchen tana cewa.
"Ummey! Ummey ga Adda Shatuna".
Da sauri Ummey ta fito, ta amshi wayar.
Cikin murya mai cike da sanyi tace.
"Aysha na!".
"Wasu zafafan hawayene, suka zubo mata,
Cikin rawan murya tace.
"Na'am Ummey na! Ya jikinki?".
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
"Jiki da sauƙi, Shatu yaushe zaki zo?".

Bappa da yanzu ya iso daga rakiyar da yayiwa Rafi'a ne, yayi murmushi tare da cewa.
"Bani wayar nan".
A hankali cikin girmamawa ta miƙa mishi wayar.
Shi kuwa amsa yayi tare da karawa a kunne.
jin muryar bappa yanayi mata sallama ne yasata jin sabbin hawaye masu masifar ɗumi,
sabida tausayinshi.
Duk da tsufanshi mugayen ƙabilar ɓachama basu barshiba, sun kashe mishi babban ɗan
shi.
Kana sun tafi da uku, sun barshi cikin zulumin suna raye ne ko sun mutu? A ina
suke? Me akayi musu? Me sukeyi? Sannan itama data rage anyi mata wani irin bahagon
auren da yafi kama da na mulkin mallaka.
Muryarsace ta katse mata mgnar zuci da takeyi da cewa.
"Shatu kina Lfy ko?".
Murya na rawa tace.
"Lfy lau Bappa, amman bana jin daɗin gidan, ina kewarku, ya jikin Ummey na? Ya
lbrinsu su Ya Gaini an samu wani lbrin ko har yanzu shiru? Ya Ba'ana bai muku komai
bako? Ya tafi ne ko yana nan?".
Murmushi yayi tare da cewa.
"To Shatu wacce tamɓaya ɗaya zan amsa miki'.
Tana kuka tace.
"Duka".
Cikin hikima da jinƙai irin na iyaye yace.
"To sai kinyi shiru kin dena kuka".
Da sauri tasa hannu ta share hawayenta tare da cewa.
"Na bari".
Taku biyu yayi zuwa uku kana yace mata.
"Ba'ana bai mana komaiba! Ya gudu ya bar ƙasar ma baki ɗaya! Jikin Ummey ki da
sauƙi sosai! Su ya Giɗi munata addu'a in Sha Allah, in Allah ya yarda zasu baiyana
garemu da izinin ubangiji.
Kafuran nan kuma mun rigada mun karya ƙarfi su yanzu bazasu sake samun damar cutar
da muba, in Sha Allah munfi ƙarfi su."
Sai kuma ya ɗan tsagaita jin, tana murmushi mai ɗan sauti alamun jin daɗi,
a hankali yaci gaba da cewa.
"Rafi'a tazo, nayi mata bayanin komai, kuma in ta dawo zata zo, in an barta zata
shigo".
Da sauri tace.
"Zan gayawa Ummi ta sanarwa sarkin ƙofa in tazo a barta ta shigo".
Cikin danne ainihin tarin ƙunar watsewar gidanshi yace.
"Yauwa to haka zakiyi.
Sannan in sunƙi yarda kada ki damu.
Umarnine gareki, kibi dukkan umarnin mijinki, kiyi mishi biyayya a cikin dukkan
lamuranshi nasan bazai saki mugun abuba, kada ki saɓawa umarninshi.
Kada kiyi komai saida amincewarsa.
Ki kasance mai kula da lamuran rayuwarsa kada ki bar wani abun cutarwa tare dashi.
Yanzu shine gatanki. Shine madadin Giɗi, Ganin, Seyo, Lado, ƙannenshi mata ki
kallesu tamkar Junainah, mahaifiyarshi ki kalleta kamar Ummeynki, yan uwan
mahaifiyarshi ki kallesu kamar yadda kike kallon innarku, yanzu sune ƴan uwanki.
Domin naki basa kusa Ki zama GARKUWAR sa".
Shiru yayi jin kuka na son kubce mishi.
Ita kuwa tuni hawaye na kwaranya daga cikin manyan idanunta.
Cikin sanyi yace.
"Gobe zamu tafi, lardinmu, zamu koma can na wani lokaci".
Wani irin tsananin razana da tsoro ta zaro ido tare da cewa.
"Bappa zaku tafi Kardi kuma!? Ni ku barni a nan ba kowa nawa!?".
Cikin sanyi yace.
"Zamu dawo Shatu. Donke zamu dawo.
Dole muje, in sanarwa iyayen innarku abinda ya faru da ita da yaranta.
In kuma gayawa yan uwana halin da nake ciki a kan ɓatan yayunki, bayan salla zamu
dawo. Can zamuyi azumi. Bakiga yanzu a nan ko tinkiya ba'a bar manaba".
Cikin gamsuwa da zancen Bappa ta ɗan danne shessheƙan kuka tare da cewa.
"Allah ya kaiku lfy ya dawo daku lfy. Amman Bappa ku barmin Junainah mana, a kawo
min ita mana in samu iƴar uwa kusa dani".
Cikin tausasamata zuciya yace.
"Kada ki damu, su nan bazasu barki da maraiciba.
Sai mun dawo zan kawo miki Junainah da kaina".
Kit kiran ya ƙatse sabida kuɗin sun ƙare.
Hibba da tun ɗazu ta shigo tana gefenta ne,
ta ɗan kalleta cikin sanyi tace.
"Aunty Shatu, meyasa kikace bakya jin daɗin zama a gidan nan? Munayi miki wani
abune?".
Cikin zubda hawaye ta jujjuya mata kai.
Hibba bazata fahimci halin da take ciki ba, bazata gane matsalar rayuwarta ba.
Ita kuwa Hibba cikin sanyi tace.
"Aunty Shatu nima ƙanwarki ce, duk abinda zakisa Junainah tayi miki nima kisani zan
miki kinji ko".
Cikin share hawayenta tace.
"To Hibba ngd".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Yauwa kuma Umaymah ta aika Ya Jamil ya sayo miki sabuwar waya iPhone".
Cikin sanyi da son tsaida hawayenta tace.
"Ngd".

Haka yammacin ranar ta yishi a bedroom ɗin ta.


Sai Hibba dake ɗebe mata kewa ne.
Da Umaymah taga basu fito bane itama taje.

Washe Gari yau Jumma'a, kuma yaune ta cika sati ɗaya cib a gida.
Kuma tunda yazo gidan sau uku taga Sheykh Jabeer, tun randa ya wucesu, suna batun
abinci bata sake ganinshi ba, koda a gilme ne.
Yanzu ta saba da Umaymah Sosai hakama Ummi
Ita da Hibba kuwa shaƙuwa ta fara ƙarfi a tsakaninsu.
Tana jin Hibba kamar Junainah.
Jamil da Jalal Haroon suna ɗan zama asha hira dasu.
Yau ne kuma Haroon zai tafi Leddi julɓe, sabida yayi masifar kewan Jannart ɗin shi,
wacce taƙe ƙanwace ga Aunty Juwairiyya, kuma ƙawance ga Ibrahim.

Ƙarfe ɗaya dai-dai, Sheykh Jabeer, ne tsaye gaban dreesing mirror yana fesa turare
bayan ya gama shirin jummarsa tsab.
Yau shigar baƙar Al'kebbar da farar jallabiya yayi.
Yayi wani irin kyau mai cike da sheƙi.
Kusan a tare suka jero da Haroon wanda yake cikin shigar ƙananan kaya.

Su kuwa suna falon suna, zaune.

Jamil da Jalal da Ya Jafar kuwa suna tsaye alamun fitowar Sheykh suke jira.

A hankali Shatu ta ɗan ɗago kanta jin wani irin masifeffen ƙamshi mai daɗin shaƙa.

Da sauri ta janye ƙwayar idanunta,


Sabida idonta da suka faɗa cikin ƙwayar idanunshi.
Wanda shi kuwa Jalal yake kallo ganin wani shegen wondo wai shi crezi ne ko meye ne
oho, duk yana ɓuɓɓule har kana iya ganin farar fatar cinyarsa.
ga saɓulellen wonɗo ga kafurin aski.
fuskarshi ya tsuke tare da jan gajeren tsaki wanda shiyasa Jalal juyawa, ya nufi
hanyar fita yana cewa.
"To Ni banifa da manyan kayan nan, yanzu bari inje in duba ko inada jallabiya sai
in saka a kai zan biyoku daga baya."
Da ido suka bishi. Haroon da Jamil kuwa murmushi sukayi.
A haka suka fita suka tafi. Har sunje bakin ƙofar fita ba tare da ya juyoba yace.
"Umaymah ku tashi lokacin salla yayi". Ya ƙarishe mgnar suna fita
To tace.

Kana suma su Ummi suka nufi ɗakinsu.


Aunty Juwairiyya kuma ta wuce Side ɗinta.

Ita kuwa Shatu da Hibba suka tafi ɗalinta.


Hibba ce ta fara shiga tayi al'wala.
Sannan itama Shatu ta shiga.

Tana fitowa daga bathroom ɗin tayi wani irin....!

Uhummmmmm tuni mun gama shimfiɗan lbrin GARKUWA yanzu dai muna cikene dumu-dumu .

By
*GARKUWAR FULANI*Tsayuwa tare da kasa kunnuwanta.
Tana jin sautin zazzaƙar muryashi.
Yana kudba.
Akan laduban fuskantar watan Ramadan wanda zuwa yanzu kwanaki ne suka rage.

A hankali ta fara taku tana


Nufo inda Hibba ta shimfiɗa musu sallaya.
Ita kuwa Hibba ido ta zuba mata ganin yadda ta kasa kunne.
Cikin murmushin tace.
"Aunty Aysha me kikeji".
A hankali tace.
"Wannan me sunan malamin da yake huduban nan. Kamar inada wa'zuzzukanshi amman
kuma, ban san sunanshi ba, kamar dai kam nasan wannan Muryar".
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Lallai ma kam Aunty Aysha wai muryar Hamma Jabeer ɗin ne ma kike cewa kamar kin
santa, kamafa kikace, lallai kam my Aunty".
Da sauri ta kalli Hibba domin zuwa yanzu ta gane waye suke cewa Hamma Jabeer, Ko
Sheykh, ko Jazlaan, ko Muhammad wani lokacin Umaymah na kiranshi haka.
Ta kuma fahimci wai shine mijin da aka aura mata.
Ta kuma gane sun taɓa haɗuwa sau biyu kafin yau.
ganin tayi nisa a tunnine yasa Hibba cewa.
"Aunty Aysha".
Murmushi ta ɗan yi tare Dasa hannun ta amshi hijabin da Hibba ke miƙo mata.
Cikin ranta take mgnar zuci.
"Uhumm mutun duk rayuwarsa tana cike da ƙalubale da matsaloli Magauta sun sashi a
tsakiya kota ina ya juya suna tare dashi.
Amman bauɗewa ta hanashi ganewa, sai anyi mgn yace wai anayi mishi ihu a kai.
ko shi kunnen macijine dashi da yafi kowa jin sauti.
sai iya lillibka ɗika-ɗikan al'kyabbar yanata ɓoye jiki kamar wani mace".
Mitsss ta ɗanja gajeren tsaki tare daci gaba da zancen zuci.
"Yana nan jiki duk matsaloli ya bari mutun yaga iya inda abunda ke kan yatsunshi
ma, ya gagara, shine kullum cikin al'kyabba har ƙasa uwa shine limamin harami.
Sai an kasheshi a banza yasa ƙannenshi da iyayenshi a matsala.
Danni matsalar rashin yayuna har huɗuma ya isheni damuwar duniya bazan ƙarawa kaina
damuwar waniba".
Da sauri ta juyo ta matso kan sallayar sabida jin har masallacin sun sallame
sallar, sabida ta daɗe a tsaye tana zancen zuci.

Nan dai sukayi salla, kana Hibba ta miƙa ta fita


Ita kuwa Shatu, sabuwar wayarda aka saya mata jiya da sabon layi aka haɗa mata
komai ne, tasa hannunta,
ta jawo.
tare da komawa ta kwanta bisa sallayar.
Layin Bappa tasa kana ta kira.
Jin bata shiga bane yasata gane, sun tafi kenan.
Cikin sanyi ta kira ɗaya layin na wancan ƙasar tasu.
Cikin sa'a kuwa ya shiga sai dai ba'a ɗagawa.

Sau uku ta kira jin ba'a ɗaga ba, ta haƙura.


Number Rafi'a tasaka ta kira.
Tana ɗagawa tace.
"Rafi'a Garkuwa ce".
Cikin tsananin jin daɗi Rafi'a tace.
"Alhamdulillah Garkuwa ya kike? Ina kike? Ashe kuma abinda ya faru kenan.
Alhamdulillah mun rabu da matsalar Ba'ana, jiya naje Rugar Bani, wai yau su Bappa
zasu tafi Lardi".
Cikin murmushi tace.
"Kai Rafi'a kimin mgna da ɗaɗɗaya mana zanfi ganewa".
Cikin dariya tace.
"Eh kyace haka mana kinyi bulunbuƙui a masarautar Joɗa".
Cikin sanyin jiki taja numfashin tare da cewa.
"MASARAUTAR Joɗa ko matsala, komai a bai-bai yake Rafi'a, bana fahimtar komai,
tunda nazo cikin wannan masifeffen masarauta kaina a juye yake. Jina nake kamar a
rami".
Cikin rauni tace.
"Rafi'a abubuwan sunmin yawa, da wanne zanji.
Tabbas nayi farin cikin tsira daga tarkon ya Ba'ana, to amman ƙaddara batayi min
adalciba data kawoni wannan wurin.
Kin sani Allah ya sani ina son Ya Salmanu".
Da Sauri Rafi'a ta katseta da cewa.
"Kice Astagafirullaha kada ki mance da auren wani a kanki kike cewa kina son wani".
Hawayen da suka cika mata ido ta share tare da cewa.
"Bana sonshi! Bana ko son ganinshi, kuma shima hakane baya sona baya son ganina.
sauƙina ɗaya da shima ba sona zaiyiba, kowa zaiyi rayuwarshi babu ruwanshi da wani
shiyasa hankalina bai tashi sosaima, sai dai ina cikin tarin damuwa Rafi'a, babu Ya
Giɗi,Gaini, Seyo, Lado, Inna. Sannan Junainah,Ummey da bappa da nake gani inji
sanyinma wai sun tafi Lardi,
ya zanyi inji farin ciki, ga wannan gida mai mutantani daban-daban wasuma naga
tsanar shi wancan mai jajayen kunnuwan zasu ɗora a kaina, ko uwar meye haɗina
dashi, da magautanshi zasu haɗa dani a ƙiyayyarsa, suji dashi mana, tunda bansan
meya shuka musuba, dan shima na lura ba kanwar lasa bane bakine dashi, kan ace
ɗirin yake ce musu konɗi, rashin tsoronshi na bani tsoro."
Murmushi Rafi'a tayi tare da cewa.
"Yanzu dai ya batun karatunki?".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"Zan gayawa Umaymah".
Cikin shaƙuwarsu Rafi'a tace.
"To sai na shigo, dan mgnar bazata ƙare a wayaba".
Da sauri tace yaushe zakizo?".
Cikin sauƙe numfashi tace.
"In sha Allah dai kafin azumi zan shigo".
Cikin sauri tace.
"Kafin azumi kuma azuminfa da ɗan saura bama kice gobe ko jibiba, Rafi'a in bakizo
minba wa nake dashi da zai zomin?".
Ta ƙarishe mgnar cikin rauni,
Cikin tausayin Rafi'a tace.
"To gobe ko jibi in sha Allah".
Cikin jin daɗi tace.
"To sai kinzo."
Daga nan sukayi sallama.

A ranar da yamma Haroon ya wuce jiharsu Jannart inda nanne masarautar sarkin
musulmai take.

A hankali dai kwanakin sukayi ta gungurawa suna cuɗewa Ramadan nata ƙara gaba towa.
Yayinda duk al'ummar Annabi suketa shirye-shiryen tarban watan Ramadan.

Yau dudu saura kwana bakwai ne ake zaton za'a fara azumi, in bai cikaba ma kwana
shida.
Tuni Umaymah nata shirin komawa Jihar Tsinako sabida Abban Haroon ya matsa ta dawo
sabida shirye-shiryen Ramadan.

Ita kuwa Umaymah tana jiran kayan auren data aika a haɗo mata a Dubai su isone.
wanda ƙawarta ce ta bawa aikin kuma ƴar nan cikin jihar Ɓadamaya ne!

Yau Lahadi ne, ta kama ranar bautar al'jihun baya ne.


Wannan yasa duk manya-manyan Coci na cikin garin Ɓadamaya ya cika maƙil da mabiya
bayan addinin Kirista ci.

A hankali motocinsu suka fara fitowa cikin masarautar Joɗa, suna kama babban hanyar
da zata sadasu da asibitin taraiya na jihar wato Genaral Hospital Ɓadawaya.
Kamar kullum haka tawagar take, Lamiɗo zaije kai ziyarar dubiyar marasa lfy kamar
yadda ya saba duk ƙarshen mako.
A ƙalla motocin sun kai goma.
Suna tafiya a jere a jere.
Har suka iso yankin da asibitin yake, inda nan babbar hanyar hada-hadan cikin garin
ne, wanda babbar kasuwar jiharma take kan titin.

Wani tabkeken cocine mai zaman kashi a bakin babban titin LCCN, yana ta hannun
hagu.
Kana ta hannun dama kuma wani tsabtaceccen masallacin juma'a ne mai ɗan karen
girma, haka ya zama suna fuskantar juna masallacin da cocin.
Kana sai an wuce ta gabansu za'a ratsa konar shiga asibitin.

To kasan cewar duk ranar jumma'a ƴan agaji na toshe hanyoyin daga ƙarfe sha biyu da
rabi zuwa kan a idar da sallan jumma'a su buɗe,
sai kafuran nan suma suka tsiri duk ranar Lahadi tun shida na safe zasu,
Toshe hanyoyin nan, sai shida na yamma.
Wanda hakan ke jawo cinkoson ababen hawa ata yankin wuri. Sai ya zama duk masu son
yin salla a wannan masallacin jumma'a to ranar a sai tsare musu hanya,
sai dai masu zuwa da ƙafa.

Wannan abun ya damu musulmai, koda aka kai ƙorafi ga gwamnatin jihar sai cewa tayi.
"Ita bata son fitina, a bar kowa yayi addininshi salin alum".
Haka musulmai suka haƙura dan a zauna lfy. To masarautar Joɗa bata da wannan lbrin
sai yau da suka fito ranar lahadi da yake kullum asabar suke zuwa.

A jere a jere motocin ke tafi kasan cewar da sanyin safiya ne,


lokacin sun gama rufe hanyoyin kana sunata tsastsafowa gabas da yamma kudu da
Arewa.
Cikin Mamaki motar su Lamiɗo da saura duk suka tsaya, sabida ganin motocin gaba sun
tsaya.
da sauri Sallama ya fita, tare da dawowa baya.
zuwa gaban motar Lamiɗo yayinda Motar Sheykh Jabeer kuwa take can bayansu, shi
sauri yake zaije Valli Hospital dan yiwa wata mata aiki.

Rusunawa Sallama yayi tare da cewa.


("Allah rene halkaleru en mabɓi labi mai".) Allah rene kafurai sun rufe hanyoyin".
Da sauri sarkin ƙofa ya fito yazo ya buɗewa Lamiɗo marfin yadda zasuji juna da
kyau.
Cikin mamaki Lamiɗo yace.
"Lfy meya faru zasu rufe hanyoyin".
Da sauri dubagari yace.
"Ai haka sukeyi duk ranar Lahadi, su hana mutane sakewa su rufeshi tun safe sai
yamma".
Cike da Mamaki Galadima da yanzu ya iso wurin yace.
"To duk hakan na menene?".
Cikin sauri Duba gari ya ɗan rusuna tare da cewa.
"Wai sabida musulmai na rufe hanyar duk ranar jumma'a sabida bada tsaro wai suma
shine suka tsiri, hakan ankai mgnar wa gwamnatin kuma ta goyi bayansu".
Cikin ta ajjudi suka kalli juna,
kana cikin bada umarni Lamiɗo yace kaje kace, su buɗe hanyar yanzu nan.
Kuje da sarkin aike".
Nan take suka juya suka nufi can inda yaransu ƙananan ke tsaye su kakkafa Road
closed and stop.
Suna zuwa jim kaɗan suka dawo.
Tare da cewa ai yaran sunƙi sabida sunce Gwamnatin jihar ta amince musu da haka.
Wannan mgnar yayi masifar tasa zuciyar Lamiɗo.
Cikin ɓacin rai ya zaro wayarshi ya danna mai girma Gwamnan kira.

Inda yace maza, ya bawa kafuran nan damar buɗe waɗannan hanyoyin da suka rufe.
Ba kunya gwamnan yace, to ai. Dokace Allah rene da kunbi wata hanyar ai yafi ko."

Cikin tsananin tarin takaici Lamiɗo yace.


"Muje duk ku shiga mota, mu canza hanya."

Sun shishiga kenan sai kuma sukaji.


matasa irin wanda suke gefen wurin suna cewa.
"Jahan! Jahan!! Jahan!!!".
Da Sauri Duk suka fara leƙawa suna kallon wanda ake kira da Jahan, ɗan jarida
mai zaman kanshi wanda jihar Ɓadamaya da kewaye ke alfahari dashi. Duk da ya
kasance Musulmi mai sunaga ba nasu bane, kafurai kuma suna alfahari dashi a
matsayin nasune.

Cikin isa da karsashi yake taku cikin wasu irin zafafan ƙananan kaya masu masifar
kyau. Jahan kekyawane aji ƙarshe a kyau, fari ne ƙal hanci har baki shiyasa da yawa
kance shi iyamurune, idanunshi farare ƙal-ƙal gashin kansa gwanin kyau sai dai
kafurin askin dake kanshi.

Yaran suna hangoshi suka matsa.


Shi kuwa Jahan da kanshi ya buɗe hanyoyin gaba ɗaya.
Kana ya nufi motar fadawa dake gaba.
Haɗe hannunshi yayi wuri ɗaya tare da.
Musu alamar suyi haƙuri kana ya musu alamar su wuce.
Daga nan motar Waziri ya nufa, suma ya basu haƙuri. Haka yayi tayi har gaban
motarsu Lamiɗo,
cikin sanyi ya rusuna gaban marfin motar, tare da jinjinawa Lamiɗo kana yace.
"Tuba muke Lamiɗo, ga hanya an buɗe".
Wani irin sanyi da daɗi Lamiɗo yaji, gashi duk da Gwamnatin ta kasance ta musulmi
siyasa ta hanashi adalci.
Gashi wanda ba nasu ba ya zantar da adalci".
Haka ya rinƙa bawa mutanen cikin motocin haƙuri suna wuce.
a haka har yaje mota ta ƙarshe,
Yana isa yasa hannu ya buɗe marfin motar.
Wani irin kallo mai cike da ma'anoni yakeyi mishi.
sai kuma yayi wani munafukin murmushi.
Ganin hakane ya ja motarshi ya tafi.

Washe gari ranar Litinin. Da hantsi Hajia Kubra aminiyar Umaymah ta iso.
da yan rakiyanta.

Kai tsaye har bakin part ɗin Sheykh Jabeer sukayi parking.
Kana ta shiga cikin

Cikin farin ciki suka ruggume juna ita da Umaymah cikin dariya Umaymah tace.
"Hajia Kubra amman kin shamma ceni".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ato ai naga kin zaƙu kina son ki koma Tsinako ne nace bari dai in hamzarta
indawo".
Ta ƙarishe mgnar tana zama tare da miƙa Jalal car key ɗin ta tace.
"Yauwa Jalal Jamil ku shigo da kayayyakin."
To sukace kana suka amshi key ɗin suka fita.

Nan suka buɗe motoci biyun wanda tazo a ciki da wanda drever'nta yazo a ciki.
Nan suka rinƙa kwatsar akwatunan suna shigarwa.
Set biyune masu fasifar kyau da tsadan gaske.

Umaymah kuwa tuni tasa Juwairiyya ta cika Hajia Kubra kayan kwalam a gabanta.

Robar Inabi ta ɗauka tana buɗewa ta kalli Umaymah cikin raha tace.
"Hajia Khadijah ina ɗiyar tamu".
Cikin murmushin Umaymah ta ɗan juyo ta kalli ƙofar falon Shatu tare da cewa.

"Hibba! Hibba!!".

"Na'am".

Hibba ta amsa tana miƙewa tsaye


Kizo keda Aysha ga Mommy Kubra tazo".
Cikin jin daɗi Hibba ta miƙe tare da cewa Shatu.
"Wayyo Aunty Aysha tashi muje".
Cikin nitsuwa ta miƙe tsaye,
mayafin Arabian gawd ɗin dake jikinta ta gyara.
Kasan cewar shi guntu yasa bai ida rufe mata jelan gashin kanta data tubkeba.

Suna fitowa Hibba ta faɗa jikin Hajia Kubra tare da cewa.


"Oyoyo Mommy Kubra".
Ruggume Hibba tayi tare da cewa.
"Oyoyo My Muhibbat".
Sai ta kuma kalli Shatu dake ƙoƙarin rusunawa.
da sauri ta riƙo hannunta tare da cewa.
"Zo nan kusa dani kema ɗiyata ce, bakya ganin yadda Hibba tayiin".
Murmushi tayi sabida fara'ar matar ya burgeta cikin sanyi yace.
"Mommy Ina wuni".
"Lfya lau ɗiyata ya gida ya baƙun ta?".
Cikin girmamawa tace.
"Alhamdulillah".
Hibba ce ta zamo daga jikinta tare da cewa.
"Mommy wannan kayanfa?".
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
"Na Aunty Shatu ne".
Da sauri ta zamo tare dasa hannunta zata buɗe akwatin dake gabanta, cikin haɗe
fuska Umaymah tace.
"To uwar azarbaɓin, waya saki. Tashi kije ki kira min yar uwata kice mata ga saƙon
sun iso".
Da sauri ta miƙe tare da cewa.
"Aunty Aysha zo muje Side ɗin Hajia Mama mu kirata".
Da sauri ta jujjuya kanta tare da cewa.
"A a sai kin dawo".
Tana faɗin haka ta miƙe ta koma falonta.
Ummi Aunty Juwairiyya da Umaymah kuwa kallon junansu sukayi.
Hajia Kubra ce tace
"Kunya ko". Murmushi Umaymah tayi tare da badda zancen da haka.

Ita kuwa Hibba da sauri taje ta kira Hajia Mama, aiko kusan tare suka taho, da
Botool.

Koda sukaje Umaymah ta aika Ummi a matsayin ta na Jakadiyarsu take ta sanarwa


Gimbiya Aminatu tazo taga kayan auren da ta haɗa amryar Jazlaan ɗin ta.

Bayan duk sun zone, Suka bubbuɗe akwatunan, goma sha biyun nan duk cike suke maƙil
da kayayyakin bukatar amare.
Abun sai wanda ya gani.
Lokacin da aka buɗe akwatunan turaruka gaba ɗaya Side ɗin ya cika da ƙamshi tako
ina.
Manyan akwati biyu aka cika da dogayen riguna masu masifar kyau da tsada da taushi.
Sai kuma biyu da aka cikasu da atampopi da shadda da lace.

Sai kuma babba daya da aka cikashi maƙil da laffaya masu azabar kyau da tsada, babu
kalan da babu a ƙalla sun kai kala ashirin da huɗu.

Sai biyu daga ciki ƙananan kayane birjik

Sai wani babban bakko, da aka cikashi da takalma a ƙalla kala goma sha biyar,
bakwai daga ciki sunada hand bang, hudu daga ciki pase garesu.
hudu kuma masu siffan sayyadane masu kyau.

Sai kuma kayan tarkacen mayuka da sabulai na jiki da kai.

Kai abun dai masha ALLAH.

Da sauri Hibba ta zari takalma uku daga ciki takalmomin ta nufi bedroom ɗin ta da
sassarfa tana cewa.
"Aunty Aysha bari inzo ki gwada takalman nan, Ni dai sai inga kamar zasuyi miki
kaɗan.".
Tana shiga ta ajiye mata takalman a gabanta tare da cewa.
"Gwada mu gani".
Sosai takalman sukayi mata kyau, haka yasa ta zura ƴar kekyawar farar ƙafarta.
Ai kuwa tayi mata cib-cib cikin dariya Hibba tace.
"Ashe dai zai miki dai-dai".
Murmushi tayi tare da gyaɗa tare da cewa.
"Uhumm ba kin raina ƙafar tawaba".
Daga nan ta juya, ta koma falo, nan ta samu Hajia Mama na cewa.
"Wannan kaya haka Khadijah kin kashe kuɗinki a banza ƙanwata wannan yarinyar ba
matar auren Muhammad bane".
Cikin yin ƙasa da murya Umaymah tace.
"Karkice haka Hajia Mama".
Cikin ɓacin rai tace.
"Khadijah ai dole ince haka, ke har yanzu baki gane cewa wannan yarinyar ba matar
ahlin masarautar Joɗa bace, a gabanki fa, taƙi shan madarar Barka da zuwa
Masarautar Joɗa.
ta kuma kwaɓar dana hannun Jabeer wanda shine na Barka da zama magidanci.
Hakafa zatayi ta kwaɓar da duk wani abun ci gaba ko nasara a rayuwarsa."
Batool ce ta ɗan gyara zamanta cikin danne baƙin cikinta tace.
"Uhummm a tsallake ƴan uwa jinin sarauta aje a kwaso mishi bagidajiya ba fullatanar
daji, ba dole tayi halin dabbobiba tunda cikinsu ta tashi. Tasan menene masarauta
bare tasan ƙai dojinshi da kuma, nasabarsa."
Ta ƙarishe mgnar tana son maida hawayenta.
Allah ya sani tana son Sheykh Amman ta lura, Hajia Mama taƙi sa baki abin yayi
gashi har an auro mishi wata.
Cikin murmushin Umaymah tace.
"Batool zaki auri mai matane?".
Cikin sauri tace.
"In wanine bazan auri mai mataba, amman in Hamma Jabeer ne, wlh ko mata uku gareshi
da ƙwar-ƙwara biyar in zai aureni zan yarda in zama ta tara,
Kowa ya iya allonsa ya wonke".
Murmushi Hajia Kubra tayi tare da cewa.
"A lallai kam".
Ita dai Hajia Mama miƙewa tayi ta fice rai a ɓace.

Gimbiya Aminatu kuwa, murmushi tayi tare da cewa.


"Ji ƙarfin hali ita kafin uban Jabeer ya arota Allah ne kaɗai yasan adadin dukiyar
da aka narka.
Sam iyayen mazan yanzu sai a hankali."
Cikin sauri Hajia Kubra tace.
"Matan ƴaƴan ma na yanzu ba irin na da bane.
Shiyasa aketa samun matsala tako ina kowa kansa ya sani".

Ita dai Umaymah murmushi tayi tare da cewa Juwairiyya.


"Juwai keda Hibba kuje ku kimtsa mata komai a ɗakinta ku shirya mata drower'nta.
Kana ku kimtsa mata kan dreesing mirror.
Kai kuma Jamil ɗauki bakon takalman nan ka juye takalman.
Juwairiyya kisa Shadda bakwai lace bakwai, atampa bakwai, kampala Bakwai, swiss
voile bakwai.
A cikin atamfofin kisa
Super wax biyu English wax biyu, Holand biyu sai swiss atampa ɗaya.
Sai kusa a bakon.

Jamil sai ka kaisu wurin telan Juwairiyya.


Ayi ɗinkunan da wuri."

Haka kuwa akayi akani komai yadda tace.

Bayan sun gama kimtsa mata komai da jera komai a muhallin shi ne,

Suka fita, sannan Umaymah ta shigo, gefenta ta zauna cikin nitsuwa tace.
"Ɗiyata ga kayan sawarki naso ace sun iso tun kafin yau.
To sha'anin nesa, shiyasa kikaga bai iso da wuriba, duk kayan nakine kisa wanda
kikeso a sanda kikeso.
Sabida ke akayi komai."
Cikin tarin jin daɗi da ganin darajar ta tace.
"Ngd Umaymah Ngd matuƙa, Allah ya saka da al'khairi".
Amin Amin tace kana ta miƙa tare da cewa.
"Naga kina son dogayen riguna ranar da zan aika kince su kikafi so, gasu an kawo
miki su da yawa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Nagode sosai Umaymah Allah ya ƙara girma".
Amin Amin tace kana fita.

Ita kanta Shatu tasan babu ƙaranta a duk kayan da aka jinbga mata.
Komai mai kyau ne.

Yau talata da hantsi suna zaune a falon.


Hadimai sukayi sallama da Jakadiyarsu, bayan ta basu izinin shigowane.
Suka fara shigowa suna wucewa kitchen da kayayyakin abinci kamarsu shinkafa ta tuwo
buhu biyu ta wara buhu biyu, sai gero ƙaton buhu, wanda a surfe yake, taliyar manya
data yara katon biyar-biyar, kiret-kiret na ƙoyaye biyar, jarakunan mai dana manja
bibbiyu katon ɗin maggi ɗaya dasu doya da dankalin turawa mai yawa.
Haka suka rinƙa jida suna kaiwa store.
Bayan sun gamane, Umaymah ta kalli Aysha cikin yin ƙasa da hannu ta miƙa mata dubu
biyar.
Kana tace.
"Engo basu tukuici, wannan daga store ɗin masarautar Joɗa ne, duk ko wani sashi
haka ake kai musu in Ramadan ya kawo kai."
Cikin jin kunya tasa hannu ta amshi kuɗin kana ta miƙa Hibba tare da cewa.
"Hibba basu".
Da sauri Umaymah ta girgiza mata kai, sai kuma ta kalli hadiman suna shirin fita
tace.
"Kuzo matar Sheykh na kiranku".
Ɗaya daga cikin sune, ya dawo.
a hankali ya iso ya rusuna gaban Shatu tare dayin ƙasa da kanshi.
Cikin nitsuwa yace.
"Gashi mun gode Allah ya kaimu baɗi lfy".
Amin Amin suka amsa baki ɗayansu.
Kana ya amsa ya miƙe ya fita.

Su kuwa sukaje sukaci gaba da hirarnsu.

Washe gari kuma ranar Laraba.


Wanda ana zaton kwana huɗune ya rage Ramadan, koma biyar.

Umaymah ce zaune ita da Sheykh,


ido ya zuba mata har ta gama mgnar da yakeyi na batun ran jumma'a fa zasu koma.
ta jaddada mishi kadafa ya mance yanzu yanada mata.
Kanshi ya jingina jikin kujerar tare da son kauda wannan zancen yace.
"Jadawalin jerin malam da zasuyi tabsirin Ramadan a jahohi mabanbanta ya fito".
Cikin alfahari da hakan tace.
"Wacce jahar kuma aka turaka bana?".
Ɗan gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Tun da da nake ta son a barni a jihata, kullum sai a turani wata jihar, sai bana
kuma da nake son in tafi wata jihar suka barni a nan".
murmushin jin daɗin hakan tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah kaga darajar aure ko".
Bai tanka mataba,
itama bata jira ya tanka matanba tace.
"Ya batun tafiya umarah kuma".
Kanshi ya ɗan ɗago ya kalleta hannunshi yasa ya shafa sajenshi cikin nitsuwa yace.
"Sha biyar ga watan zan tafi".
Da sauri tace.
"Zaka tafi ko zaku tafi?".
Kanshi ya ɗan dafe tare da nazarin ya zai yanke mgnar cikin nitsuwa yace.
"Eh zamu tafi".
Yalwataccen murmushi tayi sabida bata gano manufarsa ba.
Cikin kula yace.
"Kefa yaushe zakuje".
Tana ƙoƙarin miƙewa tace.
"Shatara ga watan Ramadan zamuje".
Da sauri yace.
"Umaymah". Komawa tayi ta zauna tare da cewa.
"Na'am".
Cikin kwaɓe fuska yace.
"Muna mgna kuma zaki tafi, me zakije kiyi ne a can ".
Cikin murmushin tace.
"Zanje wurin Aysha akwai mgnar da zamuyi".
Ba tare da ya san waye kuma wacce mai suna Shatu'n ba yace.
"Uhumm shike nan".
Cikin kula tace.
"Ko akwai wani abu ne?".
Kai ya girgiza mata, ganin haka yasa ta miƙa ta fita.

Shi kuwa ya miƙa ya shiga bedroom ɗin shi dan yana son yin baccin tsakanin azahar
da la'asar, sabida wannan baccin yanada al'fanu.
Dan zai taimakawa mutun wurin tashi da dare.

Ita kuwa Umaymah a falo ta samu.


Shatu da Ummi. Dan Hibba tana can sashin Aunty Juwairiyya.

Gyara zamanta, tayi tare da kallon Ummi cikin nitsuwa da shaƙuwarsu tace.
"To Ummin Jabeer, Ni dai tafiya ta ƙara to in Allah ya kaimu, jibi jumma'a zamu
tafi, zan barki da sauran aikin".
Cikin sauri Ayshs ta ɗago kanta ta kalli Umaymah cike da fargaba tace.
"Umaymah tafiya?". Ta ƙarishe mgnar cikin sanyi.
Ido Umaymah ta ɗan zuba mata cikin karantar yanayin da take ciki tace.
"Eh Aysha zamu tafi jibi da yamma jirginmu zai tashi zamu tafi Hibbab ya dawo yace
yana kewar Hibba".
Da sauri tace.
"Ayyah Umaymah dan Allah kada ki tafi da Hibba, ayyah Umaymah a bar mana Hibba".
Ta ƙarishe zance fuska cike da rauni".

Shiru Umaymah tayi sabida ganin hawaye suna shirin zubo mata,
sai kuma ta miƙa da sauri ta nufi ɗakinta, sabida jin bazata iya danne hawayen
nataba, Allah ya sani ta saba da Hibba sosai, itake ɗebe mata kewar Junainah,
Umaymah ke meye mata gurbin Ummeynta, sannan wai duk zasu tafi.
Tabbas ta saba da Ummi amman ba kamar Umaymah.
Sam tama kasa yarda da Juwairiyya kam ma.

Koda ta tafi, Umaymah da Ummi murmushi sukayi.


Cikin sanyi Umaymah ta fara mgn da Ummi bisa dukkan alamu mgnace ta sirri domin
nima banjisuba.

Na dai ga daga ƙarshe duk suna zubda hawaye.

Bayan sallan isha'i ne Hibba ta nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.


Dan amsowa Hamma Jabeer ɗinsu aiken da ya mata.

Bayan ta dawone ta ajiye Foodflaks a gaban Umaymah tare da cewa.


"Umaymah gashi, a kai mishi".

"Jeki gayawa matarshi tazo ta kai mishi."


To tace tare da juyawa ta nufi falon Shatu.

Ganin bata falone yasa ta wuce bedroom.


A kwance ta sameta bakin gado.
Ta konta rubda ciki, tanayin kuka mai sanyin sauti.
da sauri ta zauna gefenta tare da cewa.
"Aunty Shatu meya faru?".
da sauri tasa tafin hannunta ta shere hawayen, kana ta miƙe zaune hannun Hibba ta
kama ta riƙe tare da zuba mata ido cikin sanyin murya tace.
"Please Hibba mu zauna kada ki koma, ki cewa Umaymah zamuyi azumi a nan."
Shiru Hibba ta ɗanyi kana ta ɗan yi murmushi tare da cewa.
"To zan gaya mata, kuma kema ki gayawa Hamma Jabeer in shine yace mata ta barni
bazata hanani ba."
Cikin sanyi tayi shiru, alamun nazari, ta ina? kuma ta yaya? yaushe zata mishi
mgna? Mutumin da ko kallon inda take bayayi! Anya kuwa yama sanni ne?!.
Tayi mgnar zuci.
Ita kuwa Hibba cikin murmushi tace.
"Allah muwa in kin gaya mishi za'a barni".
kai ta jinjina tare da komawa zata jingina da kan gado, da sauri Hibba ta kamo
hannunta tare da cewa.
"A' a taso Umaymah tace kizo".
To tace tare da miƙewa, a tare suka fito falon.
Cikin kulawa Umaymah ta nuna mata Foodflaks ɗin.
"Ɗauki ki kai mishi falonshi".
da sauri ta zaro ido cike da mamaki, gane hakane yasa Umaymah kauda kanta,
ita kuwa Shatu shiru tayi tare da zubawa kulolin idanu.
Muryar Ummi ce ta kuma ratsa kunnuwanta.
"Ɗauki ki kai mishi in dare ya ɗan yi nisa bazai cibafa".
Bazata iya musu musu da gardama ba.
haka yasa cikin sanyin jiki ta sunkuyo ta ɗauki Foodflaks ɗin, kana ta juya a
hankali ta nufi corridor da zai kaita Side ɗinsa,
tafiya takeyi cikin nitsuwa kanta a sunkuye.

A bakin ƙofar falon ta ɗan tsaya cikin sanyi murya can ƙasa tayi sallama , yadda
ita kanta batayi dan wani ko zaton wani yajiba.

Yana can Dinning area, yana zaune bisa ɗaya daga cikin chairs ɗin Dinning table
ɗin.
Yasa System nashi a gaba.
hankalinshi duk yana kai, ga woyoyi a ƙalla uhu suna gefenshi.
sai cup mai cike da madarar shanu mai ɗumi.

Murya can ƙasa bisa saman tattausan jajayen laɓɓansa ya amsa sallamar da ya jita
raɗau cikin kunneshi sai dai bai fahimci mai muryar kai tsayeba,
asalima ji yayi kamar muryar Umaymah ce.

A hankali ta turo kanta ta yaye labulen kana ta sako ƙafanta cikin, falon da bata
son koda kallon ta inda yake, ba don bai mata kyauba sai dan wasu manyan dalililai
da abubuwan da take gani tako ina a falon,

A hankali take taku, i zuwa inda ta hangoshi zaune ya bawa ƙofar shigowa baya.
cikin nitsuwa ta take step ɗin forko,
tare da ɗago kai ta kalli ƙeyanshi.
baki ta murguɗa tare da taɓe bakin kana ta manna mishi harara bisa tattausan suman
ƙeyan nashi.
A haka ta ƙara motsowa, shi kuwa Sheykh Jabeer tabbas yasan da mutun a bayanshi.
Ya kuma gano wancan abun ne, shiyasa ko ta kanta baiba.

Aikin da yasha mishi kai yakeyi ba kama hannun yaro.


Da sauri ta ajiye Foodflaks ɗin bisa glass ɗin Dinning table ɗin, wanda hakan ya
bada wani sautin.
Idonshi ya ɗan rumtse tare da buɗesu, kana yaci gaba da aikinshi ko gefen da take
bai kalla ba.
Ita kuwa sai ruwan harara taketa manna mishi tako ina.
kana kuma dai tana tsaye bata juya ba.
a ƙalla 55 second bata tafiba, bata kuma ce mishi komaiba, sai hararan da takeyi
mishi har ta fara jin idonta na ciwo,
sabida harara ba ɗani'arta ta yau da kullum bane, sai in tana masifar jin haushin
mutun da tsanarsa take mishi wannan abun.

Bai kulataba, ganin ba kulata zaibane yasa ta ɗan ja wani gajeren tsaki can cikin
maƙoshinta, a zatonta baijiba.
shi kuwa Sheykh Jabeer kanshi ya ƙara rusunarwa sabida sam ya lura wannan abun ba
kunya ne dashiba.
Cikin murhuɗa baki da harara tace.
"Dan Allah ka cewa Umaymah ta bar min Hibba muyi azumi a nan".
Ta ƙarishe mgnar da ɗan ƙarfi.
Shiru yayi tamkar bai jitaba ko baisan da ita a wurinba,
Sabgogin gabanshi yakeyi tamkar babu wani halittan dake wurin.
cikin kufula ta kuma cewa.
"Dan Allah kace a barta muyi azumi anan".
Ko gezau baiba. Sai dogayen fararen yatsunshi da yake sarrafawa bisa ma dannin
System ɗinsa tamkar shiya ƙirƙirota.
Shi sauƙinshi ɗaya tunda yanzu zuciyarsa ta dena bugawa da tsinkewa in mayyar tana
kusa.
A karo na uku ta kuma yin mgna tare da juyawa ta fita.

Bai kulataba bashi kuma da niyar kulata.


Ita kuwa Shatu cikin takaicin sheretan da yayi ta fito.
Ita in ma badon batun Hibba ba mai zai sa tayi wa wannan mutumin mai ɗan karen
mannin hauka da ƙasaita mgn.

A falo ta samu su Umaymah dasu Jalal, gefen su ta ratsa ta wuce, da sauri Hibba
tabi bayanta.

Tana shiga tace.


"Aunty Aysha me yace?".
Cikin nuna damuwarta tace.
"Uhum yace Umaymah ce taƙi, sai dai in ita zamuyiwa mgn".
Ta ƙarishe mgnar da nazarin ta yayama zata cewa Hibba tayi mgna bai ko kalli inda
takeba bare ya kullata.
Hibba kuwa da sauri ta juya tare da cewa.
"To bari inje in lallashi Umaymah."

To tace wanda. Tunima Hibba kam ta fita.

A gaban Umaymah ta zauna cikin sanyi tace.


"Ayyah Umaymah dan Allah a barni inyi azumi anan, kinga Aunty Aysha ta roƙi Hamma
Jabeer yace ki barni yace kin yarda ne, gata can tana fushi".
Cike da mamaki da jin daɗin yadda akayi sukayi mgna dashi, har ya gaya mata yadda
sukayi dashi jiya kan ta bar Hibba tace a a.
Jamil ne ya ɗan kalli Umaymah tare da cewa.
"Dan Allah Umaymah ki barta, in anyi salla Ni da kaina zan dawo miki da ita tunda
jakar ratayawarki ce ita".
Cikin dariya Ummi tace.
"Eh dan Allah ki barta in dai mahaifinta zai yarda, kinga tana ɗebewa ɗiyar taki
kewa".
Murmushi Umaymah tayi kana, ta kalli Jalal da bai sa musu bakiba.
Aunty Juwairiyya ma magiya take a bar Hibba, hakane yasa Umaymah tace to ba matsala
zata bar musu ita aron wata ɗaya ran salla dai zata koma, cikin jin daɗi sukace sun
yarda.

Ai da gudu fa Hibba taje ta gayawa Shatu.


Sosai taji daɗi har ta ɗan saki jiki.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko inda Foodflaks ɗin suke bai kallaba, sabida ba tsarinshi
bane cin abu mai nauyi in dare yayi, haka yasa iya madarar yasha,
kana yaci gaba da aikinshi.

Washe gari ranar Alhamis, wuni Umaymah tayi tana shirye-shiryen komawa.

Ta sallami duk mutanen da take mutunci dasu a fadan.


Dama cikin masarautar Joɗa cewa Gobe jumma'a da mangriba zata koma.

Washe gari ranar jumma'a, da misalin karfe sha biyu.

Duk suna zaune a falon harda Jafar, Jalal, Jamil, Imrane, Ya Hashim, duk suna cikin
shigar jumma'a.
Dakon fitowar Sheykh suke jira.

Umaymah da Ummi da Aunty Juwairiyya kuwa, suma suna nan, cikinsu ana ɗan hira.

Hibba kuwa da Shatu suna kitchen dan Hibba tace in Shatu ta iya awaran couscous ta
koya mata.

Suna nan zaune, Hajia Mama da hadimanta


Suka shigo.

Cikin jin daɗi Umaymah tace.


"Yanzu nake tunanin zanzo Side ɗinki Adda na".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Oh ai bazaki zoba, yadda kike tsakiyar yaranki yar uwa kam an manceta".
Murmushi sukayi baki ɗayansu,
Batool da yanzu ta shigo da wasu hadiman suna rirriƙe da manyan bokitayen kande
tsiraran masu cike da markaɗeɗɗen gyaɗa na kunu da miya sai ƙananan su kuma turaren
wutane a ciki da biyu ɗaya dakekken yajin daddawa ɗaya dakekken yajin borkono komai
bibbiyu. Sai galullukan man shanu. Da na zuma sai na Humra, kana sai manyan bako
guda biyu.
cikin murmushin Umaymah tace.
"Iye Addana me na samu hakane?".
Cikin sakin fuska tace.
"Abubuwan daɗi nasan kina son kayayyakin gargajiya".
murmushi tayi tare da cewa.
"Duka wannan ai yamin yawa".
Kallon kayayyakin tayi tare da cewa.
"Keda su Ummi ne, suma za suyi amfani dashi a Ramadan, Musamman ma da ɗan naki anan
zaiyi azumi bana".
Cikin jin daɗi Umaymah ta kwallawa Hibba kira tare da cewa.
"Kizo keda Aunty naki".
To sukace kana suka kashe Gas ɗin da yake dama sun gama aikin.

Suna isowa Hibba taje ta zauna kusa da Hajia Mama da sauri tare da cewa.
"Hajia Mama an barni a nan zamuyi azumi".
Cikin murmushi ta shafa kanta tare da cewa.
"Kai naji daɗi na."
Sai ta kuma kalli Aunty Juwairiyya tare da cewa.
"An kai miki naki kayan Side ɗinki".
Godiya tayi.

Ita kuwa Umaymah hannun tasa ta jawo bako ɗaya ta zuge zib ɗin shi ta fara fiddo
ledodin dake ciki wanda dakekken busasshen kayan miya ne kamarsu.
Kuka, kuɓe, daddawa, citta, kanumfari, ganyen na'ana, zogale, da dai ire-iresu ne a
ɗaɗɗaure a manyan ledodin masu layin baki da fari.
Cikin jin daɗi kayayyakin Umaymah tace.
"Kai nako gode naji daɗin kayan miyar nan, dan mu wurinmu suna wuyar samuwa."
Sai kuma ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta,
Tayi wani irin kici-kici da fuska babu alamun wal-wala.
Cikin nuna jin daɗi tace.
"Ɗiyata ga kyautan Hajia Mama, komai bibbiyu ne ɗaya naki ɗaya nawa ne, kiyi
godiya".
Cikin wani irin kallo mai cike da ma'anoni da sarƙafe-sarƙafe ta gyara zamanta,
tare da komawa ta jingina da kujera, ƙafarta ɗaya ta ɗaura bisa ɗaya tare da fara
karkaɗa ƙafar cikin fuska a haɗe kana a daƙile ta nuna kayan tare da cewa.
"Bama so, Umaymah Bama buƙata".
Cikin tarin mamaki da al'ajabi duk suka juyo gareta suka zuba mata ido.
Ummi da Umaymah kuwa har suna haɗa baki wurin cewa.
"Sabida me? Akanme zakice bakya so?".
Ba tare da ta kallesu ba tace.
"Ba cewa nai bana soba, cewa nayi bamaso, itama Umaymah bata so."
Cikin tsananin mamaki suka bushe suna kallonta,
Jalal ne ya zuba mata ido cikin haɗe fuska.
Hajia Mama kuwa wani irin kallo mai cike da tsoro da mamaki da al'hini da jin
tsanar Shatu cikin ranta, ta rasa me wannan yarinyar take nufi da ita,
ta kasa gano me take gadara dashi.
Cikin tarin takaici da zafin rai tace.
"To kuma baki isa da gidan ba,
Bare ki zana layi a biki, ke in banda rashin sanin darajar manya har zaki gaya min
haka, ko gidanku ba manya ne?."
Cikin isa da ɗaga murya tace.
"Yesss! Gidanmu babu manya irinka, Bama so bazamu amsaba ki tattara tarukucenki
kije ki bawa wasu can ba dai muba".
Cikin tashin hankali Umaymah ta daka mata tsawa tare da cewa.
"Ke Aysha ki nitsu kisan da waye kike mgna".
Cikin ɗaga murya tace.
"Na sani Umaymah na sani nasan da wacece nake mgna kece bakisan wacece itaba".

Cikin mamaki da sauri Sheykh ya ƙarisa fitowa cikin tamfatsen falon shi.
sabida ya gama shirin jummarsa,
jiyo hayani da hargowane yasa ya nufo falon da sauri.
To jiyo muryar Umaymah ne yasashi buɗe ƙofar falon da hamzari ya fito.

Da sassarfa ya nufo falon.


Dai-dai lokacin daya isone,
Aysha ta miƙe tsaye cikin faɗa da tsawa ta nunawa Hajia Mama da hadimanta da Batool
hanya tare da cewa.
"Maza ku tattara waɗannan banzayen tarkacen naku ku tafi dashi, ku ɓace min da
gani. Ku fita daga nan! Ku fitarmin gidana".
Ta ƙarishe mgnar da ƙarfi.
Wani irin miƙewa tsaye Umaymah tayi tare da yin sauri tasa hannunta ta....!
By
*GARKUWAR FULANI*Ta kamo hannun Jalal da ya miƙe tsaye da nufin
yarfa mata mari.

Cikin wani irin masifeffen tsana, Hajia Mama takalli Shatu.


Kana da sauri ta juya ta nufi hanyar fita.
Sheykh da tunda ya fito yake tsaye tamkar an dashi ne,
yayi saurin bin bayanta tare da cewa.
"Hajia Mama! Mama!! Mama dan Allah kiyi haƙuri, kizo karki fita Please Mama karki
fita, babu wata halitta da zata miki iyaka da sashina, in kin tafi kenan kinbi
umarninta."
Cikin tashin hankali yake waɗannan kalaman yana mai binta a baya.

Jamil kuwa miƙewa tsaye yayi ya zubawa Shatu idanu tamkar zasu faɗo ƙasa.

Aunty Juwairiyya kuwa, wani irin kallo mai sarƙafe da ma'anoni takeyiwa Shatu.

Ya Jafar kuwa wani irin kallo mai surke da murmushin jin daɗi yakeyiwa Aysha.

Ummi kuwa tuni jikinta rawa yakeyi da abinda ya faru.

Imran, Ya Hashim, kuwa ido suka zubawa sarautar Allah.


Hibba kuwa kuka takeyi tare da riƙo hannun Shatu tana ja tare da cewa.
"Aunty Aysha ki bari, Mamace fa! Kizo mu tafi ɗaki".
Tanayi tana jan hannun Shatu da ƙarfin tsiya, dole yasa Shatu ta bita a baya.

Umaymah kuwa wani irin tashin hankali da tafasan zuciyane ya dirar mata lokaci
ɗaya.
Da wani irin kallo tabi bayan Aysha dashi.

Duk wanda ya ganta yasan tana cikin tashin hankali.


Gaba ɗaya jikinta rawa yakeyi.
Sun daɗe a haka, da kyar dai
Cikin wani irin tafasan zuciya ta saki hannun Jalal.
Tare da komawa ta zauna.
Da yatsa ta nuna musu hanyar fita daga falon. Murya a hargitse tace.
"Kul kada ka sake tunanin gigin ɗaga kayi nufin taɓa lfyar Aysha, bana so kul.
Maza Ku tafi masallaci".
Sai lokacin suka jiyo sautin muryar Jabeer yana Hudba.
Wanda daga jin muryarsa kasan yana cikin baƙin ciki.

Wani irin numfarfashi Jalal ya sabke tare da yin koffa kana ya juya ya nufi hanyar
fita shi matsalarsa meyasa Umaymah na mgn Aysha na mgn Umaymah na hanata abu
tanayi.
Haka su Jamil da su Imran da ya Hashim da Ya Jafar suka fita.

Ita kuwa Aunty Juwairiyya wani irin tashi tayi ta fita ta nufi Side ɗin ta.

Ya zama Ummi da Umaymah ne kaɗai suka rage a falon.

Shiru sukayi tamkar ruwa ya cin yesu.


"Uhuhhmmmm". Umaymah ta fesar da wani zazzafan numfashi mai ɗumi.
Hakama Ummi tagwayen numfarfashi masu nauyi ta sauƙe.
Kallon juna sukayi, cikin shiga al'hini wannan al'amari cikin tsoro da karaya
Umaymah tace.
"Toh wai meye hakan? Meke faruwa ne? Me hakan yake nufi? Kaina ya kulle. Wani zagon
kasan kuma aka shirya tsakanin Shatu da Hajia Mama ko dai dama da zagon ƙasan ne?.
Wake saƙa gadar zare, muna na bi ta kai ya rubta da mu".
Wani numfashin Ummi ta fesar tare da cewa.
"Tabbas akwai babban al'amarin dake faruwa wanda bamu saniba Ni tsorona ɗaya kada a
juya ƙoƙwalwar yar mutane."

Shiru sukayi cikin ta'ajjudin al'amarin. A hankali suka miƙe a tare suka nufi
ɗakinsu jin har an idar da sallan a masallacin.
Al'wala sukayi kana sukayi salla daga bisani suka, fara tattauna wani abu na sirrin
masarautar Joɗa.

A cikin ɗakin Shatu kuwa, tunda suka shiga ta kwanta bisa gado.
Bacci tayi bacci, hakama Hibba.
Sai ƙarfe uku dai-dai Shatu ta tashi.
Cikin kasalan baccin da bai gama isarta ba, ta miƙe ta shiga bathroom.
Wonka tayi tare da al'wala.
Bayan ta fitone, ta tada Hibba, ita kuma ta kabbarta sallah.

Kafin ta idarma Hibba ta fito, gefenta tazo itama ta kabbarta sallan.

Basu tashi bisa sallayan ba, sukaji kiran aallan la'asar.


Haka yasa sukayi sallan. Suna idarwa Hibba ta miƙe ta nufi ɗakin Umaymah.
Ita kuwa Shatu ninke sallayar tayi kana ta dawo gaban dreesing mirror.
Mai ta shafa tare da ɗan murza fauda a fuskarta, kama ta shafa man baki.

A cikin sanyi taje gaban drower'nta,


hannu tasa ta buɗe drower'r, wata tattausar doguwar riga mai masifar kyau ta zaro.
Kalar rigar Black blue mai sheƙi, saman rigar a ɗan tsuke daga ƙasan ƙugunta kuma a
buɗe,
yanada wasu duwasu kamar na Daimond daga sama har ƙasan gaban rigar.
Hannunta kuma masu faɗi.
Tayi kyau sosai cikin rigar, dogon gashinta ta haɗa ta tubke wuri ɗaya ta kitse
jelar kana ta nannaɗe jelar a ƙeyarta,
sannan tayi rolling kanta da mayafin wanda dai dai inda zai zauna a goshin akwai
duwatsun.

Turare ta fesa, kana cikin sanyi da kasala ta nufi, falo.

A falon ta samu, Hibba a kwance tayi shiru.


Ganin bata gan fitowarta banema,
Yasa ta nufi inda take gefenta ta zauna tare da cewa.
"Hibba ɗauko mana awaran".
Cikin sanyi Hibba tace.
"To". Kana ta miƙe ta nufi falon, jin shiru ba kowa a cikine, yasa ta nufi kitchen
a hankali-hankali.
Foodflaks ɗin da suka sa awaran da suka soya ta ɗauko.

Tana dawowa ta zauna kusa da Shatu tare da cewa.


"Gashi". Kai ta gyaɗa mata tare da nuna mata kitchen ɗin ta, tace.
"Ɗauko mana plate da roban yajin da Gimbiya Aminatu ta aiko mana.
Kizo mana da ruwa".
Ba tare da tace komaiba ta juya ta tafi.

Bayan ta dawone suka zauna suka fara cin wanda suka zuba.

A can falon Hajia Mama kuwa,


duk mgnar da Umaymah da Ummi keyi, shiru tayi ta zuba musu ido.
cikin sanyi Umaymah tace.
"Addana kiyi haƙuri, kin san yaran sai a hankali, dan Allah kada kisa wani abun a
ranki wata ran ko ance tayi miki bazatayi ba".
Murmushi tayi mai cike da ma'anoni kana tace.
"Uhummm ba komai Khadijah jekici gaba da shirin tafiyarki, karki damu kinji".
Ido suka zuba mata domin duk basu gamsu da mgnarta ba, to amman ya zasuyi tunda
tace ba komai.

Haka suka tashi suka dawo falon.


Yau su Jalal ma basu zoba.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, tunda aka idar da sallan azahar ya dawo, ya wuce su Umaymah
a falon ba tare da yace musu ƙalaba.
koda ya shiga ɗakin ya samu yayi bacci tsakanin azahar da la'asar kamar yadda ya
saba, hakan bai samuba.
Sabida abubuwan dake ranshi.
Bathroom ya shiga ya sakarwa kanshi ruwan sanyi, tare da fara yage towel ɗin dake
hannunshi.
haka yake tsaye a ƙasan ruwan har saida yaji an kira sallan la'asar. Nanne ya fita
ya tafi masallacin.
Bayan an idar da sallan ne ya dawo gida.
Ganin babu kowa a falon ne yasashi zama, bisa kujerarsa.
Ƙafarshi ɗaya ya ɗaura kan ɗaya.

A haka su Umaymah suka sameshi.


Gefenshi Umaymah ta zauna bisa kujerar dake kusa dashi.
Ummi kuwa gabanshi ta zauna bisa carpet.

A hankali ya buɗe kwayar idanunshi.


Cikin tarin ɓacin rai ya kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi ina wannan fitsarerren abun da bai san darajar manya ba!?."
Cikin sanyi Ummi tace.
"Allah ya huci zuciyarka tuba takeyi, in sha Allah bazata sakeba, Hajia Mama da
kanta ta yafe mata".
Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Ummi ko dai kece kika bata dama da matsayin yiwa Mama hakane?".
Cikin sauri tace.
"Wanne ni wlh bani bace".
Kanshi ya ɗan juyo ya kalli Umaymah da itama shi take kallo cikin ɓacin rai yace.
"Umaymah har akwai wani abun da zai hana mama shigowa sashina? Har yaushe waccar
babyn robar ta samu dama da ikon bada izinin shiga da fita cikin sashina da abinda
ya shafi rayuwata?
Me take nufi dani da iyayen nawa."
Kauda ido Umaymah tayi daga kallonshi kana a hankali tace.
"Ba isa bane! Akasi aka samu! Nifa inaga har yau Shatu'n bata gama sanin mutanen
masarautar Joɗa da kuma dangantakar makusan tankaba, ayi mata haƙuri a mata uzuri a
dai wannan karon".
Juyowa yayi ya kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi a kira min waccar abar".
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa to.

A falon ta samesu, cikin fuskar da babu yabo babu fallasa ta kalli Shatu dake gefen
Hibba da alamun ta cire hannunta a cin awarar kanta ta ɗan kauda tare da cewa.
"Kizo Sheykh yana kiranki".
Kai ta gyaɗa tare da cewa "Toh". miƙewa tayi taje Dinning area ta wonke hannunta,
kana tazo tabi bayan Ummi.

A gabanshi Ummi ta zauna ganin haka itama ta zauna a gabanshi.


shiru tayi tana kallon yatsun fararen sawunshi. Shi kuwa kanshi na gefe ba tare da
ya juyo ya kalleta ba yace.
"Ke ki shiga hankalin ki, kisan abinda kikeyi da wanda zakiyi! Ke har kin kai
matakin da isar da zaki ƙaddamar min da iko da isa a cikin gidana? Ko dai ce miki
akayi gidan nakine?".
Kai ta gyaɗa mishi alamun eh ance mata gidan natane!.
Wani irin tsuke fuskarsa yayi tare da ci gaba da mgna dan shi bai ga sanda ta gyaɗa
kanba hakama Umaymah, sai Ummi ce kaɗai ta gani, su kuwa sai murmushi sukayi.
Cikin kausasa murya yace.
"In baki san darajar manya da iyayeba, to ki zama kurma bebiya makauniya a cikin
giddannan kafin Ubangiji ya zantar da Hukuncin da ikon zamanki da barinshi dan
ikone na Allah bana waniba.
Har kin isama Mama tazo ki koreta dan idonki basu da ɗigon kunya.
Ko karen gidannan baki da ikon hanashi abu da sakashi bare Mama.
ke ta bawa abun ne da zakice bakya so.
Kece mai bakin mgn uwar fitsararru ko?".
Sam abinda bai saniba zuwa yanzu hankalinta, tunaninta nitsuwarta, jinta, da
ganinta duk suna kan farar ƙamarshi ta dama, da zanen maciji ke liƙe kamar macijin
na tafiya.
Wani irin ba hagun numfashin ta sauƙe a hankali,
tare da rufe manyan idanunta da azaban ƙarfi.
Sabida gani takeyi Tamkar macicijin ne ma da kanshi ke manne a jikinshi yana kuma
motsa ɗan bindinshi dake saman babbar yatsarshi.
A hankali ta buɗe idanun kana tabi kan rumfar ƙafar da ido, inda take ganin zanen
maciyar yabi.
Kasan cewar a zaune yake ya kuma ɗan tattare al'kyabbar jikinshi.
Shi yasa tana iya ganin har ƙarshen rumfar tafin ƙafar nashi.
Inda iya nan jallabiyar jikinshi ta rufe.
da sauri ta ƙara rusunar da kanta wai ko zata ga ci gaban tafiyar macijiyar.

Umaymah ce ta ɗan kalleta cikin wata iriyar murya tace.


"Ki tashi muje ki bawa Hajia Mama haƙuri, ku nemi yafiyarta ki kuma kiyaye gaba,
kinji".
Cikin sanyi tace.
"Toh".
Still Bata miƙeba, cikin ɗan ɗaga murya yace.
"Tashi muje yanzu ki bata haƙuri, in ta haƙura kinyi babban Sa'a".
cikin sanyin jiki ta miƙe tsaye.
Shima miƙewa yayi, Ummi kuwa da sauri ta nufi ɗakin Shatu.
Jim kaɗan ta fito da wata kekyawar al'kyabbar matan masarauta ta zuramata.
Bayan ta gama gyrashi ne, tasaka hular.
Shi yayi gaba ita kuwa.

Tabi bayanshi Umaymah da Ummi suka biyo bayanshi.

Suna isa bakin mashigar farfajiyar Side ɗin Hajia Mama,


ta tsaya gis tare da yin ƙasa da kanta.
Ummi ce tace.
"Muje mana".
Shiru batayi mgna ba, jin hakane yasashi juyowa, karon forko kenan da ya zubawa
tsawonta ido.
cikin ɓacin rai yace.
"Muje ki lashe aman da kikayi da kanki".
Cikin sanyin sauti tace.
"Ni bazan shigaba".
Da mamaki Umaymah tace.
"Innalillahi wai ke Ayshs wani irin taurin kaine dake? Menene manufarki?".
Murya can ƙasa yana rawa alum zatayi kuka ta kalli Umaymah tace.
"Kiyi haƙuri Umaymah ki gafarceni, amman ni bazanje ba, in kuma zanje to ku ku
koma, zanje ni ɗaya zan bata haƙuri".
Cike da al'ajabi Umaymah tace.
"To sabida me bazaki je da muba".
Cikin faɗa Sheykh yace.
"Sabida muna furci mana, ba zuwa zatayi ba, shiyasa zatace sai dai in ita ɗaya
zataje, maza wuce muje a gabana zaki bata haƙuri".
Cikin sanyi Umaymah tace.
"Jazlaan barta mu tsaya mu jirata anan in dai zataje ita ɗayan".
Kanshi ya dafe tare da cewa.
"To wai Umaymah mu bayaninta ne da zamu tsaya muna jiranta".
Ummi ce ta mishi alamun yayi haƙuri ya yarda.
Shiru yayi tare da komawa gefen jerin bishi yoyin namiji kwanɗa ya zauna bisa
kujerun silver dake zagaye da wurin wanda ko wani side akwaisu.

Itama Umaymah da Ummi zuwa sukayi suka zauna.


Ita kuwa Shatu a hankali ta fara taku ta nufi cikin farfajiyar, suna hangota har ta
isa bakin ƙofar.
turawa tayi ta shiga, kana ta maida ƙofar ta rufe.

Bayan kamar 37 minutes ta fito.


Cikin wani irin tafiya mai baiyana tsantsar jin daɗi, fuska cike da fara'a ta
nufosu.
A hankali ta isa gabanshi ciki ɗan ɗaga murya tace.
"Na bata haƙuri ta yafe min, ta samin al'barka. Kaima kayi haƙuri ka yafe min".
Da mamaki suka kalleta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer wari irin kallon tuhuma yayi mata, kana ya miƙe tsaye tare
da cewa.
"In ma ƙarya kikayi, ni ba'amin ƙarya".
Sai ya kuma kalli Umaymah tare da cewa.
"Umaymah kuje ki ƙarisa shirinki bari inje wurin Hajia Mama".
To tace kana taja hannun Shatu suka tafi. Shi kuwa da Ummi suka nufi cikin Side
ɗin Mama.

Bayan sallan isha'i, cike suke a falon. Gaba dayansu, Umaymah zaune a tsakiyarsu da
jakarta, Sheykh Jabeer na yi mata addu'o'in isa lfy suna amsawa da Amin Amin.
Bayan sun shafa addu'o'in ne ta miƙe tsaye, tare da kallon su baki ɗaya, murya na
rawa tace.
"Jazlaan zan tafi, zan bar hankali na, a nan ko na koma banda nitsuwa, kullum ina
cikin taraddadin abubuwanda yake faruwa, Jazlaan na sani kaine GARKUWAR yayanka da
ƙanneka. Ga wani sabon nauyi ya ƙarun maka.
Aysha baƙuwace bata san komaiba kam al'amuran Masarautar Joɗa, dan Allah in tayi
abinda ba dai-dai ba kuyi mata uzuri.
Ita komai a sabon abu zata ganshi abinda bata taɓa ganiba.
Mun rabata da iyayenta yayunta ƙannenta mun kawota tsakiyarmu, mu kasance mata
adalan masu masauƙi.
Na sani Jazlaan ka fini sanin haka da kuma haƙƙoƙinta da suka rataya gareka."
Sai ta kuma kalli sauran yaran yar uwarta ɗin tace.
"Jalal, Jamil, Aysha matsayin yar uwarku take, yayarku ce, matar yayanku. Bana son
raini especially kai Jalal, ban gamsu da irin mu'amalat ɗin ka da itaba.
Babu wanda yake nuna min yadda nakeso a kanta sai Jafar, a duk sanda ya ganta zaiyi
mata murmushi kamar yadda yake min, in yaga bata nan zaiyi ta dube-duben da nasan
da yanada baki zai tambayeni lfyarta.
Zan bar Hibba saboda itane, bana son taji kanta a matsayin bare."
Shiru sukayi gaba ɗayansu sabida yadda take kuka da yin mgna tamkar mai bar musu
wasiya, ko wacce wani tsohon damuwa ya taso mata.
Sharce hawayenta tayi tare da cewa.
"Ummin Jabeer zan tafi zan barki da sauran aiki, dan Allah ki kula da Shatu da
mu'amalarta da Hajia Mama, ki nuna mata uwar miji ba abun rainawa bace".
Sai kuma ta miƙowa Aysha da taketa kuka hannun ta jawota tsaye ruggume ta tayi
cikin zubda hawaye tace.
"I dan akaga damuna ana zaton yabanya zatayi kyau, kallon damuna nakeyi miki a
cikin ahlin yar uwata.
Ina jin zaki zamo mana haske mai yaye duhun daya maye ganinmu, tun kafin yau ni na
sanki a mafarkina Allah ke nuna min ke a matsayin matar Jazlaan ɗin na, kuma Allah
yana nunamin abubuwa da dama a kanki a cikin mafarkaina, wasu kuma sunma tabbata na
gansu.
dan Allah ki riƙe min Jazlaan amana, ki lura da ƙannenshi yadda zaki lura da naki
ƙannen ki kula da Jafar kada ki tsoraceshi bazai cutar da keba ki ɗaukeshi a
Matsayin wa".
Cikin zubda hawaye Shatu tace.
"In Sha Allah Umaymah zan kiyaye zan kuma zamo yadda kike zatonta, koda sanadin
haka zan rasa jigo biyu na rayuwata rai da lafiya ta".
Kalaman Umaymah da Aysha kuramen baƙine da su kansu ɗaya bata fahimci abinda ɗaya
take nufiba, hakama ɗayar, bare su Jalal dake tsaye.
Jawo Hibba tayi ta haɗa su ta ruggume,
kana ta jawo Juwairiyya tace.
"Ku duk yara nane ku zauna lfy".
Gaba ɗaya da to suka amsa.
Cikin sauri Umaymah ta sakesu kana ta miƙa wa Ummi hannu sukayi musababa, tare da
bar mata sallahun yaran.

Daga nan suka fita, gaba ɗayansu.


Sai Shatu da Hibba da suke kuka, ganin hakane Ummi ta dawo ta zauna dasu.

Jabeer da Jafar da Umaymah kuwa Side ɗin Mama sukaje, tayi sallama da ita, suka
rabu suna hawaye.
Daga nan Side ɗin Lamiɗo da Gimbiyar shi sukaje.
Nan sukayi sallama dasu kana suka fito, inda suka samu Jamil da Jalal sun kawo musu
motoci. Daga nan suka shiga suka tafi Airport tare da rakiyar motocin fadawa guda
uku ya zama motoci biyar ne suka tafi kaita Airport.

A gida kuwa, da kyar Ummi ta samu ta lallashi Shatu da Hibba da cewa in basuyi
shiruba, zata, sa akai Hibba Airport ta tafi da Umaymah.
jin hakane yasa Hibba tayi shiru. Ita kuwa Shatu dama ba kuka mai sauti takeyi ba,
zubda hawaye takeyi.

Ƙarfe tara dai-dai jirginsu Umaymah ya tashi zuwa jihar Tsinako.

A gida kuwa tuni Shatu da Hibba sun shiga kuma har sunyi bacci sabida kukan da
sukayi.

Ita kuwa Ummi tana falo, saida taga dawowarsu sannan taje ta shiga ɗakinta dan
yanzu ta dawo da zama a nan kenan ɗakin da Umaymah ke sauƙa in tazo.

Washe gari ranar asabar kuwa,


haka suka wuni gidan shiru ba daɗi gaba e kewar Umaymah ta hanasu jin daɗin gidan.

Ranar ne kuma duban forko na watan Ramadan.

Tunda magriba tayi, al'ummar musulmai keta cekinta labarin ganin wata.
Wannan ya tambayi wancan wancan ya tambayi waccan.
Jira kawai akeyi aji lbri ko gani.
Yayinda duk irin wannan rana duk inda yanki musulmai suke a faɗin duniya suna
jimirin da tsumayin lbri.
A wasu wuraren har matasa maza da dattawan kanyi dandazon da fuskanta yamma dan
ganin watan

Har dai akayi sallan magriba babu ƙaƙƙarfan lbrin ganin wata.
Bayan anyi sallan isha'i ne, Sarki Nuruddeen Lamiɗo kenan ya tara hakima shi a fada
suna jiran ko akwai ta inda labari zai riskesu.
Kasan cewar ana yanayin damuna ne yasa ba ko ina keda yaƙinin ganin watarba.

Sheykh Jabeer kuwa, wanda ranar bai samu yayi salla a masallacin Masarautar Joɗa
ba.
Sabida wata ƴar tafiyar da yayi, sai bayan Isha'i ya dawo.
Kai tsaye Side ɗinsa ya wuce.
Yana shiga falon wayarshi dake cikin al'jihunsa ta fara suwa a hankali.
Gefen Ummi ya iso tare dayi mata sallama.
cikin kula tace.
"Sai yanzu?".
Kai ya gyaɗa mata yana mai amsa wayar.
Sannu da hanya tace mishi.
Cikin sauƙe numfashin alamun gajiya yace.
"Yauwa Ummi sannu da aiki".
Sai kuma ya kara wayar akunnen shi cikin nitsuwa yace.
"Wa alaikassalam".
Ɗan jim yayi kana yace.
"Alhamdulillah".
ya ƙarshe mgnar yana shiga cikin falonshi.

Shatu kuwa dake gefen Ummi shiru tayi tare da binshi da ido.

A can falon shi kuwa zama yayi bisa kujera tare da fara zare al'kyabbar daka
hannunshi, wayar na kunnenshi yake cewa.
"Eh Jadda Alhamdulillah rahotanni sun nuna cikin Ɓadamaya al'umma da yawa sunga
watan Ramadan.
Kuma nima naga watan Ramadan da idona".
Cikin jin daɗi Jadda yace.
"Alhamdulillah, ko yanzu mun samu gamsassun hujjoji daga bakin salihan bayi,
Dan jihar Tsinako sarki Abudulfata da kanshi ma yaga watar ya sanarmin.
Hakama jihar Noki, Jaltarba, Magom, Shibb, da dai sauran jihohi mu na arewaci anga
wata sosai tako ina.
Kana yanzu kuma munyi mgna da Sheykh Abdulkareem shima yace anga wata.
Mu nan jihar Leddi julɓe kusan kowa yaga wata."
gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"To Alhamdulillah. Allah ya nuna mana ƙarshen sa lfy, yasa muribantu da watar
al'farma Annabi da Alqur'ani".
Amin Amin Sarki musulmai Jalaluddin, yace.
Kana ya sallameshi.

Daga nan aka bada sanarwan anga wata, inda shi Sarki Jalaluddin ya kira manyan
masarautun gargaji yana shaida musu.
Kana manema labarai duk sukayi dandazon zuwa, nan aka sanar tako ina musamman
kafafen yaɗa labarai na yanar gizo.

Nan take ko ina ya ɗauka.

Suna zaune a falon suna cikin hira.


Sukaji wani irin ƙara mai firgitarwa da bada tsoro.
darararam-dam sautin ƙarar bindigar toka mai ƙarfin amo.
Wani irin tsalle Shatu tayi tare da motsowa jikin Ummi, tare da toshe kunnuwanta,
sabida sake jin ƙaran.
Gaba ɗaya jikinta kerma da kerketa yakeyi,
Cikin tsoro take cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani'imanwakil!".
Da sauri Ummi ta riƙon hannunta datasa ta toshe kunnuwanta cikin ɗaga sauti take
cewa.
"Shatu ba komaifa, kada ki razana bindigar sanarda ganin watane! Shaidar gobe zamu
tashi da azumi".
Cikin tsinkewar zuciya tace zamo daga kan kujerar ta zauna a ƙasa kusa da sawun
Ummi, wani irin duka ƙirjinta keyi didib didib, didib.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Aunty Aysha tsoro haka".
Cikin yamutsa fuska tace.
"Ya kamata ku gayawa duk wani baƙo wannan bahugawar al'adar taku in ba hakaba wata
rana tsoro zai kashe irina".
Sheykh da tun ihunta na forko yana bakin corridor yana kallon yadda take karkarwa,
wani irin murmushin muguntane ya tsubce mishi.
Sai kuma ya tsuke fuskarsa kamar bashi yayi gajeren murmushi ba, cikin faɗa yace.
"Nifa bana son sakarci sam bafa na son anamin ihu a ka da hargowa a gida".
Cikin tura baki ta bishi da ido.
Shi kuwa fita yayi yana murmushi a cikin zuciyarshi tare da magar zuci.
"Ga rashin ta ido ga tsoro, ga tsiwa da fitsara ga makirin karaya.
Ai da anyi ta sakin sautin bindigar har sai tayi fitsari a zani".
Da haka ya wuce ya nufi fada,
nan suka fara tattauna yadda lamuran zasu tafi.

Ummi kuwa murmushi tayi ganin irin kallon harara da Shatu ta raka Sheykh dashi.
Cikin murmushi tace.
"Taso ki zauna muyi mgna".
A hankali ta miƙa ta hau bisa kujerar da Ummi take ta zauna, Hibba kuwa, tuni ta
nufi Side ɗin Aunty Juwairiyya.

Gyara zama Ummi tayi tana fuskantar ta da kyau,


Cikin nitsuwa tace.
"To Alhamdulillah kinga anga wata gobe zamu tashi da azumi in Allah ya kaimu, akwai
ƙarin aiyuka a Side ɗin nan wanda ko da can baya ko Sheykh bayanan yana ajiye komai
na buƙatar rayuwa akanyi girki a nan kamar akwai mace, sabida anan su Jalal, Jamil,
Hashim Sulaiman Imran Affan in yana nan suke shan ruwa."
To yanzu bana Sheykh ba inda zaije sabida a jerin jadawalin malaman tabsir da ake
turawa jihohi bana ba'a turashi ko inaba tunda ya girma ya fara tabsir sau ɗaya
yayi azumi a nan shekarar da ciwon Jafar ya tsananta, to anane naga zahirin yadda
yake gudanar da al'amuran rayuwarshi cikin Ramadan.
To bana ma. Anan cikin Ɓadamaya zaiyi tabsir ɗin shi.
To aiyukan mu sunada yawa.
Dole kisan yadda tsarin komai ke tafiya."
Cikin sauƙe numfashin ta gyara zama ta fuskanci Ummi da kyau kana a hankali tace.
"To".
Itama gyara zama tayi da kyau kana tace.
"Azumi goma sha biyar zaiyi a nan, ƙarishen 15 ɗin a ƙasa mai tsarki zaiyi su.
Ma'ana zai tafi Umrah.
Sannan yanada masallatai uku da yake tabsir a kullum.
Da safe misalin karfe sha ɗaya na safe zai tafi masallacin jumma'a na cikin kasuwa,
a can zaiyi tabsir sai ƙarfe shabiyu saura mintuna goma zai taso.
Daga nan kafin ya iso masarautar Joɗa tafiyar mintuna goma ne.
sha biyu dai-dai, zai zauna tabsir masallacin Masarautar Joɗa.
Sai ƙarfe ɗaya na rana zai tashi.
Daga nan bazai dawo gidaba, sai anyi sallan azahar.

To ana idar da salla zai shigo, gida al'adar rayuwarsace tun yana yaro.
Zaiyi baccin awa ɗaya tsakanin azahar da la'asar.
Ƙarfe uku dai-dai na yamma zai tashi zaiyi wonka, ya canza shiga, kafin ya gama an
kira salla.
Yana fitowa zai wuce masallacin Masarautar Joɗa, inda yake limanci ana idar da
salla zai tafi masallacin jumma'ar dake jami'ar Joɗa. Inda zaiyi tabsir daga ƙarfe
huɗu zuwa biyar na yamma zai taso.

Akan hanyar shi ta dawowa yana tsayuwa wurin mashigar laleko zai sayo kayan buɗa
baki ƴaƴan itatuwa.
Yana dawowa zai ajiyesu.
Ya wuce Side ɗinsa, wonka zaiyi kana yasa sauƙaƙƙun kaya, ya dawo falonshi ko ya
wuce cikin Garden acan zaiyi ta karatun al'ƙur'ani ko kuma wani lokacin ya ɗan
konta ya huta.

Kafin lokacin shan ruwa, Ni kuma da hadimar da Gimbiya Aminatu ke bani duk Ramadan
ta tayani aiki.
Tuni mun gama aikin buɗa baki. An shirya komai a dinning table, nasu Jalal kenan.
Suma kuma gab da magriba zasu zo.
Shi ma zai fito yakan zauna tsakiyar Jalal da Jamil ko kuma tsakiyar Jalal da
Jafar.

Baya cin abu mai nauyi iya karshi dabino da inabi da tuppa, sai ruwan zam-zam wanda
dashi yakeyin buɗa baki.
Daga nan zai wuce masallacin Masarautar Joɗa wani lokacin zai fita dasu wani
lokacin zai rigasu fita.

Ana shirya mishi abincinsa na musamman a ajiye mishi a dinning table ɗin dake can
falonshi a Foodflaks ɗin shi na musamman, wani lokacin Gimbiya Aminatu ke aiko
mishi.

In ya fita bazai dawoba sai anyi sallan isha'i Dana asham.


Amman su Jalal su zasu dawo suci abinci kafin isha'i sai su koma masallacin.

Idan ya tashi daga Masallacin kai tsaye zai wuce.


Gidan radiyo ABC Ɓadamaya, inda yake gabatar da shirin.
"Fatawa. Za'a ayi mishi tambaya kan Ramadan dama sauran abinda ya shafi addini yana
amsawa, wasu kan tura tambayoyin wasu kuma kira sukeyi a da number da ga suke
badawa, suyi tambaya ya bada amsa.
Ƙarfe takwas da rabi ake fara shirin tara dai-dai ake gamawa.
Tara da mintuna ashirin yake isowa gida".
Ɗan tsagaitawa tayi ta kalli Shatu dake cewa.
"Tab agogo sarkin aiki to shi baya gajiya ne, ga azumi ga zirga-zirga ga kuma duk
inda yaje dole ba shiru zaiba mgna zaiyi ai ƙishi zai mishi illa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"To ai in yaje gidan radiyo tarba ta musamman akeyi mishi, sai dai shi ba ko ina
yake cin abinci ba tunma yana yaro.
Ko a gida nan ba abincin kowa yake ciba.
To shiyasa tara da rabin nan zai dawo a gajiye cikin yunwa,
to nan zaici abinci sosai.
Kana yayi wonka zuwa sha ɗaya dai yayi bacci.

To ƙarfe biyu kuma zai tashi, wani lokacin ma biyu bayayi zai tashi yayi ta
nafilfilinshi da karatun Alqur'ani.

Daga nan kuma baya komawa bacci.


Har ayi sahur ayi sallan asuba.
In ya dawo yayi Azkar, to nanne yake samun yayi bacci mai tsawo dan tun bakwai da
rabi ko takwas na safen zaiyi bacci sai goma zai tashi ya fara shirin tafiya
masallacin jumma'a na kasuwa."
Kallonta ta ɗan yi tare da cewa.
"Kin gane lokutan da yake aiki Dana hutuwa dana bacci ko dana cin abinci ko?".
Cikin murmushi tace na gane.
"Da safe zai sha bacci son ranshi, daga takwas zuwa goma kafin ya tashi ya shirya.
Yaje masalacin jumma'a na kasuwa sha ɗaya tayi yayi tabsir ɗin awa ɗaya, daga nan
ya dawo masallacin Masarautar Joɗa,
shabiyu ya fara tabsir sai ƙarfe ɗaya ya gama, ayi salla ya dawo.
Ya sake shan baccin awa ɗaya.
Kafin kuma ayi la'asar ya tafi masallacin Joɗa state University. Yaje yayi tabsir
in ya dawo, kuma ya lokacin hutawane har magriba.
Daga nan kuma ayi buɗa baki a wuce masallacin daga can a wuce ABC.
Sai tara a dawo.
To yaseen wataran yunwa zata kadashi a hanya, ƙattin rigunan nan da yake sawa sune
zasu jashi su kaishi ƙasa.
To ma wai Ummi to yaushe yake zuwa aiki kuma?".
Murmushi tayi tare da cewa.
"To in baya garin an turashi wani state ɗin yana zuwa aikin ne?".
Kai ta girgiza alamun a a.
Cikin murmushin Ummi tace.
"Shiyasa ko yana nan in dai a Ramadan ne baida lokacin zuwa Valli Hospital, bare
Genaral Hospital ko kuma Asibitin jami'ar Ɓadamaya.
Shine dalilinshi na ƙin yin aiki a asibitin gwamnati sai ƙarshen sati-sati yake
zuwa sau ɗaya, duk wanda zai duba kyautane aiki".
Naɗa hannunta tayi tare da cewa.
"Batun yunwa ta kadashi kuma, yanzu aikin kine, kula da abinda zaici".
Taɓe baki tayi tare da cewa.
"To shi wannan da tsarabe-tsaraben falsafa nasan irin abinda zai cine ma.
Mutun fuska a haɗe kullum kamar mai damuwar rashin jigo".
Miƙewa Ummi tayi tare da cewa.
"To kika sani ko hakanne.
Kuma ai gani duk abinda kike son sani a kanshi tambayeni.
Abincin da yafiso kuma yafi son ganyayyaki, fruits and vegetables sai kuma kayan
ruwa, kana yana son nama da kifi in an mishi irin sarrafawar da yakeso.
Sannan yana son abincin gargajiya wasu lokutan musamman a wurin yin sahur.

Kai ta jinjina tare da cewa.


"Uhumm lallai kam, wannan ai yafi Lamiɗo ma iya ƙasaita".
Dariya tayi tare da cewa.
Zo muje store kiga kayayyakin da yasa aka kawo ɗazu."

To tace tare da miƙewa tabi bayanta.


Suna shiga kitchen ɗin suka ɗan haura suka taka steps ɗin da zai sadasu da ƙofar
store wanda wani ƙaton freezer ke konce a wurin sai ma dai daicin Fridge.

Hannu Ummi tasa ta buɗe freezer'n.


Motsowa tayi tare da zaro ido ganin yadda aka cika freezer'n maƙil dasu Kabej Karas
kokumba green beans, masu kyau sabbi.
Ɗaya sashin kuma nama ne jibge sai kifi a gefe,

Sai ɗaya Fridge ɗin kuma cike yake da ababen sha na ya'yan itatuwa dana kwalba.

Rufewa tayi kana ta buɗe mata drower'n kitchen cabinets ɗin.


Kiret-kiret ɗin kwaine kusa goma suke jere a wurin ɗaya gefen kuma katon ɗin
manyan gongonayen madara da millo ne.
Sai katon ɗin sugar irin mai ƴaƴan nan. Sai katon ɗin Lipton. Da ganyen na'ana. Sai
can gefe kuma su maggine da sauran kayan ɗanɗano.
dasu kanan fari citta da dai sauransu.
Cikin yin hamma tace.
"Ummi duk yaushe aka kawosu?".
Juyawa tayi suka nufi cikin cikin store tace.
"Ɗazu da yamma kina bacci ya dawo, suda Jalal da Jamil".
Kai ta gyaɗa tare da bin bayan Ummi. store ɗin cike yake da kayan masarufi na
buƙatar rayuwa.
Danginsu shinkafa, gero, waken suya, wake ƙosai dasu alale, sugar katon-katon na
taliyar manya data yara, da dai sauransu.

Sai kuma doya da dankali dake jibge a gefe, kana sai al'basa da sauransu.

Fitowa sukayi kana suka dawo kitchen.


tukunya Ummi ta ɗaura tare da ɗebo nama tazo ta wonke sabida an yanka wasu dai-dai
misalin na miya, wasu kuma anyisu dogo-dogon yanka.
a tukunyar ta zuba shi, kana ta ɗauko al'basa mai girma ta yayyanka a ciki.
Sannan tasa tafarnuwa kaɗan kana tasa garin citta da kanamfari.
Tare da maggi da kori da sauran kayan ɗan-ɗano.

Kana ta kunna Gas ɗin ta ɗaura tukunyar,


ɗanyen kuɓewa ta ɗebo ta miƙawa Shatu tare da cewa.
"Wonke ki yanka min shi".
To tace tare da amsa ta wonke kana ta fara yankawa, ita kuma Ummi al'basa da
tattasai da tatuhu kaɗan ta ɗiba ta wonkesu kana ta markaɗesu dai-dai yadda takeso.

Zuwa lokacin kuma gaba ɗaya kitchen ɗin dama Side ɗin gaba ɗaya ya cika da ƙamshin
tafashen naman.

Juyeshi tayi a wani kwano.


Kana tasa mai kaɗan tasa manja kaɗan. Tare da watsa jajjagen kayan miyar,
ta soyasu. Kana tasa naman da sauran ruwan tafashen.
ta kuma ɗauko bandan kifin tarwaɗa bandanshi, ta gyara ta wonƙeshi da ruwan ɗumi.
ta watsa a ciki. Sannan tasa ɗan dakekken yajin daddawa kaɗan."
sannan ta rufe tukunyar.
ta amshi kuɓewar tana ƙarisa yankan. Tukunyar data ɗaura ruwan tuwo ta ɗan kalla
ganin yana tafasane tace.
"Gacan garin semo na tankaɗeshi ɗibi kiyi mana talge."
To tace tare da juyawa ta ɗebo tayi talgen.
Ita kuwa kuɓewar ta saka, kana ta tsalli ɗan toka ta saka.

Bayan wasu yan daƙiƙu miyar tayi lugub tayi kyau tayi kalar kore mai kyau. sabke
tukunyar tayi kana tasa,
man shanu a ciki.
Sannan ta meda tukunyar gefe.
Tuwon ta tuƙa ya ɗan turara kafin ta kwasheshi tana yin mal'mala tana sawa a leda.
Saida ta cika wani madaidaicin Foodflaks mai ɗan girma.
Kana ta ɗauka ruwan zafi.
Ta tafasa tea ta ɗura a flaks tare da tarfa kanumfari da citta sai na'am.
Sannan ta rufe, ta kimtsa komai a kitchen ɗin.
Ganin Shatu nata Hamma ne tace.
"Jeki kwanta tunda mun gama aikin. Sai kuma da asuba."
Cikin alamun bacci tace.
"To Ummi saida safe".
Ta fita tana haɗiye minyau dan ƙamshin da miyar keyi.

A falo taci karo da Hibba Aunty Juwairiyya ta rakota, da Foodflaks a hannunsu


alamun abincin sahur ne a ciki.
Cikin baccin da takeji tace.
"Mun yi girki ma, Aunty Juwairiyya".
Kai Juwairiyya ta ɗan gyaɗa tare da cewa.
"A lallai kam sannu da aiki".
Ta ƙarishe mgnar tana ajiye kulolin bisa dinning table.
Ita kuwa Shatu harara ta watsawa kulolin tare da wucewa tayi ciki.
Hibba ce ta biyo bayanta bayan tayiwa Aunty Juwairiyya Saida safe.

Har sun shiga Ummi ta kira wosu.


Falo suka dawo duk suna hamma alamun bacci, ganin Hamma Jabeer na zaune ne, gasu
Jalal gaba ɗaya yasa suma suka ƙarasu cikin falon.
Gyara zanshi yayi tare da kallon Hibba da Aysha da duk alamun bacci ya cikasu,
cikin sakekkiyar murya yace.
"T....!

Uhummm Ramadan da daɗi, Ya Allah ka nuna mana ka kaimu watan lfy ka nuna mana
ƙarshensa lfy ka maimata mana.

Rayuwar Masarautar Joɗa a Ramadan yanada tsari da masifar daɗi da burge duk
musulmi.

Kabcen Shatu da Sheykh a kwanakin Ramadan da bikin salla yana sani murmushi da
shauƙi.😘🤝🏻
🥰🤝 🏻

By
*GARKUWAR FULANI*"To Alhamdulillah. Allah ya kawomu watan Ramadan,
wata mai tarin al'farma da al'barkatu da tarin ni'imomi. Mutane da dama Allah bai
basu wannan damarba, da yawa sun rasu.
Wasu kuma basu da lfy, basu san me sukeyi ba ko a ina suke, bare su ribaci wannan
dama da Allah ya bamu.
An ga wata wanda haka keda tabbacin gobe zamu tashi da azumi.
Duk kuyi niya, ɗaukar azumi talatin ko talatin ba ɗaya."
Sai ya kuma ya ɗan tsagaita tare da kallonsu Jalal da Jamil cikin sanyi yace.
"Dan Allah Jalal Jamil ku nitsu kunsan halin da muke ciki. Kun san matsalar
rayuwarmu kunsan damuwarmu, wannan dama ce da zamu yi amfani da ita wurin tsananta
addu'o'in ba dare ba rana.
In sha Allah, Wata rana komai zai dai-dai-ta domin Allahu sami'uddu'a ne.
Jamil kaji tsoron Allah ka ribaci wannan watar, ka raba kanka da zuwa club, ka
yayewa kanka masifar nacin liƙewa mata da waya."
Juyowa yayi ya ɗan kalli Jalal kana yaci gaba da cewa.
"Jalal yawon bin yan iska da wani shegen shiga mara kan gado ba tsarine na Musulmin
ƙwarai ba.
Aunty Juwairiyya Hibba Ummi Ke uwar bacci".
Ya ƙarishe mgnar da kallon gefenda Shatu da take zaune tana ɗan lullumshe ido,
da sauri ta waresu don a sama taji muryar tasa. Baki ta tura tare da sunkuyar da
kanta, shi kuma jenye idonshi yayi daga gefen da take cikin ɗan ɗaga sauti yace.
"Watan Ramadan ya bambanta da sauran watanni.
Domin a cikin watanne daren laylatul Ƙadir yake, kuma a cikin watanne Allah ya
sauƙe al'ƙur'ani mai girma.
Kana a cikin watar akwai ranakun da malamai sukeyi hasashen a daren laylatul Ƙadir
yake, Daren 21, 23, 25, 27, 29. Sai dai ba'a tabbatar, da sahihin rana ɗaya
tsayeyye ba ƙauli mafi rinjaye shine ranar 27.
Abi mafi kyau shine kada mutun ya sake koda dare ɗaya na Ramadan ya wuceshi.
Mu raya dararen da ibada da ambaton Allah, wajibine mutum ya tsare bakinsa, da
munanan zantuka walau a baki walau a rubuce a social media,
Domin mu ribanci watar da ambaton Allah da samun ruɓanyar lada, wannan abubuwane da
kullum nake gaya muku su, sai dai aiki dasu ya gagareku."
Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa.
"In Sha Allah zamuyi ƙoƙarin kiyayewa".
"Allah yasa yace, tare da sallanmansu duk suka fita sai Ya Jafar da Ummi.
Ganin yadda Hibba keta zuba hamma ne ya sashi cewa.
"Muhibbat tashi
Kije ki kwanta".
Kusan a tare ta mike ita da Shatu.
da sauri yace.
"Banda ke". Cikin bacci ta turo baki tare da cewa.
"Ayyah dan Allah fa".
Murmushi Ya Jafar yayi tare da zuba mata ido.
Wanda koda baya mgna ana iya gano yadda yake sonta a ranshi, so kuma irin son da
yakeyiwa su Hibba.
Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"A barta tai bacci aiki mukeyi tun ɗazu".
Shiru bai kulasuba, ganin haka ita kuma tabi bayan Hibba.
A zatonta bai saniba, har sunje bakin ƙofar taji yace.
"Saura ki binƙire kiyi ta bacci, kada ki tashi ki raya daren. Sai gari ya waye ki
buwayi mutane da ife-ife da rashin kunya".
Ya ƙarishe mgnar cikin jin haushinta tare da Binta da kallon fitinenneyar yarinya.

Ganin Ya Jafar ya miƙa ya juya zai fitane yasa yayi saurin.


Bin bayanshi ya rakashi kana ya dawo ya konta.

Ummi ma ta konta.

Ƙarfe ɗaya da rabi Sheykh ya tashi yayi ta nafilfilinshi tare da jere addu'o'in da
neman warakar damuwar rayuwarshi data ahlinshin.

Ummi ma tuni ta tashi. Ƙarfe uku ta fito.


Falon hango haske a ɗakun Shatune ya tabbatar mata sun tashi.

Kitchen ta wuce. gas ta kunna ta ɗumama musu miyar, kana ta haɗa plate spoons and
cups tazo ta jere bisa Dinning table.

Sannan ta koma kitchen ta ɗauko musu drinks and water masu sanyi tazo ta jere komai
yadda ya dace.

Kana ta dawo falon ta zauna riƙe da carbinta.


Ƙarfe huɗu dai-dai su Jalal suka buga ƙofar sanin sune yasa, ta tashi ta buɗe musu.
Suna shiga ana buga bindigar sanarda mutanen masarautar Joɗa cewa lokacin sahur
yayi.
Bayan mintuna talatin kuma za'a kuma sakin bindingar.

Cikin gudu Shatu ta fito falon jiki na rawa, kiciɓis tayi da Ummi da takeda niyar
zuwa ta ta kirasu suzo suyi sahur.
Ruggume Ummi tayi ƙam-ƙam tare da neman inda zatasa ranta.
Allah ya sani tana tsoron ƙaran abu biyu, ƙaran aradu da walƙiya da kuma ƙaran
harbin bindiga".
Cikin mamaki Ummi tace.
"Oho Aysha duk wannan tsoron na ƙaran harbin bindiga ne, lallai kuwa in baki sababa
kafin Ramadan ya ƙare zakisha wuya."
Hibba ce ta fito tana dariya tace.
"Allah ko Ummi ana ɗaukan alhaƙin Aunty Aysha".
Babban Falon suka nufo yayinda duk jikinta ke karkarwar."
Dinning area Suka wuce.
Bayan duk sun zaunane Ummi tace Hibba tasa musu abinci.
Buɗe kulolin tayi.
Jolof ɗin taliya da kifi Aunty Juwairiyya tayi, sai kuma
Flaks ɗin kunun gyaɗa.
nasu kuma tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewan sai tea da sauran kayan sha.
Ta zubawa kowa abinda ranshi keso.
ita dai Shatu mamakin abincin Aunty Juwairiyya na yau takeyi sabida idonta bai gano
mata wani mugun abu a cikiba.

Haka yasa itama shi taci. Da kunun.


duk sunyi nisa a yin sahur ɗin. Amman shi bai fitoba,
Sai ƙarfe huɗu da rabi ya fito.
A hankali ya iso Dinning area ɗin gaban washing hand Baby ya ɗan tsaya tare da
wonke hannunshi.
Ita kuwa Shatu tana ganinshi ta ɗanyi gyatsa tare da cewa.
"Alhamdulillah kana ta miƙe".
Kujerar dake gefen Jalal ya zauna,
Yana zama ita kuma ta juya ta nufi cikin falon.
Shi bai ma kalli inda takeba.
Cikin falo ta koma hannunta riƙe da cup ɗin kunun da take sha.
Cikin kula Ummi tace.
"Sai yanzu?".
ta ƙarishe mgnar tana zuba mishi tuwon semo da miyar ɗanyar kuɓewar da yaji nama da
kifi da man shanu.
gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"A jinkirta sahur a gaggauta buɗa baki Ummi Manzon Allah yace."
Murmushi tayi tare da cewa.
"Hakane".
Bismillah yayi tare da gyara zaman shi, ya fara cin abincin.
yaci mai ɗan yawa dan daren jiya baici komaiba.
tea ta haɗa mishi.
Hannunshi ya wonke kana ya amshi tea ɗin ya fara sha.
Jalal, Jamil, kuwa ci sukayi sukayi haninƙan kana suka miƙe zasu tafi.
Cikin kallonsu yace.
"Kadafa kuje ku kwanta, kuyi al'wala ku wuce masallaci."
To sukace kana suka tafi.
Shi kuwa yana gama yin sahur ɗin ya koma Side ɗinsa,
Wonka yayi tare da al'wala kana yayi shigarsa ta farar jallabiya.
Bayan sun idar da salla gari ya ɗanyi hasken ya taso ƙeyansu, suka dawo gida.

Side ɗin su suka wuce. raka Ya Jafar yayi har Side ɗinsa kafin yazo ya shiga
sashinsa.
Shiru falon babu kowa, bisa alamu kuwa tuni Ummi ta kimtsa ta share da goge ko ina,
ta sassake labulaye, tare da sa turaren wuta mai ƙamshi.
Kana ta kashe hasken ko ina, babu abinda ke tashi sai ƙamshi da sanyin A/C da
karatun Alqur'ani mai girma da kuna.

Falonshi ya nufa yana shiga,


ya zauna a falo, Dua Azkar ya fara yi cikin zazzaƙan muryarshi.
Bayan ya isane kuma ya fara karatun al'ƙur'ani. Sai bakwai da rabi dai-dai ya shafa
addu'a kana ya wuce bedroom ɗin shi.
Wutan ya kashe tare da ƙara ƙarfin gudun AC.
sannan ya nufi luntsumemen gadonshi ya kwanta bisa gefen damanshi tare dasa hannun
ya jawo blanket ya rugu.
A hankali lips ɗinshi ke motsawa, alamun tasbihi yakeyi.
Cikin 13 minute bacci mai daɗin gaske ya kwasheshi".

Haka can wurinsu Shatu ma, saida tai karatun al'ƙur'ani sosai kafin ta konta hakama
Hibba.

Ummi kuwa wonka tayi tayi al'wala ganin bakwai ta wuce ne tayi walahan ta raka
biyu.
Kana tayi karatu sai ƙarfe tara da rabi ta konta take kuwa bacci yayi awon gaba da
ita.

Ƙarfe goma dai-dai ya tashi daga baccin da yakeyi.


Wonka yayi tare da al'wa kana ya fito ya kimtsa cikin shiga ta al'farma. Turare mai
ɗan sanyi ya fesa kaɗan kana.
Ya ɗanyi tafiya kaɗan zuwa gefen Bedside drower'n dake tsakanin gini da gado,
wanda akwai tazarar fili mai ɗan faɗi ana yake shimfiɗa sallayarsa wurin ya zama
keɓantaccene.
Walaha, yayi raka biyu kana yayi addu'o'in yau da kullum ya shafa, miƙewa yayi ya
ɗauki System ɗinshi ya riƙe a hannunshi, kana ya ɗauki woyarshi ɗaya cikin su huɗu
da suke bisa Bedside ɗin.

A hankali yake taku, har ya fito tsakiyar falon. Shiru gidan tamkar babu mai rai a
ciki.
A haka ya buɗe ƙofar ya fita, tare da ja musu ita ta baya.
Koda ya fito asalin farfajiyar masarautarma ko ina shiru kakeji, sai ɗan zirga-
zirgan fadawa da hadimai masu tattara ɗan sharan dake ko wanne bakin part.
Suma kowa a hankali yake aiki alamun akwai bacci tare dasu.
Motarsa kirar Tolls Royce, wacce kuɗinta zai iya kai kimanin Billion 4, 959,630,
naira. Baba Lado shine Drevernshi da sauri ya taso yana suka tafi.
Daga nan masallacin jumma'a na kasuwa ya wuce.
Sha ɗaya saura ya isa, inda ya samu tuni masallacin ya cika yayi maƙil da al'ummar
Annabi maza yara da manya tsoffi da tattawan, yan kasuwa sun cika sunyi maƙil iso
warshi kawai dama ake jira.

Motarshi na gama tsayuwa yan agaji suka rufa mishi baya, babban cikinsu ne ya buɗe
mishi marfin motar tare da ɗan rusunawa yace.
"Barka da safiya Malam".
Cikin tsananin kulawa Sheykh Jabeer ya kalli dottijon da ya kai ya haifeshi.
Hannu ya miƙa mishi tare da cewa.
"Barka dai Baba Sule Ya ibada".
Cikin jin dadi yace.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ya kalli sauran wanda yawanci bazasu wuce sa'annim ƙaninshi mai binshiba
Affan kenan,
Murmushi yayi tare da basu hannun yana mai tuna cewa tabbas da Affan yana ƙasar nan
To bana a Ɓadamaya zaiyi azumi, kuma ya sani da yanzu suna tare anan, dan shi ba
irinsu Jalal bane.
Zagayeshi sukayi suna buɗa mishi hanya yana wuce.
Ta kofar da liman ke shiga ya shiga.
sit kakeji da yake duk mazane, gashi kuma ansan ƙa'idarshi shi baya son surutu in
yana tabsir.
Zama yayi tare da kallon ɗan agajin dake saƙala mishi abin ɗaga sauti mgn a jikin
al'kyabbar jikinshi.
Yayinda wasu kuma suka koma bayanshi wasu suka tsaya gefenshi, yan ɗaukan awazin
kuma na gidajen Radio da TV duk sun kafa na'ura su a gaban table ɗin da yake
zaune.
Bayan an gama kimtsa mishi komaine, ya gyara zamanshi tare da kallon alaramma
Abdulƙadir wanda shine zai jamishi baƙi.
System ɗinshi ya buɗe tare da gyara mata zama, haka shima Alaramma Abdulƙadir yayi
da Qura'an ɗin gabanshi.

Gyara murya Sheykh Jabeer Habeebullah Nuruddeen Bubayero yayi tare da fuskantarta
taron al'ummar dake gabanshi cikin ɗan ɗaga sauti yace.
"Bismillah rahmanirrahim. Assalamu alaikum warahmatullahi wa barka tuhu.
Innal hamdalillah nahmaduhu wanasta inuhu wanastagfiru wana uzubillahi min shururi
am fusina wa sai'yi ati amalina. Manyahadillahu fala mudillah, famanyuddul fala
hadiyala wa asshahu'alla'ila'ha'illalahu wahdahu lasheri kallah, wa asshahadu
annamuhammadan abduhu warasulu.
Ya ayu allazina amanuttaƙullaha haƙƙa tuƙatil wala ta mutunna illah wa antum
muslimun ya ayu hannasu taƙu rabbakum.
Kalakum min nafsin wahida, wa kalaƙa minha zaujaha wa bassa minhuma rijalan
khasiran wa nisa'ah wattaƙullah lazitasa'aluna bihi, wal'arhama innallaha kana
alaikum raƙiba, ya haiyu allazina amanutaƙullah wa ƙulu ƙaulan sadidah yuslahlakum
amalakum wayagfirlakum zunuba kum, waman yuɗillah wara sulahu, faƙadfaza fauzan
azeema ambaduhu fa inna'asdaƙal hadisi kitabullah wa'ahsanal hadi hadiyu Muhammadin
(S.A.W) wa sharal umuri muhdasatuha fa innakulla mudasatin bidi'a wa kulla
bidi'atin balala wa kulla balaltun finnar."
Nufamshi ya sauƙe mai ɗan nauyi sabida jan dogon numfashin da yayi, kana ya kalli
taron al'ummar musulmi dake zaune gabanshi manya da yara, masallacin yayi maƙil har
woje.
Kusan gaba ɗaya taron jamar suka haɗa baki wurin cewa.
"Wa alaikassalam warahmatullahi wa barka tuhu".
Kanshi ya ɗan rusunar tare da ci gaba.
Gyara masaƙalin abin sautin mgnar dake wuyan al'kyabbar jikinshi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah. Kamar yadda aka saba haɗuwa a wannan masalaci mai Al'barka bana
kuma Allah ya ƙaddara dani za'ayi.
Kamar yadda aka fara a wancan shekarar, zan ɗaura a kan darasin da Malam Abubakar
ya fara, duba da kasantuwar mafiya yawa yan kasuwa ne, to zamuyi maudu'in bisa
haƙƙin tauye mudu, da kuma barin salla ta wuce dan gudun cinikayya ya wuce ka."
Daga nan ya shiga cikin shirin gadan-gadan.
Yayinda gaba ɗaya mutane sukayi tsit suna jin nasiharsa da hujjoji da yake jawowa
daga al'ƙur'ani zuwa ahadisai, yana shigarsu yana ratsa musu jiki, jini, da zuciya.
Musamman dama mutane nason wa'azinshi.
Haka yasa koda lokacin tashi yayi sai suka ga kamar miti biyar sukayi ba awa ɗaya
ba.

Yana tashi a wurin yan agaji sukayi mishi rakiya, har bakin motarshi.
Daga nan Masallacin Masarautar Joɗa ya nufa.
Sha biyu dai-dai tayi mishi yana cikin masallacin
tuni an shirya an kimtsa komai yadda abu zai tafi, shiyasa yana isa shida Alaramma
Abdulƙadir suka fara.

A can cikin masarautar Joɗa kuwa.


Dai-dai lokacin Shatu ta fito cikin ɗakinta ta nufi falo.
Shiru babu kowa, haka yasa ta wuce kitchen da nufin yin wonke-wonken da sauran
gyara-gyare ganin komai tsab-tsab ne yasa ta dawo falonta.
A hankali ta nufi ɗakin Ummi.
daga bakin ƙofa ta tsaya tare da yin sallama.
Cikin kula Ummi ta amsa mata tare da cewa.
"Ki shigo mana".
To tace kana ta shiga, cikin sanyi tace.
"Ina kwana Ummi".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Lfya lau Alhamdulillah, amman yanzu dai ina wuni ne ko".
Cikin murmushi tace.
"Eh hakane fa, yanzu har sha biyu da rabi tayi".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ai tunda naji Sheykh ya fara tabsir nace to rana ta tsala".
Shiru suka ɗan yi tare da kasa kunne, ras muryarshi ke tashi sabida ansa amsa kuwa
ta cikin masarautar.
shiru Shatu tayi tare da yin ƙasa da kanta tana mai lumshe ido, Allah yasani tana
masifar son tabsir ɗin shi, in taji yana jan baƙi sai take jinta kamar a harami
take.
Ummi ce ta ɗan kishin ƙiɗa tare da cewa.
"Gyara zamanki muji wa'azin."
Kai ta ɗan ɗago tare da cewa.
"Ummi naje kitchen zan mana wonke-wonken na samu an gyara komai ba dai ke kikayi
aikinba?".
Cikin maida hankalinta ga sauraron tabsir ɗin tace.
"Nice nayi, amman daga yau Saratu zata na zuwa tanayi wanke-wanke da share-shere da
yan gobe-goben da dai sauran ƴan wasu aiyuka, kamar fere dankali ko doya da tsinkan
ganyen ko wanke wake ko jiƙa shinkarfa masa da kai markaɗe, duk itace zatayi mana,
mu kuwa in munyi azahar mu shiga kitchen,
zatake ɗan taimaka mana da wasu aiyu kan. Amman banda girki, hadimar Gimbiya
Aminatu ce, amman duk azumi nan ake bamu ita".
Cikin gamsuwa da hakan tace.
"To ba damuwa Ummi, amman dan Allah in ɓata zoba, kada kice zakiyi aikin ki barshi
ni zanyi".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Zama tazo, kullum da asuba ana idar da salla zata zo.
In ta gama aiyu kanta kafin ƙarfe goma dai zata tafi, sai anyi sallan azahar kuma
zata zo.
Daga nan kuma sai mun gama aikin buɗe baki, ta tafi dana Gimbiya Aminatu da nata,
sannan sai ansha ruwa anyi sallan isha'i da asham sai ta dawo tayi yan wonke-wonken
da taimaka mana aikin sahur, to in ta tafi kuma sai washe gari in anyi sallan asuba
ta dawo."
Cikin ɗan fito da idonta tace.
"Wannan zirga-zirga haka Ummi to ta zauna anan kawai mana ta huta".
Juyowa tayi ta ɗan kalleta kana tace.
"Mijinki ba irin waɗannan mutanen bane, baya son a turo mishi yara suzo suyi ta
zirga-zirga a kanshi, kinga duk lokutan da take zuwa basa haɗuwa."
Baki ta ɗan taɓe tare da yin mgna a zuci.
"Kai mutun komai tsari, wannan babu shakka baida gskya ne wannan ɓoye-ɓoyen waya
sanima ko cin zan-zanane a jikinshi da saɗaure wata ƙil shiyasa yake kima tabka-
tabkan Al'kyabbar ajikinshi dan ya boye abubuwan".
Murmushi Ummi tayi dan ta lura Shatu bata san mgnar ta fito fili ba.

Shiru Shatu tayi ganin alamun Ummi na jin wa'azin,


Hakane yasa tayi shiru sabida kada ta takura mata.

Ƙarfe ɗaya dai-dai na rana, akayi addu'a aka rufe taron sai kuma Goben in Allah ya
kai rai.

Da yawa mutane basu fitaba,


mafi akasari Kur'anai suka ɗauka suna karatu.
Kamar yadda Sheykh yakeyi.

Ƙarfe ɗaya da rabi aka kira sallan azahar.

Miƙewa Shatu tayi tare da cewa.


"Ummi bari inje inyi salla zan zo muyi wata mgna".
Cikin binta da ido Ummin tace.
"To".

Bayan anyi sallan azahar an idar ne, ta fito ta nufi ɗakin Ummi, ganin bata nan
ne, yasa ta nufi falo, nan kuwa ta sameta zaune bisa kujera.
gefenta taje ta zauna.

Tana zama wata ƴar matashiyar budurwa ta shigo,


cikin nitsuwa tazo ta rusuna gabansu tare da gaidasu, Cikin kula Ummi tace.
"Yauwa Saratu kin zo ko?".
Cikin nitsuwa tace.
"Eh Ummi nazo ɗazu bakwa nan sai na koma sai yanzu na kuma zuwa".
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Yayi kyau,". Inda Shatu take ta ɗan kalla tare da cewa.
"Ɗiyata ga Saratu. Saratu ga Saiyada Shatu matar Sheykh Jabeer".
Cikin mamaki da dariya sunan da Ummi ta liƙa mata wai Sayyada, ta kalli Saratu tare
dake gaisheta cikin ladabi da biyayya,
fuska a sake ta amsa.

Cikin sanyi Saratu tace.


"Ummi me za'ayi ne?".
Gyara zama Ummi tayi tare da cewa.
"Ki wonke shinkafar masa dama na jiƙata, kana ki gyara mana ganyen alaiyahu, sannan
ki fere Arish.
Sai kuma ki jajjaga kayan miya, ki yanka al'basa mai ɗan yawa."
Cikin nitsuwa da bin umarni tace.
"To Ummi".
Ta ƙarishe mgnar tare da miƙewa ta nufi kitchen, tana shiga ta fara aiyukan da aka
sata.

A falon kuwa, gyara zama Shatu tayi tare da kallon Ummi cikin sanyi tace.
"Ummi dama mgnar da zamuyi ko!."
Sai kuma tayi shiru tana nazari, jin muryar Ummi nace mata,
"Uhum ina jinki faɗi".
Sunkuyar da kanta tayi a hankali tace.
"Uhumm dama cewa, zanyi in ba matsala a rinƙa yin abun buɗa bakin ana kaiwa
masallacin Masarautar Joɗa mana, tunda dole talakawan gari na zuwa nan sallan
magriba."
Murmushi mai yelwa Ummi tayi tare da cewa.
"Allah sarki, Shatu mai tausayi, ba matsala amman ki tambayi mijinki in ya amince
dai ba matsala, dama kuma ana fitar da abinci a sashin Gimbiya Aminatu, da Gimbiya
Saudatu da kuma gidan Galadima, da Hajia Mama.
Da gidan Dr Aliyu da sauran duka, kuma ko Juwairiyya ma tanayi".
Murmushi ta ɗanyu tare da cewa.
"To Ummi muma ai muna son ladan wannan aikin".
Da sauri tace.
"A sosai ma kuwa. Sai dai ki sanar da maigidankin in ya yarda yanzu incewa Saratu
ta ƙara hannun sosai".
cikin kwaɓe fuska tace.
"To Ummi shi wannan sarkin zirga-zirgan ina zan ganshi?".
Cikin yin ƙasa da murya Ummi tace.
"Yana falonshi yanzu ya dawo, yana wucewa kina fitowa, jeki sameshi da sauri kada
yayi bacci ya zama kin tadashi a bacci dan babu abinda yafi ɓata mishi rai sama da
ya fara bacci a tadashi".
Cikin juya ido tace.
"Ummi to ni me zan ce mishi?".
Murmushi Ummin ta kumayi kana tace.
"Abinda kika cemin shi zaki ce mishi, tashi kije musan yadda zamu fuskanci aikin".
Ta ƙarishe mgnar tana miƙar da hannunta, a hankali ta miƙe tsaye, doguwar rigar
jikinta ta gyara tare da yane mayafinshi.
Ganin ta tsaya ne yasa Ummi cewa"
"kije mana." Allah yasani badon tana son ladan aikin ciyar da marasa ƙarfi da basu
abin buɗa bakiba da bazata sake zuwa tambayar abu wurin wannan kurman ganganɗinba,
tun randa taje tana mishi mgnar yacewa Umaymah ta bar musu Hibba ya shareta take
jin haushinsa in ta ganshi kamar ta ɗirka mishi dundu a baya.
Muryar Ummi data kuma jine yasata, juyawa, ta nufi corridor'n da zai sadata da
falonshi.

A hankali take taku, tana jin sanyin tayis ɗin wurin na ratsa mata ƙafa,
sallama tayi a bakin kofar tare da kutsa kai ciki, tana mai murtuƙe fuska.
Bisa 1 str ta sameshi zaune, da alamun waya yakeyi da Umaymah.
Dan taji yana kiran sunanta.
Gefenshi ta ɗan tsaya tare da kallonshi ta wutsiyar ido.
Shi wai ko shi kaɗai ko a ɗakinshi shi ɗaya sai ya zauna da kima-kiman riguna,
ganshi wata ƙil basa damunshi".
Haka taketa maganar zuci, har ya gama wayar da yakeyi bata, saniba.
shi kuwa baibi ta kantaba yaci gaba da ɗan aikin da yakeyi a wayar.
Jin shirune yasa ta ɗan kalleshi, ganin ya gama wayar da yakeyi ne yasa, cikin
dakiyar murya tace.
"Uhummm dama so nake in ba matsala ko zamu rinƙa yin abin buɗa baki ana kaiwa
masallacin, da kuma bawa bayi nasu daban".
Bai kulata ba, asalima yamutsa fuskarshi yayi, ya lura wannan abar bata gama iya
sanin makamar mgna ba, ji yadda take mgn a kaikace.
Kamar ba ba fullatanaba, bayan anyi ittifaƙin bayan larabawa babu ƙabilar dake da
luggar iya sarrafa harshe sama da Fulani.
Shiru tayi tare da tura baki kana ta ɗan murguɗashi, tare da cewa.
"Ayyah ka amince mana?".
kanshi ya sunkuyar tare da ɗaga system ɗinshi ganin biyu dai-dai ta cika.
Miƙewa tsaye yayi tare da motsa lips ɗinshi a hankali yace.
"Eh". Da sauri ta juya ta fita tana hararan bayanshi.
Shi kuwa bedroom ɗinshi ya wuce.

Rage kayan jikinshi yayi kana yasa hannunshi ya jawo pillow'nshi ya wurgar can gefe
gaban gadon inda babu carpet,
a hankali ya kwanta a wurin,
Gudun kada daɗi gado yasashi yayi baccin da zai makara sallan la'asar, Yana konciya
ba jimawa yayi bacci.

Ita kuwa cikin jin daɗin amincewar da yayi, tacewa Ummi.


"Ummi ya yarda yace muyi".
Miƙewa Ummi tayi tare da nufar kitchen a tare suka shiga.
Tana cewa.
"Yauwa to taho mu gayawa Saratu abinda za'ayi.

A tsaye suka sameta a tsakiyar kitchen ɗin kusa da kitchen table, tana gyara
ganyen.
"Yauwa Saratu kin wonke shinkarfa masan ne?".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Eh na wonke,kuma mafa tun ɗazu da nazo kuna kuma bacci na jiƙa wani, sai dai
hannuna ya zarce yayi yawa, yanzu ina gama tsinkar ganyen zan kai markaɗen ne in na
dawo an kwaɓashin sai in fara firan Arish ɗin".
Ajiyan zuciya Ummi tayi tare da cewa.
"Mugamshin".
Babbar robar dake gefenta ta jawo tare da cewa.
"Gashi kinga yayi yawa wlh mancewa nai sai naga kamar na gidan Gimbiya Aminatu zan
jiƙa shiyasa, kinga da na haɗa da wanda kika jiƙan yayi yawa sosai, ko zamu rabashi
biyu".
Murmushi Shatu tayi ganin shinkafar tanada yawa, kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ba matsala hakanma yayi dama mai yawan akeso".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ga kuma ƙullun na dafa tun ɗazu har yayi sanyi, shiyasa nake sauri in kai markaɗen
naga lokacin yayi nisa".
Motsowa tayi inda take tare da cewa.
"Ɗauki markaɗen ki kai bari in ƙarisa wannan aikin".
Cikin mamaki tace.
"A a bar".
Da sauri ta katseta da cewa, jeki".
To tace cikin mamakin sauƙin halinta ta ɗauki robar jiƙeƙƙiyar shinkafar da ta kai
mudu biyar har ta ɗaura a kai,
Ta kuma sauke jin Shatu na cewa.
"Yauwa naga akwai murjejjiyar gyaɗa, ɗebo, da wata shinkafar kizo ga dabino da
kwakwa a nan ki haɗa ki jikasasu ki tafi dasu, na kunune kafin a markaɗa wannan na
masan shinma ya jiƙa sai a markaɗa miki shi.
Da sauri ta juya tayi yadda tace ɗin tanayi tana nuna mata dai-dai yadda takeso,
saida ta gama kana rufe babban roban da marfinshi sannan ta ɗaura ƙaramin a kai ta
tafi.

Ita kuwa Shatu matsowa tayi taci gaba da tsinkan ganyen, ita kuma Ummi freezer'n ta
buɗe tare da ɗebo kayan ciki mai yawa, tazo.
Ta wonƙeshi fes, kana ta watsa al'basa mai yawa a ciki, Sannan tasa
citta,kanamfari, cory tare da sauran kayan ɗanɗanon.
Gas ta kunna ta ɗaura tukunyar, sannan ta dai-dai-ta wutar.

Wani babban roba ta ɗauko kana ta nufi Store Arish ta ɗebo mai ɗan yawa tazo tana
fereshi cikin ɗan injin ɗin firar lokaci ɗaya tayi nisa a fitar.
Ita kuwa Shatu tana gana gyaran ganyen ta ɗebo kayan miya tazo ta jajjagasu yadda
takeso.
Kusan a tare suka gama da Ummi.
Wankeshi Ummi tayi bayan ta yishi tsillk-tsillk kana ta sashi a tukunya, tare ɗan
yaryaɗa gishiri, ta rufeshi.
Ta ajiye gefe.
Ita kuwa Shatu cikin kula ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi me za'ayi da ganyen?".
"Miyan da za'aci masar dashi".
To bata amsa tana komawa cikin Freezer'n fruits ta ɗebo.
Tazo tana wonkesu tare da shiryasu cikin tray mai girma, kana ta shirya wasu kuma a
wani ɗan madaidaicin tray mai masifar kyau.
rufesu tayi kana taje tasasu cikin Fridge.

It's kuwa Shatu can nama ta ɗebo dai-dai misali wonƙeshi tayi tasa a tukunya tare
dasa kayan ƙamshi dana ɗanɗano.
ta ɗaura a wuta. Ummi kuwa ruwan tea ta ɗaura a ɗaya murhun dake gas ɗin babbane.

Naman na sulaluwa ta kwasheshi tasa mai saida yayi zafi tasa al'basa,
ya soyu yana ƙamshi kafin tasa jajjagen kayan miyar ta,
Ya soyu kana ta ƙara wonƙe ganyen miyar yazo tasa, ta soyashi da kyau.
kana ta zuba naman da sauran ruwan miyan.
Tasa duk sauran kayan hadin ta rufe tukunyar.
Sosai Ummi tayi mamakin yadda ta haɗa miyar, to sai dai bata damuba sabida sanin ko
wacce mace da yadda take sarrafa girkinta, kai yadda kakeyi daban in wani ya gani
yayi mamaki, yadda wani keyi da ban in ka gani kayi mamaki.

Cikin ƙanƙanin lokaci dai suka haɗa duk aiyukan da zasu iya ajiyesu ba tare da sun
samu matsalaba.
Ita tayi miyar masan, ta kuma ƙarisa ferfesun kayan cikin da Ummi ta fara.
Ummi kuwa ta tafasa musu tea ta ɗuɗɗura a flaks,
Kana ta tafasa Arish ɗin.
Dai-dai lokacin kuma Saratu ta dawo.
Ita Ummi ce ta ɗan amshi ƙullun masar tare da cewa.
"Gskya mun ɗan makara aikin Masar nan gashi ni hannuna baya tashi da wuri".
Da sauri Shatu ta matso tare da miƙawa Ummi roban markaɗen kunun.
Tace.
"Ba matsala Ummi ni hannuna na tashi da wuri.
Yanzu tace mana marƙaden kunun bari in kwaɓa mana Masar."
Haka kuwa akayi Ummi ta fara tacewa.
Ita kuwa kulun dafaffiyar ɗanyar shinkafar ta murmusa cikin marƙaden Masar,
Kana tasa fulawa tare da yis kaɗan sannan ta tarfa gishiri kaɗan.
Kana ta rufeshi a robar dan babbace, motso da robar tayi kusa da Gas ɗin yana ɗan
jin ɗumin wuta.
Gefen Ummi ta dawo wacce ta gama tace markaɗen
A babbar tukunta ta zuba shi kana ta ɗaura kan wuta tare da dai-dai-ta wutar tanayi
tana motsa kunun.
tare da ɗan tarfa wanda ta rage, da surkin lemun tsami.
Cikin Sa'a ɗaya ta dama kunun shinkafar fari ƙal tamkar madara.
Sugar tasa ta juye a a ƙatuwar kula kana tasa a maidaciyar kula, Sannan tasa a
flaks ɗaya, sai kuma tasa a Mug mai marfi duk ta kimtsasu gefe.
Tuni Side ɗin ya ɗin ke da ƙamshi miyar masan da ferfesun nan.
Buɗewa tayi ganin miyar tayine ta sauƙe ta maida gefe.
Kana ta kalli Ummi tace.
"Ummi je kiyi salla la'asar tayi, in kin dawo sai inje inyi".
To Ummi tace ta fita tana mamakin saurin aikin Shatu.
Koda taje tayi sallan ta dawo ta sameta tana sauƙe tukunyar ferfesun.
ganin Ummi yasa tace. "Yauwa Ummi komai yayi dai-dai yanzu kaskon tuya zamu daura
kinga kullun ya tashi".
Cikin mamaki Ummi ta kalli Robar da taga har kullun na shirin zubewa.
Ita kuma ɗiba tayi a wata roba kana duk tasa yankekken al'basane a ciki Sannan tasa
sugar ta gauraya,
sannan ta matso da kasko biyu,
juyowa tayi ta kalli Saratu tace.
"Yauwa Sara matso. Ke ki rinƙa yi kina sawa a wannan babban kulan in ya cika kisa
a wannan shima.
Ummi ke kuma kisa mana namu anan suyanki mukeson ci".
Murmushi Ummi tayi kana tace.
"To jekiyi salla".
To tace kana ta fita.
Ita kuma Ummi ta juya ta kalli Sara tare da cewa.
"Kema kije kiyi salla".
Cikin ci gaba da aikinta tace.
"Ai nima nayi".
"To shike nan". Ummi tace kana sukaci gaba da tuyan.

A falo ta haɗu da Hibba da Jamil, sai dariya yakeyi cikin dariyar yace.
"Yauwa Aunty Shatu dama idonki nazo in gani, dan ga Hibba kam ta kusa kasawa".
Murmushi tayi dan bata da sauran ƙarfin yin dariya.
Cikin ɗan fito da idanunta da suka ɗan faɗa tace.
"Gani ras dani".
Dariyar ƙeta mai cike da alamun yunwa da ƙishi yayi tare da cewa.
"Inafa ras kalli yadda idonki ya fito kamar kinyi azumi goma".
Murmushi tayi kana tace.
"Um bari inje inyi salla".
Sai ta kuma kalli Hibba dake lankwabe tace.
"Sannu Hibba kwanta ki huta".
Jalal da yanzu ya shigone ya ɗan taɓe baki tare da cewa.
"To me tayi da zata huta tunda fa gari ya waya in anga ta tashi dai yin salla ne,
tun tuni birgima take a tayis wai sanyi take nema".
Dariya sukayi mata baki ɗayansu,
Ita dai Shatu ciki ta wuce.
Salla tayi kana ta fito. Koda tazo kitchen ta samu Hibba na suya musu Arish ɗin,
tayi mamaki.
Cikin wasa tace.
"Kawo in karɓeki jeki kwanta".
Cikin sanyi tace.
"Ai Hamma Jabeer ne yace min in ina aiki bazanji wuya ba, zanfi ganin lokaci ya
gudu".
Dariya sukayi mata kana kowa yaci gaba da aikinshi.
Ita Shatu miyar sahur na asuba ta ɗaura musu.

Cikin ikon Allah shida dai-dai suka gam kan aikinsu.


Bayan Shatu'n ta taya Hibba suya kwai daban, ta jerasu a Foodflaks, in ta ajiye
fefeyin soyayyan ƙwai da yaji haɗi da diddigin kifi, sai ta zuba soyayyan Arish a
kai kana ta kuma rufeshi da fefeyin kwai haka ta rinƙa jerasu saida ta cika kulan.

Ummi kuwa ta sawa Saratu komai nata.

Sannan suka kimtsa wurin fes suka fito da komai suka jera a dinning table.

Nan duk suka wuce ɗauki.


Wanka sukayi, kana sukayi al'wala sannan suka fito falo. A nan suka samu Imran,
Jalal, Jamil, Sulaiman.
Cikin gajiya Ummi tace.
"Yauwa Jalal ku ɗauki manyan kulolin nan ku kai masallaci.
Sauran madaidaitan kuma ku ajiyewa sarkin bayi.
A bawa bayi da hadimai".
Murmushi Jamil yayi tare da cewa.
"Eh lallai bana bayi sun samu uwar gijiyar data tuna dasu, bayan kuma anayi musu
nasu na daban".
Cikin lumshe ido Shatu tace.
"Eh suma suci abinda muke dafawa da kanmu, ba sai na gandun nasuba".

Miƙewa sukayi suka ɗauki kulolin sun zo falon kenan Sheykh na shigowa, wani hadimi
na biye dashi da manyan ledodi cike da ƴaƴan itatuwa.
Kusan a tare suke mishi sannu da dawowa.
Murya a bushe alamun ƙishi yake amsa musu kana ya nunawa Ummi leda ɗaya yace.
"Ummi a wonke wannan a haɗa da dabino mudu uku a basu su kai masallaci".
Ya ƙarishe mgnar yana wucewa.
Da sauri Ummi tace to.
Ta miƙe kenan Shatu tace.
"Ummi zauna bari in wanke sun".
To tace kana ta koma ta zauna.
Ita kuma taje ta wonke ta zubasu a tray kana ta ɗauko plates and cups masu yawa,
tazo ta miƙawa Imran.
Da sauri suka amsa suka tafi.

Jim kaɗan suka dawo, cikin gajiya Jamil yace.


"Ummi ansha ruwafa mun samu Ladan na cin dabino".
Da sauri Hibba ta miƙa tare da cewa.
"Su ladanannan haka suke basa kiran salla sai sun sha ruwa."
Dariya sukayi mata kana suma suka miƙe sukabi bayanta.

Zama sukayi bisa kujerun kowa da abin yake hari.


Sai dai kab ɗibsu da dabino suka fara.
Ummi ce ta kalli Shatu tare da nuna mata babban tray'n da aka shirya komai na buɗa
cikin Foodflaks guda 3 madaidata masu kyau, sai plate ɗin da aka shirya fruits masu
ɗan karen sanyi, tupa, inabi ,kankana, abarba, gwanda, Lemu, ayaba, kana da dabino,
da kwakwa,
Sai goran zam-zam madaidaci, kana sai cup da tea spoon a ciki, sai fork and knife a
gefe da gefen plate ɗin dake cike da fruits ɗin komai biyu akasa.
Kulolin kuma ɗaya masane a ciki, ɗan namiyar kuma miyar Masar ne, sai ɗayan kuma,
soyayyan ƙwai da dankalin, ɗayan kuma ferfesun kayan cikin ne.
Cikin nitsuwa Ummi ta ɗago tray ta miƙa mata tare da cewa.
"Yauwa gashi kai mishi lokacin shan ruwan na tafiya, yanzu zakiga ya fito".
Cikin sanyi da gajiya ta amshi tray'n kana ta nufi falon nashi, cikin nitsuwa take
takun, a hankali tayi sallama tare da kutsa kai cikin falon.
A can bisa Dinning area ta hangoshi yana zaune, kan kujera ɗaya, ya kuma jawo ɗaya
kujerar ya ɗaura sawunshi a kai ya miƙesu, System ɗinshi na bisa cinyarshi.
A hankali take takowa saman steps ɗin tare da ratsa cikin jeren ziri-zirin
igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu darajar sheƙin Daimond sai sunkuyar da
kanta tayi sabida ɗauke mata ido da suke.
A hankali ta isa kusa dashi, cikin tura baki tare da ɗan murguɗashi ta ajiye
tray'n, a tsakiyar table ɗin.
ɗago kanta tayi da niyar ta ɗan juya, ta fita.
Wani irin buɗe idanin tayi gaba ɗaya tare da zubasu, bisa sharaban ƙafarsa ta dama,
wanda sanaɗin zaman da ya ɗan yi ya miƙe ƙafafuwan nashi bisa ɗaya kujerar ne yasa
suka ɗan baiyana, wani irin kallo mai cike da ɗimuwa takeyiwa zanen dake bisa
ƙafarshi ta dama, da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannun hagun ta kama kanta
sabida wani irin sarawa da ya farayi da ƙarfi.
Cikin sauri ta juyo tare da miƙa hannun damanta ta sauƙeshi kan...!

Akwai kayan gyara na amare da uwar gidaye da masu jego, ga mai buƙatar
saya ga number ta 09097853276

By
*GARKUWAR FULANI*Ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu
darajar sheƙin Daimond da yayiwa wurin labule.
Yayin da kuma hankalinta da idonta duk suke kan ƙafar tashi tana kallon zanen da
take gani har kamar motsawa yakeyi a jikinshin, da kuma suffar macijiya.
A hankali ta ɗago ƙafarta tare da take step ɗin forko, hankalinta kuwa duk yana
baya, har ta juya kanta gaba ɗaya sam ganinta baya gaba.
Cikin rashin sa'a kafar ta tsallake step ɗin forko bata isa kan dandamalin ta biyu
ba, ta sauketa, cikin akasi ƙafar ta sule tare da yin shuuuuu tayi gaba.
Wani ƙara mai ɗan karfi irin na maiyin azumi ta sake tare da rumtse idanunta da
ƙarfi tana jiran taji ta ina ɗin ta zai karye.
Wani irin ihu ta kuma sakewa, lokacin da taji ta faɗi gib a kan stpes ɗin kanta ya
bugi dandamalin sama.

A hankali ya juyo kanshi ya kalleta a fakaice,


Ba tare da yace mata ko ƙalaba ya juyar da kanshi ya fuskanci tray'n data ajiye
mishi, plate ɗin fruits ya ɗan buɗe kana, ya ɗauki Fork ɗaya, janye ƙafafuwan shi,
yayi ya sauƙo dasu ƙasa kana ya gyara zamanshi ya fuskanci Dinning table ɗin da
kyau.
Fork ɗin yasa ya fasa cikin dabino da yake irin na kwali nanne mai laushi ne,
ture ɗan yayi gefe kana ya soki dabinon a hankali ya kai bakinshi, bayan yayi
addu'o'in buɗa baki.
Ido ya lumshe jin lokacin da sanyi da zaƙi da ɗanɗanon dabinon ya game mishi baki.

Ita kuwa Shatu kuka tasa tare da riƙe ƙugunta, da kanta cikin muryar kuka take
cewa.
"Wayyo Allah na. Wayyo Ummey na, bayana ya karye ƙuguna ya ɓalgace, kaina ya fashe
ƙeyana ya tarwatse".
Ta ƙasa Glass ɗin table ɗin ya ɗan kalleta, kana ya maida kanshi yaci gaba da cin
dabino, yana maijin wani irin masifeffen dariya na taso mishi jin raki da Shatu ke
zubawa.
Saida yaci ƙwaya bakwai, kana a hankali ya fara tsira Fork ɗin kan ƴaƴan inabi
masu masifar sanyi da daɗi, ci yakeyi yana jin ƙishin daya addabi moƙoshinsa na
wucewa.
saida ya tsinke nonon inabin kab ya cinye, kana ya fara soka kankana da akayiwa
ƙaƙanan yanka kana aka barbaɗa garin madara a samansu, shima shanye rabinshi
yayi.
Wani sassanyan gyatsa yayi tare da ture tray'n gefe.

Ita kuwa Shatu sosai taji zafin faɗuwan ga azumi ga gajiyan aiki ga faɗuwa ga
haushin yadda duk ihun da tayi babu wanda ya kulata, bare a kawo mata agaji, abun
ya haɗe mata sai hawaye share-shere ta tabbatar da a gidansu ne tayi wannan ihun da
gaba ɗaya iyayenta da yayunta da ƙanwarta duk suna kanta, da tuni an ɗagata a wurin
ma.
Bege da kewa da kukan rashin yan uwanta da watseman ahlinsu ne ya tunzura
hawayenta.
Ta kasa tashi sabida jikinta duk rawan yunwa da gajiya yakeyi ba ƙarfi sam.

A hankali ya miƙe tsaye bayan ya sha ruwan zam-zam mai ɗan sanyi kan ƴaƴan itatuwan
da yaci.
System ɗinshi ya ajiye kan Dinning table ɗin, tare da wayarshi.
Gefenta ya ɗan ratsa ya fara taka steps ɗin tare da kallonta a fakaice.
Yana gab da sauƙane ya ɗan motsa lips ɗinshi tare da cewa.
"Kaɗan kenan in dai baki dena samin ido a jikina ba,
Faɗuwa harda kareireyewa zakiyi in baki kiyayi yimin kallon ƙurillaba, na lura ku
mutanen wancan dajin bakuda abinda kukafi so sama da kallon killataccen wuri na
jikin mutun.
Muddin baki dena satan kallon jikina ba, sai waɗannan mayatattun idanun naki sun
tsiyaye kin huta ki zama makauniya babu ɗan jagora.
Kiyi dai a hankali ko kya samu ki mutu da idonki,".
Ya ƙarishe mgnar yana tafi kamar bashi yayi mgnar ba.
Ita kuwa Shatu hannun tasa ta sharce hawayenta tare da rakashi da hararan kai
mugune.

A falon ya samu su Ummi sunata dariya.


Cikin sauri ya kalli su Jamil yace.
"Kai wannan dariyar na menene, ku taso mu tafi masallaci".
Cikin dariya Jamil yace.
"Allah ko Hamma Jabeer ina zaton Hibba bata taɓa azumi ba sai bana.
Ga yadda ta dawo wuni ɗaya, wai a haka kuma har ta fara lissafin wai yauwa yau mun
kai ɗaya mun rage".
Ɗan gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Muhibbata tashi kije kiyi salla sai ki ɗan konta ki huta kafin a kira isha'i ko".
Cikin sanyi tace.
"To Hamma MJ".
Jalal kuwa cikin yin ƙasa da murya yace.
"Gobe ma zakiyi ne ko zaki huta".
Cikin kwaɓe fuska tace.
"Zanyi Umaymah tace, bana ko ɗaya in nasha sai na biya".
Murmushi ya ɗan yi tare da cewa.
"Ashe dai kin girma".
Da sauri ta sunkuyar da kanta, shi kuwa yabi bayansu Jamil.

Duk sukayi gaba, Sheykh kuwa na bayansu.


har yaje tsakiyar falon sai kuma ya ɗan tsaya jin Ummi na ce mishi.
"Shetu fa".
Cikin saurin tafiya masallacin yace.
"Tana can ta faɗi wai ko ta karye ne naji tana cewa ban dai san mataba".
Yana kaiwa nan ya fita, ita kuwa Ummi da sauri ta miƙe cikin zaro ido tace.
"Karaya kuma? Innalillahi yaushe".
Tayi maganar tana nufar falonshi,
A bakin ƙofar shigowa sukayi kiciɓis da ita, da sauri ta tareta tare da tallabota,
jin yadda jikinta ke rawane ta jawota suka fito falon cikin tausayawa tace.
"Sannu Shatu".
Cikin tausaya Hibba taketa jera mata sannu.
Ajiyeta bisa kujera Ummi tayi tare da cewa.
"Baki sha ruwan ba ma ko?".
Kanta ta gyaɗa mata alamar eh.
Hakane yasa Ummi tacewa Hibba ta ɗebo mata, abin shan ruwan a take kuwa ta kawo
mata.

Bayan tasha ruwanne duk suka nufi cikin ɗaki dan yin salla.

Daga yin sallan magriba su Jamil suka dawo sukaci abinci kafin aka kira sallan
isha'i, kana suka koma akayi sallan isha'i da asham sannan suka nufi harkokin su.

Shi kuwa Sheykh Jabeer daga Masallacin gidan Radio Ɓadamaya ya wuce, wurin yin
shirin Fatawa.

Sai tara dai-dai ya dawo, gida.


A kitchen ya jiyosu.
Bisa alamu duk girkin abincin sahur sukeyi.

Shi kuwa bayan ya shiga, wonka yayi-yayi shirin bacci kana ya fito falonshi.

Soyayyan Arish da kwan ya ɗanci tare da tarfa ferfesun ya ɗan ci. masa biyu.

Jin cikinsa yayi tib ne, ya miƙe ya dawo falon.


zama yayi bisa kujera yana kiran Umaymah,
tana ɗagawa tace.
"Jazlaan ina autata, ya azumin yau dai?".
Gajeren murmushi yayi tare da cewa.
"Umaymah autarki akwai raki, yau ita har ta fara lissafin an kai ɗaya saura 29/28".
Dariya ta ɗanyi tare da cewa.
"Kaɗan ma daga aikin Hibba".
Sai kuma tace.
"Ina ɗiyata kuma, ya azumin?."
Kanshi ya ɗan jingina da kujera kana yace.
"Alhamdulillah". Jin muryar Haroon na cewa.
"Wai ɗazu ina ka shigane inata kiran wayar ka baka ɗagawa".
Gyara zamanshi yayi tare da kurban coffee ɗinshi kana yace.
"Na bar wayar a gida, da ɗaya na tafi na Fatawa".

"To ya Amarya?".

"Ban sani ba".

Cikin dariya Haroon yace.


"Allah baka haƙuri".

Amsar wayar Umaymah tayi sukaci gaba da mgnar kan tafiyarsu Umrah.
Daga bisani sukayi sallama, ya miƙa ya nufi ɗakin baccinsa.

A kitchen kuwa, bayan sun gama komai na sahur ne.


Ummi ta cewa Shatu taje ta ɗauko Foodflaks ɗin dake falonshi.

To tace kana ta juya ta tafi.


Koda ta shiga ɗan kalle-kalle tayi ganin baya nan, yasa ta harari falon ma gaba
ɗayatare da cewa.
"Mugu". Sannan ta ɗauki kwanukan ta fito.

Duk sauran abincin Saratu suka haɗawa ta kai musu ita da sauran hadiman.
Wanke-wanke tayi kana ta tattare komai sannan ta wuce part ɗin su.

Su kuma ganin har goma tayi ne, yasa sukayiwa juna saida safe duk suka shiga.
Yauma kamar daren jiya haka sukayi.

Washe garima haka suke tafiyar da rayuwarsu. Cikin tsari da kuma samun damar hutu
da ibada dan ribatar watan Ramadan ɗin.

A hankali aka fara nisawa cikin watan Ramadan, kwanaki suna ɗan mirginawa da kaɗan-
kaɗan.

Yau wunin azumi na biyar kenan.

Da hantsi bayan sunyi walaha sunyi karatun al'ƙur'ani.


Sanin yanzu Ummi na jin tabsir ɗin da yakeyi a masallacin Masarautar Joɗa ne yasa,
Shatu tana gaisheta ta fito.

Hibba kuwa Side ɗin Aunty Juwairiyya ta nufa.

Ita kuwa Shatu falonta ta fito.


Bisa kujera ta zauna, tare da kiran
number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu
zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare.

Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa.
"Ban gane wake mgna ba".
Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace.
"Junaidu Adda Shatu ce fa".
Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa.
"Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu,
ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah".
Cikin sauri tace.
"Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri
da Laure da Innaji da jikin".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida
Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai.
Sai dan Baba Madune yana shan wuya,
Satin daya wucema an sake yi mishi aiki".
Cikin sanyi tace.
"To yanzu su waye ke kula daku".
Kanshi ya rausayar tare da cewa.
"Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun
samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci.
An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje".
Cike da jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi".

Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa.


"Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,".
Uhum tace a taƙaice.
Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi.
"Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado.
Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu
dawo? Kina mgna dasu ne?".
Cikin dariya tace.
"Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu.
Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo."
Da sauri yace.
"Dan Allah Adda Shatu turo min number su".
To tace tare da gyara konciyarta.
Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama.
Sannan ta tura mushi number su ɗin.

Suna gamawa ta kira Number Bappa.


Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga.
Cikin jin daɗin jin muryarshi tace.
"Ina kwana Bappa na".

"Lfy lau Alhamdulillah Shatu ya Azumi, da baƙon wuri".


Cikin sanyi tace.
"Alhamdulillah, Bappa yaushe zaku dawo".
Dariya yayi mai ɗan sauti kana yace.
"Bayan salla".
Cikin lumshe ido hawaye na zuba tace.
"Bappa ina jin kewarku, bani da kowa nawa kusa dani.
In na tuno su ya Giɗi hankalina na tashi Bappa inyi ta kuka babu mai sanin irin
ciwon da nakeji a raina".
Cikin sanyi yace.
"Kwantar da hankalinki Shatu, su Ya Giɗi suna raye, sai dai suna cikin mawuyacin
hali, suna buƙatar addu'o'in ki musamman a cikin wannan mata mai alfarma, na sanki
bakya wasa da riƙo da ibada, amman ki ƙara kan yadda kike, in sha Allah wata rana
zasu dawo garemu, cikin sauƙaƙƙiyar hanya, addu'a itace abinda suke so, shiyasa na
gaya miki abinda Allah ya nuna min a mafarki a kansu".
Cikin sassanyan kuka murya can ƙasa tace.
"Zanyi Bappa zan ƙara zan dage, kuma zan roƙi a tayamu addu'o'in a masallatai da
wurin tabsir."
Cikin jin daɗi yace.
"Yauwa Shatu na, ki kwantar da hankalinki, ki zauna lfy da mutanen da kike tare
dasu, kiyiwa mijinki biyayya, kiyiwa mayanshi biyayya bana son musu in babba ya
gaya miki abu matukar bai saɓawa shariyar musulunci ba."
Cikin sanyi tace.
"To". Da sauri yace mata ga Junainah".
Cikin jin daɗi tace.
"To a bata waya".
Tsalle Junainah tayi tare da cewa.
"Adda Shatu, kizo Lardi garin da daɗi kullum sai an gasa mana zabbi ko Tattabaru,
insha nono da zuma inci naman insha zuma, inci su inabi sai na ƙoshi".
Cikin so da ƙauna da shaƙuwar ta da yarinyar tace.
"Allah sarki Junnu ke ko kewata bakiyi bako?".
Dariya tayi tare da cewa.
"Nayi kewarku mana harda Ya Junaidu ma nayi kewarshki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Na bashi number ku, zai kira ku gaisa".
Tsalle tayi tare da nufar ɗakin Ummey.
Ita kuwa Shatu cikin dariya tace.
"Azuminki nawa".
Da sauri tace.
"Azumi na ɗaya ranan nayi rabi daga safe zuwa azahar jiya kuma na ƙarisa rabin daga
azahar zuwa mangriba".
Wani irin dariya ne ya rufe Shatu dariya takeyi sosai.
Kewa da bege da son ƙanwar tata ya rufeta.
Da Sauri ta tsagaita da dariyar jin Junainah na cewa.
"Adda Shatu Bappa yayi aure an samo mana wata Inna mai kirki".
Cikin mamaki tace.
"Ke Junnu ƙarya ba kyau fa".
Da sauri tace.
"To ga Ummey ki tambayeta kiji".
Ajiyan zuciya ta sauƙe jin muryar Ummey cikin sanyi da jin daɗi tace.
"Ina kwana Ummey na ya gida, ya Junnuna nayi kewarku, Ummey wai da gaske Bappa yayi
aure".
Murmushi mai faɗi Ummey tayi tare da cewa.
"To duk Alhamdulillah muna lfy eh Bappa yayi aure an bashi ƙanwar innarku, Indo kin
santa ai ita take bin innarku, Bata taɓa haihuwa ba, to ashe mijinta ya rasu.
Shine yanzu aka aura mishi ita. Kuma tanada hankali kamar innarku".
Cikin sanyin jiki tace.
"Eh na san Umma Indo tanada kirki, to Allah ya baku zaman lfy yasa kuyi irin zaman
da kukayi da Inna".
Amin Amin tace kana tai mata nasiha Sannan sukayi sallama.

Daga nan ta miƙa ta nufi ɗaki dan yin salla.

Ana idar da salla suka fito, kitchen suka nufa ita da Ummi da Saratu da tun ɗazu
tana nan.
Suka fara aikin buɗa baki sunayi suna kimtsa komai.

Kafin shida ta cikama sun gama komai.

Yanzu in sun zo buɗa baki ita da Ummi da Hibba tsakiyar falon suke dawowa.
Jalal, Jamil, Imran, Sulaiman, kuma su zauna a dinning table.

Ya Jafar kuwa wani lokacin har can falon Sheykh zai wuce suyi buɗa baki a tare.
Kana su tafi masallacin.

Haka dai komai yaketa wakana cikin aminci da tsari.


A wurin al'ummar Annabi kowa ya nitsu ya maida hankali kan ibada domin neman
rabauta.

Ƙarfe takwas dai-dai suka shiga kitchen dan yin aikin sahur.
Cikin kula Ummi ta kalleta tare da cewa.
"Ɗauko kwanu kan nashi".
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ai bai dawo yaci ba ko?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Baya cin ƙosai, kuma kinga doyan ma jiya baiciba, ya gaji dasu ne, ki ɗauko a
juyewa su Saratu shi ki ɗan haɗa mishi wani abu kafin ya dawo".
Cikin ɗan kauda kai tace.
"Ummi ai ƙoshi yake shiyasa bazai ciba, a barshi kawai in yaji yunwar yacima wani
bai saniba, ai yunwa ba Umaymah bace ko ke bare zaku lallaɓashi".
Dariya Ummi tayi kana kuma ta haɗe fuska tare da cewa.
"Je kiyi abinda nace ko".
To tace ganin kamar ran Ummi ya ɓaci.

Bayan ta dawo da kwanukan ne,


Suka bawa Saratu ta juye, kana ta harhaɗa wonke-wonken ta fara.

Ita kuwa Shatu cikin yin miƙa tace.


"Ummi me zan dafa mishin?".
Juyawa tayi tana haura wurin da Fridge yake tare da ce mata.
"Duk abinda kika iya kika san ba mai nauyi bane".

Kanta ta gyaɗa tare da cewa.


"To".
Cikin ranta tace.
"Bari inyi Special Arish, in yaga dama yaci in yaso ya bari, mutun sai zaɓe-zaɓe
kamar mai ciki.
Dankali ta ɗan ɗebo da Nama, kwai, tumatur, kabeji, Bama, maggi, tafarnuwa man
gyaɗa, komai dai dai-dai misalin yadda zata buƙata duk ta ajiyesu kusa da ita.

Fere dankalin tayi ba tare da ta daddatsashi ba. Ta wonƙeshi fes kana tasa a ƴar
tukunya tare da tarfa gishiri da ruwa dai-dai misali, sannan ta tafasashi.
Kwan ta ɗauka ta fasa ta kaɗashi da kyau tare dasa yankekken al'basa da Curry da
maggi da tafarnuwa ɗan kaɗan.

Ganin dankalin yayine ta juyeshi a ɗan kondo ta tsaneshi.


Tare da ɗan barinshi yasha iska, kaɗan.
Kana ta ɗaura Naman da maggi da gishiri da Curry da tafarnuwa da al'basa. bisa wata
a ɗan tukunta.
Sannan ɗaura man ta ɗauki dankalin ta tsomawa cikin kwan tana soyashi, saida ta
gama ta ajiyeshi gefe.
kafin nan naman kuma yayi lugub yayi laushin.
saida ruwan ya kusa ƙarewa sai ta ƙara wata al'basar da tumatur suka nuna tare
sannan ta kwashesu.
Kabejin ta yayyanka ƙanana sannan ta ɗauki dafaffan kwai ta yayyanka shi da ɗan
girma.
Kana tasa Maggi da al'basa da Bama ta gauraya kana
Ummi ta miƙo mata ɗan ƙaramin Foodflaks alamun ta amsa ta saka.
Kanta ta jujjuya tare da cewa.
"Bari in sa mishi a plate kawai tunda ya dawo".
Da mamaki Ummi ta kalleta tare da cewa
"Yaushe ya dawo?"
Plate ta ɗauko tare da cewa.
"Tun ɗazu".
Da sauri ta sunkuyar da kanta ganin kamar Ummi na mata kallon Mamaki da tuhuma.
Ita kuwa Ummi cikin Binta da ido tace,
Ya akayi kika san ya dawo".
Kai ta rausayar tare daci gaba da aikin kamar bataji Ummi ba.
Plate ɗin ta ajiyeta, ta zuba Arish ɗin gefe kana tasa haɗin naman gefe, ta kuma
zuba na Kabejin shima gefe.
Ta shiryashi yayi kyau sosai.
Ɗaya plate ɗin ta kife kanshi.
Kana tasa spoon da Fork a cikin tray'n data ajiye plate ɗin.
Ɗan madaidaicin flaks ɗin coffee ta ajiye gefe, kana tasa cup da tea spoon a ciki.
Sannan turashi gefe.
Zuwa lokacin kuma tuni Ummi da Saratu su gama aikin sahur ɗin har Saratu ta tafi.
Sauran ta sako a wani plate ɗin tare da cewa Ummu gashi.
Amsa Ummi tayi tare da cewa.
"Ɗauki ki kai mishi to".
To tace tare da ɗaukan tray'n ta fita.

A tsaye ta sameshi cikin wani tattausan jallabiya da alamun wonka ya fito,


Sai wani irin masifeffen ƙamshi yakeyi.

Cikin nitsuwa ta wuce ta bayanshi, inda yake tsaye yana kunna Tv.

Bisa santa table ɗin glass mai garai-garai dake tsakiyar falon ta ajiye mishi.
Kana ta juya a hankali ta fita.

Kai tsaye ɗakinta ta wuce, nan ta samu Hibba tuni tayi bacci.
Wonka tayi da ruwan ɗumi tare da shafa mai kana tasa wata tattausar rigar bacci
gajera iya karta guiwa.
Hibaji ta zura a jikinta kana ta haura gado ta konta tare da jawo blanket ta
duƙunƙune a ciki.
Sabida ita bata son sanyi, shiyasa takesa ƙaton hijabi kana ta shiga borgo.
Badon Hibba Bama dake masifar son sanyi da kashe AC'n zatayi.
Ƙarfe ɗaya dai-dai ta tashi bacci al'wala tayi kana tai ta nafila hakama Ummi.
Sheykh Jabeer kuwa tuni ya tashi shima.
Ya kira su Jalal ma a waya ya tashesu.

Ƙarfe huɗu da rabi dai-dai ta isa falonshi da tray'n abincin sahur ɗin shi.
Ta ajiye ta juyo kenan shi kuma yana fitowa falonshi.
Tazo tsakiyar falon kenan tana tafiyarta a hankali ba zato ba tsammani taji daram-
dam ƙaran bindigar da kullum da asuba sai an saketa sau biyu, ta kuma kasa sabawa
dashi bare ta daina tsoronshi.
Wani irin tsalle da zabura tayi tare da ficewa a guje tana cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Bayanta yabi da kallo tare da taɓe baki kana ya nufi Dinnin area.

Washe gari da safe yau Jumma'a kuma, yaune azumi na shida.

Bayan sun fitone, Ummi ta kalleta cikin dariya dan tuno yadda ta fito falon Sheykh
Jabeer a guje da asuba, tana jan Allah ya isanmata ana tsinka mata zuciya,
Cikin murmushin tace.
"Ummi dariyar me kikeyi ne?".
Cikin gimtse dariyar tace.
"A babu, yauwa tashi muje ɗazu Gimbiya Aminatu ta aiko, wai tayi kewarki kwana biyu
azumi ya ɓoyeki bakije ba".
Cikin murmushin tace to muje Ummi".
Ta ƙarishe mgnar tanayin gaba Hibba na biye da ita a baya.
Cikin sauri Ummi tace.
"A haka zaki fita ba al'kyabba".
Kai ta ɗan dafe tare da cewa.
"Wayyo Allah na, Allah kuwa ni nauyi sukemin wannan tsarabe-tsaraben wuya gareshi".
Murmushi Ummi tai tare da miƙewa ta ɗauko al'kyabbar.
Tazo tasa kana suka fita.

Da Side ɗin Hajia Mama suka fara,


A falo suka samesu.
Cikin fuskar ba yabo ba fallasa Hajia Mama ta amsa gaisuwar Shatu.
Batool kuwa sai auna mata harara takeyi.
Hira suka ɗan taɓa kana suka fito.
Har sun fito Shatu ta ɗan kalli Ummi cikin sanyi tace.
"Ummi jirani anan bari inje in isar da saƙon gaisuwar Ummey na wurin Hajia Mama".
Da Mamaki Ummi tace to kana ta juya ta nufi ciki, ganin Hibba za biyota ne tace.
"A a jirani ina zuwa".
Haka suka tsaya suna jiranta.

A hankali ta turo ƙafar falon.


Da sauri Hajia Mama ta zuba mata ido fuska cike da tsana.
Batool kuwa binta da ido takeyi ganin wani irin takun isa da ƙasaitar da takeyi.
Kujerar dake fuskantar wacce Hajia Mama ke zaune a kai ta zauna.
Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya.
Kana ta jingina da kujerar, cikin tsare Hajia Mama da ido tace.
"Uhummmm kin sanni sarai, kar tasan karne, duk motsinki a tsakiyar tafin hannuna
kike, dan haka gwara kiyiwa kanki gada ki fita harka da rayuwar mijina! Da
ƙannenshi da wanshi. In kuwa kikaƙi zakisha mamakin Shatu."
Tana faɗin haka ta miƙe, tana kallon Batool da tun randa akace Shatu tazo ta bawa
Hajia Mama haƙuri da ta shigo tayi wasu kalaman ya ɗaurewa Batool kai ta kasa
tantance tsakanin aya da tsakuwa, shiyasa batayi gigin yin mgn ba, sabida tuno
abinda Shatu tace mata a ranar cewa.
"Mijina kike so ko, to kizo in ya amince ya kalli inda kike na daƙiƙi biyu rak zan
sashi ya aureki".
Da sauri Batool ta dawo daga duniyar tunanin da take jin ƙaran rufe ƙofar da Shatu
tayi.

Ido ta maida kan Hajia Mama dake gurnani kamar macijiya.

Jim kaɗan ta fito.


Cike da son gano wani abu Ummi ke binta da ido, amman ta kasa gano komai domin
Shatu ta iye takunta, ta fito kamar ba itaba gaba tayi.

Kana suka nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.


Suna shiga ta miƙowa Shatu da Hibba hannu kusa da ita ta ajiyesu.
Bayan sun gaisane ta kallesu tare da cewa.
"Azumi ya boyeku da yake ku ragwagene".
Murmushi sukayi tare da cewa.
"Kai Gimbiya jiya nefa kawai bamu zoba".
Cikin kula Lamiɗo dake shigowa yanzu zai sabunta al'wala zai wuce masallaci yace.
"Shatu matar malam bauɗeɗɗe".
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai.
Hibba ce tace.
"Sai na gaya mishi".
Dariya sukayi kana suka sallamesu suka tafi ganin lokacin sallan yayi.
Har sunje bakin ƙofa Gimbiya Aminatu tace.
"Yauwa Jakadiya kayan miyanku da saura ko ya ƙare?".
Cikin rusunawa tace.
"A'a da saura sosaima".
Kai ta gyaɗa kana suka tafi.
A hanyarsu ba komawane Shatu tace.
"Ummi wanne kayan miyan ne?".
Cikin sanyi tace.
"To ba kince bakya son na Hajia Mama ba, shine ita kuma Gimbiya Aminatu ta haɗo
miki komai yanzu dasu muke amfani ai".
Cikin gamsuwa tace.
"To wancan ɗinfa ya akayi dashi?".
"Umaymah ta tafi dashi duka".
Hibba ta faɗa mata.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ba matsala".

Nan suka tafi suna salla suka shiga kitchen yau harda Hibba.

Sannu-sannu dai bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'a jeba.

Yau an cika azumi goma. Gobe za'a shiga goma na wuya, an gama na marmari.

Yau kuma makara Shatu tayi.


Ganin har su Jalal sun zone yasa Ummi ta nufi ɗakinsu.
Ai kuwa kan gado ta hangosu.
Tadasu tayi kana ta fito.
Tana cewa.
"Shatu kiyi sauri kizo ki kaiwa Sheykh nashi".
Kusan a tare suka diro ƙasa.
Brush kawai sukayi suka fito.
Da ƙaton hijabin ta fito.
Tana zuwa Dinning area Ummi ta miƙa mata tray'n abincin nasa.

Amsa tayi ya juya ta nufi falonshi.


Tsaye ta sameshi gaban show glass ɗin dake gefen Fridge ɗinsa dake Dinning area,
Cup ne a hannunshi cike da madarar gongoni da molt a haɗe.
A hankali ta wuceshi kaɗan ta ajiye tray'n.
Kana ta juyo da nufin sauƙowa, taku ɗaya tayi a na biyu ta iso gabanshi kenan.
Aka saki bindigar shaidar huɗu da rabi tayi.
Wani irin zabura tayi tare da af....!

Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number
09097853276, domin shiga Normal group wanda a wata ɗaya za'a, gama Part one. Ko
kima kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank, domin samun shiga Special
Group wanda a sati biyu cakal za'a gama Part two da izinin ubangiji, 0005388578
Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai
09097853297.

Ke mai haushi kin turo ɗarinki uku, kinzo kinata haushi, nace ki turo ac no ɗinki
in maida miki kuɗinki kin tsaya yimin tumasanci shiyasa nayi Black ɗinki, a rashin
Sa'a na haɗa da number ki na goge. Kuma baki Turo ac na na meda miki shi ba. To
Alhamdulillah a take a lokacin nayi miki sadaka da ɗarinki uku, ubangijina shine
shaidata, banci kuɗinki ba, nasan zakiga PAGE ɗin sabida akwai waɗanda basu san
darajar Allah da Manzonsa da iyayensuba, zasu fitar, to kiji ni Shatu na sauƙe
nauyin ɗarinki uku.

By
*GARKUWAR FULANI*[3/6, 1:10 PM] +234 816 203 9950: Tare da cewa.
"Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can".
Cikin Murmushin Ummi tace.
"La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja,
Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu."
Amin Amin Hibba tace.
Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba,
Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali.
A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV'n idonta yake,
ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake
jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun
forko.

Sosai take ƙare mishin kallo tare da tsarin shigarsa dana mutanen da yake cikinsu.
Sam bazaka iya bambance shi da suba, Especially ma Sheish Jabir Ali da yake matuƙar
kama dashi.
Haka nan taji wasu irin zafafan hawaye masu ɗumi suna tsastsafo mata cikin
jijiyoyin idonta.
Ta kuma kasa janye ƙwayar idanunta kanshi. Tana kallon tsarin shigarshi da kullum
take ganinshi a matsayin takura.
Lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su.
Ummi ta kalla wacce farin cikin ta ya fito fili.
Hakama Hibba. Sai murnar abun takeyi tamkar tayi tsalle ta shiga cikin TV'n,.

Ganin sun sunkuya kai ruku'uh da zasu tafi sujjada ta biyu ne, kuma an ɗaga camerar
an maidata ɗaukar samane.
Yasa ta miƙe a hankali bisa santa table dake tsakiyar falon ta ajiye cup ɗin kana
ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi kinji masallacin Joɗa ma sun fara sallan kuma muna zaune".
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa.
"Farin cikine ya rufeni Shatu,. Muje muyi al'walan mu tafi".
Uhum tace ta juya ta nufi falonta tana mai share hawayenta da har yanzu suke
zubowa, tanajin zuciyarta na amsar wani nannauyan abu a kan Sheykh, ta yarda ta
gamsu cewa mutun me ibada da imani da ilimi abin sone a zuciyar kowane mutum na
gari.

Bayan sunyi al'wala ne suka fito cikin manyan jihabai ƙatti har ƙasa suka nufi
woje.
Ananne Shatu tai mamakin ganin yadda kusufa-kusufa matan masarautar ke fitowa, duk
suka nufi hanyar zuwa masallacin ta ƙofar dasu Lamiɗo ke bi.

Suna fitowa jikin masallacin sai ga wani ƙaton rumfa na ƙara an lailayeshi da wani
irin yashi fari ƙal-ƙal kana ga hasken wuta a cikinsa.
ko wacce da sallaya a hannunta tuni wasu kuma sunma shimfiɗa sallayunsu sunbi jam'i
hakanan matan maƙota da sauran matan bayi da hadimai duk nan suke zuwa.
A jeru gaba ɗaya ananne ga kafaɗar matar sarki gata baiwa.
Babu matsayi ko milki bare isa ko ƙasaita.

Haka dai suka bi jam'i sai ƙarfe uku aka idar akayi addu'o'in kana akashafa aka kai
sujjadar ƙarshi ta witirin.

Kana akayi taiya akayi sallama duk kowa ya nufi gidanshi.


Daga nan kuma aka kama aikin sahur.

Suna dawowa Hibba ta kuma kunna TV nan ta samu su tuni su sun idar. Wasu nata
ɗawafi ne sai addu'o'in ake jerawa.
wanda sai kaji tsikar jikinka na tashi sabida yadda yake ratsa zuciya da jini.

Washe gari da bayan sallan isha'i da asham, yanzu Jalal da Jamil ne kaɗai ke zuwa
dan Imran da Sulaiman ma dasu aka tafi.

Haka yasa yanzu duk suna zama a Dinning table suyi buɗa baki a tare.
Jalal ne ya ɗan kalli Ummi cikin cin Beans salad da Shatu tayi musu.

Hibba ce keta santi tana cewa.


"Alhamdulillah yanzu dai saura mana azumi tara ko takwas".
Murmushi sukayi, ita kuwa da sauri tace.
"Kai takwas nema in sha Allah".
Jamil kam tuni yake dariya tare da cewa.
"Tara ne".
da sauri ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi wai haka ne?".
Cikin dariya tace.
"A a ban saniba Hibbat."
Plate ɗin data zuba ferfesun jan nama ta jawo tare da fara ci tana lumshe ido tace.
"Takwas ɗin nema in Allah ya yarda".
Allah yasa haka Shatu tace.
Sai yanzu Jalal ya ɗan kallesu tare da cewa.
"Ashe dai duk kanwar jace".
Murmushi Ummi tayi kana sukaci gaba da cin abinci.

Yau dai ana zaton salla saura kwana biyar ko shida.

Da hantsi suna zaune dan yau sun tashi da wuri.


Aunty Juwairiyya ce tayi sallama tare da shigowa, Bayan Ummi ta amsa mata.
Gefen Hibba ta zauna tare da cewa.
"Alhamdulillah Ummi ɗinkunan mu sun dawo, yanzu KB ya kawosu ya shigo ko?".

"Eh ya shigo mana".


Juyawa tayi ta kalli Hibba tare da cewa.
"Je kice ya shigo Hibba yana nan zaki kanshi cikin baƙar mota".
To tace tare da miƙewa da sauri.

Jim kaɗan suka shigo tana gaba da jaka a hannunta yana biye da ita a baya da ƙattin
jakunkuna guda biyu da wani yaro shi shima da manyan jakukkunan biyu.

A tsakiyar falon bisa carpet suka aniye jakunkunan kana, ɗaya yaron ya juya ya
fita.
Shi kuwa Kabir ya zauna a ƙasa bisa carpet ɗin tare da cewa.
"Barka da hantsi Ummi".

"Barka dai Kabiru, munyi Sa'a an cika mana al'ƙawarin ko".

Murmushi yayi tare da cewa.


"Sosai ma kuwa Ummi aini telane mai amana".
Hibba ce ta ɗanyi murmushi tace.
"To ka bari a yebeka mana".
Cikin dariya ɗan matashin yace.
"A a ai duniyar yanzu kawai ka yabi kanka, dan ba lallai bane wani ya yaba maka".
Dariya sukayi duka.
Kana ya fara firfito da kayayyakin.
Ko wanne da sunan maishi a jikinshi.

In ya fito dana Ummi sai ya miƙa mata, in ya fito dana Aunty Juwairiyya da yaranta
sai ya miƙa mata.

Hakama na Hibba yana fitarwa yana miƙa mata.

Shatu da yanzu ta fitone, ya kalla tare da cewa.


"Barka da safiya Sayyada Shatu".
Murmushi tayi Allah ya sani in sun ce mata Sayyada dariya suke bata wato irin ita
matar Al Sheykh ko.
Cikin nitsuwa da danne dariyarta tace.
"Barka dai".
Sai kuma ta ƙara so ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi waye ne shi?".

"Telan mune". Ta bata amsa a taƙaicd.


Cike da mamaki tace.
"To ina ya sanni?".
Hibba ce ta amshi zancen da cewa.
"A hoto ya sanki, da mukaje kai ɗinkunanki hotonki kawai aka nuna mishi, ya ɗinka
kuma kinga komai yayi dai-dai ko".
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Lallai kam yayi ƙoƙari".

Cikin dariya yace.


"Uhum ai na iya aikina sosai Sayyada".
Yanzu kam dariya sukayi duka.
Kana ya zaro kayanta a ƙalla kala takwas ya miƙa mata.
Amsa tayi tare da cewa.
"Sannu".
Hibba kuwa irga kayan tayi tare da cewa.
"Kb saura kala bibbiyu a namu nan gani basu".
Kanshi ya ɗan sosa tare da cewa.
"Wannan yarinya akwai son kalato laifin mutum to sai jibi zan kawosu ko kuma in
bawa Su Jamil in sunje amsar kayansu".
Cikin murmushin Aunty Juwairiyya tace.
"Yauwa ka bawa su Jalal ɗin ma kawai".

To yace, kana ya miƙowa Ummi ƙatuwar jakukkuna guda uku tare da cewa.
"To Ummi ga na yaranki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Ka kyauta min Kabiru ngd matuƙa, Allah yayi al'barka".
Amin Amin yace kana ya sallamesu ya fita.

Ita kuwa Ummi Saratu ta kwaɗawa kira tana zuwa.


Ta tace.
Jeki kira duk sauran hadimai suzo duk wadannan Kabiru yazo ya gansu ranar."
Da sauri tace.
"To kana ta juya ta fita.
Ita kuwa Ummi. Inda take zaune ta nunawa Shatu.
Tare da cewa.
"Zo nan ki zauna, zasuzo, ko wacce zata gaya miki sunanta, sai ki duba sunan jikin
kayan sai kibata, su duk kala ur'uku akayi musu.

Zaki basu da kuɗi dubu biyar-biyar.


Kai ta gyaɗa kana da sauri ta koma ɗalinta.
Sabida. Sai yanzu ta gano me zatayi da wannan kuɗin da ya bata kenan.
Kuɗin ta kwaso kana tazo ta zauna.

Nan suka rinƙa zuwa suna gaidata da gaya mata sunansu. Kana Hibba ta irga dubu
biyar, ta ɗaura kan kala bibbiyu sun ta basu.
Ummi kuwa jakan gabanta ta buɗe tana basu takalma.
Aunty Juwairiyya kuwa jakar hijabai ta buɗe tana basu.
Suna godiya suna tafiya.
Haka sukayi tayi har kusan awa biyu kafin suka gama, duk kayan sun ƙare sai kuɗin
ne ya rage.

Ganin lokacin salla yayi ne, suka tafi.

Bayan sun idar da salla ne, suka fito.


Nan a falon Shatu suka zauna.
Suna ɗan hira sabida yau aikinsu baida yawa, kuma Saratu nacan na rage musu.

A hankali wayar Ummi ta fara suwa, alamun ana kiranta.


Da sauri ta kalli Hibba tare da cewa.
"Hibba ɗauko min wayata a ɗaki".

Miƙewa tayi tare da cewa to.


Jim kaɗan ta fito da wayar da sauri ta miƙa wa Ummi wayar a kunne tare da cewa.
"Amshi Ummi kiyi mgna na amsa kiran Hamma Jabeer ne, kin sanshi baya kira biyu."
Cikin sauri da tarin jin daɗi Ummi tace.
"Assalamu alaikum".
Shi kuwa Sheykh Jabeer a can saudia yana tsaye ne a gaban dreesing mirror yana
gyara igiyoyin al'kyabbar jikinshi.
Tare da saƙala wayar a kunnenshi ya matseta da kafaɗarshi.
Alamun sauri yake yana shirin tafiya haramine.

Cikin sanyi yace.


"Wa alaikissalam. Barka da gida Ummi".
Fuska a sake tace.
"Barka dai Sheykh, ya ibada?".

"Alhamdulillah Ummi, yasu Jalal".


"Suna lfy, kuma basa wasa da ibada, yanzu Jamil ya dena zuwa hirama wata ƙil kuma
ya ɓata da Khadijah naji yanzu wata Maryam yake kira, Jalal ne dai yake ɗan fita
shima ba sosai ba".
Gyara tsayuwarshi yayi tare da cewa.
"To Alhamdulillah, eh shi Jalal ba matsala fitanshi, nasan dashi.
Ya Hibba kuma tana azumi ko batayi?".
Cikin murmushin da kallon inda Hibba take tace.
"A a Hibba ai an girma yanzu ta rage rakinma".

Ɗan karamin mataji ya ɗauka yana kontar da sajenshi yace.


"To Ummi na gaisheku, na kira Aunty Juwairiyya kam nani jikin ya Jafar da sauƙi
sosai mun gaisa da Hajia Mama, har take cemin Affan ɗina zai dawo a salla".
Da sauri tace.
"Uhum Sheykh".
Ajiye kum ɗin yayi tare da cewa.
"Na'am Ummi".
Cikin sanyi tace.
"Ga Shatu".
Shiru yayi baiyi magana ba, kuma bai katse kiranba,
jin haka yasa ta kuma cewa.
"Sheykh".

"Na'am Ummi".
Ya kuma cewa.
A hankali tace.
"Ga Shatu".
Still baiyi mgn ba, hakanne yasa a hankali ta mannawa Shatu wayar a kunne ta.
Kana ta sa hannunta ta kamo hannun Hibba suka fita babban falon.

Shi kuwa Sheykh Jabeer shiru yayi tsaye gaban dreesing mirror, yana kallon
gemunshi.
A hankali yake jiyo sautin sauƙar numfashin can ƙasa-ƙasa, ɗis ɗas haka yaji ƙasan
zuciyarshi na harbawa.

Ita kuwa shiru tayi tanajin sautin tasbihi da yakeyi can ƙasan-ƙasan maƙoshinsa,
Lips ɗin shi na motsawa a hankali suna fidda sautin can ƙasa.
Jin shirun yayi yawane yasa a hankali ta buɗe bakinta tare da cewa.
"Assalamu alaikum".
Sai kuma tayi shiru ta kasa kunnen dan jiran amsarshi.
Gyara zamanta tayi tare da ƙara riƙe wayar, numfashi ta sauƙe a hankali.
Hakan yasa yaji sautin iskar.
Har ta cire tsammanin zai amsa sai kuma taji muryarshi can ƙasa yana cewa.
"Wa alaikissalam. Ashe kin iya sallama?".
Ya jefo mata tambayar a gajarce.
Cikin juya ido tace.
"Ba'a koya min da wuri bane!."
Shine mgnar da tayi niyar gaya mishi, sai kuma tayi mgnar a zuci, ta danne abun.
Sabida tana son ta nemi al'farman addu'o'in a kaba, aka yayunta da suka bace,
shiyasa cikin sanyi tace.
"Eh, Ummi ta koya min".
Shiru yayi kamar bai jitaba,
ita kuwa a hankali tace.
"Ina kwana".
Kanshi ya ɗan kalla a madubi tare da cewa.
"To Kifin rijiya su nan yanzu wunine".
Cikin sanyi da sassauta Muryar son isar da buƙatar ta tace.
"To ina wuni".
"Alhamdulillah".
Ya bata amsa.

Miƙewa tsaye tayi ta nufi bedroom ɗinta.


Tare da cewa.

"Ya ibada?".

"Alhamdulillah". ya kuma cewa.


"Har ya kai hannunshi zai janye wayar sai kuma ya tsaya jin tana cewa.
"Uhmm, Ayyah Yah Sheykh..".
Sai kuma tayi shiru. Cikin saurin jin an kira salla murya a nitse yace.
"Uhumm Ayyah, me ɗin?".

Da sauri tace.
"Dama.. dama!!...".
Gajeren tsaki yaja tare da cewa.
"Sauri nakeyi zan tafi masallaci, kada kisa na rasa damata".
Cikin rauni da muryar dake nuna cewa tana zubda ƙwalla tace.
"Ayyah dan Allah da Manzonsa.
In kaje kayi min addu'a a harami mana".
Juyowa yayi yana kallon Haroon da Ya Hashim da suka shigo yanzu alamun kiranshi
zasuyi.
Cikin wata iriyar murya a hankali yace.
"Addu'ar me zan miki?".
Murya na rawa tace.
"Allah ya dawo min dasu Yayana lfy, ya kare minsu a duk inda suke, ya baiyana
sucikin gaggawa".
Cikin rashin fahimtar zancen nata yace.
"To zan miki saboda Allah da Manzonsa da kikace".
Cikin jin daɗi tace.
"Ngd matuƙa Allah ya biya maka buƙatunka."
Wani irin sassanyan numfashi ya sauƙe tare da lumshe ido a hankali yace.
"Amin ya rabbil izzati, kema kuma kiyita addu'a ki dage da ambaton Allah zai cika
mana dukkan burinmu".
Yana faɗin haka ya katse kiran.

Ita kuma murmushi tayi tare da share hawayenta.


Cikin sanyi tace.
"Ya Allah ka dubemu da idon rahama".
Hibba dake shigowane tace.
"Amin Amin."

Daga nan suka fito falo suka kama sabgoginsu.

A kwana a tashi asarar mai rai.


Yau da gobe kayan Allah.
Kamar yau aka kama azumi gashi yau an kai azumi na ashirin da tara.
Wanda ake tsammanin tsalla gobe ko jibi.

Irinsu Hibba duk sunfi fatan wata ta dawo yau.

Gaba ɗaya wunin yau aiki Ummi da Shatu da Saratu suka wuni yi, wanda aikin salla
ne.
Zabbin da Jalal ya kawo bisa umarnin Hammansun.
Da kuma kajin da Lamiɗo yasa aka rabawa al'ummar masarautar Joɗa.
Ko wani Side in dai akwai mace kaji goma ake kaiwa.
Da tarin kayan miya komi da komi, wanda shi cikin lambun masarautar ake cirewa.
Kajin kuma daga gidan Gidan gonar MJ aka kawo, kana zabbin da aka kawo manyan
sashin Masarautar Joɗa ma daga gidan gonar MJ aka kwasosu. Haka ƙoyayen kaji.
Duk an rarraba ko ina.
kuma duk saida aka yanka su aka gyarasu aka rarrabusu, dan haka aiki kawai aka fara
babu kama hannun yaro.
Hadimai da bayi sunata aiki.

Duk sauran ɗinku nan suma sun dawo.

Kasan cewar kusan a kitchen ɗin suka wuni ne, yasa Shatu ta ɗauki zabbi uku tun da
azahar tayi musu gyara na musamman.
Hibba kuwa tana Side ɗin Aunty Juwairiyya anayi mata zanen lalle.

Akan sai dare za'ayiwa Shatu shiyasa taketa kimtsa aiyu kanta da wuri.
Dama sunje da sassafe an wonke musu kai an gyara musu.

Ummi kuwa tayi lallenta na gargajiya tana kwance a falo.


Hakane yasa Shatu ta kira Gimbiya Aminatu.
Cikin wasa tace.
"Gimbiya a ƙaro min mai taya aiki yau Ummi na tasa lalle, Hibba ma tana can ana
zana mata, nida Sara ce kaɗai a kitchen."
Dariya Gimbiya Aminatu tayi tare da cewa.
"To Sayyadar Sheykh bari Larai tazo".
Cikin jin daɗi tace.
"To Gimbiyar Lamiɗo".
Dariya sukayi duka kana sukayi sallama.

Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa.


"Tace zata turo Larai, Ummi ta iya aiki ko?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Sosai ma kuwa".
Kai ta gyaɗa alamun gamsuwa kana ta miƙa wa Ummi wayarta tare da cewa.
"Ummi sai mun nitsu ki bani number Gimbiya Aminatu".
To tace kana ta koma kitchen ɗin.

Wanke zabbin tayi fes tare da ɗan matsa lemun tsami kaɗan a ciki.
Kana ƙara lallaɓeshi.
A tukunyar ƙirar ƙasar Cameroon ta zubasu.
Kana tasa al'basa, Curry, Maggi, kanamfari, citta, tafarnuwa kaɗan, da gishiri ɗan
ƙanƙani.
Ta rufe tukunyar da zabbin uku suka cikashi.

Bisa gas ta ɗaurashi kana tasa wutan dai-dai.

Saratu kuwa sa sauran tayi a babbar tukunta tasa kayan ƙamshi da ɗanɗano.
Sannan ta ɗaura.

Dai-dai lokacin Larai ta shigo.


Bayan sun gaisa ne, ta ɗauki markaɗen waken ƙosan da zasuyi na kaiwa masallaci.

Da markaɗen tattasan da taruhu da al'basan.

Ita kuwa Shatu yau kunun basise ta dama mai kyau, ta cika kulolin.
Kana
Ta daura ruwan tea
Yana tafasa ta ɗura a flaks.

Duk wannan zabbin sunata sulaluwa suna bararraka sai wani irin masifeffen ƙamshi da
yake tashi.
Har yawunsu na tsinkewa.

Fruits ta ɗebo a Fridge ta gyarasu ta shiryasu a tray biyu shiri mai kyau.
Kana ta medasu cikin ƙaramin Fridge ɗin data kashe dan sanyi su ya daidaita.

Larai na dawowa, suka fara suya.

Ita kuma ƙullun waken kaɗan ta ɗiba.

Kana tasa dafaffan ƙan data ɓare.


Da al'basan da kifin data tafasa ta murmusa a cikin ƙullun ta sa mai da Maggi curry
da dai sauran kayan haɗi ta kulla alala.
Ta ɗaura a gefen tukunyar zabbin.

A ƙalla awa ɗaya zabbin na ɓararraka kana tazo.


Tasa jajjagen taruhu da al'basan,
A ciki.
Sai ta ɗan tarfa soyayyan mai kaɗan a ciki ganin kamar man jikin zabbin bazai mata
yadda takeso ba.
Kayan ɗanɗano ta kuma sawa, da yankekken al'basa mai yawa ta zuwa a ciki.
Kana ta maida marfin tukunyar ta rufe. A hankali danderun zabbin ya fara taushi
yana lugub cewa,
Ƙasusuwan suna saɓulewa daga jikin naman.

Tuni su Sara kuma sun gama soya ƙosan, nan ta ciccika kulolin da za'a fidda kana ta
ɗiba musu nasu, daban.
Sannan suka tattare mata wurin suka tafi sabida ita ta kusa gama nata aikin.

Koda alalan ya nuna ta kwashe tasa a kuloli biyu.


Sai kuma ƙaramar kula daya.

Ya rage zabbin ne kawai a wuta.


Rage wutan tayi sosai yadda zasuke jin wutar na ratsasu da kyau.

Tattare wurin tayi ta kimtsa komai.


Kana ta fito falo.
Ƙarfe biyar da rabi.
Tace lokacin data zauna ta ɗauki wayarta Ummi kuwa na cire lallenta.
Ya kuwa yi baƙi yayi kyau.
Hibba ce ta shigo cikin
Langwaɓe kai tace.
"Aunty Shatu me ake dafa mana yau tun waje can ake jiyo ƙamshin na fitowa a
gidanki".
Cikin gajiya tace.
"Tuwone miyar taushe".
Cikin zumbura baki tace.
"Tab wlh bazanci ba, inyi azumi a bani tuwo ta yaya zan haɗiyeshi, yaseen zan koma
wurin Aunty Juwairiyya nagama tayi awara, ƙamshin gidanki na jiyo na gudo".
Dariya Ummi tayi tare da cewa.
"Hibba dai cokali a saki a daɗi ko?".
Murmushi sukayi dukansu kana suka konta
A kan kujerun.
Ganin Ummi ta miƙene yasa Shatu cewa.
"Yauwa Ummi duba mana kitchen ɗin kiga ko Danderun yayi".
To tace kana ta shiga ta duba.
Sannan ta fito tare da cewa.
"Yayi sosaima, kai gskyar Hibba nima da bana jin ƙamshi yau naji ƙamshin girkin.
Jeki sauƙe kawai kiyi wonka kuzo ki huta kafin a kira salla".
To tace kana.
Ta miƙa taje ta sauƙe. Binta a baya Hibba tayi tare da cewa.
"Wai Aunty Shatu bakuga lallena bane banji kunce yayi kyau ba".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kayya Hibba ai yanzu kam idanunmu basa gani".
Ta ƙarshe mgnar tana sauƙe tukunyar,
Kana ta ɗauki Foodflaks guda uku biyu manya ɗaya karami.
Gaba ɗaya ƙasusuwan sun saɓule.
Romon yayi kaurin diddigin nama.
Rabin zabuwa ta sawa Sara da Larai a ƙaramar kular.
Kana tasawa Gimbiya Aminatu gudar.
Su kuma tasa musu ɗaya da rabin a kularsu.
Kular datasa alala data kosai ta jere a babban tray'n.
Da tray'n fruits, ɗin a gefe.
sannan da flaks ɗin kunu ta bawa Hibba tare da cewa.
"Ki kawai Gimbiya Aminatu.
Na ƙaramar kular nasu Sara ne".
Amsa tayi kana ta fita.

A can ta samu Ya Jafar shida Lamiɗo bisa alamu yau tare zasuyi buɗa baki.

Ita kuwa Shatu Hibba na fita.


Ta sauƙe babbar tukunyar tafashen naman kajin ta ajiye gefe.
Dama zabbin duk a freezer'n suka sasu.

Ɗan buɗe bakin tukunyar tayi yadda zasu sha iska su kama jikinsu. Jajjageggen
Attaruhu da al'basan kuma ta sashi a Fridge.

Kana ta fito da komai ta jere musu a dinning table.

Sannan ta wuce ɗakinta. Wonka tayi da ruwan sanyi duk da bata son sanyi
To amman duk jikinta huruwa yake tamkar wuta.
Haka yasa tayi da ruwan sanyi.
Tana fitowa ko mai bata shafa ba.
Wata atamta mai taushi riga da zani, ɗinkin Borno sitayel
yayi masifar yi mata kyau.
Ɗan kwalin ta ɗaura a sauƙaƙe sabida duk jikinta rawan yunwa da azaba yakeyi.

Cikin falon ta fito nan ta samu Hibba ta dawo.


Jalal, Jamil, suma sun zo.
Ummi ma ta fito da alamun tayi wonka.

Tana isa ana kiran salla.


Nan sukayi buɗe baki da fruits kawai sai kunun suka ɗansha, kana kowa yaje yayi
sallan.
Sannan sukazo sukaci sauran kayan kwalamarsun.

Suna tashi sukayi sallan isha.


Zuwa lokacin kuma anata raɗe-raɗin ba'aga wata bafa.
Wannan lbrin shiya tada hankalin Hibba da sauran mutane irinta, a gefe harma da
Jamil
Sabida azumi ɗayan nan da za'a ƙara wasu ganinshi suke kamar shekara ɗaya za'ayi
ana azumin sai kaji anata gunaguni da cewa wai anƙi a faɗa ne.
Shatu kuwa murna tayi dan ita bata samu tayi lalle ba.
haka yasa gobe zata ƙarisa aikinta a nitse.
Jin an kira salla za'ayi Asham ne yasa Hibba zubda hawaye tare da cewa.
"Wlh zan kira Umaymah da Hamma Jabeer ina dai saudi sunyi salla Ni babu ruwana
salla zanyi".
Ta ƙarishe mgnar tana kiran layin Umaymah yanata ringin ba'a ɗagawa.
Hamma Jabeer kuwa data kira baya shiga ma gaba ɗaya. Haroon kuma shima yana shiga
baya ɗagawa.
Dariya Shatu tayi tare da kunna tv tace.
"kalli Hibba suma asham sukeyi".
Da sauri tace.
"A a kam Isha'i ne".
Ganinfa da gaske Hibba keyi yasa suka sherata sukaje sukayi asham kana suka dawo.
Kitchen suka shiga, soya kajin sukayi suya mai kyau kana suka ajiye.
A gefe.
Jalal ne ya leƙo kitchen yace.
"Ummi azumi talatin zamuyi bana".
Dariya tayi tare da cewa.
"Aiko gacan Hibba nata fushi."
Shigowa yayi plate ya ɗauka ya miƙawa Shatu tare da cewa.
"Aunty a samin nan".
Amsa tayi tare da saka mishi soyayyen naman kazan.
Dakekken yaji ta saminshi a gefen
Fridge ya buɗe ya ɗauki Du-du tare da cewa.
"Wannan fa yaushe aka fara kawoshi".
Ummi ce ta kalleshi tare da cewa.
"Naga Shatu tafi sonshi ne yasa nace akawoshi".
Kai ya gyaɗa tare da cewa.
"To nima bari in taɓa shi".
Nan ya fita falon.

Su kuwa suka ƙarisa aikin.


Suna ƙoƙarin fitowa ne.
Jamil ya leƙo tare da cewa.
"To yau kuma meye za'ayi mana na sahur ne".
Jalal dake bayanshi ne yace.
"Yo azumi ɗaya ai ko tazarce zamuyi".
Hararan Jalal yayi tare da cewa.
"Hege daka ci kaji kayi tak ba, mutun kamar kura".
Murmushi Jalal yayi tare da cewa.
"Yes naci in kuma ƙara".
Hararanshi Jamil yayi tare da cewa.
"Mutun sai son nama kamar ba bafulatani ba sai kace babarbare".
Da sauri
Jalal yace.
"Yo dama aini Arbabarbare ne".
Dariya Ummi tayi,
Ita kuwa Shatu Jalal ta kalla tare da cewa.
"Me zan dafa mana to?".
Tsaki ya ɗan ja tare da cewa.
"Kiyi mana Coucous da miyar hanta kawai".
To tace kana ta juya ta fara aiyin.
Cikin sa'a ɗaya ta gama ta fito.

A falo ta samesu suna.


Waya da Sheykh yana ce musu kadafa suyi sakaci suyi sallan, dan babu lbrin ganin
wata.

Hakan dai suka haƙura.


Bayan yaga waya da sune.
Umaymah ta shigo ta sameshi zaune yanacin inabi.
Gefenshi ta zauna da wata jakar.
Miƙa mishi tayi tare da cewa.
"Kace ranar salla da safe in an sauƙo idi dai zaku tafi ko?".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"Haka dai Wannan tsohon Galadiman ya buwayeni da zancen komawar".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Abbanka ma yace min ranar sallan zaku tafi".
Kai ya gyaɗa.
Ita kuwa gyara zama tayi tare da cewa.
"Tsarabar me ka sayawa Shatu da ƴar ɗakinta Hibba".
Da sauri ya kalleta tare da cewa.
"Umaymah tsaraba kuma.
"Yo tsarabar me zanyi sai kace wani sabon zuwa, Ni ibada nazo yi ba tsaraba ba".
Jakar ta nuna mishi tare da cewa.
"To ni kam ga tsaraba ka kai musu, wannan na Shatune Hibba gobe zan dawo da nata.
Kai kuma in kaso ka koma hannu rabbana".
Kanshi ya sunkuyar kamar baijiba.
Sai kuma tace.
"Jazrah tace in gaidaka, wai tunda kazo bata ganka ba".
Cikin sanyi yace.
"Yoh dama ya zanyi in bari ta ganni yarinya sai kallon masifa".
Miƙewa Umaymah tayi ta fita.
Tana fita Haroon da Ya Hashim suka shigo. Nan suka ɗanyi hira kafin suka tashi suka
tafi masallacin dan shabiyu ta kusa a fara tuhajjudin.

Nan suka tafi.


Washe gari aka tashi da azumi na talatin.
Allah cikin ikonshi aka kaishi lfy.
Watan Shawwal ya baiyana Ramadan ya tafi kuma sai mai nisan kwana.

Shatu kuwa a wunin ranar Yar aikin Aunty Juwairiyya Sato, ta zana mata jan lalle
mai ɗan karen kyau.

Koda ta dawo kuma jarakuna madarar shanu data gayawa Gimbiya Aminatu tanaso
Aka kawo mata ta tafasashi kana tasashi a manyan kware da ƙananan kwore da kyawawan
robobi tasa tsami kaɗan a ko wanne kwarya da roba.
Ta rufesh ta jerasu a Fridge a ƙalla sunfi kore goma madaidaitan ƙananan sun kai
kore takwas sai robobin su kuma sun kai goma suma.

Bayan sallan magriba ansha ruwa anyi nak.


Hibba sai tsalle da farin ciki da kiraye-kirayen ƙawaye da yan uwa da abokai sai
tsiya Jamil ke mata.

Bayan sun gama shirya komai na aikin da zasuyi gobene.


Suna zaune a falo Ummi ta kalli Jamil tare da cewa.
"Jamil wai sai yaushe zaka share Side ɗin Sheykh ne, munyi waya da Umaymah ɗazu
tace min gobe fa zasu dawo.
Anayi sallan idi a can zasu taso".
Gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"To naga mutun ga matarsa ace Ni in mishi shara".
Ko inda suke Shatu bata kalla ba.
Ummi kuwa jingina tayi da jikin kujera tace.
"Ai bazata san ƙaidar yadda yakeson a gyara mishi ɗakinshi ba.
Dole sai ka nuna mata."
Cikin gamsuwa da hakan yace.
"To ba matsala sai gobe da sasafe mu hau kan aikin abinda ɗakin ba wani ƙura da
tarukucene da shiba".
Eh hakane Ummi tace tare da kallon Shatu tace.
"Gobe in Allah ya kaimu Shatu ku gyara mishi ɗakin nashi".
"To Allah ya kaimu. tace ba tare da ta kalli inda sukeba.
A can ƙasa mai tsarki kuwa.
Ana idar da sallan isha'i da yawa suka fara ɗawafi.
A cikinsu kuwa harda Sheykh Jabeer da mai sunanshi kana da Haroon
A nitse bisa tsari suke ɗawafin sunje ƙafa biyu ana uku sun isa dai-dai. Maƙama
Ibrahim.
Sheykh Jabeer ya juyo kanshi ya kalli gefen damanshi da sauri cikin tarin mamaki
al'ajabin Fuskar mutumin da ya ga ya wulgawa a idonshi...!

Littafin GARKUWA na kuɗine idan kina buƙatar saya ga number 09097853276 katin mtn
na ɗari uku. Normal group in kuma special Group kikeso 1k zakiyi min TRANSFER ta ac
ɗina 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa.

By
*GARKUWAR FULANI*
[3/6, 9:39 PM] +234 803 964 6842: Cikin sassarfa bisa tsarin addinin yaci gaba da
ɗawafin.
Yana mai bin bayan tawagar mutanen da yaga fuskar wannan mutumin a cikinsu.
Idonshi yaketa karkasawa amman ina ya kasa sake ganinshi.
Zuciyarshi nike da mamaki.
Haka yaci gaba da ɗawafin.
Saida sukayi. Kana suka fito.
A hanyarsu ta komawa gidane ya haɗu dasu Jannart da Jazrah da Umaymah da Sitti da
kuma Aunty Hafsat ƙanwar Umaymah dake ƙasar Masco.
nan Aunty Hafsat tayi ta sayan kayan tsaraba tana bawa Sheykh wai a kaiwa surkarta.
Dan dole ya amsa sai kuma Aunty Rahma ƴar autar Sitti itama a gaban Aunty Hafsat ta
girma.
Kuma sa'ar Sheykh Jabeer ce shiyasa akwai yar tsama a tsakaninsu.
Cikin hausarsu data fara basu wuya tace.
"Ba dai kayi auren sirri ba, in sha Allah zanzo zamuzo auren Haroon zamuga amaryar,
inga surkar tawa ya take"

Taɓe baki yayi tare da cewa.


"Ke tafi daga nan da Allah ki bar manya suyi mgna ba irinki ba".
Murmushi Umaymah da Aunty Hafsat sukayi dan sun san tsamarsu.
Kuma suna masifar shiri.
Ammi suke kiranta ita Aunty Rahman.

Jazrah kuwa hakanan take jin daɗi in ta ganshi.


Shiyasa taketa murmushi.
Haroon kuwa girarshi ya ɗagawa Jannart tare da cewa.
"Wai auren ya kusa ko?".
Cikin jin kunyar Umaymah tace.
"Ban saniba."
Haka dai sukaci gaba da tafiya.

Washe gari da safiya.


Duk kan al'amur musulmai na duniya suna farin ciki da ranar salla.
Manya da yara tsoffi maza da mata duk anata shirin zuwa idi. A dukkan ƙasashen
duniya a ko wani saƙon da suke da musulmai.

Hakace ta kasance a ƙasashen Afrika ma.


Wanda ciki ƙasar Nigeria yake.
Tun daga idar da sallan asuba.
Saratu da Larai sukazo.
Nan suka samu Ummi da Shatu suna kitchen.
Its Ummi fura take kirɓawa mai ɗan karen laushi da ƙamshi yaji sugar.
Ita kuwa Shatu dakkeren Couscous tayi, dambu inji hausawa.
Bayan sun gamane suka killace shi gefe.

Kana ita Shatu. Ta haɗa kajin nan tayi Pepper Checken mai ɗan karen kyau yaji
jajjagen taruhu da al'basa mai yawa ga kayan ɗan-ɗano dana ƙamshi sunji komai yayi
maɗau.
Su Sara kuwa robobi ta miƙo musu, suka rinƙa mulmula gumbar nan manya manyan
mulmulellen masu kyau sai sheƙi da ƙamshi gumbar keyi, dakkeren kuma a robobi Ummi
ta rinƙa zubasu.
Hibba ce data shigo tare da kuloli a hannunta tace.
"Wow Aunty Shatu lallai yau masarautar Joɗa zata amsa sunanta masarautar Fulɓe
zata kuma gane an auro mata cikekkiyar ba fulata, gsky tsarin yayi kyau".
Cikin jin daɗi Ummi tace.
"Gsky nima naji daɗin wannan abu.
Dama ace ko wanne yare ranar salla tayi abincin da yarenta keyi ta rabawa maƙota.
Hakan zaisa asan cimar juna, kuma yasa aci abincin salla da marmari, amman kayan
haushi duk sai a tafi kan shinkafa taliya masa, da dai ire-iresu.
Su kuma akeci kullum".
Murmushi Shatu tayi tare da cewa.
"Ha Ummi ai yanzuma sai nayiwa su Jalal koda dafadukan taliyace, nasan zasuce
wannan ai sai mu".
Da sauri Hibba tace.
"Tab wlh Aunty Shatu karkiyi komai, kinga yanzuma an kawo abincin gidan Barrister
Kamal.
Ga kuma na gidan Aunty Juwairiyya.
Sannan kuma Gimbiya Aminatu ma zata aiko".
Cikin sauri tace.
"Allah ko Ummi mu huta kawai kenan?".
Da sauri tace sosaima.
Dan duk yawanci sai an kawo abinci nan wai tunda ke baƙuwace, wannan karamawar
masarautar Joɗa akan bago.
Kuma koda kin dade ana aikawa juna abincin salla part 2 part".
Ajiyan zuciya ta sauƙe tare da cewa.
"Shike nan mu haɗa wannan a kai ko wanne sashin".
Ta ƙarishe mgnar tana rufe ƙatuwar Foodflaks ɗin da ta juye Pepper Checken ɗin.
Bayan ta ɗebawa sashin Ya Jafar da kuma Lamiɗo da Hajia Mama.

Ƙananan robobin da a ƙalla suma nonon dake cikinsu zai kai kwanon sha ɗaya da rabi
ta fara firfitarwa.
Kana ta fito da madaidatan ƙoren da zasuci kwanon sha biyu da kaɗan sai manyan da
sukaci kwanon sha uku da rabi-rabi.
A hankali ta jerasu kan table ɗin dake tsakiyar kitchen ɗin.
A hankali ta buɗe ƙwaryar forko dake gabanta.
Wani irin murmushi tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah kunɗirmo ya konta yayi bacci yayi kyau".
Leƙowa Ummi tayi tare da buɗe na kusa da ita.
Nonon yana konce yayi lib ya daskare yayi fari ƙal-ƙal sai alamun maiƙon man nonon
da yayi ɗan yellow-yellow kaɗan.
A hankali suka fara bubbuɗe fefeyayen tsakan zaren taburma da aka rufe ƙoren dashi.
Gaba ɗaya duk sun konta sunyi kyai
Yan madaidai robibin da akasa take ɗauka na fura ɗaya na dakkere ɗaya sai na sugar
ɗaya kana da ludayin duma. Sai ta jerasu kan fefeyayen da robobin.
Ganin haka yasa Saratu da Laraima suka matso suna taya.
Har saida ta jerasu kab. Gwanin sha'awa.
Manyan ƙore biyu ta maida cikin Fridge.
Kana ta irga sauran tsakanin manya da ƙananan
Ƙoren da robobin su
Talatin da tara
Juyowa tayi ta kalli Ummi tare da cewa.
"To Ummi gashi mun gama ki gaya musu duk inda zasu kai.
Zasu isar ko".
Cikin jin daɗi Ummi tace sosaima kuwa harma da sashin bayi zai isa sabida part-part
talatin garemu a cikin masarautar Joɗa.
Sai sashin bayi part takwas.
Cikin jin gamsuwa da tsarin Shatu tace.
"Yanzu a kai ƙore biyu sashin Lamiɗo kana duk manyan iyayen Sheykh akai musu kwarya
ɗaɗɗaya, sai sashin Ya Jafar kinga manyan ƙoren sun ƙare sai abin na tsakiyan a kai
sauran sashin ƴaƴansu robobin kuma akai sashin bayi".

Haka kuwa akayi su Sara suka fara rabawa.


Ita kuwa Ummi ita da kanta da Hibba suka kai na sashin Gimbiya Aminatu.
Kana suka dawo da kuloli har uku na abincin sallan da Gimbiya Aminatu ta basu.
Kana ɗaya daga cikin tace na Sheykh ne a ajiye mishi.
Koda suka dawo samu sukayi su Saratu sun gama rabawa kab.
Kamar yadda Ummi ta tsara.
Har sun tattare ko ina sun gyara sun share sun goge sun tafi.
Zuwa lokacin kuwa gaba ɗaya kan dinning table ɗinsu cike yake da Foodflaks iri da
kala abinci kala-kala.
Wani irin kallo Shatu tayiwa kulolin kana tayi murmushin da ita kaɗai tasan
ma'anarsa ta juya ta nufi tsakiyar falon.

A gaggauce sukayi wonka kowa yayi shirin idi.


Ƙarfe tara saura kwata duk suka fito falo.
Tuni lokacin kuma liman har ya fara huɗuba.
Su Jalal, Jamil Ya Jafar suna tsaye cikin shiga ta al'farma.
Karon forko dataga manyan kaya a jikin Jalal.
Sai kamanninshi da Hamma Jabeer ɗin nasu ya fito sak-sak kamar an tsaga kara hatta
rashin yawan dariyarsu iri ɗaya ne.
Sai dai shi Sheykh ko yaushe zakaga lips ɗinshi na motsawa yana tasbihi saɓanin
Jalal da zaka ganshi baki a tsuke.

Hibba ce ta fito cikin tarin farin ciki da son Jalal yayi murmushi tare da cewa.
"Masha Allah ya Jalal kayi kyau kafisu duka".
Ya Jafar dake karatu kamar ko yaushene ya kalli Shatu da Hibba da sukayi shigar
atampa iri ɗaya da manyan hijabai har ƙasa ga sallaya da carbi a hannunsu sunyi
matuƙar kyau, murmushi yayi musu kana ya juya yayi gaba.
Jamil ne yace.
"Aunty Shatu sai mun dawo, in munci abinci sai mu sharewa.
Oga, Dr, Garkuwa, Malam, akarmakallahu, Sheykh, mijin Sayyada, ɗin ɗakinshi".
Dariya sukayi dukansu yadda ya jero masa sunayen nashi.
Ummi dake cikin shiga ta al'farma ta miƙa tare da cewa mu tafi.

Suna fita suka rufe ƙofar.

Suka tafi masallacin. Masarautar Joɗa ɗan yin sallan idi.


Suna fita su mata sukayi gefen mata su kuwa maza sukayi gefen maza.

Bayan an idar da sallane kuma sai suka zagaya suka shigo ta asalin ƙofar sukayi
yadda sunna ta koyar.

Suna dawowa kuwa a falo suka zube nan sukaci suka sha sukayi
haniƙan.

A dai-dai lokacin kuma su Sheykh dama sauran al'ummar Annabi duk an sauƙo sallan
idi.
Suna ɗawafin ban kwana.
Sosai Sheykh ke baza ido ko zai sake ganin wancan mutumin amman ina hakan bai
samuba.

Koda suka fito daga ɗawafin ban kwana.


Kai tsaye gidan Sheykh Abdulkareem suka wuce.
Nan yayi musu addu'o'in komawa lfy.
Kusan duk baƙin gidan a ranar suka bar gidan.
Da su Aunty Hafsat ma ranar suka juya Masco hakama Ibrahim.
Koda suka iso Airport kowa da inda ya nufa.
A nan Ibrahim ya ruggume Sheykh tare da ɗan dukan bayanshi yace.
"In Sha Allah Auren Haroon dani za'ayi".
Shima Sheykh ruggumeshi yayi gam-gam tare da cewa.
"Allah yasa, ina kewar rashinka a ƙasar mu".
Aunty Rahma ne tace.
"Kai jirgifa ba jiranku zaiba oga Sheykh".
Sakin juna sukayi kana kowa ya nufi inda jirgin ƙasarsa yake.

Bayan duk matafiya sun shiga, jirgin ƙasar Nigeria wanda zai sauƙa jihar Ɓadamaya.

A hankali ya zauna.
Ya Hashim na gefenshi.
Kasan cewar yana kusa da window ne, ya ɗan juya yana kallon mutanen daketa hada-
hadar nufar inda jiragan ƙasar su jihohinsu suke.
Can cikin wasu ayarin mutane maza da mata ya hango wannan fuskar da ya gani.
Sun nufi can ciki suna tafiya yankin da jiragen ƙasar Cameroon suke.
Cikin tarin mamaki ya bishi da kallo tabbas badon jirginsu ya fara ƙugin tashiba da
ya fita yaje ya tabbatar da fuskar dattijon da yake hangowa.

A haka dai suka ɓacewa ganinshi.


Kana jirginsu ya ɗaga zuwa ƙasarmu ta haihuwa.

Ana gida Nigeria kuwa cikin Jihar Ɓadamaya a Masarautar Joɗa.


Zaune suke a falon.
Shatu na waya da Junaidu nan yake ce mata,
Sun samu sauƙi dukansu.
Ance za'a sallamesu bayan salla.
Kuma harda ɗinkunan kayan salla akayi musu.

Bayan sun gama waya da shine ta kira Rafi'a.


Nan suka gaisa har ta bawa Ummi su gaisa.
Bayan ta bawa Ummi wayarne.
Jamil ya ɗan kalli agogon hannunshi a hankali ya miƙe tare da kallon Shatu yace.
"Muje mu gyara Side din boss kar ya dawo ya samu da datti".
Kai ta gyaɗa mishi kana ta amshi wayarta da Ummi ke miƙa mata.
tare da ce mata.
"Eh dan Allah Shatu tashi maza-maza kuje share wurin da kyau".
A hankali ta miƙe tare da cewa.
"To."
Hibba ce ta bisu a baya.
Jamil na gaba ita Shatu'n tana tsakiya.
Hibba na bayanta.
A haka suka shigo falon. Da komai na ciki yake fes-fes babu wani daddi ko ƙura ko
hargitsewa, sabida an share falon safiyar yau, sai ƙamshi da sanyi ke tashi.

A hankali Jamil ya ɗan sa hannunshi tsakanin ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da


jeren duwatsu masu sheƙin Daimond dake matsayin labulen Dinning area ɗin shi.
Ita dai Shatu ido ta zuba mushi,
ganin ya zaro key ɗin a cikinsu.
Ƙofar bedroom ɗin ya nufa tare da cewa.
"Muje."
To sukace kana suka biyo bayanshi.
Tana nazarin wurin da suke ajiye key ɗin.
Key ɗin ya saka cikin raminshi tare da murzawa.

Da sauri Shatu ta rumtse idanunta.


A hankali take jin zuciyarta na harbawa da sauri-sauri.
Shi kuwa Jamil tura ƙofar yayi bayan ya murɗa key ɗin ya buɗe.
Wani irin masifeffen harbawa da azaban ƙarfi zuciyar Shatu tayi.

Kutsa kai cikin Jamil yayi.


Tare dasa hannunshi jikin ginin a hankali ya kunna wutan ɗakin hasken ya gauraye ko
ina,
jikin window ya wuce ya yaye labulen tare da buɗeglass ɗin.
Iskam cikin Garden ɗin dake bayan window wanda ɗawisu yake ciki.
Ya buso ɗakin.

Juyowa yayi ya kalli Shatu da ke tsaye bakin ƙofar.


"Ku shigo, in nuna miki yadda zakiyi mishi".
A hankali Hibba ta ratsa gefenta tare da cewa.
"Aunty Shatu mushiga".
Ido ta buɗe a hankali tare da bin bayan Hibba da kallo.
Kana ta ɗaga ƙafarta da kyar ta.
Taka cikin ɗakin, wani irin azabebben sarawa kanta yayi tamkar ana buga mata guduma
a tsakiyar kan.
Cikin rawan ƙafa ta ɗaga ƙafafuwan ta,
Tayi taku huɗu zuwa biyar.
Ta kusa isa tsakiyar ɗakin.
Kenan.
Wani irin jujjuyawa taga kanta nayi.
Wasu irin ababe masu ban tsoro ta fara gani suna gilmawa cikin ƙwayar idanunta,
shiyasa taketa jujjuya kanta.
Ta kalli gabas ta kalli yamma ta kalli kudu ta kalli arewa.
Hibba ce ta juyo tana kallonta jin Jamil nata mgna bata bashi amsaba.
Cikin sauri ta matso kusa da ita ganin yadda taketa jujjuya kai, ga idanunta da
suka juye suka zama kamar harari garke, kana sai Rollin ball eyes ɗin ta take da
sauri-sauri.
Cikin Mamaki Hibba tace.
"Aunty Shatu! Aunty Shatu!!".
Shiru ba amsa hakane yasa.
Jamil juyo kanshi ya kalli inda suke, da sauri ya juyo gaba ɗaya jikinshi ganin.
Wani irin karkarwa da jikin Shatu keyi.
Hibba kuwa da ƙarfi cikin tsoro tace.
"Aunty Shatu lfy kuwa?".
Ita kuwa Shatu, zuwa yanzu bata jinsu bata kuma fahimtar me suke faɗa hankalinta ya
juye.

Cikin wani irin layi da rawan jiki tamkar mazari ta nufi tsakiyar ɗakin.

A nan ta tsaya gis gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.


Cikin tsananin tsoro da firgita.
"Hibba ta juya a guje tana cewa.
"Wayyo Ummi! Ummi!! Ummi!!! Kizo zakiga yadda Aunty Shatu keyi."
Ummi dake falo ita da Aunty Juwairiyya,
Kamar daga sama suke jiyo muryar Hibba tana rabka musu kira cikin firgici da
razani.
Haka yasa Ummi da Aunty Juwairiyya miƙewa da sauri suka nufi corridor'n da suke
jiyo muryar Hibba na fitowa.
Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar falon.
Cikin sauri Ummi ta ture Hibba ta wuce da gudu ta nufi cikin ɗakin.
Sabida jiyo muryar Jamil na cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahuwani'imal wakil. Ummi! Ummi!!
Kizoooo".
Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka shigo.
"Dai-dai lokacin kuma rawan da jikin Shatu keyi ya tsananta.
Wani irin kuka tasa tare da tafiya ƙasa luuu zata faɗi

Kusan a tare Ummi da Aunty Juwairiyya suka tarota.


Bisa jikin Ummi ta faɗi hakan yasa itama Ummi tayi ƙasa ta zauna.

Babu abinda suke maimaitawa sai innalillahi wa innailaihi rajiun.


A kiɗime cikin tsananin gigita Jamil yace.
"Subahanallahi Ummi ta sumafa".
Jiki na rawa Aunty Juwairiyya ta juya da gudu babban falon ta fito tare da ɗauko
goran ruwan sanyi.
Kana ta juyo a da sassarfa ta nufi can.

Hibba kuwa a gigice take gayawa Jalal da Ya Jafar abinda ke faru.


Da sauri ya Jafar ya tashi ya nufi can.

Jalal kuwa ya zauna dan ya lura Hibba tayi masifar tsorita.

A ɗakin nashi kuwa,


Shiru ta lafe jikin Ummi kamar babu rai koda.
Ummi ta yayyafa mata ruwan sanyi a fuskarta, a banza saida ta kuma watsa mata a
karo na uku ne.
Kafin taja wani dogon numfashi cikin sanyi da tsoro Ummi tace.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ta sunkuyo kanta tana ɗan kiranta.
"Shatu! Shatu!! Shatu!!!".
Ba amsawa kuma bata buɗe ido ba,

A hankali ya Jafar ya zauna gefensu, karatun da yakeyi yaci gaba dayi.

Cikin sanyi ta buɗe idanunta.

Sai kuma ta yunƙura a hankali ta tashi zaune.


Da sauri Ummi ta zaro ido ganin yadda idanunta suka juye a murɗe.

Ita kuwa Shatu miƙewa tsaye tayi, cikin rawan sanyi da karkarwa, ta fara zagaya
ɗakin a hankali taje baki Bathroom nanma buɗe ƙofar tayi ta shiga.
Jim kaɗan ta fito.
Idanun suna yadda suke sai dai.
Yanzu hawayene keta shatata babu ƙaƙƙautawa.
A hankali tazo bakin gadon.
Sai kuma kawai sukaga ta faɗa kan gadon a sune!
Wannan shine tashin hankali da ba'a samishi rana.
Da gudu suka kumayi kanta, cikin firgici da tsananin tsoro Ummi ta ƙara yayyafa
mata ruwan.
Amman shiru, haka suka tsaya cirko-cirko, shi kuwa Ya Jafar sai gashi yana karatu
yana kuka kamar dai yadda yakeyi kafin a auro Shatu a masarautar Joɗa in Sheykh
baya nan.

Gaba ɗaya sun birkice sunma rasa me zasuyi.

Aunty Juwairiyya kuwa itama kuka ta farayi.


Jiyo kukanta da na Ya Jafar ne yasa, su Jalal da Hibba shigowa.
Ganin tana can yashe kan gado a sumene yasa Hibba ma kuka.
Cikin ƙarfin hali Jamil yace.
"Aunty Juwairiyya Hibba kada kuyi kuka, kuja hankalin mutane nan.
Gashi yau salla ba mamaki akwai mutane a cikin Garden."
Cikin tashin hankali Ummi tace.
"Bari inje in sanarwa Gimbiya Aminatu abinda ke faruwa, ta sanarwa Lamiɗo, sai in
biya in sanarwa Hajia Mama."
Da sauri Aunty Juwairiyya tace.
"Eh yafi kam".
Ta juya zata fita kenan sai sukaji tayi wani irin nakasheshen dogon numfashi mai
sassanyan sauti.
Da sauri Ummi ta juyo ta dawo jikin sanyi tace.
"Shatu! Shatu!! Shatu!!!".
Shiru babu amsa sai binsu da ido tayi ɗaya bayan ɗaya.
Ganin hakane Jamil ya matso.
Tofi ya farayi mata.

Ummi kuwa ci gaba da kiran sunanta tayi.


Cikin tsoro Hibba tace.
"Ummi kinga idonta ya koma dai-dai."
A tare sukace Alhamdulillah.
Sai kuma Ummi ta kuma kiranta.
"Shatu!".
A hankali tace.
"Na'am Ummi".
Sai kuma ta kalli inda take, kana ta juya ta kallesu baki ɗayansu, cikin mutuwar
jiki ta yunƙura ta tashi.
Murya a sanyaye tace.
"Jamil sharan kenan ka tsaya kanata kallona.
Gaya min ya za'ayi sharar".
Cikin sauƙe tagwayen numfarfashi suka kalli juna,
Cikin mamaki Jamil yace.
"No ki huta kawai my Aunty zan share".
Bata da ƙarfi a jikinta ko ta dage tace sai tayi sharar.
Bazata iyaba jikinta duk a mace.
Hakane yasa tace to.
Hannu ta miƙa Ummi tare da cewa.
"Ummi ɗan jamin hannuna mana".
To tace tare da kamo hannun.
Ta tsaida ita, cikin tafiyar sanɗa ta juya ta nufi hanyar fita.
Binta sukayi a baya gaba ɗayansu.

Jamil kuwa dube-dube yayi a cikin ɗakin kana.


Ya fara tattarewa da kimtsawa da sherawa, ya canza mishi beshit and blanket, da
rigunan pillows.
Kana ya goge ko ina fes
Sannan ya shiga bathroom ya wonke ya goge mishi.

Su kuwa suna biye da ita har falonta.


Ganin ta wuce bedroom ɗinta ne yasa Hibba da Juwairiyya suka tsaya.

Ita kuma Ummi tabi bayanta.

Ganin tana shiga ta hau gado ta kwanta ne a take sai bacci yasa Ummi ta juyo ta
fito.

Can babban falon suka koma suka zauna.


"Ikon Allah sai kallo wannan abu da ban tsoro da ban mamaki".
Ummi ta faɗa cikin al'hini.

Jiki a mace Aunty Juwairiyya tace.


"Sosai kam wannan al'amari ya firgitani".
Hibba dai sai zuru-zuru tayi da ido.

Nan sukayi ta mamakin wannan abin.

Jamil na fito shida Jalal suka tafi.

Shi kuwa Ya Jafar bayan matarsa yabi suka tafi.

Hibba kuwa da Ummi nan suka zauna.


Ummi ce ta kalli Hibba tare da cewa.
"Sai anjima zan kira Umaymah na sanar mata abinda ya faru".

Kai kawai Hibba ta kaɗan mata.

Ita kuwa Shatu baccin tayi mai nauyi sai kiran sallan azahar ne ya tasheta.

Su Sheykh Jabeer kuwa suna can sunata keta hazo.


Tafiya awa huɗu ne zai kawosu ƙasar mun.

A hankali ta buɗe idonta, miƙa tayi tare da yin salati.


Kana ta tashi zaune.
Bathroom ta shiga, wonka tayi da ruwan ɗumi.
Kana tayi al'wa tana fitowa.
Ta zura Hijabi tayi salla.
Bayan ta idarne, ta zauna gaban dreesing mirror.
Simple makeup tayiwa fuskarta.
Sannan ta sauya shiga, wani tattausan lace mai ɗan karen kyau da tsada tasaka
duguwar rigace tayi cib-cib da jikinta. Kasan cewarta kalar pink guava da ɗigo-
ɗigin mint green ne yasa tayi masifar dacewa da kalar jikinta.
Gyara gashin kanta tayi ta tubƙeshi tare da kitsen jelar.
Ta saketa bisa kafaɗunta.
Ɗaurin asseta tayi ya zauna ɗas a kanta, tattausan gyale minti green color ta yafa
a kafaɗunta.
Kana ta fesa turarukan ta masu daddaɗan ƙamshi.

Sosai jan lallen gargajiya dake kan ƴan fararen yatsun hannunta yayi masifar kyau.
Ga kuma zanen da akayi a saman hannun hakama ƙafafun ta, suma sun sha zanen jan
lalle tayi kyau sosai,
Ta fito ras da ita.

Baki ɗauke da sallama ta foto falon.


Cikin murmushi Ummi ta amsa sallamar tana mai kallonta,
Hakama Hibba da Ummi ta kokkontar mata da hankali taji tsoron ya ragu.
Gefen Ummi ta zauna, tana kallon Hibba na ɗaukarta hoto tana cewa.
"My Happiness Aunty kinyi kyau".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Na kaiki ne?".
Da sauri Hibba tace.
"Kin fini ma".
Murmushi ta kumayi tare da cewa.
"Ngd matuƙa".
Sai kuma ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi me zamuyi abincin dare".
Cikin jin tausayinta Ummi tace.
"A a akwai abinci harda na gobe da safe ma, yanzu kam ki huta, sai dai in akwai
abinda kikeso ki gaya min in yi miki".
Kai ta jujjuya alamar a a kana tace.
"To Ummi a kaiwa Hadimai wani abincin kada ya lalace a banza ko".
Cikin gamsuwa Ummi tace to.

A can Airport kuwa ƙarfe uku dai-dai jirgin Ahlin masarautar Joɗa ta sauƙa.
Nan motoci suka kwatsosu.
Suna isa masarautar ana kiran sallan la'asar hakane yasa matan cikine kawai suka
shiga cikin gida su mazan.
Masallaci suka wuce.
Ana idar da salla kuwa fada suka wuce baki ɗayansu.

A sashin Gimbiya Saudatu kuwa wani irin dariya mai cike da masifar jin daɗi tayi
tare da cewa.
"Dai-dai kenan yaro zai dawo ya taradda da mummunan lbrin matarsa ta zama
zautacciyar mata...!

An dauko wannan littafi daga shafin www.dlhausanovels.com.ng ku ziyarci shafin na


www.dlhausanovels.com.ng domin samun kayatattun littatafan hausa kama daga kan na
yake yake dana soyayya

Marubuci ko marubuciya zasu iya turo mana da littatafansu mu dora masu a shafinmu
kyauta don masoyansu su rika Downloading a online,

Sannan marubuta zasu iya turo mana da tarihin rahuwarsu da tarihin rubutunsu, dama
sharhin littatafansu don masoyansu su gani kuma su karu da hakan
Domin turo mana da littafi ko tarihin rayuwar marubuci ko marubuciya sai ayi mana
magana ta whatssap da wannan nambar +2348140419490

A lura dakyau - kyauta muke saka littafi a shafinmu bama amsan ko sisin marubuci,
duk wanda ya amshi kudinku da sunanmu babu ruwanmu,

Alura dakyau - manazarta bama tura littafi ta private ku dena binmu private kuna
neman mu tura maku littafi, duk mai bukatar littafi yaje website namu

Alura da kyau - Littatfanmu suna fitowa cikin manhajoji uku ne PDF,TXT da DOC amman
munfi amfani da PDF da TXT masu amfani da wayar android ko tablet ko computer zai
fi kyau ku riga dauko PDF da DOC

Masu amfani da kananan wayoyi java ko mara java TXT zakuna zaba don shine daidai
wayarku

This hausa novel was uploaded and downloaded from www.dlhausanovels.com.ng


You can download more hausa novels there
Also you can send us your novel to upload it in our website for your fans to
download it online
It is free we do not charge for uploading novel
Also if you are an Author be it online or Non online you can send us your biography
including your book summary,commentary and others via this number +2348140419490
its free we do not charge for our services

Note that - we do not charge for our services we uploaded novels and posted
biography free, any person that collect your money in our name is your fault do not
blame us

Note that - pls readers stop calling us and be asking us to send you a novels we
are not sending novels through whatssap or private our novels is public at any day,
any time you can visits our site and download it

Note that - our ebooks came as PDF,TXT or DOC format but the popular format are PDF
or TXT, those with android or tablet or pc we suggest you to download PDF or DOC
those with java phone or non-java phone we recommend you to download TXT
__

By
*GARKUWAR FULANI*

You might also like