Musayar Zuciya Complete-1-1

Download as txt, pdf, or txt
Download as txt, pdf, or txt
You are on page 1of 193

[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...

⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Bismillahir Rahmanur Rahim.....

"Hakk'in mallakar Hajja ne, kar wanda yayi min sauyi a cikin sa please."

Page *1*

A makaranta.

"Uwani halilu?"
"Present sir.."
"Baraka lado?"
"Present sir.."
"Sahura Ayuba?"
"Present sir.."
"Indo malam Hamza?"
"Labbaika, present, sir, mah, nazo..."

Saurin kallon ta malamin yayi jin yauma a yadda ta amsa mai kafin ya zare glass
d'in dake manne akan saman idan fuskar shi, ya d'ora dara-daran idanun shi akan
nata da nufin ko zata ji tsoron sa sai yaga ta kafeshi da idanuwan ta tamkar zata
cinye shi, yayi saurin wurga mata uwar harara ranshi a matuk'ar had'e yace mata
cikin tsawa.

"Ke..! Baki da hankali ne...?!"

Indo ta mik'e tsaye tana gyaran hijjab d'in ta wanda yayi dikil-dikil da daud'a
wuyan ya yage tun daga wuya har zuwa k'irjinta sannan tace,

"Da sauk'i dai malam..!"

"Naga alama ai koma gurinki ki zauna wawuya kawai.."

Ya fad'a ba tare da ya kalleta ba. Komawa tayi ta zauna sai faman soshe-soshe take
yi akan ta wanda hakan da alama ba za'a rasa kwaron kwarkwata ba dan yadda take yi
ya nuna hakan. sai da ya kammala kiran sunayen su tas! sannan ya mik'e ya fita yana
jiran lokaci ya cika sai ya kuma dawowa yayi musu subject d'in turanci wanda aka
sari basa fahimtar uban komai a ciki, idan kuwa yana son su fahimta toh sai ya
had'a musu da yaren hausa sannan zaiji ruwan amsa da tambayoyi amma idan da turanci
zai kwana yana yi sai dai su kafamai idanuwa tamkar zasu cinye shi.

Yana fita wajan mintuna biyar sai gashi ya kuma dawowa hannun shi d'auke da wasu
littattafai manya da kananu. yana shiga ya tarar duk sun kaure da surutu yayin da
ya kai idanunshi can k'arshen ajin ya hango INdo da wani yaro taci uwar d'amara da
hijjabin ta suna dambe. Dorinar hannun shi ya d'akko yayi gurin. sauran yara na
ganin shi suka fara watsewa aka bar INdo da lurwanu a gurin. yana zuwa ya fara
tsulawa INdo dorinar ganin ita ce me fifik'arewa kafin ya tsulawa lurwanu yana
cewa.

"Ke! Sakar mai riga wawuya kawai."

Axabar bulalar ne yasa ta saki amma da ba tayi niyar sakin shi ba sai ta fasa mai
baki kamar yadda ta furta tun farkon fad'an nasu. Malam Sadeeq na kallon su yace.

"Me ya had'a Ku?!"

Idanu kwal-kwal zasu kawo ruwan kuka lurwanu yace.

"Malam itace..."

Caraf be k'arasa fad'a ba INdo tace,

"Malam wallahi k'arya yake shine ya fara..."

Shima lurwanu dan kar tamai sharri ya kuma tare zan cen,

"Wallahi malam k'arya take yi kawai na ajiye..."

"Billahillaxi malam shine ya..."

"Keep silent or something else's, sha-sha-shai kawai.."

Babu abin da suka fahimta a cikin abin da yace dasu sai dai yana yin yadda yayi
musu maganar da kuma kalaman shi na karshe ya tabbatar musu da cewar fad'a yake
musu hakan yasa suka yi shiru suna bin kyakyawan bakin shi da kallo ba kamar INdo
da take tunanin ko alawace ji take kamar ta lasa dan yadda ya burgeta.

Komawa yayi wajan teburin shi ya zauna sannan yayi musu alamar suzo baki d'ayan,
suka bishi INDO sai faman ture lurwanu take yi a haka suka k'arasa wajan da malam
Sadeeq yake jiran su,

"Kai me ya had'a ku da ita?!"

"Malam itace kawai muna zaune sai tazo tana tab'ani da kafa nayi mata magana ta
dena takani shine tak'i taci gaba har muka fara fad'a da ita."

Tun kafin ya bata izinin magana INdo ta fara tana hararar lurwana bakin ta har
kumfar yawu yake sabida masifa,

"Kai..Kain uban can..! Na rantse da Allah malam shine ya d'alamin kaure a baya na
shine na rama ya kuma yi min kawai muka fara fad'a dan shi masifaffe ne ya raina
ni.."

"Ya isah haka kowa yaje ya zauna bana son surutun ban za."

Tashi suka yi suka tafi dama can karshen aji nan ne wajan zaman INdo dan haka ta
tafi malam Sadeeq yayi saurin dawo da ita, tana zuwa yace da 'yan layin gaba suyi
mata guri anan ta zauna cike da jin haushin malamin dan taga alamar baya son ta
bare yabi bayan ta a duk cikin al'amarinta.

A haka ya kammala musu yabar ajin duk sun gundure shi ga haushin basa ganewa da
turanci har sai yayi da Hausa. Ana tashi ya hau mashin d'in sa kai tsaye ya wuce
inda ya sauka. Wanka yayi sannan yayi sallar azahar ya koma gefe ya zauna bayan ya
janyo wayar shi, laluban d'an uwan shi ya fara yi cikin sa'a ta fara k'ara yana
d'agawa yace,

"Hi twins ya gida ya gurin aikin naka?!"

Daga can 6angaran ya amsa cikin sanyin murya kamar yana rad'a,

"Lafiya lau all twins ya student's da fatan dai kana samun yadda kake so koh?!"

Shafa k'eya yayi tamkar yana ganin shi sannan ya lashi lips d'in shi yace,

"Nop! Twins ga baki d'aya makarantar bata yi ba wallahi, gashi nazo an wani bani
formaster teaching kuwa sai dai nayi da hausa wata Kalmar ma ban san yadda zan
fassara musu ba wallahi sai dai na barsu a haka."

Dariya yayi mai sauti ya san dole a bawa d'an uwan shi haushi duba da yadda baya
son wasa a harkar karatu gashi an kai shi inda zasu samai hawan jini, cikin basarwa
yace.

"Common Sadeeq ka sani ko anan ma girlfriend d'inka take, dan Allah kasaki ranka
kasan 'yan kauye da son mutane za kaji dad'i kuma zasu soka kai dai kawai ka samo
mana wifey d'in ka acan..!"

Kit! Sadeeq ya kashe wayan sam beji dad'in wayar da suka yi da d'an uwan nashi ba
yau, a maimakwan ya lallab'a shima a'a sai ma yi mai fatan tsiya da yake yi na samo
mata dan wulakanci. shi kam Abubakar murmushi yayi jin ya katse ya san haushi yaji
sabida yayi mai fatan tsiya. zai samu yaje garin har gurin shi ya bashi hakuri yaga
kuma yadda suke yi.

***

Bayan wasu awanni, Sauri yake yi ya k'arasa cikin masallacin dan gudun kar a tayar
yana hanya, sai da yazo dai-dai wajan wata kwata zai tsallaka kawai yaji an kwararo
ruwan kanzo gabaki d'aya aka b'ata mai wandon dake jikin shi. Bin katangar gidan
yayi da kallo cikin wani mugun takaici kafin yayi wani yunk'urin tuni an fara
zagaye shi abin takai cin ma harda d'aliban shi. sai sannu suke zabga mai tamkar
wanda yaji ciwo.

"Kai subhanallahi Malam Sadeeq ya a kai haka?"

Kafin ya bashi amsa wanda yayi maganar ya kalli wani yaro tare da cewa,

"Kai yi maza shiga nan gidan kace a temaka mana da ruwa a buta."

Juyawa yaron yayi shi kuma headmaster ya kalli Sadeeq cikin jimami yace.

"Garin Yaya hakan ta faru Malam Sadeeq?!"

Da kyar ya samu ya tsaida takaicikin shi kafin ya kalli headmaster yana kallon inda
aka b'ata mai yace,

"Wucewa zan yi zuwa masallaci, su kuma ba tare da suna kulaba kawai suka watso
k'azanta sai kace a cikin gidan su duk ba wannan ba sun b'atan lokaci na rasa
jam'i."

"Ashha-ashha malam yi hakuri kasan kauyan namu ne sai hakuri duk haka suke yi kayi
hakuri dan Allah.

Dai-dai lokacin yaron da aka aika suka fito shi da INDO hannunta rik'e da buta
gefen butar ya fashe sai da ta d'an kar-kata ta taho tana cewa,
"Waye yake neman ruwa a buta?!"

Karaf suka had'a idanu da shi da sauri ta dashare baki tana matsawa wajan shi ruwan
sai zuba yake ta kalleshi tare da cewa,

"La'ilaha'illallahu Malam Sadeeq kaine a k'ofar gidan mu yau?!"

Banza yayi mata yana kallon butar ganinta jage-jage gashi duk ta fashe ya sashi yin
saurin juyawa tare da kallon headmaster yana cewa,

"Rankashi dad'e bari kawai na koma gida naga nan duk b'ata lokaci ne na gode..."

Ba musu headmaster yayi mai sallama da sauri ya wuce sauran mutane na bashi hakuri
ita kuma INDO tana fad'in,

"Malam ruwanfa? ko na biyo ka dahi koka ka fasa na maidahi gida?!"

K'in kulata yayi ganin haka yasa INdo ta murgud'a mai baki tamkar yana ganinta
sannan ta koma gida tana mitar kawai yasa sunyi asarar ruwan su a k'asa bayan suma
babu kala ne suke yi.

***

Yau kwana biyu kenan INdo bata zuwa makaranta, sai a kwana na uku taje tun daga
bakin k'ofa zaka tabbatar da yau tazo sabida yadda ajin ya kaure da shegen surutu
da hayani. yana shiga ya ganta zaune akan tabur d'in da malamai ke zama idanunta
sanye cikin eye glass wanda idanun (glass) d'in suka ciccire ta rik'e pencil tare
da d'ora kafa d'aya kan d'aya tana yin irin na Malam Sadeeq,

"Mary alto."
"Zuwaira jamilu."
"Mansur bawa."

Gabaki d'aya ajin aka d'auki ihu da shewa dan sam basu kula da zuwan shi ba. har
INdo ta mik'e tsaye tana dariya tare da cewa,

"Alkur'an haka malam Sadeeq yake yi.."

Suka k'ara tuntsurewa da dariya ana cewa,

"Ohhh ke INDO...!"

Tsittt taji anyi hakan yasa ta waigawa bakin k'ofar dan ganin yadda kowa ke kallon
wajan, karaf suka yi idanuwa hudu da malam Sadeeq wanda yayi kicin-kicin da fuska
tamkar hadari tayi saurin komawa wajan zamanta wanda in dai shine a ajin toh anan
take zama sai ya fita take komawa gurinta na ai na hi wato karshen aji.

Yana shiga duk aka tashi ana gaida shi kowa ka gani cikin tsoro yake dan basu san
matakin da zai d'auka akai ba,

"Good morning sir..!"

Sai da ya samu guri ya ajiye register da sauran littattafan hannun shi sannan ya
kalle su yayi musu alamar su zauna da hannu, gyara glass d'in idanun shi yayi
sannan ya kalli inda INdo take zaune ta kwalalo mai idanuwa yace mata,

"You! come here.."


Tashi tayi cikin d'ari-d'ari dan babu wanda be san kalmar come ba, tana zuwa ya
matsa mata tare da nuna mata kujerar gurin yace,

"Seat down..." (Zauna)

Zama tayi dan taga ne abinda yace sabida yau da gobe idan sun gaida malamai ana ce
musu seat down so kuwa ya san kalmar, ta zauna sai wulkita idanu take. register ya
d'akko tare da bud'ewa ya mik'a mata jan biro da blue tare da cewa,

"Oya started."

Tayi saurin kallon shi tare da cewa,

"Na'am malam.."

Keya ya salle mata da hannunsa tare da cewa,

"Ki fara kiran sunan idan ba haka ba zaki sha wahala dan naga alamar kin raina ni
so ina son kiyi musu yadda nake yi nima na gani.."

Kallon register d'in tayi sam kasa gane yadda take tayi bare aje ga karanto sunayen
ciki ba zata iya ba kuma nan J.S one, kallon shi tayi tare da marairaicewa ta fara
ba shi hakuri.

"Malam dan Allah idan kana kaunar iyayanka kayi hakuri wallahi tallahi ba zan sake
ba."

"Au ba zaki fara ba sai na zane ki...?!"

Ya fad'a yana gyara dorinar hannun shi, nan da nan INdo ta fara kuka dan tak'i
jinin a doke ta da bulala. tayi saurin zamewa k'asa tare da sake bashi hakuri akan
ya kyaleta ta tuba tabi Allah tabi shi.

Ganin duk ta gigice yasa shi ce mata,

"Tashi ki dawo nan kiyi naildown."

"Malam baka hakura ba dan Allah?!"

Ta fad'a tana matse idanuwa dan hawaye su fito amma ko d'igo, ganin yaje ya zauna
ya fara kiran suna yasa INdo tashi taje tayi abinda ya sakata dan ta san ba hakura
yayi ba. sai da ya kammala kiran sunan ya fara koyar dasu ya gama sannan ya kalleta
yana nunata da yatsa yace,

"Idan kika sake yin abinda nake yi in dai ba na karatu bane sai na 6allaki kina
jina?!"

"Eh malam ai baxan kuma bama."

"Yafi miki.."

Ya fad'a tare da kwashe kayan shi yabar ajin yana tunanin inda zai yi ya samu ayi
mishi transfer ya tsani makarantar sam ba tayi mishi ba.

Bayan sati biyu ranar wata Monday Sadeeq na shirin tafiya class d'in shi ya d'auki
duk wani abu da yake buk'ata yana shirin fita kawai yaga Abubakar twins d'in shi
tsaye cikin kananun kaya riga seegreen me dogwan hannu da wando baki sai farin eye
glass wanda yayi mai matukar kyau, sosai suke matukar kama babu ta inda zaka iya
bambance su sabida tsabar kamannin su. kallon shi Sadeeq yayi cikin tsananin mamaki
tare da k'arasawa ya kalleshi cikin mamaki yace,

"Yanzu muka gama waya da kai amma shine baka gaya min kana hanya ba why?!"

Kafad'a Abubakar ya d'aga alamar ba komai sannan ya shiga ciki ya zauna tare da
cewa,

"Twin ko class zaka shiga ne?!"

"Eh but tunda kazo sai mu wuce gida ka huta gobe na shigar musu."

Yayi maganar yana k'okarin maida littattafan dake hannun shi, da sauri Abubakar ya
mik'e tsaye yana tsayar dashi ta hanyar rik'e hannun shi yace,

"No kazo muje sai na tsayaka ina nan tare da kai har zuwa gobe."

Kafad'a Sadeeq ya d'aga sannan ya d'auka tare da juyawa yana fad'in.

"Toh muje."

Tafiya suke wanda ita kanta iri d'aya ce suke yi suna yi suna hira yara kuwa daga
cikin tagogin ajin su sai lekowa suke suna mamaki da al'ajabi ganin malam Sadeeq
guda biyu a haka suka k'arasa barandar ajin su INdo. Yauma kamar kullum cikin
surutu suka gansu sam basu lura da zuwan su ba INdo suka hango a saman dest tana
rik'e da kugunta sai gwada musu yadda malam Sadeeq yake tsayuwar shi take yi taji
Uwani halilu ta janyota tare da nuna mata k'ofar ajin tana hango su ta shige
k'ark'ashin benci cikinta sai kululululu yake sabida ta san yauma ta shiga uku.

"Goody morning sirsss..!"

'Yan aji suka fad'a baki d'ayan su tare da mik'ewa tsaye. ciki suka shiga sosai
Abubakar sai kallon su yake su kuma sun rasa gane waye malamin nasu a ciki. Sadeeq
ya k'arasa wajan bencin da INdo ke k'ark'a shi yace.

"Ke! Tashi ki fito ko na mareki.."

Jikinta na rawa ta d'ago ai tana ganin still biyu take ganin shi sai ta koma tana
ihu tare da cewa.

"Wayyo Allah na higa uku malam nayi min fatalwa, wallahi tallahi ban yi niyar yi ba
amma Maryam Aliyu tace nayi zata bani naira biyar dan Allah malam kadenayi min
fatalwa wallahi ba zan sake yi ba idan na k'ara ka...."

Bata k'arasa ba taji an janyo kafar ta sai ganinta tayi a gaban allo tana d'agowa
still ta kuma ganin su biyu kawai a take ta sulale a wajan ta sume sabida tsabar
kad'uwa da shiga cikin rud'ani.

Ko gezau Abubakar beyi ba bare yayi yinkurin yin temako sai kallonta kawai da yayi
yana mamakin ganin hauka irin nata, da sauri Sadeeq ya girgizata yana kiran sunanta
cikin tashin hankali kar yaje ta mutu ya shiga uku 'yan aji kuma sai suka fara kuka
cewar INdo ta mutu.

"Aisha! Aisha!! Ke Aisha!!! Tashi mana me aka yi miki haka...?!"

Sadeeq ya fara kiran sunanta ganin duk ya rud'e yasa Abubakar k'arasawa wajan ya
dafa shi sannan ya kalle shi a hankali cikin rashin sonyin maganar shi yace,

"Sorry my twins ba mutuwa tayi ba suma tayi da ansa mata ruwa zata farfad'o.."
Shaf Sadeeq mantawa yayi da cewar d'an uwanshi likita ne sai da Abubakar ya samo
ruwan wata yarinya a jarka ya shafawa INdo sannan ta farfad'o yana jin sanda d'an
uwan nashi ya sauke ajiyar zuciya mai k'arfen gaske na farin ciki.

Tana farfad'owa idanunta suka sauka a kansu da sauri tayi baya jikinta na rawa,
ganin haka yasa Abubakar dama shine wanda baya d'aukar raini ya buga mata wata uwar
tsawa tare da zare mata idanuwa tsit INdo tayi jikinta sai faman rawa yake.

"Ke..! Karna sake jin bakin ki yayi mana ihu, wawuya baki san ana haifar 'yan biyu
ba? Ko kinga munyi miki kama da mayu ko aljanu..?!"

Cewar Abubakar wanda ke tsaye akan INdo, da sauri ta girgiza mai kai cikin tsananin
tsoro sannan ya ce mata,

"Tashi kije ki zauna na san yanzu garau kike ba kya buk'atar wani hutu."

Da sauri ta mik'a ta wuce gurin zamanta, mik'ewa Sadeeq yayi ya koma kan kujera
tare da janyo d'ayar ya nunawa Abubakar alamar ya zauna. kallon kujerar yayi sannan
ya kallo inda yake hango INdo cikin yatsina fuska yace mata,

"Ke..! Zo nan."

Da sauri ta k'arasa tare da zubewa a gurin shi tace.

"Gani malam."

"Karki kuma kirana da malam kinji ko? Ni ba malamin Ku bane..!"

Baki na rawa INdo tace.

"Toh sir."

Had'e rai yayi tare da tsuke baki cikin takaici yace,

"Waye sir d'in?!"

INdo tace,

"Kai ne sir. ."

Hard'e k'afa yayi yana kallonta cikin b'acin rai yace,

"Stupid...! Ya sunan namijin saniya? ya ake kiran shi da hausa?!"

Cikin sauri ba tare da takawo komai a cikin zuciyar ta ba tace,

"Sunan shi sah."

Abubakar yace,

"Ahha kin ga nayi miki kama da shi?!"

Da sauri ta girgiza Kai alamar a'a tana mamakin wannan abu, toh me zata ce mishi
tace malam yace baya so tace mai sir yace ta kirashi da sunan dabba toh ko sunan
shi yake son ta fad'a ko tace mai baba amma ai be haifeta ba bare tace mai hakan.

Jan baya yayi kad'an tare da cewa,

"Zoki gogemin kujerar da zan zauna."


INdo ta mik'e tana mamakin toh yau malam sadeeq mugu ya zama kokuwa ba shi bane dan
har lokacin bata tantance waye malam Sadeeq ba cikin suba. kalle-kalle ta din ga
yi ko zata samu wani kyallen da zata goge mai amma babu ganin haka yasa shi yin
magana,

"Ke..! wai ba zaki yi aikin da na saki ba kin barni a tsaye fa."

"Mal.. Si.."

Ta rasa me zata ce mai kawai ta kalleshi tana turo baki dan ya gundire ta tace,

"Ai babu tsumma shi yasa."

Cikin rashin damuwa ya kalleta daga sama har k'asa ya tab'e baki sannan yace,

"Meye amfanin hijjabin jikinki ko d'ankwalin kanki su d'in ba tsumma bane?!"

Da sauri INdo ta kalleshi ya d'aga mata gira guda d'aya tayi saurin kallon Sadeeq
dake zaune ga mamakin ta register ma yake bud'ewa ta kalli hijjab d'inta wanda duk
ruwan kashu ya dafar dashi gashi wuyan ya yage tace mai.

"Ai hijjab d'ina ne bafa tsumma bane ba."

"Idan baki cire kin goge min na zauna ba ranki zai 6aci yanzun nan kinji na gaya
miki."

Ya fad'a cikin tsawa wadda take a slow, ba yadda ta iya haka ta kama k'asan hijjab
d'inta ta goge mai kujerar sannan ya zauna ita kuma ta koma wajan da malam Sadeeq
d'in ya tanadar mata a gaba. Malam Sadeeq ya fara kiran sunaye sannan da ya gama
yayi musu karatun da yake d'aukar su wato turanci, Abubakar dake zaune yaci dariyar
zuci dan karma yayi a fili su raina shi ko idan yaji dariyar tayi mai yawa sai ya
kara text book a fuskar shi yayi mai isar shi, lallai dole d'an uwan shi ya koka
tab makarantun gwamnati sai addu'a yake ta fad'a a cikin ranshi har Sadeeq ya
kammala musu sannan suka fita ana tashi suka wuce gidan da Sadeeq d'in yake haya a
ciki.....

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Page *2*

Bayan an tashi daga makaranta, su Indo ta k'ofar gidan da su Sadeeq suke suka
biyo. lek'en su suka din ga yi su dai suna jin hayaniya da guje-gujen yara amma
basu kula ba sai can Indo da Maryam Ali suka kuma kutsa kai suka shiga suna lek'a
tagar wani d'aki karaf suka hango Abubakar zaune a bakin katifa yana danna laptop
wanda daga shi sai 3quarter da singlet sam beyi tunanin cewar ana lek'an su ba sai
da yaji motsin yayi yawa sannan ya d'aga kai yana kallon gurin.

Mamaki da al'ajabi yasa shi saurin mik'ewa tsaye su kuma suka zaro mai idanuwa
kamar had'in baki su sam basu gane waye aciki ba kasan cewar kamannin iri d'aya ne.
Suna k'ok'arin guduwa suka ga Sadeeq tsaye a bayan su ya rufe k'ofar gidan ya jin
gina a jikin ta yana watsa musu wani mugun kallo. can Abubakar ma ya fito fuskar
nan a murtuke.

“Wayyo Allah dan girman Allah dan annabi Muhammad s.a.w idan kuna kaunar iyayanku
kuyi mana hak’uri.”

Cewar Indo tana faman tafa hannuwa alamun rok'o,itama Maryam tsugunnawa tayi tana
magiya,

“Dan Allah kuyi hakuri wallahi Indo ce tace muzo mugani ko aljanu ne ku, amma
wallahi ni banyi niyar shigowa ba.”

“Shhhhhhhhhhhhh..!”

Abubakar yayi musu bayan ya d'ora yatsan shi d'aya akan Lip's d'in shi suka had'a
idanuwa da Sadeeq suka fara matsowa gurin su yayin da jikin su Indo ya hau rawa
kamar an saka musu shock ai kuwa suka fara kurma musu ihu.

“Iiihuuu..! wayyo Allah a zo a temaka mana zasu kashe mu...!!”

Kafin kace mene har unguwar ta cika da mutane sai bugan gidan ake amma sunk'i
bud'ewa, yaran da suka taho tare da su Indo ne suka yiwa sauran mutanen gurin
bayani kan cewar ai su Indo ne suka shiga wai sai sun kallesu. wani dattijo ya kuma
buga gidan jin su indo na ihu yayi magana da d'an k'arfi yace,

“Ku kuwa bayin Allah dan Allah kuyi hakuri ku bud'e su fito ba dan halin su ba.”

Sai da Abubakar yasa su kamun kunne wajan mintina goma sannan Sadeeq yaje ya bud'e
su indo suka kwasa da gudu suka bar gidan,hatta wad'an da suke mak'otaka dashi
Sadeeq d'in sai da suka tambaya waye Sadeeq a cikin su yace...

“Gani nan baba Al-hassan.”

Wanda aka Kira da Baba alhassan yace,

“Ikon Allah toh ai kud'in ne dole ku zama abin kallon jama'a sabida ba kasafai ake
samun samarin matasa maza 'yan biyu masu matukar kama da juna ba. koni da Al-husain
d'ina kafin ya rasu ana iya gane mu amma ko babu wata alama da zata sa a gane ku
dole yara suzo kallan ku.”

Murmushi Sadeeq yayi tare da shafa k'eya yayin da Abubakar ya kalle su sai kuma ya
juya tare da komawa cikin d'aki yana tausayin d'an uwan shi akan wannan aikin nashi
daya zoyi duk babu sa'a, ba'a makarantar ba ba kuma a garin ba duk babu sauk'i
haukan garin yayi yawa.
**

Abubakar da Sadeeq 'yan biyu ne wad'an da ba zaka ta6a iya banbance Hassan ko
Husaini ba mudin suna tare sabida tsabar kamannin da suka yi. Hatta tafiyar su,
dariyar su, yana yin maganar su sai d'abi'un su ne kawai idan ka zauna dasu zaka
iya tabbatar da cewar sun ban-banta dana juna.

Engineer Alhaji Salmanu Haruna shine mahaifin su, yana da arzik'in shi dai-dai
misali Matan shi na aure guda biyu ne Mama A'i itace uwar gida kuma mahaifiyar su
Abubakar da Sadeeq sune yaran Alhaji Salmanu na farko sai kannan su da suke uwa
d'aya su biyar Hawwa, Halima, Hamza, Amina sai Khalifa sai ta biyun Umma Fatu tana
da yara uku Khaleel, Mubasshir da Rukayya. Gabaki d'ayan zuriar sun taso cikin
tarbiya da ilimin boko dana addini dan Alhaji Salmanu tsayayyan mai gida ne da yake
tsaye akan matan shi da yaran shi.
Wannan kenan..

**

Indo Aisha d'iya ce a wajan Hamza mai gyaran radio da Inna Mero sai kannanta guda
uku Sagiru, Shehu sai Nafeesa. Malam Hamza ya dad'e yana gyaran radio dan da
sana'ar yayi aure harya hayayyafa duk da suna matukar shan wahala dan wata rana ma
basa samun na abinci sai dai su kwanta haka.

Indo yarinya ce k’azama ainun domin wanka ma se juma’a jum’a take yi,shima se an
tilastata agaba bayan haka kuma gagarumar fitinanniya ce ga d'an karan tonan fad'a
da shiga fad'an da bana ta bane,tana da son wasa hakan yasa koda aka bud'e musu
wata primary aka sanyata bata kwaso komai ba sai k'arin fitina da rashin kunya a
haka harta zana jarabawar fita daga primary ta wuce secondary yanzu tana aji d'aya
ko sunanta da kyar take iya rubutawa shima a karkace cikin rashin tsari, kuma kusan
duk haka ajin yake monita ne kawai mai iya rubata sunan shi complete sannan ya
rubuta na wasu suma ba duka ba.

Gidan su na k'asa ne d'an k'arami wanda shi da kanshi Malam Hamza shi ya gina
abunshi yayi d'akuna uku da makewayi katangar tasu gajeriya ce domin idan kai dogo
ne to hak'ika idan kana tsaye sai an hangoka hakan yasa duk shirgin da suka kwaso
suk'e iya cillashi ko su watsa shi ba tare da sanin koda mutum a wajan ba dan ansha
fad'a dasu da mutanen unguwa amma sun kasa denawa har anyi shiru an zuba musu ido.

**

Da gudun tsiya ta shiga gida tana sauke wani uban nishi Inna ta kalleta tare da
cewa,

“Ke kuma lafiya kuwa kika shigo gida bako sallama 'yar nan..?!”

Inna ta fad'a kasan cewar bata iya fad'in sunan Indo sabida 'yar ta ce ta farko
kuma sunan surikar ta ne wato mahaifiyar malam Hamza. cire daddauhar hijjab d'in
Indo tayi me tashin hamamin wari tare da cillar dashi a tsakiyar gidan su tace,

“Wato inna akwai abubuwan kallo idan mutanen cikin birni suka zo nan wai...!”

Tah fad'a tana zaro idanuwa, kallonta inna tayi cike da takaici ta rasa gane kan
Indo tunda aka kawo malam Sadeeq kullum taje makaranta ta dawo da saban labarin da
zata bata akan shi dan haka tasan tatsuniyar gizo bata wuce ta kok'i inna tace,

“Allah shi kyauta miki 'yar nan, tunda aka kaiki makarantar nan ban tab'a jin kinzo
kina yin karatu ba yadda nima zanji dad'i ba sai dai tunda aka kawo sabon malamin
ku toh babu ranar da zakije baki dawo da sabon labari akan shi ba sai kace shi aka
ce kije ki koyo..”

“Kai inna ana baki kina k'in k'ar6a.”

“Eh ba zan k'ar6a ba bana so ki rik'e kayan ki.”

Indo ta kuma gyara zama tare da bugun kanta da alama kwarkwata ce tayi motsi,cikin
son bada labarin tace,

“Aikuwa inna sai na baki labarin nan dan kuwa wallahi har suma nayi aka samin ruwa
na farfad'o.”

Jin abinda ta fad'a ne yasa inna zaro ido tana dafe k'irji tace,

“Na shiga uku ni Maryama meya faru dake 'yar nan?!”

A take Indo ta kwashe labari tun daga wanda ta sani har wanda d'alibai 'yan uwanta
suka gaya mata ta k'arashe zan cen da fad'in lokacin da suka shiga gidan su shine
fa ana bud'e musu ta shigo gida da gudu.

“Ikon Allah kenan, toh ke dai babu ruwanki dasu..ah to karkije wata rana ki basu
haushi suyi miki aika-aika su cuceki Allah ya tsare ba fata ba”

“Toh inna ai na fisu iya gudu wallahi.”

“Yi min shiru wawiya kawai an ce miki wannan muguntar ta gudu ce, ke dai babu
ruwanki dasu na gaya miki.”

Da haka suka dinga magana inna na son fahimtar da ita sai dai kunya da kawaici yasa
ta kasa sai faman kwana-kwana take yi.

Ita kuma wadda ake wa dama ba wani fahim ta ne da ita ba dan haka bata fuskanci
inda maganar inna ta dosa ba.

***

“Other half gaskiya ya kamata ka nemi transfer daga wannan gajarabal d'in
makarantar, ah!wannan school da kauyan ai sai kaima su maida kai kamar su dan
wallahi rayuwa a irin wannan gurin tsab zasu canza ka su 6ata maka hobby d'inka.”

"”Kai twinnie God forbid wallahi sai dai ni na canza musu, ni sam basa yi min haka
kawai zuwanka ne yasa dan sun ganmu mu biyu shashanci sai kace akan mu aka fara
zuwa duniya mutum biyu iri d'aya...”

Abubakar ya kuma kallon Sadeeq shi tausayin shima yake dan ya san kawai yana zaune
a garin ne ba dan yana jin dad'i ba,ta6e baki yayi tare da d'aukar laptop d'in shi
ya koma cikin bedroom ya k'agara gari ya waye ya bar garin dan jin shi yake yi
tamkar akan k'aya.

Mik'ewa Sadeeq yayi tare da d'aukar mukullin motar Abbakar d'in, fita yayi ba tare
daya sanar mai ba yayi waje. Can cikin gari ya tafi wani restaurant ya shiga inda
yake zuwa cin abinci yayi musu order mai rai da lafiya sannan ya siyo musu drink's
masu sanyi ya dawo gidan lokacin ya tarar da Abbakar d'in ma bacci yake kasan cewar
sun kunna inji akwai iskar fanka. kallon shi yayi sannan ya fito ya dawo parlor ya
fara rubuta lesson plan har wajan la'asar sannan Abubakar ya farka yana fitowa
yagan shi zaune gaban shi duk takardu ne da littattafai kawai ya kalleshi yace,

"Wai twinnie har yaushe ne ka koma haka? duk ka takurawa kanka ya kamata ka sauya
makaranta dan kafi karfin koyar da irin wad'an nan school d'in."
Sadeeq ya numfasa tare da cewa,

"Meye abin fin k'arfi twinnie ? a gani na tunda teaching nake sha'awa ai be kamata
nayi korafi ba."

Da sauri Abubakar yace,

"Ba anan ya dace da kai ba twinnie kamata yayi yanzu ace kana wata university d'in
kana bada lecture's dan kafi can-canta da dacewa acan, amma nan wallahi tsaf zasu
nakasa maka ilimin da kakeji dashi ya kamata ka duba magana ta."

Kallonsa yayi har ya shige cikin d'aki sannan ya sauke idanun shi, dama tun ba yau
ba tun suna k'anana suke da ban-bancin ra'ayi wajan zab'ar samun gurin aiki sai dai
shi Abubakar ya cika burin shi yayin da shi kuma Sadeeq be samu zama pilot ba sai
aikin koyarwa a university of sokoto amma yak'i tafiya sai ya tafi ya samu a wani
secondary school itama d'in a kauye, sai gashi sam baya jin dad'in ta.

Abubakar ne ya dawo ya zauna tare da janyo take away d'aya ya fara cin abincin shi,
Sadeeq ya kalle shi tare da ture takardun gaban shi yace,

"Twinnie wai ya zancen Ummi kuwa ka kuma komawa kun dai-dai ta ko?!"

Abubakar yayi murmushi tare da ajiye spoon d'in hannun shi yace,

"Bari kawai twinnie ban koma ba sai aikowa gida da mahaifinta yayi wai ance angan
mu a tsaye toh idan na shirya na fito. kaji fa? ni ai Ummi bata cika quality's d'in
da nake da burin matata ta kasan ce ba dan haka nace a'a ban shirya ba ko ya ka
gani?!"

Dariya Sadeeq yayi sannan yace,

"Kai ma ka tsaya ruwan ido meye ai bun Ummi tsakani da Allah, yarinyar nan fa yanzu
s.s 1 zata shiga kuma gata kyakyawa to meye ya rage maka.?!"

"Gayu, twinnie ka san ina son mace 'yar gayu mai aji wadda koni idan ina mata
magana sai taga dama zata amsa amma fa Ummi kana magana kafin kakai k'arshe ta
mayar maka, no gaskiya akwai wata dai a cikin hospital din mu da suka zo sanin
makamar aiki na ga kuma kamar type d'ina ce sai dai ba zan iya mata magana ba karma
ta rainani."

"Rai ni kuma Abbakar? toh kenan idan kayi auran ma bashi da amfani tun da dole sai
wani abun raini ya shiga tsakanin ka da matar ka.."

"Kasan kuwa wani sa'in ina jin tsoron yin aure, sabida wani sa'in sai naga ba shi
da amfani."

"Ikon Allah."

Cewar Sadeeq yana yi mai kallon mamaki yayin da Abubakar d'in ya mik'e yayi waje
yana son ya samu almajirin da zai wanke musu toilet d'in su.

Yana fita ya samu wasu yara zaune suna wasa ya kira wanda suka had'a ido da shi.
yana zuwa yaron befi 10 years ba Abubakar ya kalleshi yace.

"Kai whats your name?!"

Yaron ya kura mai idanuwa kunnuwan shi sai bud'ewa suke dan beji abinda yace ba
nan ya fara kwakular hanci har lokacin idanun shi na kan na Abubakar ganin kamar be
gane ba yasa shi cewa,

"Ya sunan ka?!"

Ya dashare baki hak'oran nan yalaye kamar yasha d'orawa kafin yace,

"Suna na Sagiru Hamza."

Abubakar ya d'auke kai tare da kallon sauran yara, gaba d'aya kaf cikin su babu na
za6a har garama Sagirun dan haka ya kalle shi yace.

"Zaka iya wanke mana toilet?!"

Da sauri Sagiru ya d'aga kai duk kuwa da cewar be gane abinda ake nufi da toilet
din ba amma yaji ance wankewa yasan koma me ye zai iya wanke shi tatass.

"Toh shiga muje."

Abubakar ya fad'a yana komawa ciki, Sagiru ya juyo tare da yiwa sauran abokan nashi
gwalo.

"Yauwa Sagir kaga ga klin da hypo shi zaka d'auka ka kwanke shi sosai."

Ganin inda ya nuna ne yasa Sagiru tabbatar da cewa ban d'aki ake son ya wanke,
Abubakar na gama nuna mai ya koma cikin d'aki shi kuma Sagir ya shiga yana
wankewa.sai da ya kammala tasss sannan Abubakar ya fito ya bashi naira d'ari biyu
ai kuwa ya dinga murna sannan ya tafi gida da gudun sa yana murna tare da burin
ramuwar abinda INDO tayi mai lokacin da tana da kud'in ta naira 50 ta dinga siyan
awara tana hana su.

"INDO..! INDO...!! INDO..!! nima yau zoki ga kud'ina wallahi na samo.."

Sagir ya shiga gidan da gudu yana k'iran ta da k'arfi, da gudu ta fito daga ban
d'aki hannunta rik'e da buta tana fitowa tayi wurgi da ita tana gyara kullin pant
d'inta wanda yayi mata yawa sabida bud'ewar da yayi gashi kamar rai shi kad'ai
gareta ta k'arasa kusa da Sagiru tana raba idanuwa.

"Wai kai dalla meye kake ta kwad'a min kira ne?!"

Be yi magana ba sai kud'in daya nuna mata yana tsalle, da sauri ta ware idanuwa
cikin tsananin mamaki sannan tace,

"Kai Sagiru a ina ka sato ko kuma waye ya baka kud'i har d'ari biyu haka...?!"

"Yarinya wankin ban d'aki nayi shine aka bani ita lada."

"Ikon Allah a wane massalaci ne haka?!"

Sagir yace,

"Ba'a matsallaci bane a gidan malamin ku wannan mesa glass d'in nan."

"Tab d'i jam! toh Sagiru nawa zaka bani a ciki?!"

Wani banzan kallo yayi mata tayi kallar tausayi tare da cewa.

"Dan Allah kabani ko naira hamsin ce kaji kanina wallahi nima wata rana idan na
samo zan baka."
"Uhh-umm yarinya ba zan bayar ba."

Cewar Sagir yana danna kud'in a cikin aljihun shi, ganin haka yasa ta cewa,

"Toh kuwa yaro dama Inna tana ta neman kud'in da za'a siyo daddawa da kuka sai kazo
ka bayar tun da ai kaima da kai za'a ci tuwan."

"Ke wallahi ba zan bayar ba, ke rannan ba da naira goma a hannunki ba Inna tace ki
kawo a siyo manja da ita ba amma kikak'i sai yanzu dan kud'in ba naki bane ba zaki
ce na bayar a siyo kuka toh ba zan ba da ba."

Ganin bashi da niyar bata ko sisi yasa ta fara kwad'awa Inna kira, yana jin haka
shi kuma ya zura da gudu yayi waje nan ya barta sai faman masifa take tamkar kud'in
nata ne...

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Page *3*

Da sauri ta fito ta biyo bayan sa amma ko kyallin sa bata hango ba,ta ciza le6anta
tare da ficewa daga gidan gaba d'aya.Gidan su Maryam k'awarta ta wuce tana wak'ar
ta da d'an tsalle wasa hankalinta kwance.malam Sadeeq dake k'ofar gida ya bita da
kallon takaici ganin yadda tayi fururu ba wanka,sam bata kula dashi ba sai faman
wak'a take tana cewa.

"Indo Aisha...ta zariya mai d'an kallabi..."

Har tayi kwana sai tayo baya ganin shi da tayi, shi kuwa yana ganin zata dawo yayi
sauri zai koma cikin gida be kai ga k'arasa juya wa ba yaji tace.

"Wil dam malam. (Well done sir).."

K'in kallon ta yayi yana dan na wayar sa domin service yake nema.Ya gane abinda
take son cewa so take ta gaida shi, ko me ya kawo well done a tsayuwar da yayi.dan
haka Murya k'asa k'asa ya amsa mata,Indo ta washe mai baki tare da matsawa kusa da
shi yayi saurin daka mata tsawa ganin yadda take shige mai.kallon sa tayi cikin
mamaki ido waje ta kuma bin sa kafin tace.
"Malam Sadeeq baka gane ni bane?Indo ce fa ta makarantar gwamnati ta nan unguwar
d'an Awaisu. Ka gane ni? Nan tsefawa fa gwamman sakandare sukul." (Tsefawa
government secondary school).

"Ke! Naji me zan miki ne..?!"

Ya fad'a cikin k'ufula domin ta kai shi bango. Ita ma share shi tayi da masifar
tashi da yake mata domin tana son yi mai tambaya wadda take son jin amsar su daga
bakin sa dan haka masifar shi ba za ta d'aga mata hankali ba. kusa da k'afar sa ta
k'ara sa haushin ta ya kuma zuwar mai wuya, tsoran sa d'aya kar 'yan kauyan suyi
mai muguwar fahimta sai kauce mata yake amma ta kasa ganewa ya kuma had'e rai amma
ko ajikin ta tace.

"Malam tsakanin ka da Allah gaskiya da gaskiya zaka gaya min, shin ku 'yan biyu ne,
ko kuwa dai ni kake bawa tsoro sabida ina kwaikwayon ka a aji...?!"

Wata uwar harara ya narka mata dan yaga alamar kamar zata kawo mai rai ni shi kuma
bezo garin dan su raina shi ba, wato ma k'arya yake mata shine zata zo ta k'ure sa
dan tsabar ba ta da kunya. Fuskar sa a murtuke ya kalleta yace,

"You're very stupid."

Tana dariya cikin nishad'i tace,

"Sanki u malam Sadeeq, (thank you) wallahi shi yasa kake birge ni sabida ka iya
turanci mai kyau da dad'i. Amma dan Allah malam ka d'an fassaramin abinda ka fad'a
da hausa he nima in rik'e gurin na iya sosai..."

"Zaki bar gurin nan ko sai na 6allaki... mara kunya fitsararriya kawai.."

Ya fad'a cikin d'aure fuska. tayi baya-baya tana kallansa tare da kama ha6ar ta
tace,

"Kai malam! masifa, daga tambaya sai cibi ya zama k'ari shi kuma k'ari ya zama
k'ababa. na tafi kuma ba zan je makaranta ba a-he, sai ayi kuli-kulin tara sisi
dani.."

Ta yi maganar tana tafiya da baya da baya har ta shige lungun gidan su Maryam.
tsaki yayi ya koma cikin gida yayi kudurin sai ya gyarawa 'yan makarantar zama.
kowa tayi wa dan ba ta je makaranta ba oho mata. yara sai rashin kunya basu san
komai ba dak'ik'ai zai nuna musu shima bashi da mutunci. Ranar haka ya wuni yana
kunci jefi-jefi yakan yi tsaki har dare yayi be fita ba sabida takaicin Indo da
sanya idon 'yan gari domin fita dubu shiga dubu sai sun kalle shi gashi ya tsani
saka ido cikin lamuran sa.

Washe gari da yaje makaranta Indo bata je ba yaga ashe da gaske take yi, still
wata washe garin tayi nan ma babu labarin Indo sai ranar juma'a yana tsaye wajan
black board yana koyarwa kawai yaji ana magana a taga, juyawa yayi sai yaga babu
kowa domin da taga alamar zai ganta sai tayi saurin yin k'asa, dan haka ya cigaba
da abinda yake yi. Can ya kuma jiyo kus-kus yayi a hankali ya kalli gurin caraf
suka had'a ido da Indo tana cillowa Sa'ade wani abu a leda, dariya ta sakar masa ya
k'arasa bakin tagar yana kallonta. Sanye take cikin house wear hannunta rik'e da
faranti an jera kallik'ak'au da yajin masau da alama shi ta cillawa Sa'ade ya had'e
girar sa tare da cewa.

"Zo nan..!"

Ita yake kallo amma sai ta juya wai ko zata ga wanda yake kira amma sai taga babu
kowa sai ita, dashare mai baki tayi tare da d'an matsawa kad'an ba sosai ba tace.
"Gani malam."

"Jeki zaga yo ta k'ofa."

Ya fad'a, Indo ta tsuke fuska tare da cewa.

“Malam ai ba zuwa nayi ba yau d'in ma tallah nake yiwa mak'ociyar mu. Kasan idan na
siyar mata mawa zata bani?”

Yayi mata banza ganin ita yake kallo yasa ta juyawa ta dafe abubuwan cikin farantin
ta ruga da gudu dan ba zata yadda taje ya hana ta fitowa.

Kai ya girgiza tare da komawa ya ci gaba da yin aikinsa kuma a kwanaki biyun
alhamdulillahi suna ganewa, tamkar dama Indom ce ke hana su rashin fahimta. Yana
gamawa ya fita ya koma ofis haka ya dinga ci gaba da koyar musu har aka kusa fara
jarabawa wadda daga ita zasu wuce j.s 2 amma Indo bata sake zuwa ba shima har ya
manta da ita har ya Saba ma idan yana kiran suna ya samata absent.

Ana gobe za'a fara jarabawa Indo ta dawo makaranta. washe gari aka fara musu sai da
suka yi jarabawa hud'u sannan a ta biyar d'in zasu yi English language wato subject
d'in malam sadeeq. Kasan cewar tun da aka fara beje ajin ba sai yau da za'a yi
tashi jarabawar kuma dole sai yabi aji-aji ya kuma yi musu bayani sannan. Tare da
Abubakar suka shiga domin lokacin yazo abinsu gwanin ban sha'awa, zasu gaida su
Sadeeq ya hana dan karsu yi hayaniya, can k'arshen aji INdo take ta duk'ufa sai
satar amsa take yi cikin littafin Ayuba mati sabida ita bata da ma littafin bare
tayi karatu.

Tsayawa Sadeeq yayi a gaban alo domin shi bema san ta samu damar zuwa ba ya fara
musu bayani. Malamin dake tsare su yana zaune a kujera Abubakar yana tsaye ya hango
wata ko d'agowa ba ta yi hakan yasa shi k'arasawa gurin da take ya lek'a yaga meke
faru sai yaga ta bud'e littafi sai kwafa take yi har ta kusan cika shafin farko.

"Ke.....!"

Taji an fad'a dai-dai kunnan ta. tsoro da razana yasa ta sakin tusa burtt ba tare
da ta shiryawa hakan ba 'yan aji suka kwashe da dariya ita kuma ta zaro ido ta fara
rantse-rantsen kare kai.

"Malam wallahi tallahi...."

Da sauri ya kifawa bakin na ta mari tayi saurin toshewa da hannun ta. matsawa yayi
tare da nuna mata hanya yace.

"Fito waje kafin na yayy-yaga ki a gurin nan 6arauniyar amsa.."

"Wallahi mal..."

Zata tsaya yi mai gaddama ya yi saurin fin ciko ta tare da tura ta gaban ajin tayi
taga-taga zata fad'a kan tebur Allah ya temake ta tayi saurin sanya hannu. Kwal-
kwal idanunta suka kawo ruwa zata yi kuka Abubakar ya k'arasa gurin yace.

"Shanye shi, idan kika bari hawaye suka fito sai na zane ki 6arauniyar amsa."

Maida hawayen tayi tana nan tsaye har Sadeeq ya gama yi musu bayani sannan ya kalli
Abubakar hace,

"Twinnie bar yarinyar nan ko tayi ba dubawa zan yi ba sabida ta yaye kanta ba zuwa
take yi ba tayi degree yanzu sai zuwa tallah."
"Ohhh! No-wonder ashe dak'ik'iya ce, amma baki yi halin asalin me sunan ba shame on
you.. Kawo wannan ta hannun taki da kika sato amsar, ki d'akko sabuwar pepper kizo
nan ina jiranki."

Tafiya tayi tana gunguni tare da murgud'a musu baki, sabuwar takarda ta d'akko tare
da biro taje ya nuna mata gaban alo yace.

"Zauna kiyi anan."

Kallon gurin tayi sannan ta turo baki kai da kagani kasan zai yi fitsara tace.

"Toh malam ai babu abin d'orawa kuma yagewa takardar zata yi"

Ba tare da ya kalleta ba dama Sadeeq ya fita yace, "ki d'ora akan cinyar ki kiyi."

"Amma malam ai..."

Wata uwar harara daya yi mata ne yasa ta had'iye sauran maganar, zama tayi tana
zumbura mai baki yace.

"Idan kika sake kira na da malam sai na fasa miki baki."

Bata sake kula shi ba ganin yafi malam Sadeeq zafi da saurin kai duka, har kowa ya
gama ya fita INdo tana zaune a gurin sai raba ido take yi gashi bata rubuta komai
ba sai jagwal-gwalo. Ganin bata da niyar kawowa ne yasa Abubakar k'arasawa wajan
tayi saurin cukwaikuye takardar ya mik'a mata hannun alamar ta bashi amma taki,

"baza ki kawo ba mara kunya?" Baki ta kuma murgud'awa mai aikuwa ya sanya k'afarsa
ya doke shi da takalmin sa. INdo ta kurma wani uban ihu tare da fad'uwa k'asa tana
ihu tana birgima.

Sunkuya wa Abubakar yayi ya d'auki takardar ya sanya cikin sauran tare da bawa
invigilator d'in, ko takanta be kuma bi ba sai ma tsallake ta da yayi yabar gurin.

Ihu ta kuma saki tana shure-shure har daddaud'an pant dinta ake gani sabida wandon
makarantar ya yage d'alibai suka zagaye ta ana bata hakuri da kuma masu yi mata
dariya amma bata fasa shure-shuren ba shima malamin yayi tafiyar Sa dan yasan INdo
sarai hakan yasa be kulata ba.

"Allah ya isa ban yafe ba mugaye kawai anyi satar amsar, shi dama ba malamin muba
yazo yana cin zalin mutane..."

"Hahaha INdo me tusa burtt..."

Uba Aminu ya fad'a yana nuna ta yana dariya, ai kamar jira take yi ta mik'e tare da
cakumar sa suka fara fad’a. K'arfi ba d'aya ba shi namiji ya dinga gwarata da alo
jikake k'um...k'um amma tak'i sakinsa sabida tsabar jaraba, can akaji Uba ya rushe
da wani irin ihu mai had'e da kuka.

"Kai..kai...kai! Lafiya meya faru haka.?!"

Malam Zubairu daya zo wucewa yaji ihu ya tsaya yana tambaya.

"Malam fad'a suke yi."

"Waye da waye?!"

"INdo da Uba."
Ihu Uba yake yana hawaye gashi ya rik'e gaban sa, malam Zubairu ya kallesu ganin
INdo na rik'e kugu yasa shi cewa "ku biyo ni ofis yanzun nan."

Abokan Uba suka kamashi suka kaishi k'ofar staff room, ita kuwa tahowa tayi tana
bugun cinya alamar bala'in be k'are ba taje ta tsaya malam Zubairu yakai takaddu ya
ajiye sannan ya fito dan jin kanun zance, be fara bawa INdo damar magana ba yace
Uba ya fara yi amma ya kasa sai shasshek'a yake yi da kuka.

"Ke kuma gaya min gaskiyar abinda ya faru."

Dai-dai lokacin Sadeeq da Abubakar suka fito daga cikin staff room, tsayawa suka yi
Abubakar na waya ta fara baya ni.

"Tonona yake yi shine muka fara fad'a."

"Sai kuma aka yi yaya..?!"

"Sai kazo kace mu biyo ka."

"Kai Uba me yasa ka toneta gashi ta saka kuka..?!"

"Malam cizo na tayi a anan."

Ya fad'a yana nuna gurin, duk wad'anda ke gurin suka zaro ido Abubakar dake waya ya
zare ta daga kunnansa yana kallon INdo cikin tsananin mamaki yace.

"Ke mayya ce? Baki da hankali?ke wace irin yarinya ce ne da kika fitini kowa ne?
Stupid,nonsense, what a fool wawuya kawai, mai wasa da maza karya.."

Haushin maganar sa da kuma turancin da yake yi bata jinsa yasa ta fara murgud'a
baki tana motsa lab6anta alamar magana take yi, da sauri Abubakar yayi kanta zai
ham6are ta Sadeeq ya rik'osa yana kad'a masa kai alamar kar yayi yayin da zuciyar
Abubakar d'in ke tafasa yanajin wani tururi cikin ransa dan yaki jinin rashin kunya
da k'in gaskiya. A hankali Sadeeq ya dafa kirjinsa yana kalon INdo wadda ta makure
jikin karfe tana jiran jin saukar duka yace...

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:48 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)
*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Page *4*

"Aisha zo ki bawa yaron hakuri."

Tamkar ba taji ba sai faman wasan ta take yi da k'asar gurin da d'an yatsan ta
wanda alama ce ta baza ta bayar da hakurin ba ya kuma cewa.

"Aisha ba magana nake miki ba kika min shiru ko..?!"

"Malam fa shine ya fara tono na kuma sai na bashi hakuri ta6di jam.."

"Duk da haka ki bashi hakuri tun da kin yi mai ba dai-dai ba.."

"Hu’...uhm." Ta fad'a cikin k'asan mak'oshin ta, Abubakar yayi kamar zai wuce kawai
yayi wuf ya dank'e ta, nan da nan ta fara ihu har wasu malaman suna sake fitowa ya
damk'eta ta 6are baki tana ihu yaji wani sumumin wari ya fito daga bakin ta yayi
saurin kawar da kai tare da hankad'a ta saitin Uba ta fad'i k'asa bata San lokacin
da ta furta.

"Allah ya baka hakuri Uba kayi hakuri kaji ka hakura..?!"

"Eh." Uba ya fad'a yana share hawaye malamai aka yi ta yiwa Indo fad'a akan karta
sake yin fad'a da Namiji sannan aka sallame su. Ana tashi daga makaranta babu wanda
Indo ta kula tayi wuce warta, ba gida ta wuce ba kai tsaye ofishin 'yan agaji ta
nufa tana zuwa ta sami ogan ya kalleta yace,

"Yarinya ya aka yi aiko ki aka yi..?!"

Tace "A'a shugaba k'ara na kawo dan ance shari'ar maita bata k'arewa toh wani
malamin mu ya Ce min banza maiya jaka, toh ban yafe bane shi yasa na kawo k'ararsa
abi min hakkina."

"Au ke cema kika kawo k'arar?"

"Eh sabida ance nan ake kawowa kafin akai kotu."

Sosai ya kalli INdo wadda take faman turo baki tana taunar k'asan hijabin ta da
hak'ori.

"Toh naji yanzu shi malamin yana ina kuma a wacce makaranta yake koya muku duk da
naga inifam (uniform) d'inki na makarantar tsefawa ne...?!"

"Eh Shugaba acan nake kuma ma shi ba malamin mu bane d'ayan ne malamin mu amma kaga
ya mareni, yayi min kutufo da k'afarsa sannan yace min Mayya, ance shira'ar maita
baya k'arewa toh yazo ya fad'a a ina nayi maitar."

Shugaban 'yan agaji na k'auyan ya sake kallonta sannan yace,

"Ya sunan ki...?"

Tace "INdo malam Hamza."

"Toh INdo yanzu abinda nake so dake nasan yanzu an tasheku ki bari gobe idan Allahu
ya tahemu lafiya he muzo ki nuna mana hi malamin kin ji ko.?!"
"Kai! Shugaba, ai tafiya yake yi kuma idan an gama jarabawa ba dawowa zai yi ba a
hanyar gidan mu suke kayiwa Allah kayi ma ma'aiki kazo muje ayi Mai jan kunne ya
dena ce min mayya da dak'ik'iya."

"A'a bada ni zakuje ba bari nasa wani yabiki suje yaji abinda ke faruwa."

Ya d'aga murya yana k'iran, "Awaisu! Awaisu!!, zo dan Allah kabi yarinyar nan ta
kawo k'arar wani malamin su." Awaisu na zuwa suka tafi suna tafiya suna hira tamkar
dama sun saba har suka k'arasa k'ofar gidan su malam Sadeeq wanda shigowar su kenan
dan sai da suka tsaya suka yi juyan bak'in mai.

"Kika ce nan ne gidan ko?"

INdo tace "Eh nan ne suna ciki."

Kwan-kwan-kwan, Awaisu ya fara buga k'ofar gidan yana kwad'a sallama. Malam Sadeeq
ne ya fito sanye cikin jallabiya ya kalli INdo sannan ya kalli Awaisu cikin rashin
fahimta da kuma sanin dalilin zuwansu ya fara magana.

"Lafiya dai ko bawan Allah."

"Eh toh lafiya ba lafiya, wannan yarinyar ce ta kai k'ara cewar kana ce mata mayya.
Toh bata yafe bane yasa takai mana k'orafinta shine shugaban mu yace nazo naji
dalilin da yasa kake fad'a mata wannan kalmar."

Mamaki da al'ajabi suka cika Sadeeq, sai yanzu ya k'ara tabbatar da hauka da rashin
hankalin 'yan garin ya kuma kallon INdo wadda itama shi take kallo yayi shiru yasan
Abubakar ne dan haka ya tsaya yana tunanin abin cewa yaji INdon tace.

"Awaisu ka tambaye hi idan shine idan kuma ba hi bane toh d'ayan ne ya fito dan
tagwaye ne.."

Kallonta Sadeeq yayi ya sake tabbatar da lallai bata da kunya, shi kuma Awaisu sai
d'aga kai yake yana kallon gidan ko zai ga wani ya fito amma ba kowa hakan da
sadeeq ya gani ne yasa shi cewa.

"Naga alamar baki da kunya Aisha, toh bazai fito ba ki shiga ki fito dashi
fitsararriya kawai. Kai kuma SS ne ko d'an sanda ko soja ko menene da ta d'add'ago
ka kuka zo nan..?!"

"A'a mu mune 'yan kungiyar agaji na wannan kauyan kuma turo ni aka yi akan naxo
naji abinda yake wakana dan tace bazata yadda ba."

Cewar Awaisu Sadeeq yayi tsaki cike da takaici sannan yace,

"Toh kaji abinda na fad'a idan ba maita ba waye zai ciji mutum a mafitsara? Kuma ma
wai fad'a mace da namiji dan iskanci."

"Haka ne kam malam kana da gaskiya ke INdo baki da gaskiya dan haka zanje na sanar
cewa ga abinda ya had'a dan haka sai ki tafi gida ki dena wannan halin."

Awaisu na gama fad'ar haka ya bawa Sadeeq hakuri sannan ya juya ya tafi INdo na
kallonsa zuciyarta fal haushin sa. Da taga yayi nisa ta juya zata yi magana sai
taga ashe shima Sadeeq din ya shiga ciki ta d'aga murya saitin k'ofar tace.

"Kujini da kyau ni ba mayya bace sai dai kunemi mayya, kuma an dena zuwa bokon ai
ba aikin Allah bane rawawul ni INdo na dena zuwa tsefawar yo dan banje ba ai ba
mutuwa zanyi ba kuje ku cinye makarantar..."
Suna jinta suka yi mata banza Abubakar ya shak'a iya shak'a Allah-Allah yake ya
shirya yabar garin dan takaici. Ita kuwa tana gama fad'a tayi tafiyar ta gida tana
zagin su tare da d'aura aniyar baza ta sake zuwa makarantar ba tunda ai sai taje
zasu ganta har suyi mata maganar banza.

K'arfe 3:34pm Abubakar ya idar da alwalar la'asar yana jiran Sadeeq su wuce
masallaci dan da sunyi sallah yake son dawowa ya wuce gida. Jerawa suka yi suna
tafiya suna hira abinsu gwanin ban sha'awa mutane sai kallansu ake yi.

Sagiru dake tsaye a k'ofar gida ya hana INdo fita ya tsaya yana kallonsu, ita kuwa
INdo ganin yace baza ta fita ba yasa ta komawa cikin gida. Dai-dai katangar gidan
zasu wuce kawai Abubakar yaji an cillo wani abu ya rufe mai fuska suka tsaya ya
cire yana dubawa yaga hijjab ne yayi dik'il-dik'il dashi ya yarda shi, kafin ya
kuma yin taku d'aya yaji an kwad'o mai wani abu a gefen wuyan sa ya kalli k'asa
takalmi ne d'an madina silifas yasha d'aurin leda a wajan sanya d'an yatsa suka
kalli katangar da ake yo jifan kawai sai suka ga hannu hakan yasa ran Abubakar ya
kuma 6aci sai ga k'afa can sai gata ta dirgo tim...!

Da sauri suka matsa inda take tana d'agowa ta gansu a tsaye a gabanta bata san
lokacin da ta kuma kurma ihu ba tare da juyawa zata kuma kama katangar ta koma gida
Sadeeq yayi saurin janyo rigar ta mutane suka taru yayin da INdo ke faman basu
hakuri.

Gabaki d'ayan ta tsami take yi da zarni Abubakar ya tsinketa da mari tare da


dungure mata goshi sannan Sadeeq ya sake ta Abubakar yace.

"Baki da mutunci ko?Ke mara kunya kinga abubuwan tsimmar da kika watsa min? Toh ki
saita kanki idan ba haka ba kafin nabar garin nan sai na ji miki ciwo idiot kawai
sai zarni kike yi mai fitsarin kwance jibe ki dan Allah da wani billanki a goshi
kamar zanan one..."

Yana kaiwa nan yayi gaba yayin da Sadeeq ya harare ta shima yayi tafiyar sa suka
shige masallaci. Mutane kuma suka k'arasa wajan INdo da tayi shiru tana kallon
jikin ta.

"Kedai INdo wallahi kowa sai yace baki da kunya, suma bak'i har kin fara yi musu.."

Cewar Rabi bala wadda makarantar su d'aya amma ita a js 3 take, INdo ta harareta
tare da cewa.

"Anyi d'in kizo kiyi kuli-kulin tara sisi dani munafuka kowa yasa dake.."

"Ke INdo dan ta gaya miki gaskiya shine zaki mata rashin kunya."

Wani yaro Bala ya fad'a ta kuma juyawa kanshi cikin masifa tace, "ji banza kai
tunda ga kan sunanka ansan kai d'in bala'i ne banza Bala bala'i mtwww."

Nan da nan gurin ya kaure ita kad'ai su kuwa wajan mutum goma amma babu wanda ta
ragawa, Sagiru k'aninta ya jata suka shiga gida sai da suka kai har tsakar gida
sannan ta ture shi. "Dalla can ni kyale ni banza."

Ruwa ta kindima a buta ta shiga band'aki shi kuma Sagiru ya kuma fita waje yana
cewa,

"Dama na barki sunyi miki shegen duka masifaffiya kawai."

Fitowa tayi jikinta sharkaf da ruwa wanda da alama wanka tayo amma ba a saka sabulu
ba. Cikin d'aki ta shiga Inna tana sallah ita kuma taje ta sake kaya sannan ta d'an
d'ibi man shanu ta shafa dama tana sato chuck ta d'auki d'aya ta daddaka tayi hoda
da shi ta shafa tayi kwalliya jagirar nan har wajan kunne ta sanya kantakile a
lab6anta sannan ta d'aura d'an kwali tayi waje Inna na ta faman kiranta amma ko
waigowa bata yi ba.

K'ofar gidan taje ta zauna tana jiran su dawo, ana idar da sallah suka dawo gida
tun daga nesa suka hangota kamar aljana dariya ta kusa kama Sadeeq ya daure yak'i
yi a fili yayin da yace wa Abubakar.

"Twinnie ga tanan fa kayi mata gorin wanka tayo tazo ta nuna maka." Dai-dai suka je
k'ofa Abubakar ya kalleta wani takaici ya kuma kamashi INdo tace.

"Gani yanzu kunsan abinda yasa bana kwalliya? Sabida mazan garin nan sun fiya
kallona shi yasa amma ni bana zarni."

Ta fad'a tana bubbuga kanta tare da sosawa, mtwww "ke wai kinga sa'anki anan gurin
ne?"

Kallon shi tayi tare da kura mai ido tamkar zata cinye sa ya d'aga hannu kamar zai
bugeta tayi saurin matsawa tace.

"Yoo ni ina ruwa na wannan ai ba wasa bane kuma idan anyi duniya da manzo na dena
zuwa makaranta wata za'a sake min irin ta 'ya'yan gidan kansilan mu."

Mtwwww Abubakar ya ja tsaki tare da shigewa gidan, itama ta doka cinyarta ta kalli
Sadeeq tace "Duk haka kuke babu me imani."

Sadeeq ya bita da kallo yana tunanin k'ila tana da aljanu yace.

"Kije kiyi brush."

Abubakar daya fito da car key dinsa yace.

"Bakin ta kamar kashi. Kinga yadda ake son aga hakora ba irin naki ba kamar kina
shan d'orawa."

Ya fad'a yana nuna mata hak'orinsa fari kal. Wucewa yayi gurin motar sa Sadeeq yabi
bayan sa dan suyi sallama, suna kallon sanda ta wuce tana sanya k'asan hijabin ta
tana goge hak'orin. Sallama suka yi abubakhr na sake bawa Sadeeq shawarar ya k'arbi
transfer ya k'ara da cewa.

"Bazan sake zuwa garin nan ba sai dai na hakura har ka dinga zuwa can gida ma dinga
had'uwa amma wannan garin beyi min ba."

"Insha Allahu doctor karka damu kayi min addu'ar abinda yafi alkairi."

"Toh amin ni na wuce."

Suka yi sallama ya tafi shima ya Shiga gida. Tunda ga ranar kuwa har aka yi hutu
Sadeeq be sake ganin INdo a makaranta ba sai dai a unguwar su ya ganta suna wasa ko
da farantin tallah..
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:49 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Note:- Assalamu alaikum masoya wannan labarin, dan Allah adalci d'aya zaku yi min
idan kuna so toh ku ringa adanawa. Idan nayi nisa kuka ce na turo muku sai na rasa
yadda zanyi gashi wayar ba lafiya gareta ba dan Allah kuyi min wannan agajin
please.🤭

Page *5*

Tafiya take tana dirzar hak’oran ta da k'asan hijjab ko zata samu suyi fari
itama, ai kuwa da ta gogo zata duba jikin hijjabin taga gurin yayi yellow ta
girgiza kai tare da cewa. "Kai...! Kuma fa da gaskiyar sa wallahi, dan gahi ina
kankarowa yalo na fitowa, amma shi hak'oran sa har wuta-wuta suke yi sabida kyau."

Wani shago ta tsaya a nan kusa da gidan su Sahura ta kalli me shagon tace.

"Idirisu kana siyar da burushi da abin matsawa...?!"

Yace "A'a bana siyo shi INdo sabida ba'a siyan shi, sai dai kije kasuwa ranar
laraba ki siyo."

Tsaki tayi tare da fad'awa gidan su Sahura, ita dai sam ba ta son zaman gidan su
domin bata ta6a yin cikakkiyar awa d'aya sai ta fita, bata taya Inna da aikin komai
sai dai da taji yinwa taje taci idan ba'a gama ba ta hau sababi. Sai kusan magariba
sannan ta koma gida shima dan tana son tambayar baban su kud'i zata je mahad'a wato
inda 'yan mata da samari ke had'uwa suyi hira.

"Baba sannu da gida."

Yana jin haka ya san akwai abinda zata tambaye sa dan haka yayi mata banza, ta kuma
fad'a sai ya d'aga mata kai kurum ta ciza yatsan ta cikin ranta tace,

"Wallahi sai ka bani abinda nake so, kaji shi daga gani na baba yayi wani shiru."

Kusa dashi ta k'arasa ta zauna shi kuma da yake a kishin gid'e yayi saurin dan ne
aljihun sa me kud'in a ciki dan ya san tun da ta fara wannan shisshige mai d'in toh
rok'on sa zata yi shi kuma naira d'ari da sittin ne garesa kuma goma ba zai bata ba
dan yau da kyar ya samu a gurin sana'ar sa. INdo ta cire hijjab d'in jikinta sannan
ta kalli mahaifin nasu duk da ya had'e rai hakan besa taji zata fasa tambayar Sa
ba, cikin rashin ladabin magana ta kallesa tace.

"Baba nera (naira) hamsin zaka bani anjima zanje mahad'a, daga can idan naje kaga
zan siyo burushi harda abin matsawa sai kuma ka bani nera ashirin wadda zan siya
abubuwa naci.."
"Bani da kud'i uwata yanzu, amma ki bari gobe idan na samu zan baki."

Kallonsa tayi da alama bata yadda da abinda yace ba, ganin tana kallan sa yasa shi
kuma kishin gid'a kan aljihun kud'in yana k'ara volume d'in rediyon sa duk kuwa da
yana jin ana k'iran sallar magriba amma ba shi da alamar ta shi yayi alwala.

"..'Yar nan zo kije kiyi alwala bana jin yauma ko sallar asubahi kinyi bare kiyi
sauran." Inna ta fad'a tana kashe wutar kararen da ta gama tuwo. INdo naji ta turo
baki sam bata kaunar taji ance tayi wani abun a harkar rayuwar ta abu in dai ba
wasa bane ko kuma naci toh sam bata kaunarsa bare tayi. Bacci ma ban da 6arawo ne
da baza ta dinga yi ba, ta mik'e tsaye ta shiga d'aki ganin baban nasu bashi da
niyar bata ko sisi.

Garam-garam inna ta jiyo ta tana tatta6a mata kwanukan jeranta na d'aki, saurin
bin bayan ta tayi nan taga sai faman bud'e-bud'e take yi mata cikin fad'a inna ke
magana tana kallon INdon tace.

"Me kike nema anan? Ko kinyi ajiya a gurin ne zaki d'auka..?!"

INdo ta ajiye kwanon hannunta kana ta kalli Innar ta tace, "Inna fisabilillahi baba
ba zai bani kud'i naje mahad'a ba, salan naje naga su maryam su sahura Sa sauran
k'awaye na suna siyan abubuwa su yi min gori...?"

"Toh banda abinki baya ce miki babu ba idan ya samu zai baki, toh kiyi hak'uri mana
nima kuma basu gare ni ba bare na baki."

K'ad..! INdo tayi da harshe alamar jin haushi sannan tayi waje fuuuuu babu wanda ya
kula ta shima baban nasu yana ji ana k'iran sallah amma ba shi da niyar tashi yayi
yana kishingid'e abin sa. Tana fita ta shiga gidan Rukayya wadda amarya ce aka kawo
ta unguwar take yin kayan siyarwa su alawar madara, gullisuwa, k'alli-k'a-k'au,
yajin masau da dai sauran kayan siyarwa na yara, shine INdo take zuwa ta kar6a tana
siyar mata sai ita kuma ta ringa bata ladan nera talatin ko asshirin da biyar.

"Uhm su INdo sai yanzu aka ga damar zuwa ko..?!"

Rukayya ta fad'a tana kallan ta, zama tayi a kan tabarma tana dariya Rukayya ta
idar da alwala tazo ta zauna kusa da INdon tana kallonta tace "Toh me ya hanaki
zuwa yau da wuri gashi ma har an siyar sabida yau na samu 'yan sari duk sun siye
sauran albishir kawai na naira tamanin.."

INdo ta zaro idanuwa tare da dafe k’irjinta yau kenan ba ta da kud'in siyan gyad'a,
cikin karad'i tace, "kai Rukayya amma ko ki jira nazo ba komai tun da abin 'yar
haka ce..!"

Rukayya tace "A'a INdo ina zan ta jiranki bayan har gidan Ku na tura kizo aka ce
min bakya nan, sai kawai na zauna jiranki bayan ga kustoma sun zo.."

"Ai shikenan yanzu ki bani albishir d'in na tafi dahi.."

Shiga cikin d'aki Rukayya tayi ta fito hannunta rik'e da leda ta mik'a mata. k'ar6a
INdo tayi ta lek'a cikin ledar sannan tayi dariya cikin ranta tana addu'ar Allah
yasa yau ta had'u da Shu'aibu saurayin ta ya ce ta shanye ya biya kud'in. Mik'ewa
tayi tasa takalma tana cewa Rukayya.

"Toh na tafi sai na dawo Rukayya kiyi mana adda'a (addu'ah).."

Tayi dariya tana gyara hijabi tace, "Toh INdo Allah ya ba da sa'a a siyar baki
d'aya."
Tana fita ta d'auki guda d'aya tare da jefawa cikin bakin ta, zak'in ya gauraye
mata bak'i ta lumshe ido tare da sosa cikin kunnanta. K'ofar wani shago taga malam
Sadeeq hakan yasa ta k'arasa tamkar bata ganshi ba ta kalli me shagon tace.

"Wale kana sai da burushi da abin matsawa..?!"

Wale me shago yana k'ok'arin bawa malam Sadeeq klin da sabulon da ya siya yace. "Eh
guda nawa za'a baki..?" INdo ta kuma kallon malam Sadeeq sai taga ko kallon tama
baya yi sai kud'i da ya zaro yana k'irgawa zai bawa me shagwon ta ta6e baki. Yana
sane ya zamar da naira d'ari k'asa as in be sani d'in nan ba sannan ya mik'awa wale
kud'in sa ya mai da sauran aljihu. INdo na ganin kud'in tayi kamar zata d'auki
dotse kawai ta d'auke d'arin ta maze sai mazurai take yi taji ko wani zai ce ya ga
sanda ta d'auka, da taga babu wanda yace komai sai ta mik'awa wale kud'in tana
cewa.

"Toh bani guda d'aya-d'aya ka bani canji na." Sadeeq na gani ya wuce yana mamakin
ta ashe har sace-sace da d'auke-d'auke take yi, lallai yarinyar bata da tarbiya sam
sai dai be san dalilin da yasa yak'i yi mata magana ba bayan ya san hakan da tayi
ba dai-dai bane ba a cikin addini dama rayuwar ta gaba d'aya.

D'akko mata yayi sannan ya bata canjin naira talatin ta k'ar6a tayi gaba abinta.
Cikin mararta ta tura brush da makilin d'in sannan tayi gaba tana d'aukar albishir
tana sanyawa a cikin bakinta sai farin ciki take yi yau ta fito da sa'a zata yi
brush ta basu mamaki gobe.

Tana zuwa zata sha kwana taji ance mata "ke zo nan." Ta juya tana kallansa ganin
malam Sadeeq yasan ya ta rik'e kugunta tana girgiza jijinta tana harararsa "yes.."
Ganin yadda take mai ne yasa shi kuma d'aure fuska yace mata "fito min da naira
d'ari ta da kika d'auke ko kin d'auka ban ganki ba."

INdo najin haka ta gyara tsayuwar ta tare da sake danna brush d'in dan karya gani,
cikin wayan basarwa tace "kai malam Sadeeq kud'in ka? yaushe na d'auka zaka ce in
baka...?"

Matsawa yayi kusa da ita tayi saurin yin baya ya mik'a mata dogon hannunsa tare da
bud'e mata tattausan tafukan hannun da nufin ta sako mai kud'in sa ta kallesa tana
muzurai tare da tsuke baki cikin yake tace.

"Ni ban d'auki kud'in kaba, a inama muka had'u bare na gani na d'auka."

Ya kuma had'e rai sai taga yayi mata kwarjini k'irjin ta ya hau harbawa ta fara jin
tsoron Kodai ya ganta, toh me zai mata ko ba malam Sadeeq bane d'ayan ne
masifaffan. Ganin yak'i d'auke hannunsa yasa ta tabbatar da cewar lallai ya ga
sanda ta sace amma ya aka yi be nuna ya ganta ba a gurin? Cikin borin kunya tace.

"Toh na d'auka abakacin kalamin herrin maita da kayi, ai dama nace ban yafe ba toh
yanzu ka biya ni hike nan."

"Ki mik'o min kud'ina nace bana son maganar banza kina jina..."

Jin yana masifa yasa ta cewa "Toh na siyo burushi dasu ba kune kuka min wulak'anci
ba, shi yasa nasiya nima na dinga yi wallahi a gobe zaku ga bakina sai yafi naku
fari."

Tana kaiwa nan tayi gaba haushi da takaici suka cika Sadeeq yama rasa gane meye
matsalar yarinyar sai dai yafi dan gana hakan da cewar k'ila tana da aljanu. Gida
ya wuce domin so yake daya gama had'a result ya tafi gida tunda anyi hutu sai kuma
an dawo wanda yake son kafin sannan ya samu canjin gurin aiki.
Cikin kwanaki uku ya kammala komai yabar garin sai farin ciki yake yi dan ba
k'aramin takura yake yi ba da k'auyan.

_Fatan alkairi ga masu bibiyar wannan labarin, ina ganin sakwannin ku Allah ya bar
kauna. Muje ga page d'in gaba wanda daga shi ne zaku fara gano sirrin cikin
labarin._🤭

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:49 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Page *6*

Zaune suke a cikin d'akin su, babban d'aki ne domin a da a matsayin sitting room
yake lokacin da suka taso suka zama samari yasa abban su ya bar musu shi suka gyara
shi aka sanya musu katifu guda biyu d'aya na gefen hagu d'aya na dama sai durowar
kayan su ko wanne ya d'auki gefe d'aya domin kayan nasu ya bambanta. Abubakar shine
yafi son sanya k'ananun kaya sa6anin Sadeeq daya fi son manya kamar su shadda boyal
da sauran su.

Shiru Sadeeq yayi idanunsa a sama kai da ka ganshi kasan ya fad'a cikin zurfaffan
tunani, kallan sa Abubakar yayi cikin ta6e baki yace.

"Twinnie ya aka yi ne kake wannan zurfaffan tunanin?"

Sadeeq ya numfasa tare da tashi zaune ya janyo kofin zobon da Maman su ta aiko musu
dashi ya d'iba yasha sannan ya zuba wani ya mik'awa Abubakar yana cewa.

"Twinnie ina tuna nin maganar Mama ne ta jiya, kaga tace Abba zura mana ido kawai
yake yaga dame zamu fara. Gaskiya ni yanzu na fara tunanin gara na fara yin gini na
tunda ya riga ya bamu filayen kuma yace duk inda muka ga ya kakare mana toh muyi
mai magana gara kawai nazo na fara dan ina son lokacin da zan fara neman aure toh
ya zamto koda ban k'arasa ginin ba to ya zamana sauran k'arashe shi yasa kaji nayi
shiru ina tunani."

Kai kurum Abubakar ya jin-jina sannan ya mik'e tsaye, shirin tafiya asibiti yayi
ganin be ce komai ba yasa Sadeeq cewa. "Toh kai naji baka ce komai ba ka kuma tashi
zaka tafi meke nan hakan da kayi..?!"

Shafa gashin kansa yayi tare da d'aukar turare ya fesa. "Karka damu twinnie da
rashin maganata, kasan dole idan naga ka fara nima na fara har addu'a nake mana
Allah yasa mu samu matan aure 'yan biyu kawai mu aure su, dan haka karka damu kai
dai ka fara samo matar tukun na."

Sadeeq yayi dariya tare da komawa ya kishin gid'a, yana murmushi yake cewa. "Lallai
kuma a ce mun had'a gida kuma kamar su d'aya like me n you, ta6 ai sai mu kasa
ganewa haka kurum wata rana in dirfafi matar ka ko kai ka shigar min gona toh
a'a.."

Abubakar ya kyal-kyale da dariya irin wadda be ta6a yi ba ya kalli Saddeq yana nuna
shi da yatsa yace. "Amma dai my twinnie muguwar fassara gareka, babu abin da zai
faru kai dai kayi mana fatan alkairi.."

"Toh ai gaskiya na fad'a ko kuma matar ka ta fito ta ganni tayi tunanin kaine tazo
ta mak'ale min ni bazan hanata ba tunda jiki da jini, ko kuma tawa matar ta ganka
tayi tunanin nine gaskiya twinnie ka dena yi mana fatan auran twins dan ni gaskiya
ka san bani da kauda kai, shi yasa ma da Abba yace baxai bamu gida kusa da juna ba
banji haushi ba."

"Hahaha twinnie ai ina tausa yawa duk wadda zata aure ka wallahi domin zata sha
wahala, kana gani a yanzu ma baka da auran sai kayi dreaming sau uku hud'u bare
kana ganin ta."

Murmushi Sadeeq yayi tare da gyara kwanciyar sa yace "twinnie kayi tafiyar ka kana
yin late ga marasa lafiya can na jiranka ni bacci ma zanyi dan ban gama va ka tashe
ni bye."

"Hmmm ka dai kore ni toh Allah ya baka mata a kauyan daka baro tun da baka son muyi
iri d'aya."

"Wallahi ba amin ba, duk basu da hankali musamman ma INdo kai! wannan yarinya ba
hauka ne yake damunta ba harda jahilci kasan shi yafi hauka. Gasu k'azamai tunda
naje garin banga wayayye ko wayyayi ya ba wallahi, ba amin ba dan kamar yadda kake
son nutsattsiyar mata haka nima nake so kuma 'yar gayu mai ilimin zamani da na
addini.."

"Twinnie kad'auki zafi da yawa so sorry dan Allah, bari naje na dawo bye.."

"Ok sai ka dawo."

Da haka suka rabu sai da Abubakar ya shiga cikin gidan yayi sallama dasu Maman sa
sannan ya fita, yayin da Sadeeq ya kwanta duk da cewar maganar da d'an uwan nasa ya
fad'a tasa baccin ya gudu sabida takaici hakan yasa ya tuno da INdo yaja tsaki tare
da mik'ewa ya koma cikin gida ko zaiji dad'in ranshi a gurin su Maman su.

*IHSAN MEDICAL CENTER*

Ahankali yake karasawa asibitin na ihsan medical center dake unguwar sultan road
nassarawa gra agarin na kano,sanye yake cikin kananun kaya kirar suit blue tacikin
kuma fara ce hannunsa rike da jakar laptop d’insa fuskarsa sakale da farin glass se
bulbula kamshi yake haka yashiga harabar asibitin,yana shiga ya hango nurse hidaya
k’ok’arin juyawa yake ta cinmashi da sauri,

“Welkm Doctor,Ina kwana..?!”

“Fine Alhamdulillah nurse hidaya..”


Yana gama fada yai gaba ya barta wajen

Office d’insa ya nufa inda sunansa ke rubuce boldly ajikin k’ofar office din
‘Dr Abubakhr’ kamar kullum Mani Cleaner ne aciki yana tsaftace office din se
mopping terrazzo din yake dake ta shekin kyalli,da sauri Mani ya tsugunna yana
kwasar gaisuwa

“Sannu da xuwa yallabai Barka da safiya”

“Barka dai Mani.”

Kan kujera dr abubkhr ya xauna yana dudduba files din kan tebur din one by one,har
Mani yakarasa ya feshe office din da freshener,

“Yallabai na kammala”

“Yawwa Mani godia nake xaka iya tafiya”

Har Mani yakai kofa yadawo yana sosa keya,

“Yallabai anbani sako wajenka amma wallahi na sha’afa da sunan,nurse dinnan ce de


da tai transfer daga Cotonou”

Sarai abubkhr ya gano wacece naccaciyar yarinyar data nace masa ce,

“To Mani ba damuwa tunda kamanta sunan kaje kawai”

Shiru Mani yai da alama ya zurfafa tunani be jima ba ya dago yana murmushi,

“Yallabai natuno nurse natasha ce da sassafe xuwana kenan tabani sako nabaka
nikuma hartamin alkhairin Naira dubu yallabai”

“Toh madallah”cewar Abubkhr tareda shan kunu

Kyakkyawar farar takarda datasha xanen heart Mani ya ajiye akan tebur se faman sosa
keya yake don wannan bashine karo na farko ba da nurses suka sabayiwa ogan nasa
haka,cikin dakakkiyar murya Abubkhr yace

“Jeka Mani sena neme ka..”

“To Yallabai Nagode ahuta lapia..”

Mani nafita abubkhr yaja tsaki ko duban takardr beyiba ya mike don yin round na
patients fitarsa kenan suka kusan yin gware da nurse Deexah uniform dinnan sun
matse koina na jikinta ya bayyana se wani rausaya take tana karkada jiki,

“Dr..Pls”tace hakan cikin wata irin siga

“Please what ?!inada patients daxan duba pls..”yakarasa hade da kaucewa ta gefanta
xe wuce tai hanxarin shan gabansa bayan tahada tafukan hannayenta biyu sama alamar
roko,

“Dan Allah dr ka saurareni minti d’aya pls”

Allah data ambata yasanya shi tsayawa ba tare daya karasa tafiya ba amma bejiyo ba
fuskarsa kan agogon dake daure a hannunsa yana jiran minti dayan ta cika,

“Ki magana kafin minti dayan ki tacika pls”

“Dr Meyasa kake mun haka? Kaso me sonka,ka agaxawa xuciyata kaceto ta daga fadawa
kogin halaka,duk asibitin nan babu wanda na xaba amatsayin wanda zuciata take
muradi sekai”
Karasa maganar ta yayi dede da cikar minti dayan data ambata don haka yai gaba
abinsa yashiga bin round na patients sedaya kammala tsaf sannan yashiga office din
abokinsa wato dr luqman,

Sundan taba hira sunayi suna tafawa sannan luqman yashigo da wata hirar,

“Nikwa Abokina nagaji da kawo korarrafin da ake kawomun akanka wlhy,yanxunnan


nurse deexah tafita hawaye kwance shabe shabe kan fuskarta dukde akan ka,dama
yanxun nake maganar koba ka shigo ba xanxo na sameka don nikam nagaji”

Murmushin takaici Abubkhr yayi cikin nutsuwa yace,

“Toh Aboki bani shawara shin mexanyi akai?”

“Ni Ina ganin kaxabi d’aya kawai ka aura kaga ai dole sauran su kyale ka ko?!”

Ajiyar zuciya Abubakhr yai kafin yace,

“Gaskia Aboki kabani mamaki wallahi domin bantaba saka a sahun mutanen daxasu bani
shawarar naxabi d’aya daga cikin nurses dinnan na aura ba,karka manta duk wani
namiji yana sone ya auro yarinya yar mutunci me dattako da sanin yakamata wadda
‘yayan daxata haifa ma xasuyi alfahari da kasancewarta uwa tagari,

To axahirin gaskia de magana d’aya ce xanyi wallahi duk cikin nurses dinnan babu
wadda xan iya xaba a matsayin wacce xan dauka nakai ta gidana wai amatsayin matata
ta aure,Kowa Allah ya hadashi da rabonsa kawai ko ya kagani?!”

Shiru dr luqman yai yana cin faratansa da alama yarasa tacewa,knocking akai a kofa
har sau uku hakan yasanya abubkhr bada izinin shigowa bayan yace,

“Yess”

Shigowa tai sanye cikin abaya baka bakinta dauke da sallama hannuwanta rike da
files cikin siririyar muryarta kamar anbusa sarewa tace,

“Gashi Doctor,duk nagama komai har room 13 dakace nayi mata inducing ruwan..”

“Okay nurse Mareeyah thank you..Xaki iya tafiya”

Dama abinda Mareeya ke jira kenan tai hanxarin ficewa abinta,baki galala abubkhr
yabude yanabin k'ofar data rufe da kallo kafin yadawo da kallonsa kan Doctor luqman
cikin sauri yace,

“Dr ai naxatan nurses d'innan sun gama aikinsu sun koma ya kuma Naga wannan?!”

“Oh mareeyah riketa mukai wallahi yarinyar ta iya aikinta ga hankali da nutsuwa
wallahi ba ruwanta da shiga harkar mutane kullum ita kad’ai xakaga tana aikinta”

“Mareeyah..”Dr abubkhr ya maimata sunan

“Kwarai sunanta mareeyah..A’a kode kafada’a da...”ai luqman ne k’arasa ba abubkhar


yai hanxarin ficewa

Cikin sa’a ya hangota tsaye a corridor tana shimfida sallaya xatai sallah,

“Salam alykm..”cewar Abubkhr daga bayanta..

“Wa alykm Salam”tabashi amsa tana k’ok’arin gyara mayafin data yafa
Ya salam,,abubkhr yafurta azuciyarsa Dakyar da lalubo salati yasamu ya saisaita
kansa kamar bashi ba yace,

“Dama uhm..Idan baxaki damu ba magana nakeso nayi dake”

“Babu damuwa amma xanyi sallah de tukun..”

“Tohm shikenan take ur time xanjira”cewar abubkhr

Ya jima azaune sedata idar tai addu’ointa tukun sannan ta nannade praying mat dinta
ta mayar cikin jaka,

“Ina jinka dr..”

“Okay.. Sunana Dr Abubkhr..”

“Allah sarki..Ni sunana mareeyatul qibdiyya.”

“Nice name qibdiyyah,”

Nande abubkhr yashiga gaya mata meke tafe dashi da abunda ke cikin zuciyarsa,itade
mareeyah kawai kallonsa take tana mamakin dama yana magana haka?!Abubkhr be bar
maareryah ba har seda ya tabbatar ya dana mata tarkon son sa tukun sannan sukai
exchanging numbers zuciyarsa fes yakoma gidah,

Kullum de abinda ke faruwa kenan abubkhr har gidah yake xuwa xance wajen mareeyah
ashema basuda nisa su su abubkhr suna unguwar Court Road ita kuma Mareeyah tana
Hausawa,Sosai suke gwangwaje soyayya abun su shikuwa sadeeq har yanzu be samu wadda
ta kwanta masa ba duk ya gwada amma babu sa’a ga cuku cukun transfer dayake nema
amma yakasa samu haka ya hak’ura yafara shirin komawa makarantar tsefawa dake
kauyen Sani a k’aramar hukumar sumaila..

****

Ranar asabar da safe sadeeq yatasamma titin sumaila bayan yasha adduoi daga
mahaifansa da kuma dan uwansa abubkhr wanda sam be so komawar d'an uwan nasa kauyan
kayayau d'inba,

Yana shiga cikin unguwar kuka sunan unguwar tasu kenan ya fara jiyo hayaniya sama
sama be tabbatar da muryar ba seda yaxo daf da dandaxon jama’ar da suka taru suna
kallon fadan da ake ta muryarta yagane kowacece siririn tsaki yasaki jin muryar
INdo ce dan turmutsawa taron yai ya hangota sanye cikin kodadd'un kayanta se
jurwayen fitsari riga daban xani daban d"ankwali kuwa ba'a xancensa se tumurmusar
fad'a suke da wasu yara maza kuma duk itace me karfin ciki,wani daga cikin taron ne
yace

“Ke y’ar nan kome sukai miki ki hak’ura ki kyalesu tunda ke macace dan allah”

Cikin turo baki had'e da k'ank"ace idanuwa tana girgixa kugunta data d'aure da
shamilallan hijabinta tace,

“Ta kwarankwasa baxan hakura ba,Babban bala'in can,se in xauna gani sokuwa sumin
lefin sannan na hakura wallahi babu xancen hak’uri a dishenari(dictionary)na ramuwa
ta da ta taxama dole..”

Tana gama fada tacigaba da kokawar da take yu cikin xafin nama sadeeq ya k'arasa
cikin su ya wanke mata fuska da mari hade da hankadata gefe yatsan sa yasa yashiga
nuna ta,
“Ke wai wacce irin kidahuma ce ne eh?! Kina mace kike fad'a? fad'anma da maxa
dandaxon mutane akanki ko kunya bakya ji? Tukun nama me akai miki da kika kamasu
kina duka kaman wata tinkiya..”

Rike baki Indo tai tana kada Kai

“Kai ka Kai Kai Kai wacece tinkiyar?!”

“Kece tinkiyar”

“To wallahi ka bude kunnuwanka kaji niba tinkiya bace kuma kwarankwatsa ka kara
cemin tinkiya seka gani. Haba nifa kana shiga rayuwata da yawa makaranta ce de nace
ni INdo Malam hamxa nadena xuwa tsefawa inifam d'ina ma na yadashi amma saboda
tsabar shisshigi da neman sani seka tsoma wannnan bakin naka a xancen da ba naka
ba”

Tana gama fada ta shuri bokitan su ubale da idi na talla da suke fad'a tai gaba
dasu tana sharara uban gudu,ganin haka yasanya su ubale binta a d'ari suna rokonta
da tabasu bokintan tallansu da ta kwashe,

Karkad'a kai kawai sadeeq yai wani b'angare na zuciyarsa na tabbatar masa da lallai
yarinyar nan ba aljanu bane kad’ai da ita Lallai babu shakku aciki kwakwalwarta ta
tabu, da haka ya k'arasa gidansa yashiga bakinsa d'auke da sallama tamkar da mutane
a ciki.

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO*:- Sanah Isma'il matazu.

_Yau page d'in nakine k'anwara ta gidan mu, ki sani kina cikin ran Hajja domin
Hajja takici my *MISS HAFCY BCH* dear kidena damuwa kina raina kun zama H³🤙mu
shirya kinji..💋_

Page *8*

INdo kuwa tunda ta koma gida take wanke hakorinta ko abinci k'in ci tayi sabida
kar yayi daud'a malam Sadeeq ya hanata kyauta. kwanciya tayi male-male a tsakar
gida kan tabarma tamkar me yin azumi, takaici da haushi suka cika inna ta kalleta
tana daga tsaye Innan tace.

"Ke! 'Yar nan ki rufawa kanki asiri kizo kici abinci kin ganin min sakarya, banda
malamin naku mugune taya zai hanaku cin abinci sabida wani an goge baki, toh bari
ki kashe kanki ai kinyi wa kanki..."

INdo tayi shiru tana ci gaba da rik'e ciki tana birgima, baban su ne ya shigo ganin
yadda INdo keyi ne yasa shi tambayar inna nan ta sanar mishi aikuwa ya fara fad'a
tare da cewa ta tashi taci abincinta amma ko motsi INdo tayi shiru sai hawaye da
take fitarwa a hankali. Juyawa baban nasu yayi direct ya wuce gidan da Sadeeq yake
ciki, kwankwasawa yayi yazo ya bud'e sam be san shiba dan haka ya fara mai kallon
rashin fahimta baban INdo yace.

"Sunana malam Hamza uban INdo d'alibarku ta makarantar tsefawa, ga 'yata can zata
mutu tak'ici tak'i sha sabilida kunsa musu dokar yin buruhi. Toh bazai yiwuba, tun
wuri kaje kasa taci abinci dan idan ta mutu akan wata kyautar ku ba yafewa zanyi ba
kur'anikuwa.."

"Subahanallahi malam ai ni ba haka nake nufi ba itada ma ba..." Sadeeq be k'arasa


magana ba malam Hamza ya cafe zancen ta hanyar d'aga masa hannu yace.

"Karkayi min wani batukaji ko, tanacan tana malan geruwa dagani har uwarta munyi-
munyi taci abunci tak'iya wai kar bakinta yayi daud'a. Ita Uwata ai batada jimirin
yinwa ko azumi goma bata iyawa dan haka kokaje kasa taci abinci konaje har gidan
protocol (principal) d'in nayi mai bayani zaka kashe mana 'ya'ya."

Tsaki Sadeeq yaja a k'asan zuciyarsa sannan ya rufe gidan ya kalli baban INdo yace
"Muje toh amma ni ba haka nake nufin suyi ba."

Kwance suka tarar da ita tayi shame-shame tamkar wadda zata mutu gaban malam Sadeeq
ya buga mamaki da tsoro suka dirar mai cikin sanyin jiki ya kalli INdo bakin sa
yayi mai nauyi ya daure dai yayi mata magana cikin dakiya.

"Aisha tashi zaune please."

Da kyar INdo ta samu ta iya d'ago kwayar idonta tana kallon malam sadeeq d'in yayi
mata alama da ka nan ta mik'e zaune da kyar jikinta duk yayi fututu da k'asar gurin
da ta kwanta rigar jikinta daga wajan hammatar ta yage sikert d'in ma duk yasha
faci tana son mik'ewa amma ta kasa, hankalinsa ya kuma tashi lokacin wayarsa na ta
faman ringing amma ya kasa d'agawa bare yasan ko waye. Daurewa yayi ya kuma matsawa
kusa da ita yana kallonta yace.

"Aisha tashi kici abinci ai ni ba haka nake nufi ba, kinga idan kin gama cin
abincin ma zaki iya yin brush d'in amma ba'a zama da yinwa idan ba haka ba mutuwa
ake yi tashi kinji."

Kasa mik'ewa tayi saida baban ta yace da innar ta mik'ar da ita sannan aka zaunar
da ita ta jingina da jikin bango jikin duk babu kwari tayi zuru-zuru da ita kai
daka ganta kasan tana cikin wani hali. Kallon Inna malam Sadeeq yayi gabaki d'aya
tausaya musu yake sabida ganin halin da suke ciki na rashi, ya karyar da baki yace.

"Mama a kawo mata abincin taci."

Sai Inna taji wani banbarakwai daya kirata da Mama yayin da INdo ta ke numfashi da
kyar dan da kyar take iya bud'e ido. Inna ta kawo dambun mazara ta turawa INdo
gabanta Sadeeq ya kalli kwanon sam babu alamar akwai mai a ciki ya kuma kallon INdo
wadda ta luma daddaud'an hannunta wanda duk k'asa ta 6atashi yaga ta fara watsa
danbun cikin bakinta, mamaki yasa shi yin shiru ba tare da yayi magana ba har ta
cinyee besani ba yana tsugunne yana tunani.
Sai da ta gama cinyewa sannan Malam Sadeeq ya mik'e, ya yiwa Inna sallama sannan ya
fita. A k'ofar gida ya tarar da baban INdo nan ya kuma bashi hak’uri da kuma k'ara
yi mai bayanin abinda yake nufi akan su, mahaifin INdo naji ya dinga 6oye hakoransa
wad'anda suke jawur sabida tsabar cin goro da rashin kula dasu.

Yana shiga gida ya zaro wayarsa missed call ya tarar na Abubakar, sai da ya zauna a
bakin katifarsa sannan ya kira layin har sai da ta kusan yankewa sannan yaji an
d'aga.

"Sadeeq ina ka shiga ne inata kira baka d'aga ba..?!"

Cewar Abubakar cikin sanyin muryarsa da jan aji, Sadeeq ya shafa kai yana kuma
sauke ajiyar zuciya yace.

"Twinnie ina jin sai na d'auki shawararka, wannan kauyan yafi karfina wallahi
haukan su yayi yawa sosai."

Yayi shiru yana sauke numfashin takaici kafin Abubakar d'in yace.

"Da kyau gara tun yanzu ka fara gane cewar kafi k'arfin secondary teaching ka dawo
nan gara ko FCE kano ne kaje kayi lecturing."

Shiru suka yi na d'an lokaci kafin Sadeeq yace.

"Toh zan kuma yin shawara amma nima abun kauyan nan ya fara isata, abun nasu yayi
yawa ga gidadanci."

"Twinnie kullum haka kake cewa yanzu kawai aiwatarwa zaka yi mudai muna nan muna yi
maka fatan alkairi."

"Ok insha Allahu sai munyi waya anjima a gaida min da qibdiyyah."

"Zataji dakyau gata nan ma muna tare."

Beyadda sun gaisa da itaba ya kashe wayar dan yaji ta fiye shiru da yawa kuma shima
ba surutu garesa ba.

***

Tun ranar laraba Rukayya ta wanke mata kai bayan tasa mata fiya-fiya kwarkwatar sun
mutu sannan tayi mata zanan Hausa shuku, kai idan kaga kan bazakayi tunani na jiya
bane sabida ya kitsu sai dai jan gashi gareta ba bak'i ba. Uniform d'inta kuma
ranar alhamis tasa zare da allura ta d'inke so gabaki d'aya inda ya yage ta kuma
wanke su duk da sun riga sun kod'e kuma bata da wasu ba kud'in yin sabo ta goge
fason k'afarta k'afar tayi kyau duk kuwa da be fitaba gaba d'aya.

Gidan innatuwa me kunshi taje tasiyo lallen goma da talatin din da rukayya
tabata,da kanta rukayyan ta yarfa mata jan lallen ta rufe mata fason kafarnan,a
ranar da yamma indo tatafi kasuwar dakali wajen idi shoe shiner hannuwanta rike da
wasu jemammun takalma kambos duksun fatattake,

“Idi xaka iya gyara wannan takalman”

“Mugansu”cewar idi

“Gasu kambas(kambos) ne idi kaga insipehen(inspection)malamin mu xeyi ranar


juma’ar nan kuma bakaga kyautar dayake be nikuma so nake naci shadda ma yasin”
“Bari na gwada nagani xasu gyaru mana sede xaki biya kudi dayawa”

“Kai idi nawa?!”

“Nera hansin”

Rantsuwa Indo ta dinga kwasowa tana kalallame idi da kalamai tana faman xabga masa
roko ta karkare da,

“Dan manzon salati idi kayi hak’uri ka temakamin nice fa indo..Indo Malam hamxa ta
makarantar tsefawa nan nan kusa dakai.”

Cikeda isar nacin da take masa idi ya wafci takalman yashiga gyara su,yadau lokaci
yana dinkecan nane can da gum sannan yai polish d’insa se kyalli yake Kai kace
bashi bane sannan ya mikawa Indo ,cikin murna ta karba harda lashe kasan takalmin

“Ta kwarankwatsa ya fita kuma,lalle aiki seme hi,Sannu idi yasin kaci abaka
hinkafa da miyar ja me nama”

“Allah ko Indo?”

“Yasin idi”

Cikin sake gyara kananun kayan da sukai yawa ajikinsa Wai shi gaye yace,

“Toh Indo nikuwa ina lami?(kawar Indo)”

“Oh lami tana nan,oho de bansan mata bama kasan makarantar gangare take tunda
mijin kanwar babar su ixama chayamen(chairman)”

Kada Kai idi yai yana murmushi,cikin tsokana Indo tace,

“Wai haryanxu kana ciki ne?!”

“Eh mana Inason lami wallahi kawaide bata sona ne tafison shehulle”

Cikin karkad'a kugu had'e da rausaya idanuwa INdo tace,

“To ai kaine idi,dole lami tafison shehulle kullum fa tanada daurin tsire da leman
roba na yangayu Kai kwa se mammakon bala'i”

“Ba haka bane Indo amma xan gyara..”

Da haka sukai sallama da ita tana tafe tana jujjuya takalmanta ranar kuwa
barkakkiyar safar da tayi shekaru batako kallansu hasalima kama tukunya ake dasu ta
dinga durxa tana wankesu ruwa uku tai musu ,Kai kowa mamakin Indo yake har inna
tafara sanyata a sujjada idan tai sallah don gani take aljanun tsafta ne suka
shafeta kwanan nan..

***
Rana bata Karya sedai uwar d'iya taji kunya yau take juma’a tashin Indo uku kafin
asubah inna tana korata waita xata safiya tai,asubar fari kuwa ta mike tai bandaki
ranar de atakaice baccin kirki Indo batai ba.

Sega Indo tai wanka abinda yabawa kowa mamaki agidan nasu sede basu da man shafawa
sai dai manshanu ko na girki shi kuma bashi garesu ba dan haka tana saka kayan
makaranta ta fita zuwa gidan Rukayya lokacin mijinta na nan INdo ta kwankwasa musu
k'ofar d'aki tare DA cewa,
"Rukayya kina ciki kuwa? Zuwa nayi ki aramin kayan kwalliyarki inyi zani
makaranta.." Ta k'arasa fad'a tana me shiga cikin d'akin sukayi kicib'is da ita,
"Au ashe kinji ni."

"Eh INdo bari na d'akko miki su nan tsakar gida."

Cikin d'akin ta koma ta d'ebu mata su lokacin mijin ta shima yazo zai fita INdo ta
ganshi ta dashare baki tace

"Au kaima d'anlami ashe kana ciki yanzu ka tashi a bacci ne?" Ya tsaya kusa da ita
yana kallonta yace "Eh INdo yau kuma za'a makarantar kenan."

Tace "Eh gahima kuwa." Rukayya ce ta fito ta mik'awa INdo kayan kwalliyar shi kuma
d'anlami yasa kai ya fita. Tana zaune tana yi Rukayya na kwarzanta ta wai tayi kyau
ai yau sai dai in bak'in cikin ne zai hana malam sadeeq ya bata kyauta. Zuciyar
INdo ta kuma shiga cikin wani irin yanayi najin dad'i, ita dakanta tanajin sauyi a
cikin jikinta sabida iskar da take shigarta ta k'ofofin gashin jikinta. Da sauri ta
kammala kwalliyar

Tashi Rukayya tayi bayan ta kwashi kayan kwalliyar ta shiga cikin d'aki ta mayar
dasu ta mik'awa INdo turare sai faman dariya take sabida yadda takejin ta wani
daban yau. Tafeshe rigarta Rukayya tayi saurin cewa.

"Haba INdo ya kike kuma 6ata kayan makaranta salan yaga jirwaye ya hanaki...? A
jikin hammatarki zaki fesa.!" INdo tayi yadda ta gaya mata sannan tace.

"Sai nazo kawo miki kayan da zan samo Rukayya..."

Tayi dariya itama cikin jin dad'i da fatan alheri tace "Toh INdo Allah ya baki sa'a
sai kun dawo."

Gida ta shiga yau ko karin kumallo bata tsaya yi ba sabida kar bakin yayi daud'a
tayiwa Inna sallama tabar gidan yau harda littattafanta da suka yayyage tazuba a
leda ta tafi burinta yau ta samu atamfar ko ya bata wani abun da zata dinga
alfahari dashi, yau sai da ta riga kowa a makarantar zuwa principal ne kawai da
masu kula da makarantar bata riga ba taje ta zauna kusa da farkon aji da niyar ko
masu gurin sunje bazata tashi ba tafi son a fara ta kanta yau.

***
Lokacin 8:15am yana gaf da shiga ajin aka yo mai waya hakan yasa shi tsayawa dan ya
amsa. Dubawa yayi sai yaga ansa my twinnie yayi murmushi sannan ya d'anyi baya da
ajin sabida hayaniyar da suke yi ya d'aga tare da karawa a kunnansa.

"Twinnie me ya how far..?!"

Sadeeq ya fad'a yana d'an sosa k'eyarsa da k'asan biro, daga can 6angaran Abubakar
yace.

"Surprise..!"

Sadeeq najin haka yayi murmushi tare da cewa.

"Kana gate ko..?!"

Abubakar yayi dariya yace "yah kana ina yanzu.?”Sadeeq ya kalli ajin sannan yace
"twinnie me kashigo ciki ina aji uku jss 3c nima yanzu zan k'arasa shiga ciki."

"Okay..."
Suka kashe wayar Sadeeq ya shiga hannunsa d'auke da ledar viva yana shiga 'yan aji
suka tashi ana gaida shi da k'arfin tsiya dan yanzu ba k'aramin so suke mishi ba,
ya ajiye akan teburin sa ba tare daya kallesu ba yace su zauna nan ma suka ce
"thank you Sir..." Shima da k'arfin su kamar kuma had'in baki.

Waje ya lek'a ya gani ko ya k'araso yana hangosa ya d'aga mai hannu suka yiwa juna
murmushi tundaga nesa har Abubakar ya k'araso suka yi musabuha sannan suka shiga
cikin ajin, nan ma yaran suka sake tashi suka gaida d'ayan daya shigo amma kotakan
su bebiba ya tsaya suna magana sai Sadeeq d'inne yayi musu alamar su zauna da hannu
tunda shi ba yadda zaiyi d'alibansa ne dole ya kulasu.

"Twinnie ga abin zama ka zauna."

Avubakar ya kalli kujerar sannan ya juya yana kallon 'yan ajin sai ya gansu fes-fes
dasu hakan ya bashi mamaki ya kuma rasa wadda zai kira ta goge mai kujerar dan
bazai zauna a haka ba. Shi duk a tunaninsa ba wad'anda ya sani bane ya kalli Sadeeq
yana shafa sajen fuskarsa yace.

"Twinnie congrats an sake ma class."

Sadeeq yayi murmushi tare da juyawa ya kalli 'yan ajin sannan ya kalli Abubakar
yace, "twinnie sune dai wad'anda ka sani kawai canjin yanayi aka samu."

"Woww good of you."

"Thanks twinnie."

Abubakar ya kalli 'yan matan ajin kawai ya nunu Maryam Ali ya yafitota, jikinta na
rawa ta mik'e ta k'arasa inda yake tace.

"Malam gani."

Mtwww “wai ban hanaku ce min malam vane? Ko kunga nayi kama da teacher?"

"Allah baka hakuri."

Maryam ta fad'a bakinta na rawa, yayi banza da ita sannan yace "daga yau kar wanda
ya kuma ce min malam ko sir suna na doctor Abubakar Salman Harun, karna kuma zuwa
ajin nan wata tace min malam ko wani sir ku kirani da doctor Abbakar or doctor
ASH."

Ajin yayi tsit babu meyin motsi yaja tsaki tare da kallonta yace "Oya tashi ki goge
min kujerar da zan zauna."

Da sauri Maryam ta zaro ido jin abinda yace sabida ta tuno sanda yasa INdo ta goge
mai da hijjab d'inta, ya zata yi gashi ba'a duba taba yau ta shiga uku zai ja mata.

"Ko baza kiyi vane.?!"

Ya tambayeta ganin bataje tayi abinda ya sanyata ba, hawaye suka zobu mata shi kuma
Sadeeq yak'i yin magana jiki a sanyaye tana kuka taje tasa hijabinta ta goge mai
tasss sannan ta koma gurin zamanta sai kuka takeyi shi kuma yaje ya zauna tare da
d'ora k'afa d'aya kan d'aya yana d'an kad'asu. Sadeeq ya kalli Abubakar yace.

"Bari sai na fara yi musu inspection."

Abubakar ya kallesa yace "na ina kuma..?!" Sadeeq ya d'auki rular yana cewa "na
jikinsu har kyauta nake basu that's why kazo ka gansu neat." Abubakar ya ta6e baki
sannan Sadeeq ya tafi farawa wanda har lokacin bemasan INdo na ajin ba, Abubakar
yace "okey twinnie duk wani wanda beyi maka wani abunba ka turosa nan gurin." Ya
fad'a yana d'aukar wayarsa dan kiran Qibd'iyya yace mata ya sauka lafiya kuma yaji
sassanyar muryarta mai sanyi.

'Yan aji najin abinda ya fad'a kowa ya fara duba abinda beyi ba dai-dai lokacin da
Sadeeq ya k'arasa gurin bencin da yake farawa kuma INdo ce a farko dan haka kafin
ta gama duba abinda bata yiba har ya k'arasa.

"Ohh my God..! Wacece wannan kamar Aisha?"

INdo ta dashare baki kamar gonar auduga yayin da 'yan aji suka bita da kallo shi
kuma malam Sadeeq ya saki wani tattausan murmushi ganinta yau tsab-tsab da ita sai
dai makeup d'in da tayi ne duk ya cuceta dan duk ta cika fuskar da d'ige-d'igen
baki da janbaki sai dai yaji dad'i dayaga tayi wanki yace.

"Toh muga bakin." Ta bud'e mai hak'oran nata ya gani ya d'aga kai sun d'an fi na
baya ya kuma cewa "muga kanki." Nan ma ta bud'e da saurinta ya kalla gashin nan
yayi d'as da kitso ya kuma kad'a kai domin tayi k'ok'ari sosai lallai hakan yana
nuna masa cewar ba k'aramin son a bata kyauta takeyi ba yayi murmushi yana wani
sak'e-sak'e cikin ransa kafin yace.

"Toh kinyi komai Aisha muga farcanki."

Sai a lokacin ta tuna sam bata yanke ba sai ta 6ata rai idanunta yayi rau-rau zata
yi kuka dan tasan rashin yanke farcen ba k'aramin asara zai janyo mata ba Sadeeq ya
kuma cewa "muga farcan ki Aisha."

A hankali ta mik'a mai hakan yasa shi saurin kallanta domin beso ta fad'i
tausayinta ya kamashi ba yadda zaiyi dole yace.

"Aisha baki yanke farce ba, tashi kije wajan doctor Abbakar..."

Tana hawaye tace “Amma malam hikadai nefa banyi ba kuma wabillahillaxi mancewa nayi
dan Allah kayi hakuri kabani atamfar.."

"Tashi ki fito Aisha."

Tashi tayi tana kuka domin ba k'aramin haushi takeji ba ta k'arasa wajan Abubakar
wanda waya take kare a kunnansa shi kuma Sadeeq ya cigaba dayi idan yaga wanda beyi
wani abunba sai ya turasa wajan Abubakar, shi kuma ganin yara sun taru a gabansa
yasa shi cewa Qibd'iyya.

"M love bari na barki zan..." Ya kasa k'arasawa sabida ido hud'u da sukayi da INdo
zuciyarsa tayi wani rass gashi idanta yayi jah sabida kuka sai kawai yaji zuciyar
sa nayi mai wani irin zillo ya kashe wayar bema sani ba sannan ya mik'a hannunsa ya
janyo na INdo ita kuma ta fara dak'irewa a tunaninta dukanta zaiyi ta fara ihu tana
bashi hakuri shi kuma ya damk'e hannun nata sabida yadda yaji shi cikin wani irin
mood akanta....

Love u m Fan's👍

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

_Shafin yau naki ne tawan daughter'n My Nana Hafsatu Xoxo da Nana Hafsatu Rano
wato *BILLY S FARI* wannan mata Allah yayi miki abinda kikeso duniya da lahira, ya
azurtaki da 'ya'ya na gari masu albarka. Hajja ce tana sonki kamar yadda take son
H², Allah yabar k'auna da soyayya.😍_

Page *7*

Da gudu suke bin ta suna cewa ta basu bokitan su na talla amma tamkar iska gudu
kawai take har se da ta shige cikin gida sannan ta dire bokitan ta zauna tana maida
numfashin wahala. Inna ta kalleta tana jimamin hali irin na 'yarta ta ganin babu
ranar da zata fito ta fad'i INdo bata yi wani abun na zagi ba, wannan dalilin ne
yasa tayi niyar zuwa gidan me salati ko zata samu wani temakon da za'ayi mata akan
fitinar ta amma baban su ya hana yace shi 'yarsa lafiyar ta sumul.

Kad'a kai kawai Inna tayi ta cigaba da mark'ad'an ta akan irin dutsen nan, INdo na
gefe su kuma su Idi sai faman kumbura suke ta bud'i bokitan Ubale me d'auke da
awara ta d'ibi guda biyu sannan ta tura mai bokitin nasa, ta janyo na idi shima ta
d'ibi wainar rogo ta mik'a mai sauran tana cemusu.

"Naci lada kuma wabillahillazi kuka sake ganina kuka fad'i wata kalmar sai na
jamuku asara kuce ba suna na A’isha ba." Suka d'auki bukitan su sukayi waje kowanne
da irin kalar wulak'ancin da zai mata a zuciyarsa, Nafeesa k'anwarta ta shigo gidan
tana ganinta tayi saurin 6oye kwanon awarar dan karta d'aukar mata.

"INdo rowar jaraba." Cewar Nafeesa tare da k'arasawa wajan INdon ta zauna harda su
tankwasa k'afafuwa ta mik'a mata hannu alamar ta sammata.

Mtww "idan ni marowa ciya ce dalla malama kekuma mecece? Ungoni ki matsa ki bani
guri." Ta juya tana kallon Inna tace "Inna ga awara idan zaki ci."

Inna ta k'araso gurin tana cewa "Ni wallahi 'yar nan bana son wannan fitinar taki,
inda Allah ya temaka ma kun koma makaranta zaku shiga ajin gaba ni banaci na k'oshi
da abin fitina." INdo ta fara sosa kai tana kanne ido d'aya sabida jin zafin yajin
bakinta tace "Inna wallahi bazan koma makarantar nan ba wata zaku sakemin, wai
d'azu harni malam Sadeeq zai cewa tinkiya! Wallahi toh bazan koma ba yaje yacinye
makaranta."

"Yanzu kin dena zuwa 'yar nan? Toh wacce kike son a mayar dake ke ba tsayayyan
saurayi ba bare ayi miki aure yau na shigesu ni Maryama."

"Inna wallahi bazan koma tsefawa ba na fasa zama likitar dama temako zan dinga yi
toh yanzu kuma nafasa suje sunemi wata." Inna ta kad'a kai babu abinda zata iya
cewa akai koda baban su ya shigo ma bata gaya maiba bare su d'auki wani mataki haka
suka barta kullum bata nan unguwar bata waccen har aka d'iba sati biyu ko hanyar
makarantar bata bibare asakaran zata shiga, tsab Sadeeq ya manta da ita domin ya
toshe duk wata hanya daya san suna had'uwa.

**
A 6angaran Abubakar kuwa yana matuk'ar son Mareeya har hakan ya fito fili ragowar
nurses suka fuskanta, wasu suka hakura dashi yayinda wasu kuma suka d'auki tsana da
takura suka d'orasa akan ita Mareeyan suna ganin itace tayi wani kulla-kullan har
ya karkata wajanta ya barsu. Sosai suka shaku Abubakar har ya had'a su da Sadeeq
awaya suna gaisawa hakan ya sake narkar da sonta a cikin zuciyar Abubakar d'in.

**

Wata ranar juma'a ne Sadeeq dayaje makaranta dama duk juma'a yakewa 'yan ajinsa
duban tsabta, yana duba farcensu, hak'oransu, mata ya duba kitso maza kuma aski da
kuma uniform duk wanda yafi kowa tsafta zai bashi kyauta. Ashe INdo ta samu labari
yau yana cikin dudduba su sai gata ta shigo askwane cikin ajin malam Sadeeq ya
kalleta cikin tsananin mamaki kamar aljana uniform d'in nata sharkaf da ruwa a haka
tasa su gashi tayi wata mahaukaciyar kwalliya kamar wata ifirituwa ta fara tafiya
zuwa bencin su Uwani halilu suka matsa mata har ta kusa kai duwawunta k'asa yayi
saurin dakatar da ita ta hanyar yi mata wata razananniyar tsawa ya had'a da cewa.

"Ke meya kawoki wannan ajin? Wacece ke haka? Daga wane sahun aka zakuloki..?!"

INdo ta kalli kan teburinsa taga kayan kyaututtukan da zai bayar sai ta dashare mai
jawur d'in hak'oranta domin tunda ta siyi brush da makilin d'in nan bata ta6a yi ba
zuwa tayi ta zubesu a gida toh dama ba'a sababa ta k'arasa zama tukunna tace masa.

"Haba malam Sadeeq nicefa INdo malam Hamza."

"Will you shut up...Nonsence, zoki fitar min daga aji wawuya waya kawoki jss 3?
Keda har yanzu kina jss 1 shine yau zaki wani shigo min zoki fita kafin na lahira
ya fikijin dad'i." Yayi maganar yana nuna mata k'ofar data shigo ransa a matuk'ar
had'e, sai ta fara kallon 'yan ajin d'aya bayan d'aya tare da mutsittsike idanuwa
taga dai still sune dai 'yan ajin nasu na da amma ya za'ayi yace wai nan ba ajinta
bane dan shi munafukine, tokuwa babu inda zata dan nan gwamnati ta tsaga mata dan
haka tayi kicin-kicin da fuska wai taga ko zai kuma cewa tafita.

"Ke Aisha ba magana nake yi miki ba?"

Ya fad'a yana k'arasowa bencin da take, INdo tayi saurin mik'ewa tana kallonsa tace
"Yo toh malam duk fa k'awayena ne kuma 'yan ajinmu ne ya zakace na fita ina zanje
ni."

Yace "Tallah, koba ita kika fiso ba? And bakin ce bazaki sake suwa tsefawa fa yau
kuma wane munafuncin ne ya shigo dake da wasu jik'akk'un kayanki kila ma fitsarin
kwance kika yi, oya zoki out kina 6ata mana lokaci."

Duk cikin maganarsa babu wacce take k'ona mata rai irin yace tazo ta fita, kuma
kallon kayan kyautar tayi kawai sai ta rushe da kuka tana fad'in "Kai malam.. Kai
malam, sai da kaga nazo na kusa cinye kyautar nan shine zaka ce natafi ba ajina
bane. Toh malam wane ajin zan koma kuma?."

Tsananin mamaki ya cika Sadeeq ganin tana kuka, tunda yake be ta6a ganin hawayenta
ba sai yanzu haka kurum kuma sai yaji duk ya tsani kansa domin yasan ita d'in
mahaukaciya ce ya kamata ya dinga bata kulawa ta wani 6angaran ko Allah zaisa ta
gyara wani abun hakan yasa shi juyawa yanaci gaba da duba 'yan ajin har ya zabo
mutum shidan da zai bawa kyautar . Yana zuwa kan INdo tundaga kan uniform ya fara
rankwashin ta domin haka yake yiwa duk wanda yake da gyara, INdo tayi saurin dafe
gurin tana furta.
"Kai...kakai...kakai..! Malam da zafifa." Yace "ha..bakin muga teeth naki." INdo da
taji yace ha bakin yasa ta bud'e mai tamkar zata cinyeshi yayi saurin matsawa
sabida wani hamami dayake tasowa daga ciki yana toshe hanci yace.

"Such a stupid hak'oranki zaki nuna min bawai cewa nayi ki hangame min ba."

Hannu tasa ta toshe bakin tunawa da tayi lokacin da sukace bakinta yayi yalo ya
kalleta yace.

"Bazaki bud'e ba saina mareki..?!"

Ta d'aga maikai bakinta a toshe da hannunta tace "Malam gara ka marenin da na bud'e
ma ballahillazi." Mtwww yaja tsaki dan yasan babu abinda za'a za6a a gurinta, ya
kuma matsawa ta baje hancinta tana shak'ar k'amshin turaren jikinsa yace "muga
farcenki." Tana jin haka tayi saurin zame hannunta daga baki ta cukwaikuye hannuwan
acikin hijjabi tana zaro mai ido ya kuma kuluwa yace "muga kanki..?!"

A hankali ta bud'e shi ya kalla tare da ta6e baki ya bar gurin, akwai kitso saidai
ya tsofa sosai dan ko tsagar ba'a gani gashi gashin nata jah ne kamar gashin akuya
sai dai da ka ganshi kasan zaiyi laushi domin irin me yalai-yalai d'in nan ne, ta
kalli Uwani halilu tana sosa hanci tace.

"Uwani kin ta6a cin gasar kuwa?!" Uwani ta harareta tare da k'in bata amsa ganin
haka yasa tayi mata kallon sama da k'asa tana fad'in "ji banza kina jima ina
tambayarki." Malam Sadeeq ya d'akko wani yadi na maza ya mik'awa D'ahiru Miko ya
durkusa har k'asa ya kar6a sannan yayi godiya malam Sadeeq yace.

"Ku tafawa D'ahiru miko ya samu wannan kyautar ne saka makon d'inkin uniform d'insa
sabo ne, yayi aski sannan baya barin farce zak'o-zak'o gashi yana k'amshi babu wari
a jikinsa hak'oransa ma sun fara haske.." Aka fara tafawa raf-raf-raf INdo sai
k'arayi take da k'arfi har aka gama yi sau biyar yadda ya koya musu INdo bata
denayi ba sai da yace "ke inji..!, ya isa haka baki ji yadda suka had'u suka yi
nasu ba ne a tare?" Sai a lokacin ta dena amma fa bakin nan a wangale tamkar ita
aka bawa yadin.

Mace kuma Murja Ashiru ce ta samu ya bata fallen atamfa biyu itama aka tafa mata
still INdo sai da ta zarce har wani dak'irewa tayi sai da Atika bawa ta bige mata
hannun sannan ta denayi yace musu "Yau Atika bawa tafi ko wace mace tayi kitso
harda kunshi, kayan makarantar ta harda guga babu farce ta yanke itama tayi brush."
Aka sake tafawa sam INdo bata iya ba da kowa zai denayi amma ita sai ta k'ara. har
ya kammala bama ragowar suka koma suka zauna yayi musu nasiha akan tsabta sannan ya
kwashi littattafansa zai fita INdo tayi saurin cewa.

"Malam...!" Ya tsaya cak ba tare daya juya ba tace, "nima wata juma'ar zanyi duka
amma ni hadda (shadda) nakeso ruwan bula kaji ko...?!"

Juyawa yayi ya kalleta sannan yace "Toh kiyo amma bake zaki gaya min abinda kike so
ba sai abinda nayi niyar bayarwa kinjiko..?!" Tayi shiru bata amsa mai ba yayi
tafiyarsa ta zauna tana cewa "kajishi fa, salan kawai a baka abinda bakaso mtww."
Babu wanda ya kulata ta mik'e ta koma wajan Atika ta k'arbi atamfar tana gani ji
take inama ta tace har ta hango irin d'inkin da zatayi dan taga wani style a jikin
Rukayya amarya. Duk wanda aka bawa kyauta sai da taje ta ansa ta gani har ta fara
Allah-Allah wata juma'ar tazo itama taci za6e....
*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

Page *9*

Still hannunsa na rik'e da nata ya rik'e sai kallon fuskarta yake dan ba k'aramin
kyau kwalliyarta tata tayi mai ba, INdo kuma sai k'ok'arin ture mai hannunsa take
tana hawaye murya k'asa-k'asa kamar munafiki yake mata magana yace.

“What's your name make up artist..?!”

INdo tayi shiru sai tasa ka hijjab d'inta ta sharo hawayen fuskarta duk bak'in
kwallin da tayi kwalliya ya wanke hijjabin daga gaba Abubakar ya kalleta sosai shi
har lokacin begano taba domin be ta6a ganinta tsab-tsab kamar yau ba ya kuma cewa.

"Baby ya sunanki ne.?!"

Sai a lokacin INdo ta fahimta ya kalleta ya kuma cewa,

"kinga kin goge kwalliyan naki da kuka ki dena kinji ko? Ya sunanki??"

Ta share majina da bayan hannunta wanda be rik'e ba ai yana gani yayi saurin sakar
mata d'ayan hannun ita kuma ta matsa baya tare da cewa cikin kuka.

"INdo malam Hamza." Abubakar ya d'an zaro ido waje kad'an kafin yace.

"Zonan gurin." Ya nuna mata inda yake son ta tsaya da k'afarsa, a hankali taje
gurin ta tsaya sai dai idanunta nakan tebur din da malam Sadeeq ya ajiye kayan
kyautar da zai bada. Tsaye tayi mai k'ik'am sam hankalinta baya kansa shi kuma ya
kalleta yana murmushi yace.

"Woww sunan Mama na gareki, toh amma ba zaki tsugunna ba kika min k'erere..?!" Da
sauri ta tsuguna still fuskarta na wajan kayan, ganin bashi take kallo ba yasa shi
maida kujerar sa saitin da idanta yake gurin tayi saurin kallansa ya tsuke fuska
yace. "Menene baki yi ba aka fito dake?!" Ta cukwai-kuye hannunta tun kafin ta
bashi ansa dan tasan mugune a hankali tana turo baki daya sha bakin kwalli a le6an
tace.

"Wallahi nayi komai, kawai farce na manta ban cire ba shine malam Sadeeq yace na
fito kuma wallahi malam..." Ya zabga mata harara tayi saurin toshe bakinta da
hijjab kafin taga ya dena tace. "Kayi hakuri dakta Habubakar mantawa na keyi kace
ba sunanka malam ba, amma wallahi nayi niyyar yankewa niko dan naciyo atamfa amma
duk saina manta hef (shaf).."
"Ohh muga farcan naki.." Ta fito dashi yasha lalle a yatsun ta nuna mai, hannu yasa
ya janyo nata yana kallah murya sanyaye INdo tace mai. "Dan Allah Dacta Habubakar
kace ya bani ni yanzu ma zan iya cire farcen, dan iyayanka kace ya bani dan Allah
kaji..?!"

Sadeeq ne yazo gurin ya kalli d'an uwan nasa rik'e da hannun INdo hakan ya bashi
matuk'ar mamaki da al’ajabi cikin sauri Sadeeq ya zare hannun INdon daga na
Abubakar cikin harshen turanci Sadeeq yake mai magana cewa.

"Twinnie why na?am i day dreaming or are you really the one holding a village girl
hands,and if you have forgotten about it then I haven’t ,this villagers are cruel,I
don’t want them to think something else in their mind ..This is so not you”

Cikin ko’a jikinsa abubkhr ya daga kafada sannan yafara magana,

"Habba twinnie sunan Momcy gareta fa shi yasa, gashi kuma tayi kwalliya irin wadda
nake so that's y kaga ina iya rik'e hand's na ta."

Mtwww "inajin baka ganeta bane shi yasa kake sakar mata fuska, toh bari na tuna
maka kowa cece INdo malam Hamza, wannan me satar amsar ce me cizon maza nasan yanzu
ka harbo ta."

"Really my twinnie? Abubakar ya fad'a yana sake maida kallonsa fuskar INdo,
kwakwalwarsa kuma tana sake hasaso mai lakacin daya kamata ta duk'ufa tana kwafar
note dan sam koda ta kwafo ma bagurin da aka tambaya bane, ya kuma kallon Sadeeq
cikin mamaki yace

"Gaskiya m twinnie kayi k'ok'ari indai haka ne. Ashe k'azan tace duk ta maidasu
mahaukata Gaskia I'm sure nan gaba za'a sha mamaki indai suka d'ore da haka za'aji
dad'i sosai."

K'afarsa yaji ana jijijigawa hakan yasa shi saurin kallon k'afar kawai yaga INdo ce
take mai alamar magiya tana nuna mai ya samo mata kyauta kota meye Sadeeq dake fito
da kayan zai bawa wad'anda suka ci ya kalli Abubakar dake kallon INdo kawai yaja
tsaki sabida takaici. INdo kam sai nunawa Abubakar malam Sadeeq takeyi alamar be
zabo mataba zasu k'are yayi dariya cikin zuciyar sa ya kalli sauran masu kuskuran
yace.

"Kuzo nan muyi photo daku." Suna jin haka suka ruga bayansa suka jeru amma sam INdo
batayi gigin zuwa ba hankalin ta yana wajan malam Saseeq dayake ta rabo zuciyar ta
tamkar ta fito tsabar fargaban karsu k'are.

"Humaira zo mana ayi dake." Abubakar ya fad'a yana kallon Indo , ita kuwa bata
masan da ita yake ba tana ji tana gani har malam Sadeeq ya kammala bada kyautukan
taji wata muguwar tsanarsa tundaga k'asan zuciyar ta ya game da ilahirin jinin
jikinta tayi ta zagba mai harara bemasan tanayi ba yana can yana sake yiwa wad'anda
sukaci kyautar nasiha da kuma muhimmancin tsabta da Ilimi.

“Kuje kuma ku zauna kowa yaje gida yayi karatu ranar Monday zanyi muku test duk
wanda ya fad'i ni nasan irin hukuncin dazan d'auka akansa kunajina ko?!"

Malam Sadeeq ya fad'a bayan yaga yau twinnie d'in nasa da mutunci ya shigo, duk
'yan ajin suka ce "OK uncle." Dayake yana k'ara d'an wayar dasu, amma INdo data
tashi sai da ta d'auki ledar littafinta ta faki idonsu duk da cewar Abubakar nason
yayi mata photo da kwalliyar ta yana can yana tambayar Sadeeq mezai iya bata koda
ba babba bane ba sukaji tana cewa.

"Baza'ayo karatun tess (test) d'in ba, kai idanma kun sake ganina a makarantar nan
dan Allah ku soya ni. Wallahi malam Sadeeq yayi karya kuma ance babba me karya d'an
wuta ne gobe k'iyama yana kusa da fir'auna, Allah ya sakamin sabida na kashe
kud'ina garin yin kunhi da gyara kambas d'ina sai Allah ya saka min. Yo dan baka
bani atamfar ba seme, nima Inna ta zata sai min ai sallah ta kusa."

Tana gama fad'a ta murgud'a baki ta juya da gudu zata arce taji an rik'eta gam
cikin tsananin tsoro da tashin hankali tayi k'ok'arin juyawa taga waye sai taga
malama Murja ce ta cafketa tare da tura ta cikin ajin, tana zuwa ne da yake period
d'inta ya shiga sai taji irin rashin kunyar da takewa malamin hakan yasa tayi shiru
sai data kai k'arshe zata gudu tayi saurin kamata.

Tsananin mamakinta suka kama Abubakar, sai yanzu ya kuma tabbatar da cewa itace ya
tashi a fusace yayi kanta jin yadda take gayawa twinnie d'in nasa magana. Sadeeq ne
yayi saurin taresa yana kad'a mai kai alamar karya doketa, yana wani irin numfashi
ya ture hannun Sadeeq d'in daga kafad'arsa yana cewa.

"Ka rabu dani Sadeeq bakaji yadda take had'aka zama da fir'auna ba, barni naci uban
shegiyar yarinyar nan da har ina tausaya mata ashe batada mutunci har yanzu."

"A'a twinnie barni da ita, kayi hakuri ka kwantar da ranka. Malama na gode da gudun
mawarki, ke kuma zonan..." Sadeeq ya fad'a yana damk'o hannunta Abubakar kuwa
jiyake tamkar ya ham6areta sabida 6acin rai. Fita yayi da ita sai ihu take musu har
suka k'arasa cikin staff room ya kalleta yace.

"Kama kunnanki."

"Dan Allah malam kuyi hakuri."

Babu wanda ya kulata sai dai duk malam cikin staff room d'in saida suka bada shedar
rashin kunyar INdo, ganin babu mebada hakuri ne yasa ta sunkuya ta zura hannunta
tana nishi tana cewa "malam wallahi hannuna baya kaiwa abakacin sa kace nayi nibdom
(kneel down) kaji."

Jiyosu ma tayi suna hira babu wanda ya kulata dan yau takaisu bango, tun tana
magiya har tayi shiru. Ta dad'e tana kamun kunnen kawai suka ganta ta fad'i k'asa
Abubakar dake kusa da gefenta besan lokacin daya kai hannu zai tarota ba amma saida
tayi k'asan, ashe baccine ya kamata, kuma duk da fad'uwar da tayi hakan besa ta
tashi ba saima zarcewa da tayi tafara sauke munshari.

"Twinnie mu wuce tunda ka gama."

Beh jira cewar sa baya k'arasa inda INdo take kwance sai uban munshari takeyi
tamkar wata babbar mata a hankali ya dinga k'iran sunanta amma inah ko motsawa
batayi ba, hannu yasa dai-dai kafad'arta yana jijjigata nan ma still bata motsaba.
Ganin yadda yake bin ta a hankaline yasa Sadeeq mik'ewa ya d'auki dorina yana zuwa
ya tsula mata a baya. A razane ta mik'e ta rarumi Abubakar dake tsaye kusa da ita
tana cewa.

"Wayo Allah atamfata ce."

Sak'e tsula mata yayi tayi saurin sakin Abubakar tayi k'ark'ashin tebur d'in malam
yahaya tana kuka tana sosa gurin cikin kuka take bashi hakuri yayin da shi kuma
Abubakar ya fita daga cikin staff room d'in. Sai da wasu malam suka bawa malam
Sadeeq hakuri sannan aka ce taje ta tsugunna ta bashi hakuri tayi sannan ya hakuri
yace kuma duk sanda ta kuma yin fashin zuwa makaranta sai yasa ankamota yayi mata
duka tace toh.

Fitowa yayi amma bega Abubakar d'inba har ya fita gate babu bare alamun motarsa,
sosai Sadeeq yayi mamaki sai ya nufi gidan shima amma abin mamaki bako motarsa a
gurin hakan yasa shi kiran wayarsa aka sanar mai cewar a rufe take, mamaki ya kuma
sark'e Sadeeq. Yana tsaye a gurin har su INdo suka wuce suna gulmarsa be kulasu ba.

Shi kuwa Abubakar yana fita motarsa ya hau yakama hanyar gida, haka kawai yau yaji
baya son jin kukan INdo zuciyarsa har zafi take mai duk kuwa da cewar yasan itace
batada kunya amma ya rasa dalili, tunda ya taho tunaninta yakeyi yayi-yayi ya
halasto qibd'iya ya kasa sai dai INdo da kamanninta ya buga sitiyarin motarsa yafi
sau ashirin harya k'arasa gida. Yana shiga yaji Maman su na cewa.

"Kajishi can najiyo tsayuwar motarsa da alama ya dawo. Toh shikenan 'biyu kyautar
Allah kaima Allah yayi maka albarka." Sai da ya bari ta kashe dan yasan da Sadeeq
takeyin wayar sannan ya shiga cikin gidan nasu bakinsa d'auke da sallama....

_Kuyi hakuri da wannan, kunsan bawa duk yadda yaso yayi abu idan Allah bebashi dama
DA iko ba toh babu abinda zai iya yi a rayuwarsa. Nagode luv you all._ Gaisuwa da
fatan alkairi zuwa ga aunty Sdy jegal, Ina miki fatan alkairi a duk inda kike,
Allah ya raya mana baby boy d'inmu cikin addinin musulinci.😘

*HAJJA CE*👈
[7/1, 4:53 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

_Shafin yau na kune 'yan grp d'ina wato *HAJJA CE NOVELS GRP* da *ZAURAN BIEBIE
ISAH* tare da *🅿HERTY NOVELS* da *MUSHA KARATU N YBK2* gara nayi muku jam'u domin
idan na tsaya lissafoku sai kunji haushina kunce dama typing nayi muku da wannan
lissafin. Hak'ik'i ina jin dad'in yadda kuke tare dani, comments d'inku nasani
dariya da kuma nishad'i uwa uba kwarin gwaiwa. Nagode sosai #ana tare da INdo
malama Hamza._🤝😍

Page *10*

Amsawa Maman tayi tana had'a musu zo6o. k'arasawa yayi ya zauna akan kujera 'yar
tsugunno sai faman shafa sajen fuskarsa yakeyi. Umma Dijeh ce ta fito daga parlor
kasan cewar muhad'u a parlo ne ta kallesa tana murmushi cikin wasa tace mai.

"Likita bokan turai, daga sallar juma'a kuma sai ina? Ko yauma za'a lek'a mak'ota
ne..?!"

Wayarsa ya zaro zai kunna domin tunda ya baro makarantar ya kasheta sabida yasan
dole Sadeeq ya nemeshi, shikuwa beshirya abinda zai gaya masa ba. Kallan Umma Dije
yayi sannan yayi murmushi yace.

"Haba Umma jiya fa naje, kuma yauma bata nan." Dariya suka yi itada Maman sannan ya
tashi ya fito yashiga d'akinsu, kayan jikinsa ya rage ya zauna daga shi sai vest da
boxer shorts sannan ya kuma d'aukar wayarsa dai-dai lokacin kuma Sadeeq ya kuma
kiransa. Babu yadda zaiyi dole ya d'aga kodan ya kare kansa daga wajan abokin
haihuwar tasa, cikin basarwa ya kara a jikin kunnansa tare da fad'in, "My twinnie
sai kaga na taho ko?!" Sadeeq dake zaune a k'ofar gida ya ta6e baki sannan yace.

"Ba gani nayi ba nemanka nayi na rasa wanda kuma ni bansan dalilin yin hakan ba,
twinnie kasan irin tashin hankalin daka sakani? Da police station zanje nakai
report sai kuma muka yi waya da Mother take cemin gakanan ka k'arasa why did you do
this to me ah?!"

Duk sai Abubakar d'in yaji babu dad'i ganin yadda duk ya tayarwa da d'an uwan nasa
hankali, da kyar ya samu mafitar da zai wanke kansa ya numfasa tare da cewa.

"Kayi hakuri nima saida na taho naga rashin dacewar hakan tunda bamuyi sallama ba,
abinda ya faru shine ina fitowa Dr Inuwa yake sanar dani ana nemana a cikin
asibitin da gaggawa shi yasa duk na rud'e na kashe wayana dan karsu dunga damuna
sorry twinnie kaji kayi min afuwa.."

"Okk bakomai yanzu tunda naji kana gida sai anjima."

Kamar ya tambayesa INdo sai kuma yayi shiru suka ajiye wayar shi kansa besan yadda
zai fad'i abinda yakeji ba har mamaki yake yi ya ajiye wayar yashiga toilet. Wanka
yayi lokacin har an kawo mai abincinsa an ajiye amma ko kallansa beyi ba sai wayar
ya sake d'auka ya shiga gallery, hotunan dayayi mata ba tare da kowa ya sani ba.
Yana gani yana duba na e so yake yagano meke damunsa amma inah..ya kasa tantancewa
sai faman k'aryata zuciyarsa yake yi da abinda take shaida mai.

INdo kuwa tana zuwa gida ta fara cire kayan jikinta tana killarwa ta sanya wata
kod'add'iyar shadda doguwar riga wanda ta d'age mata sannan ta dawo tsakar gida ta
zauna tana kallon kunshinta. Wani irin tsanar malam Sadeeq da Abubakar suka sake
mamaye cikin zuciyarta ta cewa Inna.

"Inna wanki zanyi gobe na tafi gidan yakumbo Tsahare, wallahi billahillazi bazan
sake zuwa makaranta ba saye zan yi tafiya ta naga ta tsiyarsu mugaye."

Cikin dafe k'irji Inna tace "ke 'yarnan saye kuma? Kiyiwa Allah da ma'aiki kiyi
shiru da maganar tafiyar nan kinsan dai babanku baya son zuwanku garin nan tun
abinda ya faru tsakaninsa da jummala."

"Inna wallahi saina tafi, kina jinfa abinda mugun malamin nan yace, wai idan na
dena zuwa makaranta saiya saka an d'akkoni toh wallahi barin garin zanyi hena dad'e
sannan zan dawo a'he."

Hankalin Inna ya tashi dan tasan idan baban su yaji toh lashakka sai anyi fitina
duk da cewar tsaharan k'anwarsa ce amma tun a haihuwar shehu suka samu sa6ani akan
naman suna shikenan sukayi baram baram kuwa yace bashi ba d'an wansa sannan yacewa
Inna ya haramtawa 'ya'yansa zuwa garin idan sukaje kuma Allah ya isah. Tashi INdo
tayi tabar gidan ta shiga gidan Rukayya, tana ganinta ta fara murna tare da cewa.

"Kai INdo shine ko a kawo min kyautar ingani ko?!"

Saida INdo tasamu guri ta zauna sannan tacewa Rukayyan "Yo ai basu bani ba, wai
wani ban yanke farce ba ninasan dama malaman nan ba kaunata sukeyi ba kawai dan dai
nafi karfin sune bayadda zasu yi dani shegun."
"Kan uba! Yanzu kina nufin babu abinda malam Sadeeq yayi miki?!"

"Sai duka nama dayayi kuma nace Allah ya isa." Nan suka cigaba da hira har INdo na
bata labarin tafiyarta saye gobe Rukayya tace.

"Kai INdo sai kuma yauhe zaki dawo?!" INdo na watsa shinkafa da wake tana cewa
"babu lokaci idan na tafi henayi aure zan dawo yasin."

"Kai INdo baxaki dawo ba kenan?!"

Rukayya ta kuma tambaya cikin jimami, ita kuwa INdo ko'ajikinta tace "Eh bazan dawo
ba he randa malam yadena zuwa garin nan."

"Kai Allah ya wadaran wannan malamin da yaja zaki tafi, zamuyi rashinki INdo barema
Inna."

"Kyale Inna can na barota sai masifa take dan nace zani saye wai bazani ba toh
alkur'an saina tafi."

Haka suka dinga hira da Rukayya har bayan la'asar sannan ta koma gida inda ta tarar
da Inna ta gayawa babansu yace toh babu inda zata ta kule d'aki bata sake fitowa
ba. Tun asubar fari ta farka ta tsinci kayanta tasa a d'ankwali ta d'aure ta
d'auk'e fitilar da aka haska d'akin da ita wato shekarau mekwayayen nan k'ananu a
jikin katako tayi sad'ab-sad'ab gidan a kulle yake ta jefa kullin kayan ta katanga
sannan itama ta kama ta dirga ta kwashe kayan nata ta an taya da gudu sai bakin
titi ko tsoro bataji.

Tayi tafiya sosai sannan gari ya fara haske daman babu buk'atar yin sallah dan
bawani yi takeyi ba sai taga dama. Mota na zuwa ta tsayar dasu ta shiga dama da
d'ari ukunta a hannu data ara wajan Rukayya. Can gida kuma tunda suka farka suke
neman Inndo, duk gidan da akasan tana zuwa saida akaje bata nan. Kuka Inna tasanya
domin tasan yau INdo tayi mata abinda zai iya 6allamata aure, lokacin da baban yaji
cewa yayi k'arya Inna takeyi tasan ta tafi dan haka itama ta shirya tabi bayanta su
dawo tare kasan cewar sunsan zata iya zuwa. Ko kud'in mota Inna batada su amma a
haka malam Hamza ya takura mata kan cewa sai taje ta dawo da INdo haka ta fito tana
hawaye. A bakin titi malam Sadeeq ya ganta harya wuce ya dawo duk da cewar ta rufe
fuska da mayafin jikinta tana share hawaye yaje yace.

"Baiwar Allah kiyi hakuri lafiya dai ko..?" Shiru batayi magana ba duk da besan
kowace ba ya zaro d'ari biyar ya bata babu yadda zata yi ta k'ar6a tana ta zazzaga
mai addu'a shidai ya wuce ita kuma mota na zuwa tashiga tana fatan Allah ya
temaketa can din INdo ta tafi, ayau bazasu kwanaba zata dawo da ita.

Wajan k'arfe biyu da rabi INdo ta shiga wata rugar fulani anan cikin sayen bakinta
a washe hannunta d'auke da kullin kaya, suna zazzaune k'ark'ashin bishiya suka
hangota nan da nan yakumbo tsahare ta had'e rai fuskar nan babu yabo babu fallasa
tana dakan fura haka INdo ta k'arasa gurin tana dashare musu hak'ora.

"Wacece wannan kamar mai sunan Gwaggo..?!"

Cewar talatu yayar malam Hamza dake kwance, INdo ta k'arasa tare dayin cilli da
d'ankwalin kayan nata tace.

"Nice nan yakumbo talatu ahe duk kuna nan, yau dai gani a garin ku ina
kwananku...?!"

Duk suka amsa suna tambayar ta su Sagiru da Nafeesa da Shehu tace lafiya lau amma
banda yakumbo tsahare daketa faman dakan fura, ko ajikin INdo ta mik'e tare da zuwa
wajanta tana cewa.

"Sannu yakumbo tsahare, ina su lawisa take..?!"

"Ke karki yimin rahin kunya aradun Allah kuwa, idanma Ubanki ne yau ya turoki toh
dagake harshi d'in zan iyayi muku rahin mutunci jacan ki bani guri ni."

"Allah baki hakuri daga tambaya.."

INdo ta fad'a tare da komawa wajan su yakumbo talatu aka kawo mata d'umamen tuwo da
fura da nono tana ci suna hira har su lawisa suka dawo daga tallar nono, murna da
farin ciki ba'a magana duk da cewar Lawisan cikima gareta har tayi aure tsiranta da
INdo shekara biyu ne.

Cikin gidan suka wuce suna zazzaga shirmen su. Inna kuwa la'asar sakaliya ta iso
saye sabida da kyar ta samu motar da ta kawota a d'ari da talatin. Saida tayi
sallah sannan taci kwad'on rama da fura bayan sun shaida mata cewar INdo tazo amma
sun tafi tatsar nono, hankalin Inna ya tashi tace ta kalli malam iro mijin yakumbo
talatu tace.

"So nake a yau mu koma gida gahi bata kusa kuma ina neman yadda zanyi mu samu
kud'in komawa." Malam iro ya kalleta da mamaki sannan yace.

"Haba dai Maryamu, yanzu fisabilillahi har yaushe zaku koma gida, hasalima ita
INdon bata kusa kuma da kyar idan zata yadda tabiki dan tasamu yara, kuma na
tambayeta randa zata koma tace sai an kori wani malami a garin naku."

Inna ta fashe da kuka malam iro ya kalleta yana jin tausayinta dan yasan tsoran
d'an uwar matar tasa takeyi. Hakuri ya dinga bata ita dai hawaye kawai takeyi gashi
tana matukar kaunar malam Hamza duk da cewar shima yana matukar santa amma hakan
baya hanashi yimata wulak'anci. Har magariba su INdo basu dawo ba sai wajan k'arfe
takwas na dare, koda taga Inna batayi wani murna ba kotaji tsoro ita kuma nauyin
mutane ya hanata yi mata magana.

Cikin dare Inna tasamu INdo ta gama lalla6ata akan ta yarda gobe su koma amma fir
tace wallahi bazata koma ba nan zata zauna sai lawisa ta haihu koda zata koma. Da
gari ya waye haka Inna ta kama hanya dama tunda taje yakumbo tsahare bata ko kalli
inda Inna takeba har ta kama hanyar komawa sumaila.

Koda Inna ta koma gida malam Hamza baya nan, kafin ya dawo harta sarrafa musu gero
tayi musu burabusko yana dawowa yaci yayi hani'in data sanar masa cewar INdon tak'i
dawowa sai yace. "Kyaleta Maryamu ni kaina na huta da fitinarta taje can karta dawo
d'in."

Bayan sati biyu.


Tunani da damuwa da begen son ganin INdo suka addabi zuciyar Abubakar, duk iya
yinsa na ganin ya kawar da hakan daga cikin zuciyarsa hakan ya gagara. Ya rasa
meyagani a tattare da ita har yakejin irin abinda yakeji cikin ransa da gangar
jikinsa, yasan duk lokacin da asirin zuciyarsa ya fito fili zaisha wulak'anci gurin
Sadeeq dama sauran abokansa. Tashi yayi ya tafi Sumaila kauyen na sani direct babu
wanda ya sanarwa.

Yana zuwa zuwa ya tarar su Sadeeq sun tashi daga makaranta yarama sai fitowa
sukeyi, samun kanshi yayi dayin gaba zuwa unguwar su INdo ko Allah zaisa ya ganta,
amma har Sadeeq ya dawo ya tarar dashi besamu yaga ko kyallin kallabinta ba hakan
kuma ya hargitsa ilahirin tunaninsa na Ina zai ganta?

"M twinnie..! Ta6 lallai kaida kace min kaida garinnan saidai in wucewa zakayi
shine yau na ganka at this time..?!"
K'ak'alo murmushi Abubakar yayi yana kallon hanya dan befidda ran zai hangota ba.
Ganin yadda Sadeeq d'in ke kallansa ne yasa shi saurin cewa.

"Malam Sadeeq nasu INdo, wai kuwa har yanzu kana basu kyautar?!"

"Meza'a fasa twinnie? Itace dai tun ranar bata sake zuwa ba, dana tambayi babanta
rannan danaje gidan yace wai ta gudu kauyen su sai randa aka koreni zata dawo kaga
kuwa ba rana kenan.."

Daram..! K'irjin Abubakar ya buga besan lokacin da ya furta "what...?!"

*HAJJA CE*👈
[7/1, 5:02 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

_Shafin yau naki ne tawan *HALEEMATU G KHALEEL* (Aneesa didi), Allah yayi miki
albarka ya k'ara nisan kwana Allah ya tayaki rik'on Namcy na khadijatu (shareefat)
Allah ya azurtaki da miki Nagari ina sonki fisabilillah like H³_💋

Page *11*

Sadeeq ya bishi da kallon mamaki ganin yadda ya furta kalmar tamkar yace masa
shine yabar garin ko Mama. Kallansa ya kumayi kafin ya juya yayi hanyar shiga gida
yana cewa.

"Kai twinnie bafa Qibd'iyya nace maka ba naga har kana ihu."

Harya bud'e gidan ya shiga Abubakar betaso ba, hanyar gidan su INdo yabi da kallo
ji yake tamkar zai ganta amma bako kurarta haka ya k'araci zamansa kafin ya tashi
yabi Sadeeq cikin gidan. Lokacin daya shiga tararwa yayi Sadeeq harya shiga wanka
hakan yasa shi zama tare da dafe goshinsa sabida tsananin saramai dayaji yana yi.
Fitowa Sadeeq yayi zama yayi kusa dashi yana kallansa soyake ya gano wani abu a
tattare da d'an uwannasa, Abubakar ya d'ago ya kalli Sadeeq ganin yana mai kallon
tuhuma yasa shi wayan cewa ta hanyar cewa.
"Twinnie wai yaushe zakuyi hutu ne?!"

Sadeeq ya mik'e tare da janyo singlet zai sanya yace "kasan ba'a fiyeyin hutun
maulud ba so kawai sai term ya k'are ni yanzu mafa na farajin dad'in makarantar
sabida suna bani had'in kai yanzu shi yasa na dena neman transfer."

"Oh idan na fahimta kana nufin kace dama Humaira ce ke baka matsala duk fad'in
makarantar ko?!"

Abubakar ya tambaya yana zaro ido, Sadeeq yafara shafa mai yana cewa, "eh toh idan
nace maka a'a nayi kamar kuskure idan kuma nace maka eh toh shima banyi karya ba
domin tun sanda ta dena zuwa nake ganin students d'in suna k'ara maida hankali,
haka nima ban sake zagin wata ko wani ba, kai banma sake rik'e bulala ba kaga kuwa
idanma nace itace matsalata banyi k'arya ba.."

Abubakar ya dafe kai jin Sadeeq yace INdo ce matsalarsa yaji haushin Sadeeq sosai
saidai ya danne dan yanzu so yake INdon ta dawo gida bayajin zai iya hakura har
ranar da tayanke hukuncin zata dawo yayi yace.

"Amma twinnie a ganina a matsayinka na malami kamata yayi ace kaine ka fara
k'arfafawa yarinyar nan gwiwa wajan ganin tasamu wani kyakyawan abun dazai taimaka
mata a rayuwarta kuma a matsayinta na mace."

"Kai twinnie kasan kuwa yarinyar nan? Ka manta abinda tace min da addu'ar datayi
min, wai ko'a lahira ina kusa da fir'auna. Wallahi a yadda naji zuciya ta a lokacin
ko naso in targad'ata Allah yayi malamai suka saka baki na kyaleta."

Ganin yadda Sadeeq yad'auki zafine yak'arawa Abubakar damuwa, babu ta yadda zai iya
samun ganin INdo sai ta hanyarsa yau gashi ta kaishi bango yace bazai temaka mata
ba. Cikin nuna halin damuwa Abubakar yace.

"Okey naji ni nayadda zan tallafa mata koda dawani abunne nasan wata rana al'umma
zasu amfana da ita. Yanzu inason kasanya kaya kaxo muje gidan su muji inda ta
tafi."

"Twinnie wai yaushe kadawo me sauk'in kaine? Kodai-kodai so kake ka kiwata ta tun
yanzu kafara banruwa?!"

Mtwww Abubakar yaja tsaki dan shi kansa jinsa yake a wani bai-bai, yau ko kiran
Qibd'iyya beyi ba sabida zumud'in son ganin INdo.

"Kai meye haka twinnie? Ni kamar ni zan tsaya jiran wannan kurkurar yarinyar, har
yaushe ma zata waye tayi kamar yadda nakeson Qibd'iss? Kawai dai ina son mu sami
ladane ta hanyar gina mata wata rayuwar sabuwa wannan shine kawai manufata..."

"Ohh toh ai akwai irinta da suke buk'atar hakan m twinnie bawai dole sai itaba, ni
wallahi na tsani yarinyar nan garama data bar garin wawuya kawai sai idanuwa kamar
na mayu.."

"Shhhhiii m twinnie duk meyayi zafi hakan? Kayi hakuri nitunda nayi niya zan temaka
mata insha Allahu tunda kai kayi fushi..."

"Hakan dai yafi.."

Cewar Sadeeq. Sun dad'e suna hira har akayi la'asar zasu tafi masallaci Abubakar
yake cewa "M twinnie idan mundawo ina son karakani muje gurin baban ta ko Maman ta
dan Allah."

"Ohh wai daman baka manta da zancen ba?"


Sadeeq ya tambayesa yana dariya, Abubakar ya kalli katangar gidan ya tuno lokacin
da ta watso mai hijjab da takallmi yayin da Sadeeq ya tuna sanda ta watso mai
ruwan k'anzo suka wuce Abubakar na murmushi yayinda Sadeeq ke faman jan tsaki.

Suna dawowa Sadeeq ya d'auka ko mutumin nasa ya manta dan haka yak'i kallon koda
gidan su yarinyar, suna zuwa zasu yi kwana Abubkhr yayi saurin dakatar dashi ta
hanyar rik'e masa hannunsa yana cewa.

"Ya haka ne twinnie? Ina kuma zakaje?!"

"Oh wai dama baka manta ba?"

"Eh ai kasan ba'a manta yin alheri musamman idan mutum yayi niya."

Sadeeq yace "naji toh karka gayan magana,ke shiga kice ana sallama da malam Hamza."

Yayi maganar yana kallon Nafeesah dake zaune a k'ofar gida, ta kallesu ganin su iri
d'aya sak bakinta bud'e haushi ya Kama Abubakar cikin takaicin kallon da take yi
masa yasa shi cewa "Ke bazaki kibane kika saka mana na mujiya?!" Da sauri tayi
firgit tana susa tace "Ai baya nan yana can wajan aikinsa a bakin hanya."

Kallon Abubakar Sadeeq yayi dan yaga yazai yi amma sai yaga ya wani ta6e baki irin
sunyiwa kansun nan amma cikin zuciyarsa kwata-kwata ba haka bane suka juya suna
tafiya Sadeeq yace.

"M twinnie muje na kaika inda zaka temaki masu neman temako domin bawai rayuwar
INdo ce kad'ai take buk'atar hakan ba, indai kayi niyar temakawan to kazo muje wani
gidan."

Mtwwwww Abubakar yaja tsaki ganin yadda Saseeq d'in ke takura masa da zancen wani
gidan, shi duk gaba d'aya mafa yafi buk'atar yaga INdon ko zaiji wani 6arin na
gangari jikinsa da ruhinsa sun samu sassauci amma Sadeeq ya kasa ganewa ya kuma
had'e rai cikin basarwa yace, "okey bari next week zan dawo sai musan abinyi yanzu
bari na koma sabida aikin yamma gareni." Yafad'a yasan duk bala'i nan da ranar
asabar INdo ta dawo, shi dai Sadeeq be damuba dan dama be d'aukarwa wani aiki ko
takura ba bare yasa kansa cikin damuwa, yana yin alheri a duk lokacin da yake da
kud'i. Sallama suka yi a bakin k'ofa Abubakar ya tafi yayin da Sadeeq ya shiga
cikin gida cike da kewar abokin haihuwar tasa.

Abubakar kuwa tsakanin sa da Qibd'iyya sai hange daga nesa, sam yanzu ya dena
ganin kyawunta bare yaji kwarin guiwar zuwa wajanta. Ita kuma ta rigada ta kamu da
kaunarsa domin ya riga yayi mata dashen zazzafar soyayyarsa gashi ta dena kula kowa
sabida shi, yau kimanin sati uku kenan ta kasa ganokanshi ya rage nemanta ko
kiranta a waya bare ya taka yaje gidansu tad'i sam ya dena har abun ya fara
damunta.

Kwanaki na tafiya Abubkhr na kuma shiga cikin damuwa da tunani. Ana ya gobe zai
koma sumaila kauyen na sani k'aninsa Khaleefa ya shigo d'akin nasu, kwance ya tarar
dashi yayi rub da ciki ko shirin tafiya asibiti beyi ba khaleefan ya k'arasa ciki
tare da cewa.

"Yaya Habu Abba na k'iranka yana d'aki."

Beko juyo ba ya d'aga mai hannu sannan khaleefa ya fita shi kuma ya mik'e dakyar ya
sanya zilaika sannan ya fita yana wani 6acin rai. Kwankwasa k'ofar yayi Abba yace
ya shiga, yana shiga ya gaidashi sannan yasamu guri ya zauna abban yace.

"Yauwa Abbakar dama zance Mariya ne, mahaifinta yayi min magana an tambayeta wanda
ta tsayar tace kai shine nace toh ya bari nazo naji ta bakinka ya ake ciki."

Gabaki d'aya ya daburce besan lokacin da yace.

"Abba aure kenan fa..?"

Yafad'a cike da tashin hankali dashiga cikin d'imuwa, Abba ya kallesa tare da cewa.

"Eh Abbakar aure tunda ai kaine kaje gidan nasu."

"Amman Abba da an d'an k'aramin lokaci kafin ayi maganar auran nawa zuwa nan da
wani d'an lokaci."

"Amman kai Abbakar kasan dai bazan zuba ido kaida d'an uwanka kuzauna har yanzu
babu Aure ba? Kuma gashi kai har gidan su yarinyar sunsan da zamanka."

"Eh Abba ai bayi ne baza muyi ba, lokaci kawai nakeso ka k'aramin dan inason
tabbatar da wani abu dan Allah..."

"Tom naji zan k'ara maka lokaci aman da sharad'in wanan maganar tamu ta karo
karatunka zuwa k'asar Spain dan nariga na samu duk abinda ake buk'ata. Yanzu gobe
nakeson kaje abuja zakayi wani signing na tabbatar da tafiyar taka, sai kuma na
koma kan Saddiqu shima a sake mai wajan aiki."

A rud'e yace "Abba har yanzu dama kananan da burinka na k'aro karatun mu?
Innalillahi."

Ya furta cikin sanyin murya, Abba yace "Eh Ina nan da wanan burin Abbakar Ina
matukar kaunar naga kun cigaba a duniya, don Allah kucika min wanan burin nawa dan
wata ran kune iyayen k'annanku, sannan nima naji dad'i a tattare daku."

Nan da nan jikin Abbakar yayi sanyi, babu yadda zai yi dole yacikawa Abban su
burinsa ya mik'e da kyar yana had'a bango harya koma cikin d'aki.

Kwanciya yayi ruf da ciki ya fara tunanin taya zai iya samu yaga INdo har ya
tallafi rayuwarta sannan ya bawa zuciyarta abinci dan yana son ganinta ra'ayul Ayn.
Ina zaije yasake ganinta kafin ya tafi, yanzu ya yarda ba shida wani buri sai son
ganishi tare da INdo...

*HAJJA CE*👈
[7/1, 5:03 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.


_*HASKE WRITER'S ASSO..* wannan shafin na kune yau na bakushi kyauta. Allah ya
k'ara had'e kanmu ya kuma k'ara fasaha mai amfani #ana tare all_🤝😍

Page *12*

Washe gari Abubakar ya tafi abuja danyin abinda Abba yasa shi. Tunda kuma ya
dawo daga abuja kullum akwai inda zashi sam baya samun zama gashi yayi-yayi Sadeeq
ya d'aukar masa amana da alk'awarin nemo INdo ya kula da ita amma Sadeeq yak'i shi
adole idan zai tayashi toh saidai ya canza wata amma ba INdo ba, da haka sukayi
bankwana baram-baram kowa najin haushin d'an uwansa.

INdo kuwa wayyo Allah tazo saye kauyanci da k'arin abubuwa duk sun dad'a k'aruwa ta
zama tamkar 'yar garin duk inda kaje sai kaji labarinta kaf kauyan sun-santa dan
akwai shiga jama'a. Da mutum d'aya ne basa shiri wato yakumbo tsahare, sam basa
jituwa da juna ko a layin band'aki.

Ranar da lawisa ta haihu kuwa su INdo sune masu jigo, anyi ruwa anyi tsaki tazama
tamkar itace me jegon dan ta kanainaye komai lawisa kuwa sai kawaici take bata
magana. Ranar suna aka sanyawa yarinyar Raihanatu suna kiranta da Ladi kasan cewar
ranar lahadi aka haifeta.

Watan INdo biyar a garin saye ta kuma irin wayewar nan ta karkarar fulani. Jin
dad'inta kawai takeyi samari kuwa su tara ne kowa sonta yakeyi suna yi mata
kyaututtuka sosai dan da haka take tattara kaya sawa tana kuma siyan kayan kwalliya
abin sai wanda ya gani duk bak'in cikin yakumbo tsahare sai dai ta kawar dakai.

Ta manta dasu Inna tama manta dasuwaye malam Sadeeq sam yanzu rayuwarta takeyi babu
takurawa...

*BAYAN SHEKARU UKU*

K'arfe hud'u da rabi da minti shida, Sadeeq Salman Haruna ne cikin mota 403 ash
color yana bin bayan wata kyakyawar budurwa. Tafiya take cikin nutsuwa da iya bawa
k'asar da take takawa hakk'inta, duk da cewar taga ana binbayanta hakan besanya ta
waiga ko tayi alamum tsayawa ba har ta shiga kwanar gidansu.

Shima beyi mata magana ba yana ganin gidan data shiga yayi murmushi sannan ya juya
kan motarsa yabar layin yana sak'awa da kwancewa ta yadda zai fara tunkarata da
kalma mafi tsada da daraja a gurin wata d’iya mace.

Saida aka d'ibi kwanaki hud'u yana bibiyar rayuwar budurwar ba tare da tasani ba
sannan. Ranar asabar da misalin k'arfe hud'u da rabi ya dira a k'ofar gidan, yaro
yajira yazo yace yashiga ya k'ira masa Fatima Kabir ya'u. Ba jimawa sai ga yaron da
wani matashin saurayi wanda zaiyi sa'an Sadeeq d'in sun fito tare, yana zuwa suka
kalli juna cikin tsananin mamaki matashin yace.

"Kardai ace twin's d'in dana sani ne? Abbakar ne ko kuma Sadeeq?!"

Dariya Sadeeq yayi tare da bawa saurayin hannu suka tafa yana cewa "cinka da kanka
Shamsu kabeer Ya'u dama kananan.?!"

"Hahaha ina nan mana, dallah ka tabbatar min waye a ckinku kasan kud'inne sai a
hankali."

Sukayi dariya dukansu sannan yace.


"Sadeeq ne Shamsu ya rayuwa."

Shamsu yace "Alhamdulillahi, gaskiya na dad'e ban sake sanya ku cikin idona ba tun
sanda mukayi candy a GSS kwankwaso, ya wai kaine kenan ka biyu sisi na gida."

Shafa kai Sadeeq yayi bayan ya zame hular zannar shi sannan yayi murmushi yana
cewa.

"Wallahi kuwa ashe ma k'anwata ce. Anywaya nidai nagani kuma ina so ya za'ayi
kenan?”

"Toh ya zanyi tunda kazo kawai zaka jamin raini, k'anwata ce Fateema kuma kayi sa'a
this year tayi graduation but gaskiya munan gidan ba'ayi wa mace aure sai tana da
ilimin NCE ko Diploma, gashi ita kofarawa batayi ba yakenan?!"

Murmushi Sadeeq yayi cikin jin dad'i domin hakan yayi dai-dai da lokacin dawowarsa
daga k'wara state. Cikin rashin nuna damuwa yace.

"Shamsu babu damuwa ni dai burina gidan ku susan dani, kuma a bani dama mufara
fahimtar juna tun yanzu."

"Karka damu tunda kana dani babban yaya, wai yanzu wane aiki kake yi..?!"

Sadeeq yayi murmushi tare da cewa "Toh kasan rayuwa babu yadda bata zuwar mawa d'an
Adam, da ina teaching ne a wata secondary school amma yanzu ina nan BUK shekarata
d'aya da dawowa nan ina lecturing, sai dai akwai wani business danakeyi acan k'wara
state hope babu wanda ya rigani Fateema..?!"

Dariya Shamsu yayi tare da sake bawa Sadeeq hannu suka tafa yace.
"Karka damu abokina insha Allahu zaku dai-daita bari ma naje nafito maka da ita."

"Toh godiya nake dad'in aboki a gidan su budurwa🤪." suka kuma tafawa sannan Shamsu
ya koma gida. Yana shiga falo ya kalli Fatima dake kwance tana karatun wani novel
akan kujera, had'e rai yayi shi a dole babban yaya yace.

"Ke Fatima tashi ki shirya kije waje abokina yana jiranki."

Da mamaki ta d'ago tana kallasan yace "eh ko bazaki jeba ne?!"

Fatima tace "Haba Yaya Shamsu amma kasan dai baba yace karna kula kowa ko..." Ya
sake had'e rai sannan yace, "ke! Toh waye baban yanzu a gabanki? Zaki tashi kosai
na bugeki, sakarai kawai."

Tashi tayi tana zumburar baki ta kalli Umman su ganin harkar gabanta kawai takeyi
yasa Fateema shiga d'aki tana gunguni. Hijabi ta zurma ta fito Shamsu ya kalleta
tare da cewa.

"Ke koma ki shafa hosa da janbaki, kinsan ko waye yazo gurinki kuwa.?"

"Gaskiya ni Yaya..." Yayi saurin katseta ta hanyar daka mata tsawa yana cewa,
"Baxaki je Kiyi abinda nasaki bane?!" Sake komawa tayi harda hawaye sannan ta shafa
hoda tasa coffee d'in janbaki sannan ta kuma fitowa, Shamsu ya kalleta sannan yace
"Good girl sauran kuma kije kiyi mai fitsara ko ki gayamai babu dad'i ranki saiya
6aci wallahi domin 6atamana suna zakiyi wuce."

Fita tayi tana kunkuni, a zaure tagan shi suka had'a ido Sadeeq ya sakar mata
Murmushi tayi saurin kawar dakai tare da tsayawa ta jingina jikin bango. Jitayi
yayi mata sallama ta amsa yayi dariya kad'an ta kuma d'agowa ta kallesa karaf suka
had'a ido. Samun kanta tayi dayin murmushi sannan ta gaidasa ya amsa tare da
gabatar mata da kansa tana jidai amma batace komai ba sai daya ce mata.

"Ina fatan zaki yarje min nashiga cikin rayuwarki har muyi aure, nayi miki
alkawarin kare duk wani hakkinki da kare miki duk wani mutuncin ki burina kawai ki
yarda dani."

Samun kanta tayi da cewa "Shikenan na gode tunda har Yaya nane ya baka damar da
banta6a tsayawa da wani ba kamar haka."

"Toh godiya nake yiwa Yaya Shamsu, sai kuma yaushe zan kuma dawowa Zarah..?!"

Ya tambaya yana kasheta da salon shi tayi murmushi cikin sanyi, ita kanta batasan
lokacin da take maida reply ba. Ya had'u iya had'uwa dan k'irjinta banda bugawa
babu abinda yakeyi.

"Nima ban sani ba."

Ta bashi amsa yace "Toh sai wani satin insha Allahu a gaida Umma." Da sauri ta
shiga gida yayi dariya yana zuwa mota sai ga Shamsu ya fito yace.

"Kai abokina irin wannan shaf-shaf d'infa wai har kagama siye tane?!"

Sadeeq yayi dariya tare da cewa, "ban fad'a ba nidai, kawai dai dama zuwa nayi na
gabatar mata da kaina."

"Hakan ma yayi kyau mutumina, toh Ina Shi Abubakar d'in."

"Yana Spain sun rik'esa amma nan da one month zai shigo k'asar insha Allahu."

"Ahh lallai kaji manya toh Allah ya dawo dashi lafiya muna murna."

"Toh Shamsu godiya yake bari na gudu nima ka kular min da mata."

"hmmm harta zama makenan, Allah ya kiyaye hanya a gaida mutanan gidan."

Suka yi sallama Sadeeq ya tafi, tun daga lokacin indai yana kano toh zaije gidan su
Fateema idan baya nan suna mak'ale da waya ta hanyar shamsu domin babanta yaki
yadda ta rik'e waya sai ta fara karatu. Sun shaku sosai fateema na sanshi shima
yana sonta alkairi kuwa duk zuwa da abinda zai kaimata.

Doctor Abubakar Salman Harun, matashin saurayi mai tak'ama da kyau da ilimi nagarta
da wayewa ya zama babban likita wanda duniya ta sanshi take kuma tak'ama dashi. Tun
bayan gama karatun sa da shekara biyu a, k'asar Spain suka rik'esa domin suma ya
ceto al-ummar su ta hanyar kwarewarsa, yana gudanar da aikin cikin walwala da jin
dad'i duk da cewa tunda yabar k'asar tunanin INdo be ta6a gushewa daga cikin
al'amransa ba, ya sakawa ransa cewar Allah ne zai bashi INdo bawai wani abun nasaba
hakan yasa ya kwantar da hankalinsa yacigaba da karatunsa cikin nutsuwa da
sadaukarwa rayuwarsa akan Al-ummah.

Ganin yak'i dawowa ne hakan yasa mahaifinsa ya umarce sa da yadawo gida domin
taimakawa 'yan uwansa 'yan Nigeria, bai k'i tayin mahaifin nasa ba saboda shima
bak'aramin missing d'in gidan yayi ba. Ga wasu mafarkai dayake yi game da INdo da
yake kusan kullum yana son ya ganta yana kaunar sake had'uwa da ita. Hakan yasa
yayi niyar komawa gida bayan yayi wa asibitin *CANTABRIA HOSPITAL* bankwana. ba
suji dad'in barinsa aiki ba aman sun bashi damar duk lokacin da yake da buk'atar
dawowa suna maraba a kowane lokaci..

Wednesday morning at 8:30am cikin airport d'in malam Aminu kano matashin saurayin
mai shekaru 32 ya sakko daga cikin jirgin Nigerian airlines. Sanye yake cikin wasu
dakakkun suit coffee color sai ta cikin white da cover shoe gashin kansa a saisaye
bakikk'irn ya gyara kyakyawan sajansa sai wanda ya ganshi zai iya tantacce d'an
wace k'asar ne.

Sadeeq ne ya fara ganinsa dan haka shi yafara k'arasawa wajan cikin fara'a suka
rungume junansu. Abba ma ya karasa Abubakar yayi saurin tsugunnawa yana mik'a
gaisuwa mutanen gurin sai kallonsu ake, zuciyar Abba tayi fari ganin yadda 'ya'yan
nasa suke bashi respect aduk inda suka had'u.

"Welcome twinnie am glad to see you sai daifa yanzu bama kama kazama bature."

Cewar Sadeeq suna tafiya ajere, Abubakar yayi dariya har suka k'arasa cikin mota
suna tsokanar junansu. Kwanansa d'aya da dawowa batare da kowa ya sani ba yatafi
Sumaila kauyen sani, ba laifi anyiwa kauyan sauye-sauye ya nufi gidan malam Hamza
direct cikin ikon Allah kuma ya sameshi a k'ofar gida bayan ya tambaya annuna masa
shi.

Bayan sun gaisa ne shi duk a tunaninsa malam Sadeeq ne shi kuma Abubakar be nuna
bashi bane ya kalli malam Hamza yace.

"Malam INdo kuwa ta dawo?!"

Malam Hamza ya kad'a kai cikin takaici yace "Ai malam Saddiqu uwata dai k'arfi da
yaji ta gujemu, k'iri-k'iri tak'i dawowa, harma gidan su yaron dazata aura acan
sayen sun aiko mun kuma bashi dan idan ba haka bama uwata ba dawowa zatayi ba.
Wallahi har zuwa nayi da kaina nace mata kabar garin amma tak'i yadda mudawo."

K'irjin Abubakar ya buga jin cewar an aiko, cikin d'imuwa yace.

"Malam wane kauye ta tafi ne? Nidai wallahi inason ganin yarinyar nan tasamu Ilimi
koyaya ne, idan babu damuwa kuma ka yadda dani kagaya min kauyan da INdo taje na
dawo da ita zan samar mata da rayuwa mai inganci da ikon Allah nidai burina ka
yadda dani."

"Toh malam Saddiqu na yadda amma dasharad'in sai munje mun sanarwa dame unguwa,
shima yasani da kuma aminina malam 'Dalha.."

"Hakan ma dai-dai ne Malam na gode." Hannu yasa ya ciro kud'i duba ashirin ya
mik'awa malam Hamza ya kar6a yana ta godiya tamkar zai mai ruku'u sannan yace suje
gidan me unguwar. Suna zuwa aka yi komai sannan suka koma gida Abubakar suka gaida
Inna bayan sun kwatanta mai kauyan sayen ya koma gida cike da murna.

Da dare suna zaune a d'aki Abubakar ya kalli Sadeeq yace.

"M twinnie zaka min rakiya gobe dan Allah."

"Zuwa Ina kuma daga dawowarka?!"

Cewar Sadeeq Abubakar yayi dariya tare da cewa.

"Wani guri zamuje wajan k'arfe 12:00pm."

"Allah ya kaimu tunda gurin bashi da nisa, kasan dai Qibd'iyya tayi aure ka yaudare
ta."

"A'ah twinnie Allah ne beyi ba." Suka cigaba da hirarsu gwanin ban sha'wa.

Washe gari suka d'auki hanyar zuwa saye cikin suit d'insu iri d'aya da Abubakar ya
taho musu dashi. Tafiya suke tun Sadeeq yana kawaici harya fara magana.
"M twinnie wai ko katsina zamu je ne naga mun wuce dawanau..?!"

Abubakar yayi murmushi sannan yace "A'a kaidai zuba ido kayi kallo."

Cigaba sukayi da tafiya har suka d'auki hanyar saye Sadeeq dai yayi shiru idan ya
gaji sai ya kira Fateema har yaga sun fara shiga daji da kewaye mugayen ramuka ya
kuma yin magana.

"M twinnine ko kafara sana'ar yankan kai shine zaka fara takaina?!"

Abubakar ya kyalkyale da dariya tare da cewa.

"A'a ban faraba zuciyata nazo d'auka a garin."

"Tofa.. Waye zuciyar take twinnie??"

Abubakar yace "Aishat Hamza,what I mean is INdo malam Hamza."

"What.........???!"

_Kuyi hakuri da wannan wallahi unguwa naje amma duk da haka saida nayi muku. Ina
godiya a gareku masoya._

*HAJJA CE*👈
[7/1, 7:39 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

_page 13 na kune 'yan candidate d'in government girl secondary school Kwah, hope
zakuji dad'in shi sannan kuma ina muku fatan alkairi a cikin rayuwarku kamar yadda
kuke bin labarin nan_💍

Page *13*
"Amman dai baka min adalci ba kasani ko m twinnie? A k'a'ida yau zanje gidan su
fatma sabida gobe nakeson wucewa amma kayi min haka, wallahi danasan gurin wannan
wayuwayar zamuzo bazan rakoka ba”mtww

"Sanin idan na gaya maka bazaka yadda ba yasani k'in gaya maka sabida ina son muzo
tare dakai."

Sadeeq yayi mai banza har suka shiga cikin rugar fulanin, suna zuwa suka ga 'yan
mata yara da manya sunzo zasu wuce. Ra6awa Abubakar yayi da motar gefe kasan cewar
bazata wuce canciki ba sannan suka fito Sadeeq sai faman cin uban magani yake yi
idonsa sanye cikin dark shade shi kuma Abubakar d'an siriri ne nashi fari kal kamar
k'ank'ara.

Suna fitowa INdo dake tsakiyar 'yan matan zasu tafi kasuwar badume tana ganinsu ta
ganesu cikin karad'i tace.

"Jakar uban nan,sun biyo ni masifaffun malamn nan." Kallon sauran abokan tafiyarta
ta tayi tana gyara mayafinta tace.

"Kowa ya samu sanda zamu k'arasa wajan wad'an can malaman, kawai danace muku kulle
kukuma sai ku jibgesu."

Suka ce toh kowa ya juya ya samu sanda harda ita sannan suka nufi gurin suma su
Abubakar lokacin sun k'araso ciki sam basu ganeta ba sabida tayi girma ta zama 'yan
mata, lokacin da ta baro sani tana 12years yanzu kuma tana 15years gashi tayi 'yar
k'iba ta kuma canza. Abubakar shine ya taresu yana kallansu yace.

"K'annena dan Allah muna neman gidan da INdo malam Hamza take, wadda tazo daga
kauyen sani."

Caraf ta cafe bayan ta rik'e kugu tace, "ga wata nan lafiya kuka zo inda nake..?!"
Duk suka zuba mata ido Sadeeq dariya da takaici suka kusan kamashi ya kalleta kallo
irinna raini sannan ya juya zai koma cikin mota yaji tace.

"Wannene kaid'in dacta Habubakar ko kuma malam Sadeeq? Na ganeku rasai."

Ko waigowa beyi ba sabida haushi ita kuma ta kalli Abubakar dake tsaye yana
kallonta, sam bega wani aibu a tattare da ita ba yaji zuciyarsa ta sanyaya yanajin
tamkar ya rungumeta amma bahali gashi ya gansu da sandina kuma su ba shanu a
taredasu bareyayi tunanin cewar kiwo zasuje. Cikin sanyin murya yace. "Humaira
inason muyi magana dake, naje munyi magana da mahaifinki sauran ke."

"Allahu akubar kabiran, malam Sadeeq ni ba'a renamin hankali wallahi nan garin
yanzu sai nasa su rakaku da duka wallahi."

Ido ya zaro jin abinda take cewa ya fara bin hannayen yaran tare da tuna wata kalma
ta bahaushe da yake cewa sarkin yawa yafi sarkin k'arfi, ya d'an kalleta cikin
ransa yana tunano ko harsai yaushe ne zata yi hankali. Ya rasa ya zaiyi da su sai
yayi murmushi tare da zura hannu cikin suit d'insa ya zaro wallet suka bishi da
kallo ya ciro 2k ya mik'awa wata yarinya yace ga wannan kusha alawa.

Kallon kud'in suka yi sai kuma sukayi baya-baya suna zaro idanuwa, ganin dalla-
dallan kud'i yasa INdo tayi saurin k'arasawa zata fisge Abubakar yayi saurin janye
hannunsa tare da kad'a mata kai yace.

"A'a wannan ba naki bane, naki yana gurin Sadeeq sai kin yadda da abinda zan gaya
miki sannan zamu baki su suna can dubu ashirin."
INdo ta dafe k'irji tare da jan baya tace, "Dubu ahirin? Toh kaine dacta Habubakar
kenan, meyasa kabari aka bawa malam Sadeeq kud'ina kuma alhalin mugune ba bani zai
yi ba..?!"

"Zai baki amma sai kin yadda da maganar da zamu gaya miki."

Tana jin haka tace "kaltume ku kar6i kud'inku, kuyi gaba zan taho daga baya idan na
kar6i kud'ina."

Kar6a suka yi sannan suka tafi ita kuma ta yarda icen hannunta tare da goge hannun
jikin zaninta, shi kuma sai kallanta yake yi, sam ya rasa abinda ya gani a jikinta
yaji zuciyarsa na azabtar dashi, yace.

"Toh kinga wani dutse can muje mu zauna in gaya miki abinda muka zo sanar miki."

Ba musu suka tafi sai juyawa take tana kallon Sadeeq a cikin motar, suna zuwa
Abubakar ya zauna ita kuma ta tsaya yace.

"Humaira zauna mana."

"Karkafa kuma cemin wani humaira hekace wata yarinya e'heee."

"Sunan Mamana gareki shima humairan na fad'a ne sabida babu yadda zanyi, ki zauna
kijini dakyau abinda zan sanar miki, idan baki yadda ba zamu d'auki wata yarinyar
anan kauyan mu bata kud'in."

Da sauri ta zauna ya kalleta yama rasa ta Ina zai fara mata bayani yadda zata
faminta ta gane manufarsa karta yi mai hayaniya. Zare glass d'insa yayi sannan ya
kalli fuskarta sai faman wasa take da k'ananun duwatsu yace.

"Humairah kina son yin karatu?"

Kai tsaye INdo tace mai,

"A'a aradu nida zanyi aure."

Abubakar ya kuma kallanta, ganin tayi maganar har cikin ranta yasa shi mik'ewa
tsaye yace.

"Eh ai zakiyi auran amma ki gaya min idan kinason yin karatu kema wata ran ki zama
kamar matar gwamna ko shugaban k'asa kuma kema wata ran ki amfanar da bayin Allah
da kuma 'ya'yanki wanda zaki haifa idan kinyi aure."

Rufe ido tayi da tafin hannunta wai kunya sannan tace.

"Eh toh bank'i ta bakinka ba amma ni bazan yi wani karatu ba haka kurum naje
malamai su dinga jibgata ba a'hh jikina bana banza bane, kuma ma yazan yi da auran
saleleh tunda shaura 'yan makwanni.."

Mtwww Abubakar yaja tsaki jin ta kira salele cikin d'an 6acin rai yace.

"Waye shi salelen? Me gareshi? Ana son fito dake daga cikin duhun kai kina wani
sake dulmiya kanki? Kinga humaira ki yadda yanzu mu koma sumaila dake akwai kayan
da na tanadar miki sababbi tindaga kan, atamfofi, shaddoji, materials, mayafai
takalma, jakunkuna da kayan kwalliya, amma sai kin yadda zaki bimu mu koma can
gidan ku..."

Shiru INdo tayi ta fad'a cikin tunani, kallonta yayi ganin tayi shiru ya fara
addu'ar karta ce mai bazata ba murya a raunane yace mata.
"Please Humaira talk to me mana."

Kallansa tayi jin yayi mata turanci tace "sake gaya min abinda ka fad'a yanzu da
hausa ko da fulatanci sune yarena."

"Oh cewa nayi kiyi magana mana, inason jin matsa yarki I told you zaki samu komai
idan muka maida ke sani."

"Kai dacta habubakar kun saba cewa zaku yi amma ni bakwa bani bare ma kuma malam
Sadeeq”hmmmm.

"Humaira wannan karan nine zan d'auki duk wani nauyin abunda kike so, fatana da
burina ki yadda mu koma nayi miki alk'awarin yi miki duk abinda kike so indai befi
k'arfina ba."

"Harda kayan d'aki idan mun tashi yin aure da salele?!"

Ta tambayesa duk da yaji haushi amma be nuna mata ba sai ma eh daya ce mata.

"Toh kuwa zan biku amma hemunje mun gayawa baba iro dasu yakumbo talatu."

Wani farin ciki ya ziyarci zuciyar Abubakar yace mata.

"Toh muje."

Jerawa suka yi INdo sai d'an tsince-tsince takeyi yana hanata da haka har suka
k'arasa. Tun a bak'in k'ofa ta fara k'iran yakambo talatu tafito da d'aurin k'irji
tana tambayar.

"Lahiya mai sunan uwa.?"

"Anzo tahiya dani gida, ina lawisa da kande suzo muyi bankwana”

A gindin bishiya Abubakar ya tsaya yana kallon inda suke rayuwa ya kuma tuno cikin
garin kano kafin ya tunano garin abuja zuciyarsa ta dira a k'asar Spain. Lallai
Allah beyi ko ina dai-dai ba, wannan yafika kaima kafi wani sannan ya furta kalmar
"Alhamdulillah."

"Ina wanda yazo tahiya dake d'in, karki ce mini wannan ne?"

"Aradu baba iro shine, d'an uwan malamin mune a sani."

Tabarmar kaba aka shimfid'awa Abubakar ya zauna tare da baba iro k'arin bayani da
kuma sanar dashi cewar da izinin malam Hamza yazo d'aukarta. Abinciccika aka kawo
mai saidai beci ko d'aya ba sannan baba iro yace.

"Toh gaskiya bazan baku yarinyar nan ku tafi da itaba, hedai muje tare har garin,
idan kuma ka yankamu kaida Allah domin hine mesakayya."

Babu gaddama Abubakar ya amince, aka sanar da mutanan gari INdo taje ta harhad'a
kayanta akayi mata tsaraba da yawa sannan mutane mata da maza suka tafi raka ta
gurin mota.

"Yakumbo dan Allah idan salele ya dawo kice mihi na tafi amma ya dinga zuwa sumaila
muna gaisawa kafin bikin mu kinji.?!"

INdo ta fad'a Abubakar dake gaba ya dinga jan tsaki yana jin yadda take k'ara
jajjada sak'on da za'a gayawa salele suka k'arasa wajan mota dama tundaga nesa
Sadeeq ya hangosu ya dinga kwasar dariya ganin yadda sukayo gungo guda sai tada
kura sukeyi, suna zuwa ya had'e rai sukuma mutanen suka dinga fad'in ahe 'yan biyu
ne.

INdo da baba iro suka shiga gidan baya sannan Abubakar ya zauna a driver seat
Sadeeq na kusa dashi ya data motar suka dinga d'aga musu hannu anayiwa baba iro
adawo lafiya. Har suka fito daga surkullen babu me magana sai INdo datake lissafo
wad'anda zata yi kewa, suna hawa babban titi iska ta fara hurata ta A.C ta mirgina
kai sai bacci har rawar sanyi take yi.

*****
Sani...Suna zuwa har k'ofar gidan malam Hamza suka tsaya baba Iro ya tashi INdo duk
ta cika su da munshari wanda hakan be damu Abubakar ba amma Sadeeq iya kuluwa ya
kulu, ta bud'e k'ofar da sauri tana fitowa 'yan unguwa suka fara cewa.

"Ga INdo... Ga INdo...!"

Ta bud'e ido tare da kuma mistsike shi tana dariya, duk wanda ta gani saita fad'i
sunansa kafin ta shige cikin gida da gudu tana k'iran Innar su.

"Kai INdo yaushe kika dawo?!"

Cewar k'aninta shehu yana wankin kayansa, bata kulasa ba Inna ta fito INdo ta
d'areta cikin murna tana washe mata baki.

"Oh 'yarnan kina nan da halinki ko??"

"Ta6 Inna kenan Ina zeje, yana nan aradu wai ina Nafeesah da Sagiru duk bangansu
ba..?!"

"Suna waje k'ila dai suntai wani gurin ne, ahe yau zaya d'aukoki jiya malam ke gaya
min yadda sukayi da malam Saddiqun."

Cewar Inna INdo tayi dariya bata ma bata amsa ba tace,

"Inna ina Rukayya kuwa, oh ni INdo tana nan kuwa?!"

"Tana nan yanzu ma 'ya'yanta uku sai kuma wanda zata kuma haihuwa."

"Kai Inna yanzu cikin wani gareta kama d'ahare ta saye? Bari naje gidan naganta
nikam."

"Haba 'yar nan daga dawowar ki?!"

"Eh wallahi Inna ai Rukayya mutuniya tace kinga tunda na tahi ban mance da ita ba."

Tashi tayi ta suri takalma tayi waje, a k'ofar gida taga su malam Sadeeq da
baban ta amma ta wuce sai tsayawa take suna gaisawa da mutane. Lokacin da su
Abubakar suka gama magana da malam Hamza abubakar kasa tafiya yayi domin yana son
suyi sallama, k'ofar gidan Rukayyar ya k'arasa ya tura yaro ya kirata ya kalleta
sai faman dashare baki takeyi tana rufe ido yace mata.

"Humaira zan tafi gida, Zan dawo jibi insha Allahu karki dinga tafiya yawo idan ba
haka ba bazan baki komai ba."

"Ai bazan yiba dacta, ammafa karkak'i zuwa kaji?!"

Yace "Toh Humaira Zan tafi amma fa kiyi wanka ranar dazan zo."
Tace "Toh dacta Ina jiranka."

Yana tafiya ta koma gidan Rukayya shi kuma ya shiga mota bayan sunyi sallama da
malam Hamza da baba iro. Sadeeq yaja mota suka nufi gida. Da daddare suna zaune
abin duk ya damu Sadeeq ya kalleshi yana danna laptop yace mai.

"M twinnie can you tell me why cared Nd protect her? I know bawai dan wancen
dalilin bane tunda gashi har kana cemin zuciyar kace please tell me."

Ture laptop d'in yayi tare da kwanciya ya sanya hannuwansa ya tallafo kanshi yana
kallon fankar sama yace.

"Twinnie bazan 6oye maka ba hakan yasa naje tare dakai muka dawo da ita gida,
twinnie I'm in love with her, I can not do anything with out her. Ina son ta zama
matata, ina son na mallaka mata ragamar rayuwata koda kuwa bata zama wayayyar da
nake da burin aura ba."

Cikin tsananin mamaki da al'ajabi Sadeeq yake kallon Abubakar jin abinda ya fad'a.
Ganin Sadeeq na niyar yin magana yasa shi saurin cewa.

"M twinnie kayi min fatan alkairi, ka kuma taya ni yak'in neman yarda da soyayyar
Humaira please n please twinnie."

"Allah ya k'ara dankwan soyayya Allah yasa ayi komai muna nan."

Cewar Sadeeq yana kallonsa, Abubakar yayi murmushi tare da cewa.

"Amin m twinnie thank you."

Kowa ya cigaba da abinda yakeyi zuciyar Sadeeq fal mamaki, shi kuma Abubakar tashi
kaddarar kenan auran INdo Allah kadiran alaman yasha.

Washe gari Sadeeq ya tafi k'wara state, a day after Abubakar ya shirya tafiya
sumaila yayi sallama dasu Mama, sannan ya d'auki k'anwarsu Hawwah ya kaita wani
shago yace ta had'a mai kayan kwalliya, tayi-tayi ya gaya mata na meye yak'i tana
dariya ta had'a mai komai sannan ya bata kud'i yace tahau napep. Ya wuce a hanya ya
tsaya ya shiga wani Boutique ya siyawa INdo wasu tsala-tsalan dogwayan riguna guda
biyar da takalma guda uku ya had'asu da kayan kwalliyar sannan ya wuce sani...

*HAJJA CE*👈
[7/2, 6:33 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*

♥♥
A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈


*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO* Sanah Isma'il matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

_Ina ganinku dearest comments d'inku na k'ayatar danifa_


*K'anwata Stylish, my Xoxo, Faxyfation, phartzarah, Nuceeyluv, khady, Mmn
gausiya, UmmuMuhammad, Khady M/kano, Mmn nuceey, sumeey Q, Meela adeel, Mummy,
Hafsat A Fulani buchi, Hafsat A shitu, aunty Ag,💞 Ummul Meenal, Habeeba M, aunty
baraka, Mmn Nazir👜* gaskiya bazan iya duka ba kuyi hakuri naga nakusa yin rabin
wani paragraphs d'in🤪.

Page *14*

Yana zuwa unguwar ya ganta a k'ofar gida a zaune tayi wanka tayi kwalliya irinta
zamani lokacin ba'a gama sanin su concealer ba, amma tasa eyeshado red janbaki tayi
kuma jagira.Tana ganin mota a k'ofar gidan su ta shek’a da gudu tana gayawa su Inna
yazo kafin ta kuma fita kamar wata saban kamu lokacin harya fito yana rik'e da
murfin ya kalleta itama ta kallesa.

Sanye yake cikin wata dakakkiyar shadda getzner light blue anyi mata dinki na dark
blue ya d'ora hula fuskarsa har wani kyali-kyali takeyi kawai INdo ta saki baki da
hanci tana kallansa kallo na kurrullah tamkar tana son ganin wani abu ya mik'a
hannunsa yana zagaya shi a saitin fuskarta tayi firgigita tare da yin dariya tace.

"Dacta Habubakar wallahi kanada kyau ta6 heyau na ta6a ganin haka."

Murmushi yayi tare da rufe k'ofar ga yara sun fara mai dandazo ya ciro 2k yabasu
sannan ya shiga zauran gidan su ta bishi ya tsaya yana kallonta ganin tayi mai
wankan dayace tayi harda kwalli sai ya ce.

"Humaira babu gaisuwa? Bafa ki gaida niba."

INdo tace "Au hakane fa ina yini ya gida ya iyaye..?!"

"Lafiya lau baki tambaye ni malam Sadeeq ba why..?!"

"Ta6 narasa wanda zan tambaya hewani malam Sadeeq Allah ya tsare ni wallahi."

Kyaleta yayi ganin bilhakk'i bata son Sadeeq tun lokacin daya hanata atamfa,
kallonta yayi yace.

"Ina baba yake?”

Tace "Baya nan."

Abubakar yace "Toh Inna fa?"

INdo tace "tana ciki."

"Toh jekiki ce zanzo mu gaisa da ita."

"Kai dacta Habubakar, kawai kashiga meye na tsayawa ai bazata hanaka ba."

"A'a Humaira ba'ayin haka a musulinci dole sai kinje kin gaya mata."
"Toh hikenan tunda baka yadda dani ba."

Tana magana tana shiga gida, yana jiyo sanda take gayawa Inna sak'on duk maganar da
sukeyi yana jiyo su.

"Kai Inna toh meye na saka hijjabi dan nace miki dacta habubakar zai shigo. Lallai
saban salo."

Rintsa ido yayi jin yadda INdon keyin magana da mahaifiyarta, lallai yarinyar nan
indai yana sonta yadda yake so toh akwai jan aiki a gabansa. Dawowarta kawai ya
gani beji motsinta ba, tana dariya tare da wasa da gefen mayafinta tace.

"Tace ka higo an hinfid'a maka tabarma a k'ofar d'aki."

Tana gaba yana bayanta har suka k'arasa ya zauna, daga bakin k'ofar d'akin Inna ta
tsuguna suka fara gaisawa. Shiru babu wanda ya sake magana sai gasu Nafeesa sun
shigo itada k'awarta suka gaidashi, Abubakar yace ma Inna.

"Inna dan Allah idan babu damuwa ina son ki bani aron su Humaira suyi min rakiya
nan cikin gari."

Shiru yaji Inna tayi kafin can kuma yaji tace.

"Toh gata nan ai Nafeesah sai tazo kuje tare harda ita."

"Toh Inna na gode."

Tashi yayi yafita su kuma suka bi bayansa. A baya Nafeesa ta zauna yayin daya
kwashe ledojin kayan yasa a k'asa wajan dazata saka k'afa tace ta shiga ta zauna
sannan shima ya zagaya drive seat ya zauna tare da tayar da motar suka tafi 'yan
kauyan sai gulmarsu akeyi.

Cikin garin Sumaila suka shiga INdo badai surutu ba sai labari takeyi musu sanyin
A.c yana ratsata ga k'amshi a cikin motar ta kalli Abubakar tace.

"Dacta Habubakar wannan motar taka akwai sanyi karmuyi mura a bud'e gilahin."

Dariya yayi sannan ya mik'a hannu ya rage A.c ya juya yana kallanta itama shi take
kallo yace.

"Humaira ya akayi ne?!"

INdo tayi dariya tana tafa hannuwa tace.

"Meye kuwa, wai Ina zaka kaimu ne hefanan tafiya muke..?"

Parking yayi a bakin titi wajan wani shagon saloon ya kalleta yaga sai kallon
window take ya juya bayansa Nafeesa sai bacci take a hankali ya mik'a hannu zai
ta6a kafad'un INdo sai kuma yayi saurin janyewa tare da bud'e k'ofar yafita.
Zagayawa yayi ya bud'e mata ta fito yace su shiga cikin shagon abar Nafeesah tunda
tana bacci suka nufi shagon ya tsaya ta glass inyamurar ta hango su ta fito cikin
azama.

"Hey!good evening sir how are you.?!"

"Fine madam how is your business."

"Fine..fine oooh."
INdo tabisu da kallo sai faman tabe baki takeyi ta samu sumintin gurin ta zauna
tana kallon titi. Saidai Sadeeq ya gama gayawa madam Gloria abinda za'ayiwa INdo
sannan ya kalleta yace.

"Yauwa toh Humaira tashi ku shiga ciki."

INdo ta kalli madam gloria cikin mamaki ta maida kallonta gurin Abubakar tace.

"Mezai kaini wajan arniya dacta Habubakar? Arniya cefa kake cewa naje gurinta, me
zata min...?!"

Ganin yadda takeyi ne yasa hankalin Abubakar tashi har mutane sun fara taruwa da
k’yar ya satayi shiru yace mata.

"Kayanki zata baki amma tunda bakya so zomu tafi gida."

Da sauri ta nufi madam guloriya tana cemai. "Yo toh ai kaine bakayi min bayani
ba."Gloria na gaba tana bin bayanta Abubakar ya girgiza kai sannan ya koma wajan
mota yana jiran fitowar Gloria .

INdo kuwa suna shiga gurin taga abubuwa birjic ga manyan madubai ta kalli fuskarta
sosai sannan ta fara gyara kwallin daya zazzago mata wajan kumatu Tese yarinyar
Gloria ta cewa INdo.

"Sister come and seat here."

Sam INdo batasan da ita ake ba Tese ta kuma yi mata magana still INdo bata juyo ba
Tese taja tsaki tare da zuwa ta janyo hannun INdo tare da zaunar da ita a wajan
wankin kan sai masifa take da turanci ita kuma INdo tana Hausa.

Cige d'ankwalin Tese tayi taja wani uban tsaki ganin ko tsefewa batayi ba, gashi
Mommy d'inta tace tabita a hankali dan wanda ya kawota yace zata iya guduwa. Kibiya
tad'auka ta tsefe mata gashi akwai laushi da tsayi saidai babu cika gashi kuma jah
ne. Mayukan wanke gashi ta d'ebo sannan ta janyo kan INdo ta malala mata sai mita
takeyi har aka gama Madam guloriya ta kuma shigowa hannunta d'auke da riga da
takalmi wanda Abubakar ya bata yace abata tasa ayi mata kwalliya.

Lokacin da aka saka kan INdo a dryer taji zafi sai ta saki wani uban ihu wai zafi,
Madam Gloria tazo tana d'anyi mata wasa tare da takura mata har aka gama kannan
yayi kyau gashi an tura mata shi yayi baki Tese ta nuna mata bathroom a shagwan ta
nuna mata tace tayi wanka, INdo tayi da sabulai masu k'amshi gashi ruwan d'umi
sannan ta fito sanya da kayan data cire babu wanda ya kulata Tese tayi mata
kwalliya sannan aka bata doguwar rigar suka ce ta saka. Duk bayanin da sukeyi mata
toh da hannun suke nuna mata tamkar wasu bebaye.

Wata irin had'add'iyar abaya ce pink da belt black sai kwalliyan ma black ta
jikin rigan, fitowa tayi daga d'akin bayan tasa saidai jikinta babu bra madam
Gloria ta tambaye ta bayan ta nuna mata ta jikinta kasan cewar itama INdo akwa
breast d'in ta turo baki tana k'unk'una da alamar dai batada ita.

Babu kunya madam Gloria tafita wajan Abubakar yana zaune suna hira da Nafeesa tace
k'anwarsa batada bra amma suna siyarwa ya bada kud'in. Abubakar kunya ta lullu6esa
yace toh abata zai had'a a cikin kud'in gyara sannan ta koma aka cire dai-dai size
d'inta ta saka suka d'aure mata belt d'in sai ta koma tamkar ba wadda ta shigo
d'azu ba. Tese ta sa mata veil bayan ta jera mata ribbon INdo tayi d'as da ita
tamkar ba INdo malam Hamza ba.

"Wowww nawawoo see this girl ooooh, you look so beautiful my daughter."
Ita kanta INdo data kalleta a cikin madubi saida ta sake ta6a fuskarta dan a
tunaninta ba ita bace, Madam Gloria ta fesa mata turaruka sannan ta kamo hannunta
suka fito Tese sai dariya takeyi. Abubakar na ganin sun fito ya mik'e yana kallon
INdo k'irjinsa na mugun bugawa, ita kuma ta kasa kallonsa domin wata irin kunya ce
da nauyinsa suka dirar mata a lokaci d'aya. Da kyar Abubakar ya iya kallon madam
Gloria yayi mata godiya tare da zaro 15k ya mik'a mata ta k'ar6a sai k'ara kod'a
INdo takeyi shi kuma ya juya tare da bud'e mata k'ofa ta shiga ta zauna ya rufe.

Cikin tsananin mamaki Nafeesa ke zuro kai tana lek'en fuskarta kafin tace.

"INdo..! Koba kebace ne? Nashiga uku, wallahi kece dan ga fashin gohi nan."

Banza da Nafeesa INdo tayi domin ita kanta tunda aka haifeta bata ta6ajin ta a wani
irin yanayi na cikar kamala ba irin yanzu. Abubakar ya kalleta yana lek'en fuskarta
shima yayi murmushi tare da cewa.

"Humairah kinyi kyau sosai."

K'irjin INdo ya kuma bugawa kanta ya fara sarawa jitakeyi tamkar an sauyata gabaki
d'aya, bakinta kuwa ji takeyi tamkar ansa zare da allura an d'inkeshi ta kasa cewa
ko uffan ta kuma kasa kallonshi.

Kunna motar yayi suka fara tafiya sai magana suke mata shida Nafeesa amma tayi
shiru, farin ciki takeyi yau gata cikin rigar da ko a cikin mafarki bata ta6a zaton
zata sanya taba ga takalmi d'an ubansu tayi shigar da duk kauyen Sani babu wanda ya
ta6ayin irinta. Shin mezata cewa dacta habubakar akan wannan abun dayayi mata,
shida ba yayanta ba, ba wani nata ba a'a d'an uwane a gurin wani malamin su..!

Saida ya tsaya a wani shago ya siyo musu abubuwan kwalan da makulashe sannan ya
nufi kauyen Sani. Daga shi sai Nafeesa kawai suke magana amma ita batayi rigar
jikinta kawai take kallo tanajin ina ma salele zaizo yau ya ganta ta zama sabuwa.

A k'ofar gida ya tsaya Nafeesa ta fito ya bata ledojin INdo ma tazo zata k'ar6a ya
girgiza mata kai sai da Nafeesa ta dawo ya bata harda ragowar kayanta sannan ya
kalleta yace.

"Humaira kina son yin karatu..?!"

Shiru tayi tana faman muzurai, a zahirin gaskiya batada wani sha'awar yin karatu
domin tun farko dama batasa shi a cikin tsarin rayuwar taba.

Gani takeyi ma yanzu wace makarantar zatayi dan tafi k'arfin tsefawa sabida duk
mate d'inta sunyi candy dan haka ma ta kuma cire san makaranta a zuciyarta.
Kallonta yayi yaga yanayinta ya canza ya ciro wayarsa yana yi mata photo wannan
kuwa harda su style, ya d'an matsa kusa da kujerarta tare da cewa.

"Matso toh muyi photon tare."

INdo ta matsa suka kusan had'e fuska yayi musu selfie kusan sau biyar yana d'aukar
su gaba d'aya sunyi kyau musamman Abubakar dayasan shika-shikan iya selfe. Agogon
tsintsiyar hannunsa ya kalla biyar sauran minti uku yace mata.

"Humairah zan tafi sai na dawo please take care."

Murmushi kawai tayi mai sabida bata san abinda ya fad'a ba bayaga (zan tafi sai na
dawo). Ya zaro 5k ya mik'a mata tana kallonsu ta wutsiyar ido tana son k'ar6a tana
jin wani iri ya d'ora mata a kan cinyarta ta d'auka zata bud'e k'ofar yayi saurin
rufewa tare da cewa.
"Humairah baki min godiya bafa zaki tafi, haka akeyi daman."

Tayi saurin rufe idanu tare da cewa.

"Kayi hakuri inata son yima na manta, angode Allah ya k'ara bud'i."

Yace "yauwa kokefa harnaji dad'i, duk wanda yayi miki kyauta ki dinga ce mai angode
kinji ko?!"

Tace "Toh zanyi sai anjima yaushe xaka dawo garin mu?!"

Da sauri ya kuma kallonta jin tana neman ya dawo, cikin wata irin murya yace.

"Humairah kina son na kuma dawowa?!"

INdo ta d'aga kai alamar eh yayi murmushin jin dad'i sannan yace.

"Toh shikenan wani satin zan dawo amma ki dinga kwalliya gashi can na siyo miki
kayan kinji..?!"

"Toh Nagode ka kaida gida."

"Zasuji amma bakice nagaida malamin kuba."

Tace tana yatsina fuska.

"Ai bayida kirki da kaine bakada kirki amma yanzu shine bashida kirki."

"Toh kiyi hakuri ya dena kinga 'dan biyu nane."

"Naji na dena kace ina gaidahi."

"Zaiji a gaiheda Inna da baba."

Yafad'a cikin kwaikwayon maganarsu, ta fita daga motar lokacin su Uwani halilu
sunzo gulma, shi kuma yaja motarsa yabar unguwar zuciyarsa na kudurta mai son
auranta.

*HAJJA CE*👈
[7/3, 10:06 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)
*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

_Shafin yau naki ne *Yayya Nabeelah* ina miki fatan alkairi aduk inda kike #much_😘

Page *15*

Da sauri ta shiga gidan su Uwani da Maryam na biye da ita lokacin su duk da yaransu
sunyi aure,tana zuwa taga Nafeesah tayi d'aya-d'aya da kayayyakin cikin ledar su
Sagiru da shehu sai shan sweet da chocolate sukeyi INdo tayi kukan kura tare da
fad'awa kan kayan tana yiwa Nafeesah masifa.

"Dan uwarki wane d'an iskan ne yace idan kin higo ki bud'e min kaya na? Kodan kin
rakani hine zaki dinga min hihigi cikin abubawa na, ai danni aka siyo. Bani kayana
banza kawai sutofes (stupid)."

"Ke INdon nan wallahi masiffiya ce, ba mubiyu ya siyowa kayancin ba, ai na san
kayan sawar naki ne amma ai daya higa shigon nan ya dawo cewa yayi idan mun dawo
muhya. Ke wallahi rintoh gareki."

"Ah Kakan cewa yayi mu raba. ke waima wayake son ya dinga yiwa mutunci? Ni ko keh?"

"Oho ba'a sani ba, kuma yasin komai rabahi za'ayi dai-dai."

Sagiru daya hango wata alawa k'ark'ashin k'afar INdo yayi wuf ya d'auke tare da
6arewa yasa baki da sauri dan karta juyo yana cewa.

"Wallahi kuwa Nafi karki sake ta cuceki a raba shi ki fara d'auka."

Da sauri cikin bala'i wanda har rufe mata ido yake yi tace,

"Toh munafiki algungumi zugata, wallahi hekaja ink'i rabawar banza kawai..."

"Oho dai a raba mugani."

Ya kuma fad'a cikin tsokana tayi mai banza tare da maida kayan da jakar kayan
kwalliyar ta cikin leda sannan ta kalli Nafeesah tana hararart tace.

"Ki za6a raban Allah za'ayi ko kuma raban gaskiya kike so..?!"

Nafeesah ta murgud'a baki tare da cewa.

"Rainin hankali, toh raban Allah da ma'aiki zaki yi mana babu wani rabon gaskiya
'yar latsi..!"

Suna kallonta saida ta fara ware komai daban sannan ta kwashi me yawan ta turawa
Nafeesah kad'an tace.

"Gashi nan."

Nafeesar ta kwaso wata uwar ashariya ta zubeta sannan tace.

"Idan kin isa kice ba uwatace ta haifeni ba kanbala'i..."

Inna na kallonsu tun shigowar INdo k'irjinta ya fara bugawa kanta yana juyawa ganin
yadda 'yar tata tadawo sabuwa, Allah yasa dai ba wani abun yayi mata ba ko yake son
yimata ya fara kowa mata shiga masu kyau. Duk fad'an da suke yi ta kasa cewa dasu
uffan bakinta fal addu'a da fatan Allah ya cire mata wasi-wasin da take yi akan
lamarin Abubakar.

"Gaskiya kema INdo kinso kanki dayawa, taya ance kiyi rabo tsakani da Allah sai
kiyi yadda kikaga dama dan mugunta..."

Cewar Maryam Aliyu tana bawa d'anta nono. Can Sagiru ma yace rabo beyi ba Nafesah
karta yadda ita kuma Uwani tana bayan INdo dankar sai an gama fad'an ta hanata
komai. INdo ta matse nata tsakanin cinyoyinta tare da cewa.

"Saida na tambaye ki rabon Allah ko rabon gaskiya kika ce na Allah toh ai Allah
baya rabawa dai-dai sai dai yabawa wannan meyawa ya bawa wani kad'an, alal misali
kinga ai Maryam ke mijinki yafi na uwani kayan gona kuma dacta Habubakar shima yafi
baban mu kud'i ko ba haka ba..?!"

"Oho miki banza muguwa kuma bari ya dawo saina gaya mihi."

"Sai ki fad'a ko'a jikina wallahi."

Ta fad'a tana jan tsaki. d'aya-d'aya ta bamawa su Uwani, babu wanda beji
haushinta ba sabida ko 'ya'yansu bata bawaba suka tashi suka tafi. Kallon Inna INdo
tayi ganin tayi tagumi yasa tacewa.

"Inna kizo kiga kayan da ya kawo min, ya kaini aka sani a inji mezafi aka gasa min
kai aka dinga hyafamin wasu abubuwa akaina Inna jibi yadda gahina ya zama.."

Tana magana tana bud'e kanta, gabaki d'ayansu suka kalleta baki bud'e cikin mamaki
Inna tace.

"Nahiga uku ni Maryamu 'yarnan kanki nekuwa?"

"Hehehe kaji Inna da wani batu, toh inba nawa bane jikin kuma nawaye kema dai."

"Ta6 lallai INdo anyi klin kinga yadda aka nannad'a miki gahinki kamar na
indiyawa."

Cewar sagiru yana kwakulo chocolate d'in daya mak'ale jikin jajayan hak'oransa.
Banza tayi mai taci gaba da nunawa Inna kayayyakin daya siyo mata, Inna tayi godiya
cikin rashin nuna kyashi ga uwa a wani bigire da wasu 'ya'yan keyi INdo ta d'akko
wani flat shoe tare da janyo k'afar Inna tana cewa.

"Inna saka wannan mugani kozai yi miki."

Tana saka mata kuwa yayi cif-cif a k'afar Inna INdo tayi dariya tare da fad'in.
"Inna k'afarmu d'aya Ashe, toh nabar miki wannan innata kema kidinga sakawa idan
zaki unguwa ko kauyen ku."

Da sauri Inna ta zare takalmin daga k'afarta tare da rik'o hannun INdo tace. "A'a
'yarnan barshi na gode miki Allah yayi albarka amma bazan k'ar6a ba, sabida ke aka
bawa tayaya zan k'ar6e miki ya gansu a jikina a'ah."

"Toh danya gani kuma Inna heme? Zece kibahi ne? Kawai ki k'ar6a nina baki ai yariga
ya siya min."

Ganin ta dage yasa Inna ta k'ar6a tare dayin godiya sannan INdo ta shiga da kayanta
cikin d'aki ta zuba a cikin Ghana must go d'inta. Tashi tayi tafita zuwa gidan
Rukayya, duk inda tayi mutane sai sunyi mata magana, maza kuma su tsayar da iya
amma sai hura anci take kanta a d'age tana 6are alawa tana sha hankalinta kwance
duniya tayi mata sabunta jinta takeyi tamkar akan iska.

****

Qarfe 2:35pm ya fito daga office d'inshi, sauri yake yaje gida yayi wanka dan yana
son zuwa sani a yau. Da sauri yafita yana zuwa gida wanka yayi tare da shiryawa
cikin k'ananun kaya white jeans da black shirt me dogwan hannu ya d'ora facing cap
dama ya riga yayi sallah yaci abinci a office dan haka ledar d'in kunan daya bawa
Hawwa ta d'inkawa INdo su ya d'auka yafita sai bulala k'amshi yake tamkar anyi
6arin turaren.

Passenger seat ya ajiye kayan sannan ya tada motar ya wuce domin yau kwanansa goma
sha hud'u rabansa da kauyan Sani, yayi missing d'in INdo ba kad'an ba domin babu
waya a hannunta.

Yana shiga unguwar yara suka yayyame shi yayinda suke ta mik'a mai gaisuwa, yau
kam suna da yawa harda matasan samari ya ciro 3k ya basu yana mamakin abinda suka
maidashi tamkar wani kansilan su ko chairman d'insu. Shehu ne ya k'arasa jikin
motar yace.

"Bari a k'irata tana gidan k'awarta."

Abubakar yayi murmushi tare da d'aga kai sannan shehu ya ruga da gudu gidan Sahura
kokafin yaje Ashe har an gaya mata suka had'u a hanya shehu na gaya mata irin
kyawun da Abubakar yayi yau ita kuma ta k'agara tagani hakan yasa ta yin gudu.

Ta glass ya hangesu ya zaro idanuwansa yana kallonta ganin tun rigar datasa ce a
jikinta tayi jirwaye su manja bak'in tukunya ne gashi nan dai ya kifa kansa akan
sea-tearing. Ashe babban aiki ne a gabansa na aniyar ganin INdo ta waye, toh meye
amfanin wad'ancen kayan na gurinta gashi yau harda k'aro mata kala shida duk
atamfofi, yasan ma aikin banza ne yanzu ya zaiyi. Kafin ya nemo amsa yaji tana mai
magana a hargitse sai uban nishi takeyi ya d'ago da kansa a hankali tare da zuba
mata fararan idanunshi akan nata yana lumshewa cikin wani irin salo.

Bah k'aramin kyau da had'uwa taga yayi mata ba taji k'afarta na rawa zuciyarta na
harbawa muryarsa a sark'e yace mata.

"Humayrah ook at you, da alama yau ko wanka bakiyi ba a matsayinki na 'yanmata


wadda ta kusa yin aure jibi tun rigar last week meye hakan..?!"

Tana wasa da belt d'in rigar daya fara zarewa tace.

"Wallahi dacta bansan zaka zoba yau danayi kwalliyar."

Tsaki yaja d'an k'arami sannan ya fito daga cikin motar ya jingina yana kallonta.
Tundaga sama har k'asa take binsa da kallo yace mata.

"Dena kallo na." Toshe baki tayi tana dariya jin abinda ya fad'a ashe yana kallon
yadda take mai ya kuma cewa.

"Tunda naga alamar bakya son yin wanka toh zan canza ki na koma kan Nafeesah domin
tafiki wayewa. Ko kuma na dena zuwa tunda abin naki haka ne."

"Wayyo dacta dan Allah kayi hakuri wallahi ko hekaran jiya da salele yazo nayi
kwalliya ka tambayi innan kaji, kaima fa dan bansan zaka zo bane."

Tayi maganar tamkar zata rarume dan duk ta rud'e jin cewar zai dena zuwa. Komawa
yayi ya zauna sannan ya kalleta yace.
"Toh jeki ki wanka ki kuma saka sabuwar riga ina nan Ina jiranki."

Da sauri ta shiga gida, kafin minti biyar sai gata cikin sabuwar riga yellow da
kwalliyar gloden ajiki sai hoda data shafa da lipstick ta fito duk dan kada ya
tafi. Kallonta yayi tare da yin murmushi yace.

"Toh koke fa, shiga muje na siyo miki wasu abubuwan ina Nafeesah ta raka mu?!"

Cikin sauri INdo tace "Bata nan taje kai nik'a muje kawai basai ta rakamu ba."

"Toh shikenan." Ya fad'a tare da shiga motar ya bud'e mata ta shiga yaja suka tafi
yana janta da hira cikin salo irinnashi. Cikin gari suka shiga yayi mata shopping
abubuwa na buk'ata su brush, makilin, sabulun wanka na wanki, mayukan gashi
turaruka, pad, cotton balls, panties dadai sauran su sannan suka juyo gida.

Abubakar ya gargad'eta sosai akan yin kwalliya sannan ya bata d'inkunanta INdo ta
dinga zuba mai godiya kamar bakinta zai tsinke sannan suka yi sallama zata fita
kawai yaga k'asanta duk ya 6aci yayi saurin dakatar da ita ta hanyar cewa.

"Humaira kinsan al'adarki tazo?!"

Da sauri ta kalli bayanta domin wannan shine karona biyu data ta6a yi, na farko a
saye yakumbo talatu tace mata kowace mace tanayi sunansa al'adah kuma inyaxo ba'a
sallah ba'a ta6a kur'ani.

Tace masa "Ban saniba yasin amma ba komai yakumbo ta gayan yadda zanyi."

Hannunta ya janyo karo na farko da hakan ya ta6a faruwa, ledar hannunta ya kar6a
tare da zaro pad yaciro guda d'aya yace.

"Kinsan wannan."

INdo ta girgiza kai yayi murmushi tare da zaro pant d'aya ya nuna mata yadda zata
yi yace.

"Yanzu idan kinje gida saiki saka a haka kinji? Duk sanda tajik'e saiki cire kiyar
kisake wata bye-bye."

Ya fad'a yana d'aga mata hannu, bud'e k'ofar tayi da ledoji a hannunta ta fita shi
kuma ya janyo yare da d'ora kyalle agurin data 6ata mai ya bar unguwar.

Bayan wata biyu.

*HAJJA CE*👈
[7/4, 6:39 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *16*

Zaune suke a cikin ajin wanda yawancin su duk matan aure ne da alama makarantar
manya ce ta yak'i da jahilci. Gefe guda kuma INdo ce ta duk'ufa tana kallon wani
littafi na alifun ba'un sai faman mamul-mamul takeyi da bakinta da alama sotake
tasan su ta kuma gane su a haka wata dattijuwar malama ta shigo hannunta rik'e da
littattafai idanta sanye da glass fari ta samu guri ta zauna. Bayan ta kammala biya
musu littafin ahkdari ta zauna tana kuma yi musu bayani har tazo tana yi musu
sharhin isra'i da mu'iraji tana basu labarin ire-iren matan da annabi (s.a.w) ya
gani a cikin wuta tace.

"Manzon Allah sallallawa'alaihiwa sallam yana cewa aure sunnah tane duk wanda baya
son aure baya tare dani, baya da alkairi mutum ya zauna yayi ta kace nace da mutum
musamman idan bata fuskar addini ba. Lokacin da ma'aikin Allah (s.a.w) ya dawo daga
isra'i Nana Fateema da megidanta sayyadina Aliyu suka je gurinshi suka tarar dashi
yana kuka suka tambaye shi menene yasanya shi wannan kukan, sai ma'aiki yace, yaga
mata dayawa daga cikin al'umarsa anayi musu nau'i-nau'in azabobi kala-kala.

Yace yaga wata mata an d'aureta d'auri irinna azaba da gashin kanta, _itace mace
baliga wadda take barin gashin kanta a waje dan wasu sugani_ ya kuma ganin wata an
zaro harshenta an nannad'eta dashi, yace _itace wadda take d'aga murya idan
tanayiwa mijinta magana duk yadda taga dama, duk abinda zai mata ta kushe, ta dinga
ganin be'iya yi mata komai_ wata kuma an tsananta d'aurin nononta, _itace wadda
bata kula da shimfid'ar mijinta, bata bashi hakk'insa, ko tayi ta garashi dan taga
yana buk'ata, sannan tana bin wasu mazan a waje_ wata kuma aka maida fuskarta ta
alade jikinta na jaki. _itace wacce ta kassance munafuka, annamimiya me d'aukar
magana takaiwa wannan taje can ta kunsa wata maganar_, ita ake yiwa wannan
azabar.."

Akwai nau'ika kala-kala daya sanar dasu wanda ya gani, anan gurin kowacce tasan
abinda takeyi na rashin dai-dai dan haka sai kowacce taje ta gyara wanda takeyi
kafin tilon ganyenta ya bushe ya fad'o ma'ana kafin ta koma ga wanda yayita. Akwai
masu iyaye a raye babanki neko Mamanki kiyi musu biyayya akan abinda besa6awa
shari'ar musulinci ba domin sa6a musu babban laifine a wajan Allah dama cikin
rayuwar mutum gabaki d'aya, Allah yayi mana kyakyawan k'arshe.."

Duka ajin suka amsa da amin sannan malamar ta fita, kasan cewar ajin duk matan aure
ne mutum uku ne 'yan mata yasa INdo bata irin wannan haukan gashi basa kulasu ita
kuma karatun ba wani shigarta yake yi ba saidai tana matuk'ar san tarihi domin
jinta takeyi tamkar agabanta akeyi wasu abubuwan.

K'arfe shabiyu da rabi aka tashesu gaba d'aya makarantar hijjab suke sawa kuma kala
d'aya shine ya zama kamar uniform d'insu. Yau kwanakinta talatin da biyar da kawota
makaranta babu abinda za'ace sai hamdala domin ta fara iya yin sallah sai dai sam
kwakwalwarta bata d'aukar hadda, a gurin za'a biya tanaji amma kuma ya zauna a
cikin kwakwalwar ne wahala.
Tana fitowa itada k'awayen da tayi sababbi Zainab da Hadiza suna maganar littafin
k'awa'idi sai ga me mashin d'inta wanda Abubakar ya samar mata yazo d'aukarta,
shine yake kawota ya kuma dawo ya d'auketa duk sati Abubakar yake bashi kud'insa
sukayi sallama ta hau suka tafi.

Zama tayi a cikin d'aki suna hira da Inna ita kuma tafito da littattafan tana
kallonsu taja tsaki tare da fad'in.

"Wallahi Inna karatun nan badai wahala ba, ni wallahi duk makarantar ta iheni dacta
Habubakar ya takura min."

Ta k'arasa maganar tana turo baki tare da yatsina fuska, Inna tayi dariya tace.

"Haba 'yar nan ki dubafa kigani zuwanki makarantar nan yanzu sallah bata wuce ki,
sannan kina zaune a gida kina k'ok'arin yin alifun ba'un d'inki aini kam naji dad'i
wallahi."

"Ta6 lallai Inna, nifa ma wallahi inajin film zan higa dan wallahi dana fara Inna
zaki ganni da narkekiyar mota wadda tafima ta dacta."

Tafad'a cikin nuna son yin abinda tace, Inna tace, "Ahir d'inki da wannan sana'ar,
yanzu keko cewa akayi kihiga ai bakyaje ba sabida ma tsarinku ba d'aya bane su
sunfiki kud'i da karatu."

"Toh Inna bakiga 'yar autah ba me sa bakin janbaki, yanzu kina nufin kice min itama
tafini kud'i ko iya film d'in...?!"

"Oh ni maryama nace bana son kiyi amma kuna dagewa."

"Toh kiyi hakuri Inna dan yau anyi mana magana akan yiwa iyaye abinda basa so,malam
Hansa'u tace me sa6awa iyaye idan ya mutu Allah ze k'onashi na denayi miki na fasa
higa film d'in."

Daga nan suka cigaba da hira duk ranar asabar, lahadi da litinin INdo na makaranta
kuma alhamdulillahi duk sanda taje ta dawo akwai abinda zata d'an tuna musamman
idan anayi musu k'arin haske akan littattafan. Shi kuma Abubakar idan yazo zai kuma
sanar da ita abinda shima ya sani da haka INdo ta fara gane fari da bak'i sannan
gashi Abubakar yana iya k'okarinsa wajan ganin yayi mata abubuwan zamani wayace
kawai yak'i siya mata sabida yasan ba k'aramin d'auke mata hankali zatayi ba shi
kuma yana son yaga ta samu wani abun a Cikin addininta.

*Bayan shekara d'aya DA rabi*

Waya ce kare ajikin kunnansa yana ta faman cike-ciken files sai faman murmushi yake
yi sannan yace.

"M twinnie na riga na gaya maka bazan samu damar zuwa gidan su wata Fateema ba gobe
sabida akwai inda zani, nifa Fateema ma ta rainani wallahi ko ta d'auka kaine babba
dan cewa tayi min wai wasan k'anin miji ta farayi dani."

Sadeeq yayi dariya tare da cewa. "My sweet heart kenan ai tayi min dai-dai kasan
wayayyen mutum gashi dama ta shiga college abin ya kuma k'aruwar mata Ina son Zarah
M twinnie."

Abubakar ya ta6e baki tare da cewa "Yh I see. Yanzu dai sai goben idan ka dawo ma
had'u nima idan naje wajan babyna zan baka ku gaisa da ita."

"Okey no problem Allah ya kaimu."


Daga haka sukayi sallama kowa ya ajiye wayar yana kewar d'an uwansa, har tsawon
shekarar nan Sadeeq besan Abubakar yana tare da INdo ba domin duk iya hutun da
zaiyi a gida baya ta6a gigin nuna mishi dan ko wayarshi gallery d'insa password
d'in a jiki bazaka ta6a tunanin ma cewa yana ajiye hoton mace a cikin wayarsa ko
laptop ko wani gurin ba sabida iya taku da d'auke kai irin nasa.

Washe gari Sadeeq ya dawo ranar raba dare sukayi suna hira. Da gari ya waye su Mama
da sauran yaran gidan anata shirye-shiryan zuwan budurwar Yaya Habu domin a ranar
yake son kawo INdo gidan su ganta itama taga 'yan gidansu.

Sam Sadeeq besan lokacin da Abubakar ya fita ba, sai shiga d'akin yayi ya tarar
k'amshin turarensa, wanka yayi ya kwanta tare da janyo waya ya k'ara Fateema
lokacin sun fito daga lecture around 2:45pm.

Abubakar kuwa yana shiga kauyan Sani yayi parking a k'ofar gidan su INdo,malam
Hamza ya fito suka gaisa sannan yace.

"Ai uwar tawa tace idan kazo kajirasu su dawo taje gidan kwalliya, nace yanzu ita
kwalliyar ce bazata yi ba sai anje har cikin garin sumaila. Wai ai waccan tafi kyau
nace toh Allah ya kyauta."

Murmushi Abubakar yayi yana shafa k'eya tare da rissinawa yace.

"Ai babu komai baba zanjira."

Fita malam Hamza yayi yana ta shiwa Abubakar albarka yana jin aransa zai iya bashi
duk abinda yake so indai yana dashi burinsa ma a yanzu kawai yaji Abubakar d'in
yace yana son INdo amma yayi likimo ko ita 6eta6a furtawa kalmar ba sai 'yan gidan
su daya dama da zancen Aisha budurwarsa. A 6angaran INdo kuwa tunda ta fara gane
kyautatawar Abubakar da karamcinsa a gareta da irin yadda yake nuna kulawarsa
gareta yasa ta mallaka masa zuciyarta gabaki d'aya, ta sallami salele jira kawai
takeyi taji Abubakar yace yana sonta amma hakan ya gagara, gashi zuciyarta ta riga
ta mutu akan sa dan ji takeyi tamkar ta fad'a mishi sai dai yanzu tana da kunya dan
a makaranta ana gaya musu cewar kunya adon macene duk macen da batada kunyar gayawa
namiji abu toh k'imarta zubewa take yi kuma bazai sota ba hakan yasa ko abu take so
yanzu bata iya gaya mai saidai ta hak'ura.

Abubakar na zaune cikin mota ya ziro k'afarsa waje yana danna waya kamar ance ya
kalli gabansa yaga su INdo da Nafeesah suna tahowa cike da nutsuwa tamkar basu ba.

"Masha Allah."

Yafurta a hankali yana yana me binsu da ido. Har k'asa suka tsuguna suna gaida ya
kasa amsawa INdo sai kallonta da yakeyi. Sanye take cikin les Orange da ratsin
green ajiki ta yafa mayafi green tamkar ranar da ake sanyata a alalle, wuyanta
yasha sark'a tasa d'ankunne yatsanta da zo6e sai k'amshin turare sukeyi yace cikin
fara'a.

"Aishatul humairah da my sweet sis Nafeesatu kunyi kyau."

Nafeesat tace, "Kai Yaya Abubakar ai kafimu nidai bari na shiga na sake takalmi."

Tayi maganar tana mik'ewa daga tsugunnan INdo tayi saurin riko hannunta tare da
mik'ewa suka shige gida ya bita da kallon mamaki ganin yanzu kunyar da take nuna
Mai tayi yawa ya kad'a kai yanajin wani mugun dad’in yanayi yana ratsa shi.

Suna shiga ba dad'ewa suka fito domin sunsan su yake zaman jira, Inna tayi musu
fatan alkhairi da addu'ar Allah ya dawo dasu lafia. Yana jingine jikin mota suka
fito a hankali ya juya yana kallon INdo suka yi four eye's ta sakar mishi murmushi
da fararan hak'oranta daya kaita asibiti aka gyara mata su le6anta yashi red
janbaki ta bud'e gidan gaba ta zauna tare da kawar dakai tana kallon k'ofar gidan
su.

Shima shiga yayi yana cewa Nafeesah, "Zamu tafi mubarki fa." Tayi saurin fisge
hannunta daga rik'on da shehu yayi mata yana bata sallahun abinda zata siyo mai
idan sun shiga cikin kano.

A hankali ya dinga tafiya har suka fita daga sumaila sannan ya fara gudu dan ayau
zai dawo dasu, suna ta hira wanda yawanci akan makaranta ne data ke zuwa lesson sai
dai abin ayi addu'a kawai amma INdo kam bata fahimtar turancin da akeyi sai 'yan
k'ananun words wad'anda basu da wahalar rik'ewa.

A k'ofar gate d'in gidan su ya tsaya, ba wani gidane had'add'e ba sannan kuma ba
wai gajari bane dai-dai magidanci me rufin asiri da kuma kwanciyar hankali. Suna
tsayawa k'irjin INdo ya fara bugawa taji kamar bazata iya shiga ba Nafeesah ta fito
INdo ta kalleshi kamar zata yi kuka ya sakar mata murmushi tare da cewa.

"Ya aka yi naganki haka?"

"Yaya Abbakar jinake inajin tsoro."

"Oh toh ai bama cinye mutane kifito mu shiga."

Dakyar INdo ta iya fitowa 'yan layin sai kallansu sukeyi suka shiga parking spaces
sunzo wani d'an corridor ya janyo hannunta tayi saurin kallansa ya kai fuskarsa
saitin tata kamar zai yi kissing d'inta yace.

"Idan kina yin haka su Halima zasu rainaki, ki saki jikinki."

Yafad'a tare da sakin hannunta, Nafeesah kuwa har takusa shiga ciki sannan ta tsaya
suka k'arasa sannan Abubakar yayi gaba sukuma suna bin bayansa. INdo kuwa abinda
yayi mata ba k'aramin sake tsuma jikinta yayi ba hakan kuma yasa ta fara mai wata
fassara domin a makaranta ana gargad'in suka akan ta6a namijin da ba aure kukayi
ba.

Da gudu k'annansa suka fito suna musu oyo-yo suka rungume INdo suna cewa.

"Yaya Habu itace ko?!"

Ya dinga d'aga musu kai yana murmushi yadda INdo da Nafeesah bazasu gani ba. A
k'atan falon gidan aka sauke su an baje musu kayan abinci dana sha kala-kala INdo
kuwa kamar ta nutse cikin carpet d'in da aka malale falon dashi.

Su Mama da Umma suka fito su INdo suka gaidasu har k'asa sannan suka huta k'annan
su Abubakar sukayi ta janta da hira suna jefo mata turanci haushinsu ya fara cika
ta domin baganewa takeyi ba su kuma a tunaninsu kunya ce take hanata yin magana
basu san duk taci ubansu a surutu ba. Sun jima kafin su sauka zasu ci abinci domin
tunda Abubakar ya shigar dasu ya koma d'akinsu ya tarar Sadeeq sai shak'ar bacci
yake yi da alama ma ko sallan la'asar beyi ba Abubkhr yace.

"M twinnie ka kashi kazo mu shiga ciki gashi na kawo maka wadda zan aura kugani."

Da sauri Sadeeq ya mik'e cike da mamaki yace.

"Are you serious?!"

"Yap tana ma ciki gurin su Mama."


Sadeeq yace "wai kana nufin kace min zuwa kayi ka d'akko ta, kuma babu wani
labari?!"

Abubakar yace "Ya daman Ina sonayi surprising d'inka."

"Ya nagani toh bari naje nayi sallah sai na shiga, nasan ko wacece wannan toh ta
had'u and degree nawa gareta M twinnie?!"

"Idan zaka shiga ka gani toh idan kuma labari kake so toh kaci gaba da baccinka."

"A'a zanso ganin matarka mana M twinnie."

Ya fad'a yana shiga toilet dan shi a tunaninsa Abubakar ya manta dawani batun INdo.
Saida ya watso ruwa yayi sallah yana idarwa Abubakar na shigowa Sadeeq d'in ya zura
kaya sannan suka nufi cikin gidan, tun daga kan takalma Sadeeq yasan budurwar d'an
uwan nasa ta had'u suka shiga tare dayin sallama Sadeeq ya zauna kan kujera ita
kuma INdo ta d'an jiya ta kallesa suka had'a ido sam Sadeeq be ganeta har ta
kaidashi sannan Abubakar ya kallesa cikin sign ya cewa Sadeeq.

"Ya tayi...?!"

Sadeeq ya jijiga kai yana kallon gefen fuskar INdo yayiwa d'an uwan nasa alamar 👌
yana kashe mai ido d'aya. Dariya Abubakar yayi ganin be ganeta ba yace.

"Aisha ce fa student d'inka ta sumaila kauyan Sani Tsefawa secondary school, idan
baka gane ba toh INdo malam Hamza ce..."

Sadeeq dake zaune sai gashi a tsaye yana mata kallan mamaki. Sai yanzu ya gane
domin ga fashin gushinta nan sannan ya fara tuna kamanninta cikin kwakwallawarsa
zuwa idanunsa cikin tsananin mamaki yace.....

[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*


♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*Duk da cewar kinfi k'arfin page amma duk da haka zan bak'ishi ba a matsayin
komai ba sai dan kawai naga nayi hakan, I am proud of you My Xoxo (miss Xoxo) Allah
ya baki abinda kike so Duniya da lahira.*❤😍

Page *17*

"Wallahi kuwa itace, INdo malam dama zaki iya zama haka? Ikon Allah da...."

Cikiin sauri Abubakar yayi magana ranshi a bace ganin yana neman kwance mata zani a
kasuwa yace,

"M twinnie ya isah haka ko ka manta matsayinta a gurina ne ah..? Kake neman cin
zarafina."

Sadeeq ya k'arasa wajan Abubakar tare da dafa kafad'arsa ta hagu yace.

"Oh sorry M twinnie ba nufina kenan ba abinne ya d'aure min kai."

Jin-jina kai Abubakar yayi yana kallon yanayin INdo yaga ta cukume ta kasa boye
fushinta sai faman cizon le6anta takeyi na k'asa tana murd'e k'asan mayafin jikinta
ya kalleta yace.

"Humaira zo muje kiga wani abu."

Kamar jira takeyi yace taje ta mik'e suka fita lokacin Sadeeq na tsaye a parking
space tsananin mamaki sun addabi zuciyarsa sai gasu, INdo na hangoshi ta k'arasa
gurin Abubakar ya bi bayanta. Tsayawa tayi tana kallon Sadeeq cikin salon raini
tace.

"Oh malam Sadeeq kayi mamaki ko? Toh aishi dama Allah ba yadda bayayi da bawansa
nasan baka ta6a kawowa ranka cewar zaka ganni a makamancin haka ba sai gashi ta
silar d'an uwanka."

"Hakane Aisha nayi mamaki kuma har yanzu ina kanyi, shin wace school kike yanzu.?”

Ya tambayeta ta yatsina fuska tare da gyara mayafi tana gyara zaman d'ankwalinta
tana son cewa, ba zamu iya magana anan ba da turanci dan ta bashi mamaki amma ta
kasa tana dai d'anjin alamu-alamun zata iya amma batason ko gwadawa ne dan karyayi
mata wani kallon (We can not talk here) tayi mata wahala kawai ta maze tace.

"I dant talk." (I don't tell you)

Suka kalli juna Sadeeq da Abubakar fuskar Abbakar a had'e ganin haka yasa Sadeeq
girgiza kai yana kallonta yace.

"Oh good Allah ya bada sa'a, Ina su Innar ku da malam..?!"

INdo tace "K'alau suke duk suna gaihe ku."

Tayi maganar tana matsawa kusa da Abubakar,murmushi ya sakar mata itama ta mayar
mai sannan tace.

"Kazo ka maida mu gida Yaya Abbakar dare nayi."

INdo akwai dad'in murya saidai ta kasa dena sh da hi musamman idan tana magana
cikin fushi.

"Toh kuje ku shirya sai mun fara zuwa gidan su budurwar Sadeeq daga can sai mu
wuce."

Abubakar ya fad'a yana kallon fuskarta, wucewa tayi ta koma ciki shi kuma Abubakar
ya gayawa su Mama cewar zaije ya maidasu. Nan fa kowa na gidan ya fara k'ok'arin
fito da abinda zai yiwa INdo kyauta dashi baga k'annan ba baga su Mama ba, haka
suka cika INdo da Nafeesah da tsaraba kala-kala.

Fita suka yi duk 'yan gidan suka rako su mota anayi musu fatan sauka lafiya. Sadeeq
ne yake tuk'in yayin da Abubakar ke kusa dashi suka su INdo suna baya har suka
k'arasa gidan su Fateema, waya yayi mata dama dawowarta kenan daga gidan suna ta
raka Ummanta, fitowa tayi lokacin anata k'iran magrib INdo ta kalli Fateema itama
Fateeman ta kalli INdo kowa ya fara sak'e-sak'en abubawa a cikin ransa.

"My Zarah ga girlfriend d'in M twinnie nan kusan juna bari muyi sallah tukunna."

Cewar Sadeeq Fateema ta kamo hannun INdo tana cewa,

"Okey My D sai kun dawo, shi yasa naga mutumin ankasa an tsare ashe-ashe."

Tayi maganar tana kallon Abubakar ya galla mata harara tare da cewa.

"Whatever dai please take care of her, if not.. Hmmm."

Dariya Fateema tayi INdo kuma ta bita da kallo, oh itakam taji abinda yace tunda
gashi tana dariya ita kuwa please d'in kawai taji amma raguwar duk bata ganeba shi
kuma Sadeeq ya zauna saman motar kafin yace.

"Ki kawo mana ruwan alwala karmu rasa jam'i."

Jan hannun INdo tayi suka shiga Nafeesa na biye dasu, a falo suka zauna Fateema na
zuba ruwa a buta tanayiwa Umma bayani kasan cewar itama alwala take a gurin. Bayan
takai musu ta dawo suka gaisa da INdo ta kawo musu juice da cin-cin a cikin wanda
tayiwa Sadeeq d'inta domin ba k'aramin so itama Fateema takewa Sadeeq ba kowa
yasani tana mugun sonshi.

Kad'an suka ci wai na 'yan birni karsuci da yawa duk da cewar yayi shegen dad'i
amma haka suka hakura, suna Idarwa Sadeeq yayi mata waya cewar su fita zasu tafi.

A bakin mota suka tarar dasu banda ban-bancin kayan jikinsu da babu wadda zata gane
waye nata, suka k'arasa Fateema ta kalli Abubakar marainin wayon nata tace.

"Toh gata na dawo da ita, kaga har 'yar k'ibama saida tayi a gode min."

Murmushi yayi tare da zagawa drive seat ya zauna yana cewa.

"Tayaya zan yadda bayan ni a yadda na baki haka na kuma kar6a, anyway thanks amma
kad'an."

Tayi dariya su INdo suka shiga mota bayan sunyi Sallama da Fateeman, a bakin titi
suka sauke Sadeeq ya kalli INdo itama tad'ago ta kallesa tana faman had'e rai dan
karma yayi mata turanci sai taji yace.

"Aisha sai yaushe?!"

Ta sauke numfashi tare da cewa, "Sai wata rana kuma."

"Okey please send m regards to your parent."

Mtwwww taja tsaki mai k'arfi cikin kufala tace.

"Idan bazakai Hausa ba kayi gaba ai bada yaren annabi kayi min magana ba."

"Lallai Aisha ni kike gayawa maganar nan?"

Sai tayi mai da fulatanci itama shi kuma yayi shiru dan shima baji yake ba ta
kallesa tace.

"Ko bakaji abinda nima nace ba? Toh duk sanda zaka ganni kayi min wani turanci nima
henayi maka wanda na iya ai kowa Allah ya tsaga ya bahi."
Juyawa Sadeeq yayi yana taran napep yana mamakin INdo, wato yanzu ta koyi rainin
hankali gashi yagano cewar tanada d'auke kai akan abinda beshafe taba amma idan ka
shiga nata zata yimaka rashin kunya duk girmanka.

"Humairah dawo gaba."

Abubakar ya fad'a ba tare daya juyo ba, fitowa tayi ta koma kamar yadda ya umarce
ta. Kallonta yayi ita kuma tana gyara rigarta yaja motar suka tafi. Tun suna hira
dashi da Nafeesah hartayi bacci, sai da yayi nisa sosai sannan ya gyara murya yace.

"Humairah meyasa kikewa Sadeeq rashin kunya..?!"

Banza tayi Mai sai kunkuni takeyi ya kuma yin tambayar tayi mai banza sannan yace.

"Baki ga d'an uwana bane? Kuma bakiga ta dalilinsa nasanki ba meyasa kikai mai
haka."

Tunda suka saba da juna bata ta6a jin haushinsa ba sai yau, Allah kuma ya k'imsa
mata yin magana cikin taushi dan da wani ne k'ila su kwashi 'yar kallo tace.

"Duk babu wanda yafiku sanin wacece INdo daga iyayena heku, meyasa hida yasan bajin
turanci nakeyi ba amma heya dinga yi min, wannan ai izgilanci ne. Kuma malamar mu a
islamiya tace mana, komai na Duniya jarabawa ce haka tace mana lafiya da Allah ya
baka jarabawaci rashin Lafiya ma haka,idan Kud'i Allah ya baka hima jarabawa ce
hakama talauci, Ilimi idan Allah ya baka jarabawa ne idan bebaka ba hima jarabawa
ce, aure jarabawa ne rashinsa ma haka, amma himeyasa yake min haka kuma yasan ban
iya ba? himeyasa baka yi mihi magana ba heni...?!"

Shiru Abubakar yayi yana tuk'i, lallai wannan kad'ai yaci ace angodewa Allah tunda
har INdo tasan shi. Murya a sanyaye yace mata.

"Haka ne kiyi hakuri."

Cigaba da tafiya sukayi har saida suka shiga garin Sumaila yayi parking akan kwanar
dazata kaisu kauyen Sani ya kalleta ta kalleshi bayan ya kunna kwan cikin motar
yace cikin wata irin murya.

"Humairah kina sonah..?zaki iya aure na...?!"

INdo tayi saurin rufe fuskarta da gyale tanajin wani farin ciki da annashiwa suna
yawo aduk wani sashe na jikinta. Murmushi yayi shima yana jin tamkar an d'auke mai
wani gungumeman abu aacikin k'irjinsa ya kuma tambayar ta INdo ta d'aga mai kai
alamar Eh sannan ya furta kalmar Alhamdulillah.

"Thank you Humairah Ina sonki so me tsanani, Zan kula dake iya gwargwadon iyawata,
zan kare duk wani hakkinki daya rataya a wuyana zan baki kulawa a cikin rayuwar
auran mu sannan zanyi iyayina wajan ganin kin cigaba da samun Ilimi ta kowacce
hanya indai alkairinki na thanks again I love you."

Tunda ta rufe Ido bata bud'e ba harya gama magana, ganin haka ne yasa shi rik'o
hannunta ta fara k'ok'orin kwacewa murya a sark'e yace.

"Idan kina son na sakar miki hannu sai kin bud'e fuskarki."

Kad'a mai kai tayi sannan kuma tak'i bud'ewa, ganin dare nayi mai ne yasashi sakar
mata hannun yana murmushi tare dajan motar suka shiga cikin kauyan har k'ofar gidan
su lokacin malam Hamza na zaune zaman jiransu.
Da sauri Abubakar ya fito yaje gurin Malam Hamza yana bashi hakuri, shidai malam
Hamzah tunda yaga yaransa sai yaji hankalinsa ya kwanta yace ai ba komai. Sim-sim
INdo ta shige gida Abubakar ya tambayi malam Hamza inda zaije ya nemi auranta Malam
Hamza yace.

"Ai malam Habu tunda ka tambayeni ai kagama tambayar duk wani wanda zai baka uwata,
yanzu kawai kaje duk sanda ka kintsa saika kazo ayi."

Godiya Abubakar ya dingayi tamkar cewa akayi an bashi kijerar president. Kayayyakin
su ya ciro musu su Sagiru suka kwashe suka shiga dasu cikin gidan shi kuma yaja
mota ya tafi yana mai jin farin ciki da nishad'i.

Washe gari yayiwa abban su magana k'annan abban sukaje har kauyen Sani aka
tambayowa Abubakar auran INdo malam Hamza ya tara abokansa suka shaida an bashi, a
take a gurin k'anin abban su Abubakar ya bada kud'in nagani ina so dubu Hamsin
sannan suka tafi suna mamakin gidan da Abubakar yazo neman aure sai dai sunsan ba
yadda Allah baya tsara abinsa dan haka babu wanda yaja da al'amarin.

Labari ya zaga gari an kawo kud'in INdo dubu Hamsin masu bak'in ciki nayi masu
murna nayi dama haka lamarin mutane yake. A cikin satin ya siyo mata waya sabuwa
tecno sabida anyi mai transfer zuwa abuja sabida haka zasu kuma yin nisa.

INdo ta cigaba da zuwa makaranta duk da tana saka wasa a cikin lamari sai dai fa ta
k'ara yin clean domin idan kaganta sai ka d'auka tana a matakin degree program ne
nan kuwa ko secondary school bata kammala ba. Ta kuma rik'e alk'awari bata kula
kowa duk kud'inka duk kyawunka duk ajinka duk meye d'inka bazata kulaka ba tace
bazata yi *MUSAYAR ZUCIYA* da kowa ba Abubakar shine a cikin zuciyarta shi kuma
take da burin aura...

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

*Gaskiya ban san me zan cewa masoya maso bibiyar labarin nan ba sai dai nace muku
love you all.*
_Shafin naku ne My Shuwa Arab, Dota Fatima, Dota Marok'i, My Shama, My Olo, aunty
Jidder_😍💋

Page *18*

*Bayan wasu shekaru.*

Gaba d'aya an kammala yin komai ansa rana da Fateemah ta kammala school za'ayi dan
haka ginin su kawai suke yi. Gidane me kyawun gaske kowanne yake ginawa kowa kuma
da yadda yake son abunsa. Gidan Abubakar yafi tsaruwa nesa ba kusa ba yafi na
Sadeeq sosai kasan cewar shi yana son ya samu wani acan inda yake business dinsa
idan sunje da matarsa babu wani fargaba dama yanada gidanshi dan haka biyu ya raba
sa6anin Abubakar dashi a abujan ma yana da k'atan gida a quarters d'in asibitin da
yake aiki.

*****
Fateema na shekarar k'arshe domin sauran 'yan watanni ta kammala, yayin da a
6angaran INdo itama sai hamdala domin zata iya rubuta wasu kalmomin harma ta rubuta
wasik'a da Hausa koda ajimi kuma iya yawancin surorin alkur'ani me girma an samu
cigaba sosai.

Kyawunta ya fito ta waye ta goge kai in baka cika ishasshe bama bata kulaka
bare harkuyi hudd'a tare. Zaune malam Hamza da Inna suka suna tattaunawa akan yadda
zasu yi da kayan d'akin INdo gashi INdo tace harda gararta zata tafi batason abin
gori.

"Toh malam ya zamu yi, iya abinda Allah ya bamu shi zamu yi mata ai suma sunsan
damu dasu ba d'aya bane sun fimu ta ko'ina."

"Hakane Maryamu yanzu dai dole naje na siyar da gonata dake can saye guda d'aya,
sannan na siyar da shanuna guda biyu sai ayi mata amfani da kud'in nasan dai bazamu
yi mata irin yadda take so ba saidai ai munyi k'ok'ari kuma mani wallahi dandai
Dacta Habu zata aura hiyasa zanyi mata duk abinda nasan Zan iya sabida yaron nan
d'an k'irki ne, duk sanda na kalli katangar nan naganta da suminti sai naji dad'i."

"Hakane kam malam toh sai a siyar d'in Allah ya bada lada."

Malam Hamza yace "Amin."

Kwana hudu dayin zance ya d'auki abokinsa malam kallah suka tafi Saye bayan
rabansa da zuwa kusan shekaru goma sha biyar kenan. Sun gaisa da kowa saidai
tsakaninsa da yakumbo tsahare babu ko kallon banza, bayan an gayawa sarkin shanu
aka yi cinikin shanun malam Hamza wanda shine ya baiwa yakumbo talatu su yace idan
sun haihu ya barmata saidai duk lokacin da yake da bukata toh zai dawo ya karbi
guda biyu. Dubu talatin-talatin aka siye su nan aka bawa malam Hamza kud'insa dubu
sittin, aka koma kan gona wani mutum ya siya dubu cas'sa'in malam Hamza ya kar6o
kudin suka dawo gida da dubu d'ari da Hamsin cas.

Had'awa akayi da kud'in nagani inaso d'inta aka had'a suka zama d'ari biyu cif
malam Hamza yace aje ayi cinikin gado madubi da wardrobe, nan aka nuna musu
kud'ad'an ko wanne babu ma na k'asa da dubu d'ari a cikin irin wanda INdo ta nuna
tana so.

Na dubu d'ari da hamsin suka za6ar mata wata yayar Inna ce da take aure a dawakin
tofa sukaje suka tayo. Sai kud'in gudun mawar da aka dinga kawo musu dan su kauye
basai ranar biki suke bada gudunmawa ba. Haka dame d'ari d'aribiyu dubu biyu
gashinan dai aka dinga vawa inna da malam Hamza suka had'e ya basu dubu hamsin da
biyar da naira ashirin. Suka had'e da ragowar hamsin dinnan aka had'a d'ari na
kujeru gaskiya INdo taci Kud'i wai...!

Sai kuma masu kawo kayan amfani na kitchen me kofi , me tasa, me plate, gashi nan
dai suma aka had'a Inna tasa aka siyar da gonarta itama sai aka sissiya abubuwan da
babu a kitchen d'in.

****
Gidan su Fateema kuwa ko shirin basu farayi ba sabida su ba wani case karatunta
kawai takeyi hankali kwance.

'Bangaren mazan kuwa, kayan lefe ake had'awa komai iri d'aya Mama tace azuba colors
ne kawai suke ban-bantawa da kuma size domin INdo tafi Fateemah jiki ita kuma
Fateemah tafi INdo haske da tsawo.

Akwatuna bakwai-bakwai akayi musu kowacce shak'are da kaya domin mazajen ba


k'aramin k'ok'ari suka yi ba sun kashe Kud'i over.

Ranar da su Fateema sukayi graduation a ranar aka kai kaya murna biyu ta had'ar
mata.

'Bangaran INdo ma ankai kayan tana gidan Rukayya kwance tana waya da Abubakar,
cikin salon mak'e muryar data koyo wajan su Zainab da Hadiza tace mai.

"My key wai me kakeyi ne yanzu?!"

"Ina office a zaune tare da frame d'inki inata kallonki."

"Yeeee naji dad'i nima ka tambaye ni.."

"Habibty mekike yi yanzu..?"

Ya fad'a kamar yana cikin maye, dariya INdo tayi me sauti sannan tace.

"Ni tunaninka nakeyi dan Allah yauhe zaka dawo.?!"

Dariya yayi tare da cewa, "Sai ending d'in month d'innan, ya mekika tanadar min?!"

Tace "kana nufin ending k'arhen Month watan nan ko?!

"Eh haka nake nufi madam."

"Toh kenan kana nufin ankusa biki."

Yace "Eh amma ai Sadeeq yana nan ba kuma zai koma ba sai an gama biki kokina
buk'atar wani abun nasa ya aiko miki dashi?!"

INdo ta kuma gyara kwanciya domin yarinyar ta iya kar6ar sakwan love tace.

"Eh akwai abinda nakeso."

"Toh madam menene shi..?!"

Tace cikin jan numfashi "Kai nake son gani."

Abubakar saida tsigar jikinsa ya tashi yarrrr ya d'ora k'afarsa kan table tare da
jin gina da jikin kujerar dayake kai, hannu yasa a k'irjinsa yana d'an bubbugawa
tsawon wani lokaci sannan yace mata.
"Sorry Habibty da ace da yadda zanyi danayi na taho, saidai na riga na k'ar6i aikin
wani abokina inason idan na taho ya kar6i nawa sabida idan munyi aure bazan dawo da
wuri ba sai na gama shan amarci na."

INdo ta guntse baki jin abinda ya fad'a sannan taji yace.

"Ko kina son da an d'aura aure na dawo."

Da sauri tace "A'a bana son ka koma."

"Toh ki tanadar min kanki a duk ranar da aka kawoki gidana."

Kit..yaji ta yanke wayar ya sauke yana kallon screen d'in yana murmushi bata san
wannan zantuttukan baya manta ranar daya fara gaya mata irin maganganun tace mai
ita ba 'yar iska bace. Ranar yaci dariya kamar cikin sa zaiyi ciwo, bebi kiran ba
yaci gaba da aikinsa yana ta murmushi INdo na bashi laugh yasan idan sukayi aure
zai dinga shan dariya.

INdo kuwa bata koma gida ba sai da tayi magariba sannan ta koma gida, wayyo Allah
dataga irin akwatinan zamanin da Abubakar ya kawo mata bata san lokacin data fad'a
jikin Inna ta rushe da kuka ba. Inna sai faman lallashi takeyi Sagiru da shehu suna
kallon kayan kowa sai nuna abinda yake sukeyi da kyar tayi shiru aka cigaba da
kallon kaya Inna ta nuna mata dubu hamsin tace,

"Gashi 'yarnan sunce kud'in d'inki ne."

K'ar6a INdo tayi tana godiya, tana gama kallon kayan suka rufe ta fita waje.
Unguwar su kezy taje ta samesu zaune sai zuk'ar sugari sukeyi ta toshe hanci tana
musu magana.

"Kai kezy aji tsoran Allah dai za'a mutu."

Tayi maganar tana sake toshe hanci, jazuli yace.

"Kefa 'yar rainin hankalice dan kinzama babbar yarinya shine zaki dinga yi mana
kallon equal.."

"Kai masifaffe ni gurinku nazo, kunsan ankawo kayan aurena, toh sonake kuzo gida
kuyi gadi Allah ma yace tashi intemake ka, idan ma kune 6arayin nidai kuzo gobe
he'in baku dubu goma."

"Kai hajiya INdo kin zama hajjaju fa Allah."

Kezy ya fad'a tace "Eh koma dai meye nidai kuyi min."

"Karki damu zamuci uwar hegen dazaiyi gigin zuwa."

"Toh nagode."

Tafad'a ta wuce ta shiga gidan su Sahura, ta dad'e kafin ta koma gida. Haka akayi
suka yi gadin gidan Allah kuma ya temakesu babu wanda yaje. Washe gari ta basu 10k
suka tafi, ta ciro atamfa d'aya ta bawa Nafeesa tayi ta murna sannan ta ciro tirmi
biyar ta bawa Inna tace tasa da biki. Inna tace a'a itama INdo ta dage tace tabar
mata. Cikin shaddojinta kuma ta za6o wata ash tace abawa babanta, gaskiya INdo
batada kyashi wajan bawa iyaye abunta amma fur taki bawa Sagiru yayi mitar yayi
magiyar tace bazata bayar ba yana da kud'i. Aikuwa yaji haushi duk abinda tasashi
bayayi mata shima.
***

Kowanne 6angare shiri akeyi ta kowanne side, 6angaran Fateema anje an fara jere
haka itama INdo an fara, saidai tsarin gidan yasa bazasu iya cewa sai sun saka mata
komai ba domin basu da halin yin hakan. Iya d'akinta kawai suka sawa kaya sai
parlon farko dining area kuwa kokalansa basuyi ba gashi gida yayi masifar yin kyau
domin yafi na Sadeeq had'uwa.

Ana sauran sati d'aya biki Abubakar ya dawo kano, gidan su harya fara cika da
bak'in nesa sai tsiya suke mai da masu nuna cewar ya auro 'yar talakawa ga gida har
gida amma babu kaya. Sharesu yayi yana yin wanka Sadeeq yazo suka fita. Gidan
Sadeeq suka fara zuwa sai sambarka domin kayane nagani na fad'a aka zubawa Fateema,
royal ne furniture d'in sannan babu inda va'a k'awata ba sannan suka wuce gidan
Abubakar babu abinda yaji aransa na 6acin rai suna shiga cikin bedroom d'in INdo ya
fad'a kan gado katifar ta lotsa da alama sakance kuma ba vita form bace ya ware
hannuwa yana cewa Sadeeq.

"M twinnie remain 6days na kwana anan nida Humairah tah."

Sadeeq yayi murmushi tare da girgiza kai gaba d'aya INdo ta rikita mai d'an uwa,
shi har yau ya kasa manta INdon da ta baya can domin duk sanda zai tuno ta a
k'azamarta yake haskilota har tausayin Abubakar yake idan yaka yana wani abun
dominta.

Cikin kwanaki uku Abubakar yasa aka sake zuba mai wasu k'awatattun furniture's a
inda ba'a zuba ba aka sanya labulaye da site na dining area ba tare daya sanar da
kowa ba sai Sadeeq domin cikin dare akaje akasa komai harda plasma TV. Koda dangin
INdo suka dawo gidan ba k'aramin mamaki suka yiba.

Ana gobe kamu/yini da d'aurin aure....

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *19*
Suna cikin d'akin su kowanne yana k'ok'arin k'arasa had'a ragowar kayanshi a cikin
trolley domin da daddre idan zasu tafi gidajen su kowa ya tafi da abinsa, Abubakar
sai murmushi yake yi Sadeeq na kallonsa amma be tambayesa ba domin yasan dole ya
gaya mai tunda abin da alama na farin cikin sune.

Jin yayi shiru yasa Sadeeq yin gyaran murya Abubakar ya sake yin dariya ya ganosa
shima sarai hakan yasa shi k'in gaya masa saya wanashi tukunna, Sadeeq ya sake
d'aukar towel yana yarfewa amma still Abubakar yayi shiru ganin haka yasa Sadeeq
yin magana da cewa.

"Kai twinnie kasani a gaba sai faman smiling face kakeyi, kagaya min muyi tare
kak'i."

"Oh sorry ai bansan kana son jiba, kawai tunani nakeyi naga tunda aka haifemu har
muka girma bamu ta6a raba d'aki ba indai muna cikin garin nan, amma sai gashi m
twinnie kana cikin garin kano Ina ciki amma mata sunsa zamu rabu muje mu kwana kusa
dasu."

Shima Sadeeq murmushin yayi yana k'ok'arin zuge zip d'in trolley d'in, shi kansa
haskilo hakan yake yana hangosa da Zarahn shi abar kaunarsa. Duk jinsu sukeyi
tamkar wasu sababbi a cikin duniyar suna jin wani nishad'i Abubakar yana hango
yadda zasu kwashe a daran yau shida INdo ya kuma yin wani murmushin har yana fitar
da sauti Sadeeq ya kuma kallonsa tare da mik'ewa yana cewa.

"Amma dai ba abinda ka gaya min kad'ai kesaka wannan farin cikin ba dan abin naka
yayi over..?!"

"Ina tunanin yadda zamuyi rayuwa ne da Humairah, ina ganin kamar bazan iya barinta
anan ba kafin a gama gyara min gidan danake acan, twinnie advice me please."

Mamaki Sadeeq yake ganin wai INdo Abubakar yake yiwa wannan sambatun tun kafinma
suyi rayuwar aure ya kuma fahimtarta. Jan trolley d'insa yayi yakaita saitin k'ofa
sannan ya dawo yana k'ok'arin cire singlet d'in jiginsa zai shiga wanka dan sai
anfara d'aura nasa auran sannan zasu wuce ayi nashi yace.

"Toh mezai hana idan kagama 2weeeks d'innaka kutafi tare sai ta zauna a gidan haka
tana ciki ana gyarawa ai tasaba da rayuwa a irin wannan yanayi bazata damu ba."

Wani banzan kallo Abubakar yayi mai kamar yasan hakan zata faru yak'i kallonsa
saima saurin shigewa toilet dayayi yana murmushi ciki-ciki. Kwafa Abubakar yayi
tare da zuge tashi trolley d'in sannan ya kira INdo a waya ringing biyu ta d'auka
yaji muryarta a dashe tana gaidashi yayi dariya yana cewa.

"Kai babyna tun yanzu.?!"

Tayi dariya murya a dashe tace "Tun jiya da yamma."

Yace "Nikam banajinki amma tunda naji kad'an bari na kyaleki inyi wanka kafin gobe
kizo kiyi min.."

Kit.. Yaji ta kashe wayar dama yasan za'arina yayi dariya tare da ajiye wayar ya
gama kimtsa komai nashi shima Sadeeq yana fitowa ya shiga kafin ya fito har
abokansu sunfara zuwa. K'arfe 11:00am suka fito cikin shiga iri d'aya hatta aikin
babbar rigar da agogonan su takalminsu da huluna duk iri d'aya ne sai faman k'amshi
suke zubawa lokacin gidan yacika da mutane, waje suka koma inda maza suke suna
gaggaisawa kafin a d'unguma a tafi gidan su Fateema bakunan su kaf yak'i rufuwa kai
daka gansu kasan suna cikin farin ciki.
Shad'aya da rabi dai-dai dubban mutane suka shaida auran Sadeeq Salman Harun da
Fateema Idris yahaya. Sadeeq murna kamar zuciyarsa zata fito sai gaisawa suke da
mutane wanda yawance basu gane waye angon yanzun sabida kowa akayiwa murna saiya
amsa. Bayan sun shiga gidan su Amaryar sun gaisa da iyaye amarya ta fito cikin
makeup tayi masifar yin kyau cikin farin les riga dazani tazo ita kanta kasa gane
waye nata tayi saida aka ce za'ayi musu su biyu sannan aka musu su uku itace a
tsakiya, ana gamawa suka fita.

Bayan an koma gida mutane sunci abinci sukuma suka kumayin wanka suka sa wasu
fararan kayan wanda suma babbar rigace kalar surfanine ba irin wanda suka cire ba
nan ma sunyi masifar yin kyau Abubakar yayi ma INdo text message cewar gashi nan
zasu taho.

Motoci ne reras sunfi ashirin aka tafi Sumaila kauyen Sani unguwa kuwa unguwar su
INdo akayi parking motocin, ana gayawa su INdo jikinta ya fara rawa hankalinta ya
tashi tsoro ya fara shigarta suna zaune a gidan Rukayya ta kule cikin uwar d'akinta
tayi shiru domin su Uwani su Rukayya duk suna bata labarin aure Abubakar nata kiran
wayarta tana gani tak'i d'auka shi kuma befasa kiranta ba. Sai da su baffajo na
saye suka shigo zauran gidan sukace a fito musu da ita sannan ta fita jikinta ya
kuma yin sanyi. Hannayenta suka kama sanye take cikin shadda maroon color sai
hijjab datasa fuskarta tashi kwalliya kaida kagani kasan amarya ce su Baffajo suka
wuce da ita wajan masu d'aurin auran Abubakar na zaune aka zaunar da ita a kusa
dashi ga uban maza waliyin amarya ya tambaye ta.

"Aisha kina son Abubakar wanda za'a d'aura muku aure yanzu..?!"

Kan INdo a k'asa jikinta sai uban rawa yakeyi Abubakar hankalinsa yayi mugun tashi
ganin tayi shiru, ana k'ok'arin sake tambayarta ta d'aga Kai alamar Eh sai a sannan
ya sauke wata uwar ajiyar Zuciya yana dafe k'irji shima wakilinsa ya tambayesa.

"Abubakar kana son INdo zaka aureta da yardarka ba takurama akayi ba ko..?!"

Yace "Eh uncle." Sannan akayi kabbara aka fara addu'ar d'aurin aure a gurin aka
damk'awa INdo kud'in sadakinta naira dubu tamanin lakadan kowa ya shaida sannan su
Baffajo suka shiga da ita cikin gida, fuskarta kunshe da murmushi ganin yadda
Abubakar d'inta ya tsure taji ta k'ara sonsa cikin zuciyarta.

Shigowa ango yayi da abokansa cikin gidan aka fara hotuna wasu sun tsaya sun shiga
cikin matan yayin da wasu abokan da girman kai yayi musu kwaliya suka ja baya cewar
mutanen basuyi musu ba wata ma mata tukin tuwo sukeyi suka saki dan ayi hutonan
dasu, hatta Sadeeq buya ya dingayi a bayan Abubakar.

Shikuwa babu ruwansa duk Matar data matso zai matsa suyi tare za'ayi musu shida
INdo yayi k'ok'arin cafko hannunta ta cikin babbar rigarsa, da sauri ta kallesa
cikin sa'a akayi musu hotuna sai hakan ya bada style zata yi magana yayi saurin
sakin mata yana dariya Sadeeq yazo akayi musu su uku sannan suka tafi sam an
hanashi amaryar su ke6e har suka kammala komai aka bar motocin da zasu tafi da
amarya sukuma su Sadeeq suka wuce.

Duk zaman dasu Abubakar sukayi a garin an hanasu ganin amarya sunyi magiyar
sunyi duk iya yinsu amma mutanan bikin nan suka hana. Sai bayan la'asar an shirya
amarya za'a tafi sannan Abubakar suka tafi yabar abokansa da zasu d'akko su duk da
yasha wulak'anci wai yaja zasu d'akko 'yan kauye a motarsu.

INdo na lullu6e su Inna nayi mata fad'a idanta har’wayau hawayen sunk'i zuwa sai
Innace keyi dan tama kasa tsayawa sosai tayi mata fad'a sai faman cewa takeyi.
"Tabi mijinta tayi zaman aure." Sune kawai kalaman Inna, haka ma malam Hamza shima
abinda yace mata kenan sai kuma nuni dayayi mata da yadda Inna takeyi mai biyayya.
'Yan uwa duk sunyi mata fad'a ana k'ok'arin fita da ita saiga malamarsu ta islamiya
malam Hansa'u tazo yi mata Allah yasanya alkhairi ta jata d'aki suka zauna ta Fara
mata nasiha.

"Toh Aisha yau dai gashi Allah ya kawo ranar da kika koma k'ark'ashin wani ba
iyayanki ba, yanzu ya koma shine uwar shine kuma uba shine danginki. Aisha kiyi
biyayya yin biyayya ga mijinki shine zaki samu aljanna, karki manta da karatun da
ake koya muku duk abinda mijinki yace kiyi toh kiyi indai besa6awa addininki ba, ke
ko cewa yayi Aisha ga wuta fad'a karkiji d'ar kifad'a din kawai, Aisha kibi aure
karki yiwa mijinki rashin kunya ko gaddama ko kiyi musu dashi yin hakan Allah zaiyi
fushi dake fushin Allah kuwa babban had'arine akan kowanne halitta.

Allah ya bada zaman lafiya Aisha ya kad'e muku fitina a cikin auranku ya baku
zuri'a masu albarka tashi muje akaiki gidanki mai tarin ni'ima da albarka.."

Sai a lokacin INdo ta fara kuka tsoro ya kuma shigarta har aka shigar da ita
jibgegiyar motar abokin Abubakar dayazo daga Abuja.

Su uku suka shiga sai driver da friend d'inshi a kusa dashi, ana gama cika motocin
suka d'auki hanya shikenan INdo tabar kauyen Sani saidai tazo da ziyara Allah ya
d'agata. Gudu suka dingayi kafin wasu awanni sun k'arasa k'ofar gidan su ango
lokacin duhu yafara yi.

Bayan an kaita su Mama sunyi farin cikin shigowarta zuri'arsu sunyi mata nasiha aka
sake d'inguma aka kai INdo gidan Abubakar masoyinta farin cikinta abin alfaharinta,
fuskarta a lullu6e aka shigar da ita cikin d'akinta.

Ita kuwa Fateema saida akayi sallar isha'i sannan aka kaita gidansu Sadeeq itama su
Mama sukayi farin cikin shigowarta cikin su sannan aka wuce da ita gidan Sadeeq
farin cikinta abin kaunarta, ta riga ta tsara musu yadda zasu gudanar da rayuwar
auransu abinku da 'yar boko wayayya.

Masu kawo INdon kauye sai da suka kwana Abubakar yace abarsu sabida dare yayi kuma
duk masu motocin sun tafi wai bazasu koma wannan kauyan ba yadai sha iskancin
abokai wanda hakan besa yaji kaunar INdo ta ragu koda da kwayar zarra ba. Sadeeq
suka raka gidansa aka yi musu nasiha shida amaryar sannan Abubakar suna k'ok'arin
fita yace ma Fateema dake lullu6e cikin mayafi.

"Ke..! Sauran kibawa twinnie d'ina wahala ko kiyi mai rowa."

Tana jinsa ta k'i cewa komai har suka fita Abubakar ya kalli Sadeeq tare da cewa.

"Kai twinnie wallahi kabi yarinyar mutane a hankali, nasanka sarai a mafarki ma
kana wuce k'a'ida bare kuma yau gaka ga mace mallakinka. Idan ka kirani da safe ba
zuwa zanyi ba ah toh..."

Hannu Sadeeq ya bashi suka tafa suna dariya kafin su rungumi juna Sadeeq yace.

"M twinnie har gobefa kai saurayi ne sorry to you wallahi but zaka iya sato Aishan
ku koma wani d'akin fa."

"Nop karka damu zan hakura harsu tafi ai daga yau ne gobe zan samo musu mota ta
maidasu."

Kamar karsu rabu haka sukeji amma babu yadda zasu yi yana fita ya rufe gidan ya
koma ciki. A hankali ya zauna kusa da ita tare da yaye mayafin kanta cikin kunnanta
yasanya bakinsa yace.

"Amarya muje kiyi alwala muyi sallah."


A kunyace ta mik'e ya kama hannunta ya kaita har bedroom d'insa cikin toilet sannan
ya fito ya shimfid'a musu sallaya ya ajiye mata sabon hijjab, tana fitowa shima ya
shiga yayi alwalan sannan yazo yajasu sallah suka yi raka'a biya ya dafa kanta yayi
mata addu'a sannan ya kalleta yace.

"Nasan akwai yinwa a cikin nan tashi muje na baki kici bana son kwana dayinwa."

Ya fad'a yana shafa mata ciki, Fateema cike dajin kunya ta mike yayi saurin rik'ota
tare da janta jikinsa suka nufi parlor. Kajine gasassu sunsha kayan had'i da lemuka
da fresh milk suka zauna yafara bata, a yangance suka gama ci sannan ya wanke
hannunsa ya jata suka shiga d'akinsa.

Kayan bacci yasa ya d'akko wata shegiyar rigar mata ta bacci ya mik'a mata yace
tasa, ta d'aga rigar nan ta ganta 'yar firit Fateema aka dinga raba idanuwa ta kasa
tashi tasa yayi murmushi tare da cewa.

"Bari nazo na temaka miki."

Ya mik'e daka bakin gadon tana ganin haka tayi wuf ta shige toilet yayi murmushi
yana lasar leb6ansa. Fitowa tayi bayan tasawo sai kuma ta nad'e jikinta da mayafi
kamar tasa lafaya ta kwanta a kunyace, shi kuma yayi musu light of (kafin naji
kici-kicin su k'ila k'ok'arin kwance mata yake yi nidai Hajja nayi kwana dan d'akin
badai duhu ba yau su Sadeeq za'a angon ce na fita zuwa gurin Abubakar.).....

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *20*

Around 1:45am Abubakar ya shiga cikin gidan nasa bayan ya gama kulle ko'ina yana
son lek'awa yaga yasuke amma yana tsoran yadda zai shiga ya gansu dan yasan matan
kauye basu fiye kwanciya da riguna ba dan haka ya koma yashiga d'akinsa ya kulle.
Wayar INdo ya dinga k'ira amma ba'a d'aga ba ya ajiye tare da shiga wanka. Sukuwa
su INdo bayan an kawota tafita suka zagaya gidan farin cikinta ya kasa 6oyuwa ganin
irin gidan da take ciki gida irinna cikin films had'add'e wanda ko cikin mafarkinta
bata ta6a zaton zata ta6a koda jikin gidan ba, tun shad'ayan dare suka barbaje
bayan sinci sunyi hani'an ga iskar fanka na kad'a su ai babu wanda ya kuma motsawa
munshari kawai kakeji yana fita hahhhussss ta kowace kusurwa.

Tun sallar asuba yafita, su kuma suna tashi suka hau shirin tafiya, saida yaje gida
yasa Mama ta bada abinci aka kaimusu sukaci wajan k'arfe goma na safe ya kawo musu
buses biyu ya biya masu motar sannan suka tafi sunata yiwa INdo Allah sanya alheri.
Saida yaga sun tafi sannan ya shiga gidan, a tsaye ya tarar da INdo tana wajan
dining bakinta a bud'e sai shafar kujerun takeyi ya tsaya yana kallonta ba tare da
tasan yana tsaye ba.

Yana kallonta ta d'an d'osana d'uwawunta akan kujerar sai kuma tayi saurin
mik'ewa tana dariya tana karkad'e gurin, ya shigo a hankali cikin rashin sa'a ta
hangosa ta cikin glass d'in drawer flat's na dining dake wajan. Da sauri tayi
hanyar shiga d'aki zata gudu yayi saurin cafko ta yana dariya yasanya ta a jikinsa.

Fisgar jikinta takeyi zata gudu amma ya hana hakan faruwa, kanshi ya zura a wuyanta
ya fara shin-shina wuyanta yana sanya siririn hancinsa cikin kunnanta iskah na
shiga ciki, INdo taji wani irin abu hankalinta ya fara tashi kwakwalwarta ta fara
aika mata da wasu bakwannin al'amra.

Jin hannunsa a kan k'irjinta ne yasata kwallara mai wata uwar k'ara, Abubakar yak'i
sakinta saima jikin bangon k'ofar da zata kaita bedroom d'inta ya jinginar da ita
gaba d'aya ta tsure ya kamo fuskarta da duka hannunsa biyu, bakinsa yakai saitin
nata zaiyi kissing d'inshi INdo ta kwalalo mai ido tana bin harshensa da kallo
tamkar idonta zai fad'o sai girgiza kai take alamar bata so.

Ganin kamar abinda yake shirin yi mata ne bata so yasa shi sonyi mata dan ta gane
cewar ba wani abun aibu bane. Gate yajiyo ana bugawa nan INdo ta fara sauke
numfashi dan tasan dole yanzu yaje ya bud'e, ba zato bare tsammani kawai taji ya
zura mata tongue d'insa tayi-tayi ta datsa bakin amma ta kasa ya fara tsotsa tare
da zame d'ankwalin kanta yana shafar gashinta. Nan da nan jikin INdo ya fara kyarma
tamkar shocking yajata yayi k'ok'arin tattarota zuwa jikinsa still mouth nasa na
cikin nata idanunta a tamke ta dunkule hannayanta jira kawai takeyi taji zubar
fitsari.

Sake bugun gate d'in ake da k'arfi amma yak'i kulawa hankalin INdo ya kuma tashi,
sai da yayi mata ya tabbar da sakon salonsa na farko ya shigeta sannan ya cikata
aikuwa ta zandama d'aki da gudu hartana bugewa da bango yayi dariya yana kallonta
harta shige sannan ya gyara wuyan rigarsa ya fita yana bud'ewa yaga sisters d'in
Mamansu ne da yaransu ya fara sosa k'eya aunty Shafa'atu ta kallesa dakyau sannan
tace.

"Doctor ko baku tashi bane ba tun d'azu sai faman bugu mukeyi..?!"

"Ah mun tashi mana aunty yanzu ma na koma ciki da 'yan uwan Humairan suka tafi."

"Oho toh." Suka fad'a tare da shiga ciki suna kiran sunan INdo.

Shiru tanajin su tak'i fitowa sabida gani takeyi kamar idan ta fito zasu gane, yana
zaune a gurinsu yaga tak'i fitowa yasan dalili hakan yasa shi ce musu yana zuwa.
Kwance ya ganta kan gado ta yaye bedsheet d'in ta cukwikuye jikinta gabaki d'aya ta
kudindine ya tura d'akin yana murmushi da mamaki ya hau kan gadon.

Qarah curewa tayi Abubakar ya janyota gaba d'ayanta ya fara warware bedsheet
d'in amma sai sake nad'ewa take cikin kasalalliyar murya domin wannan kokawar da
sukayi wani shauk'i ne ya dinga saukar mai yace mata a hankali.

"Please Humairah tashi kizo muje sisters d'in Mama ne suka zo, bana son naji sun
fara yin k'orafi dake kinji...?!"

Tana cikin zanin gadon tace mai.

"Toh amma kafita sai na fito.."

"Toh nafita kixo yanzo sai ki kawo musu lemo da ruwa."

Yana fad'a ya fita daga d'akin sai dai yana la6e, tashi tayi ta sakko a hankali ta
k'arasa gurin madubi tana shafa bakinta ta kuma bud'esa ta kallesa a cikin madubin
a fili tace.

"Kai likita da k'azanta kake wallahi irin na film yayi min, amma fa kamar da dad'i
hi har wani lumshe ido yake yi."

Dariya ce ta kusa tona mai asiri hakan yasa shi juyawa ya fita falon yana yi gashi
ya kasa denawa mutanen dake falon suka bishi da kallo suma suna murmushin kowa da
abinda yake kisamawa wanda yasa shi dariyan.

"Abin na masoya ne me ta gaya maka haka kake 6a66aka dariya."

Shafa k'eya yayi yana shirin yin magana sai ga INdo ta fitoh hannunta a saman
bakinta sai faman rarraba idanuwa takeyi aunty Siyama tace.

"Aunty amarya taho nan ki zauna."

A d'ard'ar taje ta zauna kafin ta fara gaidasu k'ananun kuma suka gaida ita, had'a
ido suka yi da Abubakar yayi mata alamar ta kawo ruwa cikin sa'a ta mik'e taje inda
taga an ajiye lemukan da ruwan ta d'ako ta kawo da yawa sannan ta koma zata zauna
Abubakar yace.

"Hunairah baki d'akko musu kofina ba."

"Au dan Allah kuyi hakuri kunji bari na d'akko."

Ta fad'a tare da shiga tsalelen kitchen d'inta, kalle kalle ta farayi domin gabaki
d'aya ta hargitse ta shagala da kallon dukiyar da aka kashe har ta manta da cewar
aikota akayi. Itace ta6a nan shafa can shinshina nan haka ta dinga yi, shirun
dayaji ne yasa shi mik'ewa yabiyo bayanta.

Tsaye ya tarar da ita tana ta6a electric oven taga hotan kaza a jiki ya bita da
kallo, sam baya ganin aibunta domin yasan dole tayi haka tunda ba ko ina akeda irin
abubuwan ba dan ko gidansu Abubakar d'in babu wasu abubuwan da ya zubawa INdo.
K'arasawa yayi ta kallesa tare da juya Mai baya yayi dariya yace.

"Ohh su Humayrah daga zuwa d'akko cups sai mukaji shiru."

"Lah wallahi mantawa nayi bari na kaimusu, amma wanne zan d'auka..?!"

Ta fad'a ba tare da tajuyo ba, ya k'arasa tare da janyota jikinsa yace,

"Kibar shi sun ma farasha da jarkar."

"Toh sakarni na fita gurin su."


"Nak'i d'in da wayace kik'i komawa..?!"

Jin ya fara shafar jikinta ne yasa ta faraturesa ya juyo da ita ta kawar dakai sai
ji tayi bakinsa a saman k'irjinta INdo ta zabura ya saketa ta ruga falo nan ma suka
bisu da kallo ita dai INdo harta zauna jikinta be dena rawa ba a haka har suka gama
zamansu sukayi musu fatan zama lafiya sannan suka fita suna tafiya wasu suka zo
ranar ma dai haka suka wuni da baki.

Misalin k'arfe goma na dare Abubakar ya shigo gidan, tsit ba kowa sai k'arar inji
ya rufe ko'ina sannan ya shiga falon, zaune ya ganta tana kallo ta kurawa TV d'in
ido sai dariya takeyi da alama film d'in yayi mata kyau.

Duk sallamar da yakeyi bataji ba sai daya shigo har tsakiyar falon ya kare mata TV
d'in sannan taganshi tana dariya tace.

"Kai dacta dan Allah ka matsa kana kare min."

Hannu ya bud'e mata alamar tazo suyi hugging amman tak'i sai ya kashe kallon gabaki
d'aya tare da k'arasawa dining ya ajiye ledojin hannunsa. Tashi tayi tana turo baki
ganin ya kashe mata gashi bata iya kunnawa ba dama su Hawwa ne suka kunna dasuka zo
ya juyo ya kalleta tare da cewa.

"Kin manta ko, da bakinki kika cemin malama ta baku labarin matar da bata bin
umarnin miji da abinda akayi mata ko? Shine yanzu nace kizo kiyi min oyo-yo kikaki
ba ruwana dake."

INdo ta tuna tayi saurin zuwa gurinsa ta tsaya, ganin haka yasa shi kuma ware mata
hannunsa a hankali ta shige bayan ta rintsa idanuwanta ya rungumeta shima. A saitin
kunnanta ya tambayeta.

"Kinyi sallah..?"

Kad'a kai kurum tayi sannan nan yace.

"Zo muje muyi wata mu yi addu'a alkairin dake cikin auran mu Allah ya tabbatar
dashi."

Tunawa INdo tayi da labarin dasu Uwani suka bata cewar indai taji miji yace ayi
sallah akuma ci nama toh ranar aikwai aiki musamman ranar da aka kaika. Janta yayi
suka nufi bedroom d'insa dama bata ta6a shiga ba, taga wani shegen gado me shegen
kyau bakin ta yak'i rufuwa yace.

"Zokije kiyi alwala."

Tace "Dacta tsaya na gama ganin gadonka wallahi yayi kyau Allah sanya alheri."

"Amin Humaira amma ai shima nakine, duk abinda kika gani na gidan nan nakine ko
mutuwa nayi baza a raba gadona dasu ba."

Cikin tsananin murna INdo tace tana kallonsa.

"Dacta da gaske kake nawane.?!"

Kai ya d'aga mata ta fara murna tana godiya sannan ta shiga bayin tayi alwala, tana
fitowa shima yayi lokacin ta dawo daga d'akko hijjab, kar6a yayi ya bata sabo tasa
sannan yajasu sukayi 2raka'at sannan ya dafa kanta yayi mata addu'a suka shafa.
Hannunta ya kama suka koma falo ya kunna musu kallo suna dining suna kallo ya dinga
feeding d'inta sai da taci ta koshi ta kora da madara sannan tace ta koshi.
12:49am suka shiga d'akinsa INdo sai hamma takeyi najin bacci, saida ya had'a mata
ruwa tayi wanka sannan shima ya shiga ya fito sanye da boxer tayi saurin kawar
dakai tana zaro ido gashi ya kulle d'akin itama daga ita sai towel ya kwashe mata
kayan ta nema ta rasa.

Turare ya shafa kawai sai na mouth sannan ya nufi gurinta dasu, zama yayi a kusa da
ita tayi saurin matsawa shima ya matsa tare da rik'ota da sauri tace.

"Na higa uku ni INdo dan Allah dacta kayi hakuri."

"Shhhh." Yayi mata tare da matsa mata turaren ya ce ta bud'e bakin ya fesa mata da
sauri ta tufar da yawu a k'asan bedside carpet yace.

"Humaira ya haka.?!"

INdo kamar tayi kuka tace "yo toh ai ba dad'i."

Dariya yayi tare da girgiza kai sannan ya tashi ya mayar tare da d'akko
handkerchief ya goge gurin. Light off yayi musu sannan ya kuma kunna bedside lamp
bulb d'in green light ya haske d'akin yayi kyau INdo ta kalli d'akin ta kuma sakin
murmushi ita dai yau tana ganin ikon Allah a gidannan. A hankali ya sargafota ta
fara zillo towel ya fara kwancewa tace.

"Wai kai bazan sa kaya bane.?"

Cikin sanyin murya Abubakar yace "Eh a haka zaki kwana ko kina son nace bana so
amma kuma kisa...?"

Ya tambaya yana shafa gashinta, wani kakkawar yawu ta had'iya tana kad'a kai, ya
janyota kan gadon towel d'in ya yaye daga k'asa INdo ta saki k'ara jikinta na rawa.
A hankali ya kuma janta jikinsa sannan ya zare mata towel d'in gabaki d'aya ai INdo
sai kuka tana cewa.

"Yaya Abbakar karka kalleni in kanawa iyayenka, ni wallahi ka dena ta6ani banasan
iskanci..."

Sam bazai iya yi mata abinda take so ba, shi amatsayinsa na likita yasan idan ya
barta besamu nutsuwa ba zai shiga tashin hankali ya kuma San akwai illah hakan. A
hankali cikin wayewa da iya *TATTALIN MACE* Abubakar ya dinga hillatar da ita yana
kuma nuna mata illar hanashin da takeyi a haka ya samu INdo ta yadda dashi ta bashi
kanta duk da tasha kuka hardasu majina.

Yana daga kwancen yace,

"Ohh so sorry my wife, please zoki rama kema."

Tana kukan ta k'asa-k'asa tace.

"Meh...?!"

Ai Abubakar besan lokacin daya kyalkyale da dariya ba haushi ya sake zuwar ma INdo
ta juya ta fara dukansa yana karewa da hannu...
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *21*

Ganin yak'i denayi mata dariya yasa ta lalubo towel d'inta ta d'aura ta kwanta tare
da janyo bargo ta rufa sabida wani sanyi dataji yana shiga cikin jikinta. A hankali
ya matsa kusa da ita tare da zura hannunsa ya rungumeta tana jinsa ta kasa yin koda
kwakwaran motsi sabida jikinta duk ya lafe a haka bacci ya d'auketa shi kuwa kasa
yi yayi se tashi mayayi yaje yayi wanka sannan yayi sallah ya d'auki sallayar ya
maida ita inda zai dinga kallon fuskarta. Yana jan carbi yana shafar gashinta tare
da shafar fashin goshinta wanda yake d'ansiriri.

Har aka kira asuba INdo bata koyi juyi ba bare asaran zata tashi ya mik'e daga kan
sallayar yashiga bathroom ya tarar mata ruwa sannan ya fito, a hankali cikin
nutsuwa ya fara tashinta amma babu alamar zata motsa sai ya yaye mata bargon ya
fara k'ok'arin kwance mata towel tayi saurin tashi tana rarumarsa tana furta
"6arawo..!" ta d'auka 6arawo ne sabida a tunaninta wannan uban gidan baza'a rasa
6arayin dazasu shigo yi musu sata ba. A mamakin ce Abubakar ya kalleta ganin yadda
ta cakumeshi tayi saurin sakinsa tare da saurin komawa ta kudindine a bargo yace
mata.

"Humairah a mimakwan yin auziya sai ki furta 6arawo? Toh ina 6arawon tashi ki gaya
min ko mafarki kikayi..?!"

Tana cikin bargon tace "Allah mafarki nayi kayi hakuri."

"Toh tashi kiyi wankan tsarki sai kiyi sallah."

"Wane iri kuma dacta?!"

Ta tambaya da mamaki yace "na janaba ko bakisan anayi ba?"

Sai yanzu ta gane kenan a makaranta da aketayi musu bayanin wanka haila, wankan
janaba da wankan bik'i shi yanzu wanda zata yi shine na janaba ikon Allah dan ita a
karatu idan ba practical ba toh theories dakyar suke shigarta.

"Kin iya ko..?!"

Ya tambayeta tayi shiru ya kwanta a bayanta tare da janyota ya matseta, ihu ta


farayi sannan tace.
"Toh sani nayi ne, ka gaya min mana."

Yace "Okey kin iya wankan tsarki na haila?" 'Daga kai tayi yace "tashi ki nunin in
gani ko dai-dai kikeyi?"

Dakyar ta tashi zaune tana gwada mai ya gyagyara mata sannan yace taje tayi amma ta
canzaxani.Ta shiga bathroom d'in da sauri wai dan yana kallonta, tana fitowa sukayi
sallah sannan yace tazo su yi karatu, tundaga Nasi ya fara mata har akazo inda ta
iya sannan yace toh zai dinga koya mata kullum da asuba indai yana gari.

Gadon ya sake janta ita INdo bata sabayin baccin safe ba hakan yasa tace mai ita
kallo zataje tayi ya hanata dole taje suka kwanta, romance d'inta kawai yayi mai
tsayawa a wuya dan tana k'ar6ar sakon yadda ya kamata kafin kace mene tuni INdo
tayi baci shima ya samu yayi har kusan 9:16am sannan ya farka yana zare jikinsa
itama ta farka a kunyace dan ko kallonsa bata iya yi.

"Muje kitchen yau dakan mu zamuyi breakfast."

Kama hannunta yayi suka fita suna zuwa kitchen ya sargafe hannu a k'irji yana jiran
yaga ta ina zata fara, itama tsayawar tayi tana kuma bin kayayyakin kitchen d'in da
ido.

"Jiya na shigo da slender bari na had'a sai ki soya kwai da tea."

Tace "Toh akan slimba d'in Zan d'ora."

"No Humairah slender itace abinda za'a zuba kalanzir toh ba shi za'a zuba ba gas
za'a saka ajona na wannan sai da kin kunna zai kawo wuta idan ya k'are kuma zakiga
yak'i kawowa."

Jinjina kai tayi tamkar ta fahimta, shi kuma dayake yasan dawa yake tare sai ya
kamo hannunta suka nufi bayan kitchen d'in, a kan idonta yasa dan watarana idan ba
kowa ya zama na ta iya. Komawa cikin kitchen d'in sukayi sannan ya kunna cooker
d'in sai ga wuta INdo ta dinga murmushi kusan duk shi yayi koma tana kallonsa suna
yi yana nuna mata amfanin komai na kitchen d'in komai saida ya nuna mata sannan
suka kwashi breakfast d'in suka kai dining.

Yauma kamar jiya daddare shi yayi feeding d'inta taci sannan shina yaci suka koma
wajan TV lokacin injinsu ya mutu suka kalli juna yace.

"Muje d'aki ki gani."

Yana rungume da ita yace suka shiga ya d'akko laptop d'insa ya kunna mata kallon
yaga alamar tana masifar son yin kallo tana zaune a tsakiyar gado ya d'ora kansa a
cinyarta tayi dariya tana kallonta. Hannunta ya kamo ya d'ora akansa tare da cewa.

"Sweetie bazaki dinga shafani ba, please inason ki koyi soyayya fa ni Ina son
love."

Sosa mai ta fara yi ya dank'e hannun tare da cewa,

"Bafa haka akeyi ba, haka...!"

Ya fad'a yana rik'e da hannunta yana shasshafa kansa, haka Abubakar ya dinga
tarairayar INdo yana nuna mata abubuwan da zata dinga mai cikin ko wane irin abu ko
yanayi sai da ya nuna mata irin abinda zata yi mai tun tanajin nauyi da kunya harta
fara sakin jiki tana yi mai ba tare da ya nema ko ya nuna buk'atar hakan ba.
Cikin sati d'aya INdo ta kuma wayewa da wasu abubuwan tayi kyau abinta ranar da ta
cika kwana takwas ya d'auketa sukaje gida su Mama suka dinga shi musu albarka INdo
bajin kai k'annansa duk babu wanda bata wasa dashi sun dad'e Kafin su tafi gidan
Sadeeq sai INdo tayi mamaki ganin gidanta yafi kyau sai akayi sa'a bata kwafsa tayi
maganar ba.

Sosai suka sha hira shima Sadeeq ya sakar mata fuska Fateema taja ta suka kule
d'aki, nan ma sun dad'e kafin Abubakar yace tazo suka tafi.

Washe gari ya d'auketa suka jajje gidan abokansa na nan sannan ya kaita har
Munjibur park wayyo farin ciki a gurin INdo ba'a musallatawa duk abinda taga anhau
sai tahau shi kuma ya biya duk bata san sai ya biya ba sha'aninta kawai takeyi suka
yi hotuna wasu tare wasu kuma ita kad'ai. Sun dad'e kafin suka koma gida INdo cike
da murna ya kalleta shima cikin shauk'inta da soyayyarta sannan yace.

"Zo kimin tausa tunda yauma kin gajiyar dani."

Zuwa tayi tana shan ice cream tana mai sannan shima ta bashi yasha wani shauk'i
yana fisgarta bata san lokacin da ta kwanta a bayansa ba a hankali ta furta mai.

"I love you mijina."

"Oh my God what did you say? Allah yasa ba mafarki nakeyi ba sweetie d'an jijjiga
ni."

Cikin dariya INdo da bugeshi a baya ya juyo tare da janyo ta aikuma ice cream d'in
ya zube a saman k'irjinshi yace.

"Aikuwa sai kin lashe shi kuma ki gama ki wanke ni ah bazan yadda ba."

"Ah my key nifa bani ce silaba kai kaiwa jikinka haka."

Ta fad'a tana masa cukali tana d'iban na k'irjin nasa tana sha yanzu duk ta waye
bata kyama ganin shima vaya nuna mata akan komai na jikinta.

"Nifa inajin zafin na cukalin nan ki ajiyeshi."

"Toh baki zansa?!"

Ta tambaya kai tsaye shima kai tsaye yace mata "Eh shi nake so."

Harshe tasa ta fara lasa har sai data sud'e tass sannan shima ya faki idonta ya
d'akko ragowar na rubar ya 6arar mata a k'irji yace.

"Ashhh sorry bari na ramamiki kema."

Dariya suka saki tare cikin dariyar tace.

"Kaifa kana sane."

Ya rik'ota yasa baki tass shima ya lashe mata daga nan kuma al'amra suka canza. Ana
gobe zai koma abuja suna kwance duk sun mak'ala juna suna sauk'e ajiyar Zuciya
kad'an-kad'an Abubakar yana shafar kanta yace.

"Humairah banson tafiya na barki anya bazan tafi dake ba?!"

Shiru INdo tayi babu amsa ya kuma janta jikinsa yana d'an shafarta tana biye mai ya
kuma cewa.
"Kinyi shiru Humaira ko dama kin k'agara na tafi.?"

Tace "A'a bansan abinda zance ba nima shi yasa nayi shiru fa."

"Okey kema kina son ki bini ko?"

Tace "Eh mana."

Hannunta ya rik'o ya d'ora a k'irjinsa tare da cewa.

"Ina sonki Humaih ina kaunarki ban ta6ajin Ina kaunar mutum ba kamar yadda nake
sonki, please kema ki soni koda bekai yadda nake miki ba kinji..?!"

"Toh ai Ina sanka nima."

Ta fad'a cikin sanyin jiki suka rungumi juna da haka sukayi bacci, washe gari tunda
asuba suka yi wanka INdo tayi kwalliya irinta kauye tasa zani daban riga ma haka da
d'ankwali. Abubakar na shigowa d'akin daga shi sai boxer da singlet ya kalleta yana
murmushi yaga kwalliyar tayi mata kyau ya k'arasa ciki yana cewa.

"Woww sweetie gaskiya sai na biya wannan wanka I like it."

"Toh nawa zaka biya domin da tsada...?"

Ta tambayesa tana jan hancinsa, bakin gado ya zauna yana rik'e da kugunta yace.

"Bari kigani."

Kissing d'in bakinta yayi duk ya kwashe janbakin datasa ya matseta a jikinsa yace.

"Allah ya miki albarka matata kafin in dawo Zan samar miki makaranta damun koma
saiki shiga."

"Kanason nayi karatu da yawa, nikuma kaga ban iya turanci ba."

Ta fad'a tana shafar sajansa ya sanya kansa tsakiyar kirjinta yana goga fuskarsa a
jiki yace.

"Zaki iya kema sweetie ai da koyo akasan gwani, abaya ma dandai baki tsaya kin koya
bane amma yanzu kisa aranki cewar kema zaki iya turanci kinji ko..?!"

"Allah yasa toh.."

Ta fad'a yace "Amin sai kuma abani bye-bye dan bazan tafi haka ba"

Rufe fuska tayi ta zauna kan cinyarsa wannan karan itace ta fara sanya mai mouth
nata cikin nashi ya k'ara tabbatar da lallai tana d'aukar naganar tana kuma jinta
tare da aikata ta a aikace. Sai da ya samu nutsuwa sannan sukayi wanka kamar karsu
rabu duk da yace mata kwana biyar zaiyi yaxo yayi weekend amma gani yake tamkar
rasa ta zaiyi, itama haka ta dinga cewa ya barta su tafi abuja tare dama bata ta6a
zuwa ba amma ya dinga kwantar mata da hankali yace kila ma jibi ya dawo idan yaje
ya rage wasu abubuwa.

'Dakinsa saka koma ya shirya duk ta nanik'e mai ya kalleta yace.

"Idan na tafi kiyi tafiyarki gidan Mama ko gidan M twinnie ki zauna kuyi hira zuwa
yamma sai ki dawo dan nace dasu Haleema suzo su zauna a nan harna dawo kinji.?!"

"Toh.."
Tabashi amsa ta fesa mai turare sukaci abincin daya dafa musu suna gamawa sadeeq na
yin knocking .

Sai data fara sanyo hijjab sannan Abubakar yaje ya bud'e masa kasan cewar ya hanata
zama a haka idan wasu suka zo.

"Aishatu Hamza..."

Cewar Sadeeq cike da zolaya tayi murmushi tare da cewa.

"Malam Sadeeq ya gida..?!"

"Kalau."

Yabata amsa Abubakar yace.

"Twinnie gidana a hannunka please ka kular min da babyna."

"Au wai kana nufin sai an kula da ita? Ta6 Aisha ai ta iya haura katanga bakada
case da ita ka kwantar da hankalin ka."

INdo ta turo baki haushinsa ya cika ta Abubakar ya janyo ta tare da cewa.

"Kabari twinnie ai dane kuma kaima ai kayi kana yaro."

Ya kalli INdo tare da cewa "Sorry sweetie karki kulasa Zan dawo na d'aukeki."

Suna dariya dukansu suka fita Abubakar ya shiga mota shida Sadeeq zai saukesa gidan
Mama idan yaje, INdo ta zagaya 6angaran Abubakar idonta yayi ruwa murya na rawa
tace.

"Allah ya kiyaye hanya."

"Amin." Ya fad'a yana zuro hannu sukayi musabuha yaja motar suka bar gidan, tana
share hawaye ta rufe gate d'in tare da shiga cikin gidan. Suna hanyar zuwa gidan
Mama Abubakar ya dinga ba Sadeeq hakkin lurar mai da gida musamman ma INdo abin ya
dinga bawa Sadeeq mamaki wai yau INdo ce take da matsayi a zuciyar d'an uwansa,
koda yake yafishi sanin INdo tun a kauyan Sani.

Bayan sunyi sallama da mutanan gidan ya kama hanya ya tafi bayan ya bugawa INdo
waya yace mata ya tafi tayi mai fatan sauka lafiya.

****
K'arfe 11:36am tana zaune a falo tana kallo bama taje gidan Maman ba ganin an
kawo wuta, shigowa yayi kai tsaye gidan tana ganinsa ta mik'e da gudu raje ta
rungume shi kamar yadda ya sabar mata. Jin jikinsa yana rawa ne yasan ya INdo
d'agowa tana kallon kafin k'irjinta ya fara bugawa sam bata gane bashi bane ta
sha'afa da kayan dayasa tace.

"My key menene? Inzo mutafi?!"

Wani kallo dataga yayi mata ne yasa hankalinta dawowa jikinsa ta zaro ido tana
kallon fuskarsa tace.

"Malam Sadeeq kayi hakuri na d'auka Yaya Abubakar ne."

Da kyar Sadeeq ya samu ya bud'e baki yace.


"Aisha jeki d'akko hijjabinki zamu gidan Mama."

INdo ta kallesa cikin sauke numfashi tana warware d'ankwalinta tayi mayafi dashi
tana cewa.

"Ah ai inajin sai anjima zani idan ma banjeba ai yace su Haleema zasu zo."

"Ki d'akko hijjab nace miki kenake jiya bawai surutu ba."

Juyawa tayi tana kunkuni ta d'akko ta fito shi kuma ya juya ya fita. Saida ta fito
sanye cikin atamfa blue da zanen ganye fari ta sanya blue d'in mayafi suka fita ya
rufe gate d'in suka shiga mota. Kasa tukawa yayi jikinsa sai rawa yake yi INdo ta
bishi da kallo cikin mamaki k'arshe ya fito daga motar yace.

"Fito muje."

A k'afa suka taka har bakin titi ya tarar musu napep suka shiga aka kaisu gidan
Mama lokacin har mutane an fara taruwa a k'ofar gida Sadeeq ya cewa INdo.

"Shiga ciki gurinsu."

Yana dad'a ya juya yabarta ita kuma ta nufi ciki tana bin mutanan da kallo. Tana
shiga parking space taji abbansu yana waya yana cewa.

"Eh wallahi Abubakar d’inne....

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

*MUSAYAR ZUCIYA:- Hak'ik'a banyi zato ko tsammanin makaranta labarin nan sunkai
yawan haka ba sai da akazo page 21, a hak'ik'anin gaskiya naji matuk'ar tsoro na
razana da ganin millions of people's da suk'e matuk'ar son Dr Abubakar da Aishatul
humaira a ranar da waya nata tarwatsewa toh da tuni an wuce babin wayata,
everywhere MUSAYAR ZUCIYA Hajja karki kashe Dr becan-canci haka ba, idan kikai
hakan kin sakamu cikin tashin hankali INdo kuma baki kyauta mata ba. Karku manta
Allah babu ruwansa da lokacin da zaka farajin dad'in rayuwa ya d'aukeka, anytime
kowane irin yanayi kake ciki idan lokacinka yayi dole ka barshi katafi ba tare da
kashiryawa hakan ba. A yanzu haka nasan wad'anda suka tanadi likaffani na mutuwarsu
sabida suna ganin sun tsufa rayuwa ta k'are musu amma har yanzu basu mutuba sai
'ya'yansu da jikok'insu wad'anda ba'a saka musu ran mutuwa sune suke mutuwa. Dan
Allah badan niba kuyi hakuri ku d'auka a cewar kuma akanku hakan zata iya faruwa
sannan kuma kowacce zata yiwa Abubakar addu'ar Allah ya sadashi da rahamarsa.
Labarin gaske ne domin da Ummi Aisha itace zata yishi so bansan Stylish Bch ta bata
labarin ba sai jiya. Kuyi hakuri harda masu cewa sundena karantawa sabida sunsan
karshe dai Sadeeq zata aura suzo suna kishi da fateema🤭toh duk kuyi hakuri kuma
sannan ku yafewa 'yar uwarku, da ace tun farko bansa muku true life ba wallahi
akwai yadda zanyi na sauya salon amma yanzu kona sauya toh araina zan dingajin abun
tunda nasan ba haka yake ba, duk wanda na 6atawa tundaga kan fara novel din har
zuwa wannan pagen kuyi hakuri ku yafewa Hajja ce👈 'yar Adam ce kamar ku sannan kuma
meyin kuskure a duk inda ta samu kanta, wallahi dana dinga ganin comments d'inku
dakyar nayi bacci zuciyata na rawa Ina ganin ban kyauta muku ba ciki rayuwarku.
Nasan da yawanku zaku dena karantawa toh Ina fatan duk wanda ya tsaya iya nan ya
d'auki wani darasi a ciki amma Zan samu na k'arasa shi a WATTPAD dan nima na samu
nutsuwar Zuciya. Nagode gaduk wanda suka karanta farkon labarin Allah ya sadamu da
rahamarsa a cikin kabarinmu Amin Love you all m fan's❤🤝❤*

Page *22*

Hark'asa INdo ta tsugunna tana gaida shi idanta akan fuskarsa tace,

"Abba ina wuni?"

Ya zura wayar cikin aljihunsa yana kallonta ya amsa.

"Lafiya lau Aisha tashi kishiga daga ciki."

"Toh adawo lafiya."

Tafad'a tana mik'ewa ta nufi cikin gidan, tana shiga sallama tayi tana k'iran
Haleema kamar yadda takeyi idan suka zo gurin da zasu had'u. Haleema dake zaune a
falo tajiyo INdo na nemanta da sauri ta mik'e ta shige d'akin su dan bata son su
had'u a cikin wannan yanayin. Mata tagani a zaune a falo wasu sunzo wasu kuma na
shigowa Mama a gefe gurin kujera ta takure Umma kuma a bakin k'ofa INdo ta dinga
binsu da kallo kafin ta k'arasa kusa da Fateeman Sadeeq ta zauna itama ta takure
tana gaida su, suka amsa mata a sanyaye. Juyawa tayi tana lek'an fuskar Fateema
wadda take faman hawaye a dai-dai fuskar tata tace.

"Kai amaryar malam menene kike kuka? Ko malam Sadeeq ne,dan nasan shi sarai tun a
makarantar mu meh yayi miki..?!"

Zame jikinta tayi daga na INdo ta juya tana kallon Mama sai taga itama ta d'auke
kai Fateema ta rasa yadda zatayi gashi INdon ta takura mata akan sanjin abinda
takewa kuka,mutane dake shigowa ne ya k'ara sanya INdo cikin wasi-wasi kuma da sun
shigo zasu samu guri su zauna a cigaba da zaman shiru sai kuma kallonta da ake yi.
Mama ce tayi k'arfin halin yin magana tana kallon su fateema tace.

"Fateema jata kushiga cikin d'aki mana."

Hakan akayi kuwa suka shiga ciki nan INdo taga Haleema a mak'ure jikin gado sai
shashekar kuka takeyi, cikin sauri ta k'arasa wajanta dayake Allah ya had'a jininsu
da ita ta janyo ta da sauri cike da damuwa da nuna kulawa tace.

"Haleema Hali dubu kyakyawa, me kikema kuka kema?!"


Rungumeta Haleema tayi yayin da INdo tayi shiru tana rik'e da ita, ita INdo ba
komai yake sanyata saurin kuka ba har sai abin yakai mak'ura sannan batada tsoro
musamman a fagen magana kafin Haleema tayi magana Mama tashigo d'akin Fateema na
zaune fuskarta cikin hijjab Mama ta rik'o INdo ita kuma jinta ajikin Mama yasa tayi
murmushi sai taji tamkar Abubukar d'inne ya rik'ota.

A bak'in gado ta zaunar da ita can suka jiyo muryar Wata tsohowa mak'ociyar su
ta shigo tana fad'in.

"Allahu akubar Garbati ankai sa'i, d'azu-d'azun nan yana fitowa daga gidannan ya
lek'a zaurena muka gaisa yace min zai tafi birnin taraiya, Allah sarki kungani ya
bani yaci inci goro Allah yajik'anka Garba.."

Ta k'arasa maganar tana nuna musu naira d'ari biyar d'in daya bata, a cikin d'aki
INdo ta kalli Mama tana zaro ido tace.

"Mama waye Garba a gidannan da ya mutu?!"

Cikin dakiya Mama ta k'arasa wajan wardrobe tana cewa.

"Anan gidan yake Aisha zakiji ko waye."

Farin hijjab ta zaro tare da mik'awa INdo shi tana cewa.

"Ciro mayafin Aisha a ajiye shi."

Kamar yadda Mama tace haka tayi tasanya hijjab d'in Mama zumbulele sannan Mama tace
ta zauna karta fito. Suna zaune zugum sai ta d'akko wayarta number'n sa ta k'ira
cikin sa'a aka d'auka cikin zumud'inta tace mai.

"Salama alaikum my key kaje ko kakusa zuwa..?!"

Taji ance "Sorry hajiya me wayar yanzu haka Allah yayi mai rasuwa."

Da mamaki tace "Rasuwa kuma? Toma waikai waye ma tukunna?!

Kashewa akayi INdo ta zaro ido tana kallon wayar tare da furta.

"Rainin hankali toh ko fad'uwa wayar tayi wani ya sace shine zaice min haka.
Aniyarka ta bika mugu 6arawo."

Ta fad'a su kuma Haleema dasu Fateema da wasu da suka shigo d'akin suka bita da
kallo. Hawwa ce ta shigo tana kuka sosai saida tazo falo ta kuma 6arkewa da wani
kukan tana shashek'a tace.

"Allah sarki Yaya Habu yanzu ya gama min waya Mama kinga kiran da yayi min yace
gobe insa aje a d'akko min Humairansa... Tazo muyi hira da daddare a maida ita baya
son ta zauna it...."

Ta kasa k'arasawa sai kuka, INdo ce ta fito fululum cikin hijjab jin muryarta ta
k'arasa kusa da Hawwa ai Hawwa na ganinta ta janyota jikinta kukan ya tsananta amma
bakin be fasa magana ba.

"Aunty Humairah kinyi rashi Allah yajik'an Yaya Habu yaso kuyi long life a tare sai
gashi Allah ya d'aukesa ya barki...."

Muryar Mama ce ta katsewa Hawwa kukan da takeyi cikin fad'a tace.


"Amma dai ban ta6a sanin bakida hankali ba sai yau Hawwa, wannane wane irin hauka
ne daga shigowarki sai kace ba gidan musulmai kika shigo ba. Toh kin gaya mata
kinji dad'i tun zuwanta kowa ya kasa gaya mata saike wawuya kawai..."

Da sauri Hawwa ta kalli INdo sai taga ta kura mata ido fuskarta a murtuk'e tun daga
nan kuma sai bakin mutane ya fara bud'ewa aka fara zance mutuwar kunnuwan INdo suka
dinga jiyo mata ai yana tafiya har ya wuce Kaduna Allah yayi masa rasuwa.

Sosai hankalin Hawwa ya tashi ganin yadda INdo ta kafeta da ido hakan ya bata
tsoro tayi saurin matsawa baya INdo ta bita cikin tashin hankali Hawwa tace.

"Aunty Humairah Lafiya? Please wannan kallon fa..?!"

A hankali INdo tasa hannu ta rungume Hawwa cikin rawar murya tace.

"Yaya Hawwa kema sokike Yaya Abubakar ya mutu? Yanzu na buga mai waya wani ya
d'auka yace min me wayar ya mutu ashe kema sokike ya mutu? 'Dazu ni narakasu mota
suka shiga shida malam Sadeeq amma meyasa kike son yayanki ya mutu? Kinga yana sona
dayawa d'azu fa har cemin yayi yana son duk wani mesona kuma zai sani a makarantar
abuja..."

"Kiyi hak'uri aunty Humairah nima inason Yaya Habu amma Allah yafimu sonshi shi
yasa yayi hatsari..."

Hawwa ta fad'a tana kuma sakin kuka, da sauri INdo ta hankad'a Hawwa baya iya
k'arfinta jikake gam..! ta bugu da kujera cikin kukan bak'in cikin maganarta yasa
INdo cewa.

"Daga yin bikin mu shine zaki mana addu'ar ya mutu sabida bakya sonmu, toh insha
Allahu sai Isyaku ya riga dacta mijina mutuwa fatanki ya biki, ance miki Garba ne
ya mutu shine zaki zo kice Yaya Abubakar ne dan bak'in ciki..."

Umma ce tayi saurin toshewa INdo baki cikin rufewar ido ta fara tureta domin ta
baya ta rik'ota ta kuma toshe mata. Cikin kwantar da murya Umma kishiyar Maman su
Sadeeq take mata magana a hankali.

"Kinga Aisha kiyi shiru kinga mutane sun fara cika gidan yi hak'uri taho muje ki
zauna kinji 'yar albarka."

Tana nishi Umma taja ta still bata dena yiwa Hawwa kallon banza ba duk kuwa da
cewar ta girmeta nesa ba kusa ba amma cewar Abubakar d'inta ya mutu shine ya d'arsa
wata k'azamar kiyayya a zuciyar INdo.

Fateema ce ta fito idanunta jawur ta kama hannunta suka koma cikin d'akin Mama,
suna zama amma sai mita INdo takeyi Mama ta shigo ta kalleta tare da cewa.

"Aisha kidinga hakuri kinji ko?"

INdo tace "Toh Mama ki gaya mata bana son wasan mutuwa."

"Toh zan gaya mata tashi muje ki wanke fuskarki da sabulu."

Babu musu ta mik'e suka shiga bathroom saida ta gama wankewa sannan Mama ta kamo
hannunta suka wuce, d'akin Abba suka shiga yana zaune yayi shiru yana bud'e
likkafani gefe turare ne a kusa dashi suka shiga bayan Mama tayi sallama. Sake
gaisawa suka yi da INdo sannan Abba ya kalleta tsawon lokaci ya kasa cewa komai,
can dai ya nisa yace.

"Aisha ke musulmace ko?!"


'Dan murmushi tayi alamar kunya tana sunkuyar dakai tace,

"Eh Abba."

"Alhamdulillahi ina son sanar dake Abubakar dai Allah ne ya bani shi, nina raineshi
tundaga zanin goyo har girmansa da temakwon Allah, bayan ya girma ya mallaki
hankalinsa shida d'an uwansa suka d'auke min duk wani nauyi nasu dana k'annansu,
kafin ya aureki ya nemi auran wata yarinya Allah ya k'adarta beyi ba sai dake, toh
Allahn daya baki Abubakar Aisha ya k'ar6i abinsa domin yanzu haka suna hanya za'a
kawo gawarsa ina son ki daur...."

Bek'arasa ba yaji ta fashe da kuka, kusa dashi ta rarrafo tare da rik'o Hannunsa
tana jijigawa tana fad'in.

"Abba... Abba wallahi ba dacta bane, ba shine ya mutu ba shi yatafi abuja k'ila dai
malam Sadeeq ne, dan Allah Abba karku ce haka wallahi yace zai dawo ya tafi dani
can garan..."

Mama Abba ya kalla alamar tazo ta zanye ta, tana zuwa INdo ta juya kanta tare da
rik'o hannunta itama tana cigaba da magana tana basu rabarin abinda yace zai yi
mata nan gaba sai kawai itama Maman ta fashe da kuka Abba ya fara mata fad'a amma
ina ta kasa yin shiru bare ta bawa INdon.

"Kutashi kuje yanzu suna hanya zasu kawo shi, karku sake kubarta tafita ko'ina
kinajina...?"

Mama ta kad'a kai tare dajan hannun INdo suka shiga gidan sai ihu take mutane na
kallonta cikin tsananin tausayawa.

Tana shiga ciki ta zu6e ak'asa jikinta sai rawa yakeyi aka rufa a kanta kowa sai
nemar mata d'auki yake ta zame jikinta daga na wata mata tana kallon Matan tace.

"Sani zantafi."

Umma ta rik'ota itada Fateema ta fara tirje musu dama INdo yaya lafiyar kura, dacta
ne yasanta ya kuma san yadda zai biyo mata gashi babushi dan haka abin nata ya kuma
yawa.

Kullesu akayi a d'aki babu me fitowa suna jiyo kukanta har aka dawo daga d'akko
gawar Abubakar, d'akinsu aka kaishi Sadeeq tamkar wani zararre fuskarsa fal hawaye
idanunsa sunyi luhu-luhu tamkar kurji ya fito ya shiga cikin gida yana neman Mama.
Da kyar ya iya tambayarta zani ta mik'e ta bud'e d'akin, suka shiga.

Gaidashi mutanan d'akin suke suna mai gaisuwa, yana furta "Alhamdulillah." INdo
tayi zumbar ta mik'e daga ruk'on da Zulaihat tayi mata, lokacin Mama ta mik'a mai
zannin ya k'a6a kawai yaji INdo ta mak'aleshi katak'am tamkar ba rik'on mace ba
tana kuka tana cewa.

"Dacta ka dawoko? Nasan dama bazaka barni ba dan Allah da manzansa kace min Malam
Sadeeq ne ya mutu ba kaiba, wallahi kaga zanyi kwalliyar da kace irinta d'azu, mu
koma gidanmu nan kana da mak'iya ciki harda Abba duk fatan mutuwa suke ma..."

"Aisha sakar ni please."

Sadeeq ya fad'a yana 6an6areta daga jikinsa amma tamkar mutum biyu ne suka rik'esa,
ya rasa dalilin dayasa takeja masa mugayan alkaba'i tun suna makaranta nan fa su
Mama suka k'arasa suna nuna mata bashi bane amma tak'i sakinsa cewa take.
"Duk inda zahi zan bihi wata k'ila akwai masu bibiyarsa basa sonshi toni ina
sonsa."

Janta yayi ganin ta mak'ale suka k'arasa bakin gado ya zaune tare da nunawa Fateema
alamar tazo ta zauna kusa dashi. Tana zuwa INdo ta kare shi alamar karta ta6ashi
Fateema ta toshe baki kuka na shirin kwace mata, haskilowa kawai takeyi tasan da
shi ya rasu k'ila da tuni itace a cikin wannan yanayin da INdo take ciki.

Kabeer ne ya shigo ya kar6i zanin domin sam INdo tak'i sakin Sadeeq, Mama kuwa so
take ta 6an6areta domin tasan hankan ba dacewa bane kuma INdo tashiga cikin takaba
hakan yasa ta fara sanya ta cikin dokokin da musulinci ya tanadarwa ga duk macen da
mijinta ya rasu...

*HAJJA CE*👈

[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*


♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

*MUSAYAR ZUCIYA:- Hak'ik'a banyi zato ko tsammanin makaranta labarin nan sunkai
yawan haka ba sai da akazo page 21, a hak'ik'anin gaskiya naji matuk'ar tsoro na
razana da ganin millions of people's da suk'e matuk'ar son Dr Abubakar da Aishatul
humaira a ranar da waya nata tarwatsewa toh da tuni an wuce babin wayata,
everywhere MUSAYAR ZUCIYA Hajja karki kashe Dr becan-canci haka ba, idan kikai
hakan kin sakamu cikin tashin hankali INdo kuma baki kyauta mata ba. Karku manta
Allah babu ruwansa da lokacin da zaka farajin dad'in rayuwa ya d'aukeka, anytime
kowane irin yanayi kake ciki idan lokacinka yayi dole ka barshi katafi ba tare da
kashiryawa hakan ba. A yanzu haka nasan wad'anda suka tanadi likaffani na mutuwarsu
sabida suna ganin sun tsufa rayuwa ta k'are musu amma har yanzu basu mutuba sai
'ya'yansu da jikok'insu wad'anda ba'a saka musu ran mutuwa sune suke mutuwa. Dan
Allah badan niba kuyi hakuri ku d'auka a cewar kuma akanku hakan zata iya faruwa
sannan kuma kowacce zata yiwa Abubakar addu'ar Allah ya sadashi da rahamarsa.
Labarin gaske ne domin da Ummi Aisha itace zata yishi so bansan Stylish Bch ta bata
labarin ba sai jiya. Kuyi hakuri harda masu cewa sundena karantawa sabida sunsan
karshe dai Sadeeq zata aura suzo suna kishi da fateema🤭toh duk kuyi hakuri kuma
sannan ku yafewa 'yar uwarku, da ace tun farko bansa muku true life ba wallahi
akwai yadda zanyi na sauya salon amma yanzu kona sauya toh araina zan dingajin abun
tunda nasan ba haka yake ba, duk wanda na 6atawa tundaga kan fara novel din har
zuwa wannan pagen kuyi hakuri ku yafewa Hajja ce👈 'yar Adam ce kamar ku sannan kuma
meyin kuskure a duk inda ta samu kanta, wallahi dana dinga ganin comments d'inku
dakyar nayi bacci zuciyata na rawa Ina ganin ban kyauta muku ba ciki rayuwarku.
Nasan da yawanku zaku dena karantawa toh Ina fatan duk wanda ya tsaya iya nan ya
d'auki wani darasi a ciki amma Zan samu na k'arasa shi a WATTPAD dan nima na samu
nutsuwar Zuciya. Nagode gaduk wanda suka karanta farkon labarin Allah ya sadamu da
rahamarsa a cikin kabarinmu Amin Love you all m fan's❤🤝❤*

Page *22*

Hark'asa INdo ta tsugunna tana gaida shi idanta akan fuskarsa tace,

"Abba ina wuni?"

Ya zura wayar cikin aljihunsa yana kallonta ya amsa.

"Lafiya lau Aisha tashi kishiga daga ciki."

"Toh adawo lafiya."

Tafad'a tana mik'ewa ta nufi cikin gidan, tana shiga sallama tayi tana k'iran
Haleema kamar yadda takeyi idan suka zo gurin da zasu had'u. Haleema dake zaune a
falo tajiyo INdo na nemanta da sauri ta mik'e ta shige d'akin su dan bata son su
had'u a cikin wannan yanayin. Mata tagani a zaune a falo wasu sunzo wasu kuma na
shigowa Mama a gefe gurin kujera ta takure Umma kuma a bakin k'ofa INdo ta dinga
binsu da kallo kafin ta k'arasa kusa da Fateeman Sadeeq ta zauna itama ta takure
tana gaida su, suka amsa mata a sanyaye. Juyawa tayi tana lek'an fuskar Fateema
wadda take faman hawaye a dai-dai fuskar tata tace.

"Kai amaryar malam menene kike kuka? Ko malam Sadeeq ne,dan nasan shi sarai tun a
makarantar mu meh yayi miki..?!"

Zame jikinta tayi daga na INdo ta juya tana kallon Mama sai taga itama ta d'auke
kai Fateema ta rasa yadda zatayi gashi INdon ta takura mata akan sanjin abinda
takewa kuka,mutane dake shigowa ne ya k'ara sanya INdo cikin wasi-wasi kuma da sun
shigo zasu samu guri su zauna a cigaba da zaman shiru sai kuma kallonta da ake yi.
Mama ce tayi k'arfin halin yin magana tana kallon su fateema tace.

"Fateema jata kushiga cikin d'aki mana."

Hakan akayi kuwa suka shiga ciki nan INdo taga Haleema a mak'ure jikin gado sai
shashekar kuka takeyi, cikin sauri ta k'arasa wajanta dayake Allah ya had'a jininsu
da ita ta janyo ta da sauri cike da damuwa da nuna kulawa tace.

"Haleema Hali dubu kyakyawa, me kikema kuka kema?!"

Rungumeta Haleema tayi yayin da INdo tayi shiru tana rik'e da ita, ita INdo ba
komai yake sanyata saurin kuka ba har sai abin yakai mak'ura sannan batada tsoro
musamman a fagen magana kafin Haleema tayi magana Mama tashigo d'akin Fateema na
zaune fuskarta cikin hijjab Mama ta rik'o INdo ita kuma jinta ajikin Mama yasa tayi
murmushi sai taji tamkar Abubukar d'inne ya rik'ota.

A bak'in gado ta zaunar da ita can suka jiyo muryar Wata tsohowa mak'ociyar su
ta shigo tana fad'in.

"Allahu akubar Garbati ankai sa'i, d'azu-d'azun nan yana fitowa daga gidannan ya
lek'a zaurena muka gaisa yace min zai tafi birnin taraiya, Allah sarki kungani ya
bani yaci inci goro Allah yajik'anka Garba.."
Ta k'arasa maganar tana nuna musu naira d'ari biyar d'in daya bata, a cikin d'aki
INdo ta kalli Mama tana zaro ido tace.

"Mama waye Garba a gidannan da ya mutu?!"

Cikin dakiya Mama ta k'arasa wajan wardrobe tana cewa.

"Anan gidan yake Aisha zakiji ko waye."

Farin hijjab ta zaro tare da mik'awa INdo shi tana cewa.

"Ciro mayafin Aisha a ajiye shi."

Kamar yadda Mama tace haka tayi tasanya hijjab d'in Mama zumbulele sannan Mama tace
ta zauna karta fito. Suna zaune zugum sai ta d'akko wayarta number'n sa ta k'ira
cikin sa'a aka d'auka cikin zumud'inta tace mai.

"Salama alaikum my key kaje ko kakusa zuwa..?!"

Taji ance "Sorry hajiya me wayar yanzu haka Allah yayi mai rasuwa."

Da mamaki tace "Rasuwa kuma? Toma waikai waye ma tukunna?!

Kashewa akayi INdo ta zaro ido tana kallon wayar tare da furta.

"Rainin hankali toh ko fad'uwa wayar tayi wani ya sace shine zaice min haka.
Aniyarka ta bika mugu 6arawo."

Ta fad'a su kuma Haleema dasu Fateema da wasu da suka shigo d'akin suka bita da
kallo. Hawwa ce ta shigo tana kuka sosai saida tazo falo ta kuma 6arkewa da wani
kukan tana shashek'a tace.

"Allah sarki Yaya Habu yanzu ya gama min waya Mama kinga kiran da yayi min yace
gobe insa aje a d'akko min Humairansa... Tazo muyi hira da daddare a maida ita baya
son ta zauna it...."

Ta kasa k'arasawa sai kuka, INdo ce ta fito fululum cikin hijjab jin muryarta ta
k'arasa kusa da Hawwa ai Hawwa na ganinta ta janyota jikinta kukan ya tsananta amma
bakin be fasa magana ba.

"Aunty Humairah kinyi rashi Allah yajik'an Yaya Habu yaso kuyi long life a tare sai
gashi Allah ya d'aukesa ya barki...."

Muryar Mama ce ta katsewa Hawwa kukan da takeyi cikin fad'a tace.

"Amma dai ban ta6a sanin bakida hankali ba sai yau Hawwa, wannane wane irin hauka
ne daga shigowarki sai kace ba gidan musulmai kika shigo ba. Toh kin gaya mata
kinji dad'i tun zuwanta kowa ya kasa gaya mata saike wawuya kawai..."

Da sauri Hawwa ta kalli INdo sai taga ta kura mata ido fuskarta a murtuk'e tun daga
nan kuma sai bakin mutane ya fara bud'ewa aka fara zance mutuwar kunnuwan INdo suka
dinga jiyo mata ai yana tafiya har ya wuce Kaduna Allah yayi masa rasuwa.

Sosai hankalin Hawwa ya tashi ganin yadda INdo ta kafeta da ido hakan ya bata
tsoro tayi saurin matsawa baya INdo ta bita cikin tashin hankali Hawwa tace.

"Aunty Humairah Lafiya? Please wannan kallon fa..?!"


A hankali INdo tasa hannu ta rungume Hawwa cikin rawar murya tace.

"Yaya Hawwa kema sokike Yaya Abubakar ya mutu? Yanzu na buga mai waya wani ya
d'auka yace min me wayar ya mutu ashe kema sokike ya mutu? 'Dazu ni narakasu mota
suka shiga shida malam Sadeeq amma meyasa kike son yayanki ya mutu? Kinga yana sona
dayawa d'azu fa har cemin yayi yana son duk wani mesona kuma zai sani a makarantar
abuja..."

"Kiyi hak'uri aunty Humairah nima inason Yaya Habu amma Allah yafimu sonshi shi
yasa yayi hatsari..."

Hawwa ta fad'a tana kuma sakin kuka, da sauri INdo ta hankad'a Hawwa baya iya
k'arfinta jikake gam..! ta bugu da kujera cikin kukan bak'in cikin maganarta yasa
INdo cewa.

"Daga yin bikin mu shine zaki mana addu'ar ya mutu sabida bakya sonmu, toh insha
Allahu sai Isyaku ya riga dacta mijina mutuwa fatanki ya biki, ance miki Garba ne
ya mutu shine zaki zo kice Yaya Abubakar ne dan bak'in ciki..."

Umma ce tayi saurin toshewa INdo baki cikin rufewar ido ta fara tureta domin ta
baya ta rik'ota ta kuma toshe mata. Cikin kwantar da murya Umma kishiyar Maman su
Sadeeq take mata magana a hankali.

"Kinga Aisha kiyi shiru kinga mutane sun fara cika gidan yi hak'uri taho muje ki
zauna kinji 'yar albarka."

Tana nishi Umma taja ta still bata dena yiwa Hawwa kallon banza ba duk kuwa da
cewar ta girmeta nesa ba kusa ba amma cewar Abubakar d'inta ya mutu shine ya d'arsa
wata k'azamar kiyayya a zuciyar INdo.

Fateema ce ta fito idanunta jawur ta kama hannunta suka koma cikin d'akin Mama,
suna zama amma sai mita INdo takeyi Mama ta shigo ta kalleta tare da cewa.

"Aisha kidinga hakuri kinji ko?"

INdo tace "Toh Mama ki gaya mata bana son wasan mutuwa."

"Toh zan gaya mata tashi muje ki wanke fuskarki da sabulu."

Babu musu ta mik'e suka shiga bathroom saida ta gama wankewa sannan Mama ta kamo
hannunta suka wuce, d'akin Abba suka shiga yana zaune yayi shiru yana bud'e
likkafani gefe turare ne a kusa dashi suka shiga bayan Mama tayi sallama. Sake
gaisawa suka yi da INdo sannan Abba ya kalleta tsawon lokaci ya kasa cewa komai,
can dai ya nisa yace.

"Aisha ke musulmace ko?!"

'Dan murmushi tayi alamar kunya tana sunkuyar dakai tace,

"Eh Abba."

"Alhamdulillahi ina son sanar dake Abubakar dai Allah ne ya bani shi, nina raineshi
tundaga zanin goyo har girmansa da temakwon Allah, bayan ya girma ya mallaki
hankalinsa shida d'an uwansa suka d'auke min duk wani nauyi nasu dana k'annansu,
kafin ya aureki ya nemi auran wata yarinya Allah ya k'adarta beyi ba sai dake, toh
Allahn daya baki Abubakar Aisha ya k'ar6i abinsa domin yanzu haka suna hanya za'a
kawo gawarsa ina son ki daur...."

Bek'arasa ba yaji ta fashe da kuka, kusa dashi ta rarrafo tare da rik'o Hannunsa
tana jijigawa tana fad'in.

"Abba... Abba wallahi ba dacta bane, ba shine ya mutu ba shi yatafi abuja k'ila dai
malam Sadeeq ne, dan Allah Abba karku ce haka wallahi yace zai dawo ya tafi dani
can garan..."

Mama Abba ya kalla alamar tazo ta zanye ta, tana zuwa INdo ta juya kanta tare da
rik'o hannunta itama tana cigaba da magana tana basu rabarin abinda yace zai yi
mata nan gaba sai kawai itama Maman ta fashe da kuka Abba ya fara mata fad'a amma
ina ta kasa yin shiru bare ta bawa INdon.

"Kutashi kuje yanzu suna hanya zasu kawo shi, karku sake kubarta tafita ko'ina
kinajina...?"

Mama ta kad'a kai tare dajan hannun INdo suka shiga gidan sai ihu take mutane na
kallonta cikin tsananin tausayawa.

Tana shiga ciki ta zu6e ak'asa jikinta sai rawa yakeyi aka rufa a kanta kowa sai
nemar mata d'auki yake ta zame jikinta daga na wata mata tana kallon Matan tace.

"Sani zantafi."

Umma ta rik'ota itada Fateema ta fara tirje musu dama INdo yaya lafiyar kura, dacta
ne yasanta ya kuma san yadda zai biyo mata gashi babushi dan haka abin nata ya kuma
yawa.

Kullesu akayi a d'aki babu me fitowa suna jiyo kukanta har aka dawo daga d'akko
gawar Abubakar, d'akinsu aka kaishi Sadeeq tamkar wani zararre fuskarsa fal hawaye
idanunsa sunyi luhu-luhu tamkar kurji ya fito ya shiga cikin gida yana neman Mama.
Da kyar ya iya tambayarta zani ta mik'e ta bud'e d'akin, suka shiga.

Gaidashi mutanan d'akin suke suna mai gaisuwa, yana furta "Alhamdulillah." INdo
tayi zumbar ta mik'e daga ruk'on da Zulaihat tayi mata, lokacin Mama ta mik'a mai
zannin ya k'a6a kawai yaji INdo ta mak'aleshi katak'am tamkar ba rik'on mace ba
tana kuka tana cewa.

"Dacta ka dawoko? Nasan dama bazaka barni ba dan Allah da manzansa kace min Malam
Sadeeq ne ya mutu ba kaiba, wallahi kaga zanyi kwalliyar da kace irinta d'azu, mu
koma gidanmu nan kana da mak'iya ciki harda Abba duk fatan mutuwa suke ma..."

"Aisha sakar ni please."

Sadeeq ya fad'a yana 6an6areta daga jikinsa amma tamkar mutum biyu ne suka rik'esa,
ya rasa dalilin dayasa takeja masa mugayan alkaba'i tun suna makaranta nan fa su
Mama suka k'arasa suna nuna mata bashi bane amma tak'i sakinsa cewa take.

"Duk inda zahi zan bihi wata k'ila akwai masu bibiyarsa basa sonshi toni ina
sonsa."

Janta yayi ganin ta mak'ale suka k'arasa bakin gado ya zaune tare da nunawa Fateema
alamar tazo ta zauna kusa dashi. Tana zuwa INdo ta kare shi alamar karta ta6ashi
Fateema ta toshe baki kuka na shirin kwace mata, haskilowa kawai takeyi tasan da
shi ya rasu k'ila da tuni itace a cikin wannan yanayin da INdo take ciki.

Kabeer ne ya shigo ya kar6i zanin domin sam INdo tak'i sakin Sadeeq, Mama kuwa so
take ta 6an6areta domin tasan hankan ba dacewa bane kuma INdo tashiga cikin takaba
hakan yasa ta fara sanya ta cikin dokokin da musulinci ya tanadarwa ga duk macen da
mijinta ya rasu...
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *24*

Koda sukaje kauyan Sani bak'aramin mamaki Fateema tayi ba da ganin gidan su INdo
da kuma kauyan da suke, lallai Allah ya d'aukakata daya aura mata Abubakar har kuma
tashiga wannan uban gidan wanda yafi nata komai da komai. Basu jima ba Sadeeq yace
zasu koma ya bada dubu ashirin Inna da malam Hamza suka dinga yi mai godiya amma
INdo fateema kawai tayiwa sallama ta koma gida 'yan garin suka cigaba da zuwar musu
gaisuwa.

Rayuwa gaba d'aya ta sauyawa INdo komai yayi zafi tunda ta dawo kauyan Sani komai
nata ya canza, tana takaba a gidan su kamar yadda malam Hamza ya buk'ata sai dai
itace inzata bayan gida sai abata sanda da wuk'a wai ta tafi da ita ko idan zatayi
bacci toh ruwanta a buta da wuka wai mijinta yana biye da ita duk da cewar ba'a
gidansa takeba. Sannan ta dinga tafiya a hankali karya tad'iyeta. wayace haka ake
zaman takaba?wannan ba musulinci ya koyar dashi ba kawai mutanene suka maidashi
al'ada har hakan ya fara zama kamar ibada. Satin INdo biyu a gida lokacin sati uku
kenan da rasuwar Abubakar su Mama sukaje garin domin ita sam hankalinta ya kasa
kwanciya, a zaure suka tarar dasu INdo suna tsinkar zogale harta fara komawa
kalarta ta dah gashi dai jikinta da kaya masu kyau amma babu tsafta tunda ta dawo
sau biyu tayi wanka wai ai duk cikin takaba ne. su Hawwah suka dinga kallonta cikin
tsananin mamaki ita kuwa ta kasa 6oye farin cikinta da ganinsu.

Bayan sun gaggaisa ne Mama ta kasa yin shiru ta kalli INdo dake tsakiyarsu Haleema
tace.

"Aisha ya naganki haka?duk kinyi wani iri anya kina wanka da kula da lafiyar jikin
ki?!"

Cikin rashin damuwa tare INdo tace.

"Ai Mama nida nake takaba ai ance ba'a wanka sai dai a sati sau d'aya shi yasa ma
banayi..."

"Subahanallahi inji waye ya gaya miki haka?"


INdo tace "Su Inna ne."

Inna nacan tana k'ok'arin had'a dambu ta samu tabasu suci Mama tace.

"Zonan Aisha na shiga uku ba haka ake yi ba a musulunci, ba haka qur'ani ya gaya
mana ba."

Tashi INdo tayi zuwa kusa da Mama ta zauna Mama na kallonta cikin tsananin
tausayawa ta janyo ta jikinta tace.

"Mecece Takaba Aisha?!"

INdo tayi shiru sai faman wulk'ita idanuwa takeyi Mama tace.

"Aisha Takaba dai itace Zaman da mace zatayi bayan rasuwar megidanta na wad'ansu
kwanaki sanannu a cikin gidanta batare da tayi ado da kwalliya ba, ba kuma data
kuma yin wani auren ba, ko sanya dukkan abinda zai ja hankalin wani a jikinta ba na
tufafi ko kayan k'arau. Aanan Takaba ta sha babban da Iddar saki, shi yasa naso a
barki a can domin d'an zaman da kikayi a gidan mu na gano cewar kinada gyara a
cikin rayuwarki. Banda iyayanki sun kafe kancewar gara kitafi babu me zuwa ya zauna
dake a cikin gidanki sannan kowa yasan mijinki ya rasu gashi idan kikaga Sadeeq
wani tashin hankalin ne da bazan bari ba wallahi yanzu gashi kinzo nan sun k'ara
dilmiyar dake cikin wani duhun kan.

Wallahi mahaifinki gaddama garesa Aisha ba yadda ba'ayi dashi ya barki ba yace
dasun dawo bakwai za'a tafi dake sabida baya son abinda kikewa Sadeeq. Shin kinsan
Gwargwadon kwanakin Takaba a musulunci Aisha?"

INdo ta girgiza kai alamar a'a Mama ta d'ago ta daga jikinta tace.

"Alokacin da mutun ya rasu, to zai bar iyalin shi ne a d'ayan hali guda biyu, kodai
ta zama tanada Juna biyu ko kuma bata da shi. Idan bata da juna biyu to Takabarta
itace tayi Wata hud'u da kwanaki goma Kamar yadda Allah yace cikin Suratul-Bak'ara
_Kumma dukkanin mazan dake rasuwa daga cikin ku subar matayan su, to matan zasu
zauna wata hud'u da kwana goma aya ta d'ari biyu da talatin da hud'u 234..._

To amma idan ya rasu ya barta da juna biyu a wannan lokacin k'arshen Takabarta
shine ta sauk'e abinda take dauk'e da shi koda kuwa ranar da ya rasu ne ma'ana ta
haihu ko tayi 6arin cikin. Misali ya rasu 10:00am na safe ita kuma ta haihu 10:05
na safiyar, shi k'enan ta kammala takabarta, idan wani ya gani yace yana so aka
d'aura aure 2:30 na ranar aure ya d'auru _(ana k'ar6ar gaisuwa ana d'aurin aure)_
Dalili kuwa shi ne. fad'in Allah (s.w. a) a cikin Suratut-Talak aya ta 4 _Kuma
dukkanin mata masu juna biyu to lokacinsu shine su sauk'e abinda suke d'auk'e
dashi_ da kuma Hadisin Subai'a Al-aslamiyyah, Ita ta kasance tana auran Sa'ad Dan
Khaulah, shi kuma ya fito ne daga gidan Amir d'an Lu'ayy, yana daga cikin wad'an da
suka halarci yak'in Badar, sai ya rasu yabarta a halin bankwana tana da juna biyu,
bata ko jima ba bayan rasuwar shi saita haihu, a lokacin data kamma biki sai tai
kwalliya, sai Abu-Sanabil Dan Ba'akk yazo wurinta, shi kuma ya fitone daga gidan
Abduddar, sai yace da ita Lafiya naga kin cancara ado haka, ko kina son ki aure ne?
Na rantse da Allah lokacin auranki bai yi ba, harsai kin yi wata hud'u da kwana
goma. Sai Subai'a tace Yayinda ya fad'a min haka maraice na yi sai na tattara
kayana naje wurin Ma'aikin Allah tsira da amincin Allah su tabbata a gareshi, na
tambaye shi hakan, sai ya ban amsa da cewa ai na kamala Takabata tun lokacin dana
haihu, ya ban dama da inyi aure a duk lokacin da naga dama. Yanzu ke Aisha kina da
ciki?!"

INdo ta kalli Yayya Hawwah kafin ta maida idonta kan Mama tace "Wallahi ban sani ba
nima." Mama ta sake kallonta sannan tace.
"Kinyi al'ada sanda kika dawo?!"

INdo ta sunkuyar da kai sannan tace,

"Ai yanzu ma haka inayi yau kwanana biyu kenan."

"Hazbunallahu wani'imal wak'il, yanzu duk da kina wannan jinin Aisha bakya wanka?!"

INdo tayi shiru jin yadda Mama tayi magana da alama abin mamaki ya bata da haushi
ita kuma ya zatayi tunda ance mata haka akeyi. Inna ce ta shigo tana tayi musu
sanna tare da kawo musu ruwa a kwanan shin ruwan malam Hamza, tsabtar kyawun kwanon
da yadda ruwan ciki yake garai-garai abin sha'awa shine ya sanya su Haleema shan
ruwan gidan.

Zama Inna tayi suka sake gaisawa Mama tayi gyaran murya bayan tace su Haleema su
fita, suna fita tayi murmshi tare da cewa.

"Dama munzo ne mu gaida ku sannan zamu tafi da Aisha za'ayi mata wani gwajin ciki
sabida shi marigayi yace yasa mata wani abu wanda koda tana da ciki toh bazata dena
jinin al'adaba toh yanzu shine zamuje a duba agani kar abar mata abu ba'a saniba ko
yana amfani nan da kwana biyu za'a dawo da ita kinsan likitocin nan da k'ak'ale."

Mama ta kifa Inna domin yanzu so take ta tafi da INdo can. cikin rashin damuwa Inna
tace "Allah sarki ai babu komai an zama d'aya bari na aika a k'ira malam dama shine
ai ke hanawa da yaji yadda takeyi idan taga shi d'an uwan marigayin."

Fitowa tayi ta lek'a waje ta samu yaro yaje ya k'ira Malam Hamza a gurin sana'ar
Sa. Tare da ila suka dawo tunda yaga mota yasan bak'i sukayi yana shiga kuwa Inna
tace Maman marigayi ce tazo, d'akin ya shiga suka gaisa da Mama Inna kuma ta kawo
mata dambu ta kaiwa su INdo ma. A nan Mama ta kuma tsara malam Hamza yayi jim
sannan kamar bazai yadda ba sai kuma yayi murmushi yace.

"Toh ai dama ni hajiya dalilin daya sa na kafe kan cewar saita dawo nan, gani nayi
yadda shi Saddiqu suke tsananin kama dashi marigayin. Sannan tun a gurin gaisuwar
naji ana zance ta fara rik'esa tana cewa be mutu ba harma sun fara samun sa6ani
itada Saddiqun wannan dalilin yasa nace dole abani ita mu dawo nan zaman lafiya
hajiya ai yafi zama d'an sarki. Amma yanzu tunda akwai wani dalili wanda kuma kune
kuke da hakk'i akai toh saita shirya ku tafi idan an kammala yi mata sai a dawo da
ita ai duk an zama guda.."

Wani farin ciki ya lullu6e Mama sai ta share hawaye gani takeyi tamkar Abubakar
d'in take yiwa a zahiri. Malam Hamza ya dinga bata hak'uri kafin ya tashi ya fita,
gurin su INdo yaje yace ta shirya zasu tafi da ita.

Wanka Mama tace tayi sannan tayi tasa kaya Mama ta girgiza kai domin duk kayan na
kwalliya ne babu wanda aka ce na takaba ne dole idan sunje tasa a dinka mata wasu
marasa style. Babu wanda yasani don Mama tace kar a fad'awa kowa kawai idan an
tambaya tana Ina suce tana gidan su marigayi amma karsu sanar da kowa akwai abinda
za'ayiwa INdo suka tafi cikin farin ciki da fatan alkairi.

*****
Tunda suka maida ita Mama ta dakatar da Sadeeq zuwa gidan tace koda itace batada
lafiya bata yadda ya shigo ba bare hakan nan. Haka kuka Mama ta cigaba da kula da
INdo har aka yi arba'in d'in marigayi Abubakar sannu a hankali kuma Mama tana
bibiyar al'amranta na addini tana gyara mata sannan tana k'ara nusar da ita abubuwa
wad'anda mafi akasari suke k'ara tunawa INdo mijinta soyayyarsa kuwa bata ta6ajin
ta kankare koda d'igo d'aya ne, bata komai sai dai taci tasha tayi bacci, idan kuma
su Haleema na nan sai suyi hira d'an turancin da suke yi jefi-jefi itama ta d'an
fara tsintar k'ananun tana had'awa da wanda Dr yake yi mata sai dai dakyar take iya
rik'ewa dan sai tayi ta rik'e kalma d'aya a kwana biyu ko uku sannan take sake
fahimtar wata word d'in.

Kusan kullum sai Malam Hamza ya bugo musu waya tunda suka zo sadakar arba'in ya
kar6i number abban su Sadeeq kusan kullum sai ya bugo musu yaji wai ko an cire mata
abun sai suce a'a likitocin sun k'ara musu kwanaki da haka har INdo tayi watannin
takabar ta wanda har lokacin Sadeeq baya shiga cikin gidan su dan ma Allah ya
temake sa yana tafiya k'wara state dan wannan tafiyar tasa da Fateema sukayi sabida
yana shan wahala.

Ana sauran kwana biyu INdo ta kammala takaba su Sadeeq suka dawo, Fateema ce kawai
taje gidan shi kuma su Mama suka fita parking space suka gaisa ya juya ya tafi.

Ranar da INdo ta kammala takaba Abba ya k'ira Sadeeq yaje ya kaisa Sumaila suna
zuwa ya samu malam Hamza bayan gaisuwa Sadeeq na mota a zaune ya bugawa Fateema
waya suna hirar soyayyar su dan haka suke tamkar zasu cinye junansu Abba ya kalli
malam Hamza yace.

"Toh malam Abubakar dai Allah ya d'auki rayuwarsa a lokacin da yake tunanin ya fara
rayuwa, ya tafi yabar matarsa yarinya d'anya yau gashi Allah yasa ta kammala
takabarta kamar yadda addini ya tanadar. A zahirin gaskiya ba wani abu da marigayi
ya sanyawa Aisha a jikinta, me d'akina ce taga bazata iya barin muku Aishan ba
hakan yasa tayi muku dabara kuka bata ita mu kuma duk muka had'e muku kai muka nuna
cewar eh lallai haka ne abinda ta fad'a."

Malam Hamza yayi murmushi tare da cewa.

"Ai munyi mamaki har muna tunanin k'ila abin k'in fita yayi ashe soyayya ce tasa
kukayi hakan ai bakomi alhaji mune da godiya da baku nuna kyama a garemu ba,
Habubakar shine sila hakan yasa bazan gajiya dayi masa addu'ar samun ni'ima a cikin
makwancinsa ba, alhaji Allah yajik'ansa yayi masa rahama mun gode madallah."

"Ba komai malam Aisha ma ai 'yata ce, sannan kuma babban abinda ke tafe dani shine.
Kaf 'yan uwana da masu d'akina suna tausayawa Aisha, yarinya ce d'anya yau gashi
Allah ya jarabce ta idan aka barta zata Shiga layin zawarci, sun had'u sun had'e
kai wajan ganin bazasu iya bari matar d'ansu d'an uwansu abokinsu ta zauna a haka
ba suna ganin yi mata hakan kamar basu rufawa Abubakar asiri ba hakan yasa ko
wannen su yazo min da k'ok'an barar su na cewar mezai hana a mayeta da abokin
haihuwar sa, ma'ana mu had'asu aure da Sadeeq domin rufin asirin mu gabaki d'aya
sannan munsan Abubakar zai yi alfahari da wannan abun."

Malam Hamza yayi shiru kafin yaje ya k'ira Inna ya kuma k'ira amininsa malam kallah
suka zauna, Abba ya kuma maimaita musu zancen auran INdo da Sadeeq Inna dai bata ce
komai ba tace sune maza masu d'aura aure dan haka ita addu'a ce kawai tata. Bayan
Inna ta koma gida malam Hamza ya amince wasu mutanan suka zo a gurin aka d'aura
auran INdo da Sadeeq Abba ya bada sadaki dubu ashirin Sadeeq yana mota a zaune duk
wainar da aka toya besani ba har Abba yayi sallama da mutanan garin ya shiga mota
Sadeeq d'in ya ajiye wayar suka tafi...

#MZ
#Fan's
#luv-all
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *25*

Har sukaje gida Abba be sanar da Sadeeq ba, suna zuwa Abba ya shiga gida shi kuma
Sadeeq daya k'agu yaje gida ya juya kan motar ya tafi. Abba na zuwa fuskarsa cike
da fara'a ya cewa su Umma.

"Toh hajiya A'i an d'aura aure yau."

"Alhamdulillah Allah ya sanya musu albarka ya kauda fitina ya basu zaman lafiya."

Cewar Umma nan da nan fa gida ya cika da murna INdo kuwa bacci take a lokacin sai
bayan da ta farka ne Mama tace.

"Aisha jeki wanka kizo kuje gyaran kai."

Da sauri INdo ta mik'e cike da murna domin tunda ta dawo gidan bata sake koda
lek'awa k'ofar gida ba, sam sun hanata ko unguwa Mama zasu sai ta kafa mata doka
akan idan ta kuskura ta lek'a waje, yau gashi zata fita kusan kwananta d'ari da
takwas raban da ta kalli waje bare taga abinda yake wakana. Ta yi kyau tayi haske
fatar jikinta tayi luf-luf sannan tayi k'iba da yake hankalinta a kwance yake suna
kula da ita sosai dan ko 'ya'yan gidan basu kaita jin dad'i ba.

Wanka tayi tana fitowa taga saban d'inki an d'akko mata a can gidan Abubakar da
takalmi da jaka da mayafi su d'ankune sark'a da kayan kwalliyar su Haleema. Zama
tayi tana kallon kayan tare da shafa jakar da takalmin sai hawaye a fili tace.

"Allah sarki dacta kai ka saimin su.."

Tashi tayi tasa kayan sai ga Mama ta shigo cikin wasa tamkar ba suruka ba tace.

"Toh wa kika tambaya da kika d'auka kika sa? Idan kuma nawa nefa..?!"

Dariya INdo tayi tana rufe baki tace,

"Ai Mama ina ganin jakar na gane su, lokacin da zai kaimu gidan abokanansa da
nad'akko zan rataya yace min basu yi match da kaya na ba na ajiye ta."
"Allah sarki Abubakar Allah yayi masa rahama Allah yayi baxaku yi tsawon kwanaki
tare ba."

Cewar Mama tana d'akko mata humra ta ajiye mata a kusa da kayan tana cewa.

"Daga yau zaki iya sanya komai Aisha sai dai zaki ci gaba dayin abubuwa irinna
matan aure domin yanzu kema Matar aure ce."

Sam INdo bata gano inda zancen Mama ya nufa ba, a tunaninta tunda ta ta6a aure toh
zata ci gaba da suturce jikinta da kuma d'ora mayafi aka. Tana gama shiryawa Mama
ta bata kud'in gyaran kai tasa suka tafi dasu Haleema.

Lokacin da ta fara zura k'afarta a waje ji tayi tamkar yau aka haifeta. Wata
ajiyar Zuciya ta sauk'e tare da kallon ko'ina na wajan taga mutane kowa yana harkar
gabansa, wasu kuma da suka santa suna sake yi mata gaisuwa tana amsa musu har suka
kai bakin titi Haleema ta tare musu napep suka shiga.

Shagon saloon suka shiga sun d'an jima sannan suka fito suka dawo gida. Da dare
bayan Abba ya dawo ya k'ira Sadeeq sannan ya k'ira INdo, Mama da Umma duk suna
zaune a d'akin. Cikin muryar ta med'an k'arad'i tayi sallama tare da shiga ta zauna
tana gaida Abba.

A hankali Sadeeq ya d'ago ya kalleta sannan ya kawar da kai cikin ransa yana
tambayar dama tana da ladabi ko kuwa har lokacin mutuwar mijinta na jikinta ta dai
kusa tafiya shima ya samu 'yancin shiga gidan ubansa.

Abba ne ya k'ira sunansa ya amsa tare da kallonsa abban yace.

"Toh Sadeeq kamar yadda ka sani tagwai d'inka Allah yayi masa rasuwa ya bar
matarsa, yau kuma Allah ya nuna mana cikar wa'adin takabar ta kamar yadda addini ya
d'ora mata. Sadeeq kaine mutum na farko daya kamata ya rufawa matar d'an uwanka
asiri ka dubi halin da zata shiga idan ta koma garin su ka kuma dubi k'ank'antar da
tayi a matsayin bazawara bawai munaja da ikon Allah bane a'a duba da yadda
rayuwarta zata fad'a yasa muka yanke wani hukunci akai."

"Babu komai Abba ni dama tuni nayi alk'awarin zan dinga tura mata kud'i sannan zan
dinga yi mata abinda take buk'ata idan har befi k'arfina ba dama jira nake ta
kammala iddar sai na tambaye ta abinda yak'e matsalarta."

Sadeeq ya fad'a ba tare da ya kawo komai ba dan sam beyi tunanin wani aure
tsakaninsa da ita ba, Fateema yake so kuma ita ya aura baya tunanin zai yi *MUSAYAR
ZUCIYA* da watanta nan gaba bare kuma nan kusa daga yin aure wata biyar.

"Toh Sadeeq ai wannan abubuwan daka fad'a koni zan iya yi mata shi, mu yanzu fatan
mu ka rufa mata asiri a matsayin ta na mace me rauni kuma matashiya domin a d'azu
da ka kaini Sumaila k'auyan su naje ne mun d'aura muku aure dakai da ita ka maye
gurbin d'an uwanka...!"

A matuk'ar razana Sadeeq ya zaro idanuwa yana kallan Abban shi, zuciyar sace take
rawa jikinsa na tsuma ya kalleshi yace.

"Abba wani auran zan kuma yi? Abba ko wata biyar ban cikasa ba ace na kuma yin
aure? Tayaya zan iya zama da mata biyu Abba bayan yanzu nayi d'ayan? Abba matar
twin d'in zan aura? Ya akayi mutuwa tayi min haka..."

"Kai ya isa haka karkayi min sakarci kaji ko? Idan baka aureta ba ya kakeso tayi
bayan tana buk'atar temako da kuma mai lallashi da tausayawa a gareta...?!"

"Amma Abba yau yau d'innan fa tayi takaba amma ace ayau za'a aura mana aure ko
fuskanta juna bamuyi ba? Abba ya Fateema zataji wannan labarin."

Ya fad'a tamkar wani maraya Abba ya wurga mai harara cikin 6acin rai yace,

"Da kuma ace kaine ka rasu aka ce Abubakar ya auri Fateeman zakaji dad'i ko kafison
ta tafi ta auri wani bare..?!"

"Wallahi Abba gara ta auri bare haba-haba sai kace jira, dan Allah Abba kuyi tunani
ni wallahi..."

Bek'arasa ba Abba yayi saurin katse sa ta hanyar cewa.

"Toh shikenan sakarta ni sai na aureta shikenan hakan yayi maka.?!"

Cikin tashin Hankali Sadeeq ya kalli mahaifinsa sai zuba uban gumi yake baki na
rawa yace.

"Innalillahi wa'inna'ilaihir raji'un Abba ai babu aure tsakanin ku gara nid'in."

"A'ah aini tausayinta nakeji Sadeeq kuma abinda zanyiwa Abubakar kenan yasan nayi
mai kara ka sake ta sai na aureta ko kuma uncle d'inku Ahmad."

"A'a Abba dan Allah ka rufa mana asiri na kar6i auran Allah yajik'an m twinnie yasa
can tafiye masa nan."

Duk suka amsa da amin banda INdo wadda tunda taji maganar da akeyi tayi kicin-kicin
zuciyarta banda bugawa babu abinda takeyi wani rad'ad'i na shigarta. Abba ya maida
hankali wajan ta ya kalleta cikin kulawa yace.

"Aisha muna fatan bamuyi miki shishigi a cikin rayuwarki ba, muna fatan zaki yadda
da auran Sadeeq gashi nan komai nashi iri d'aya ne dana marigayi..."

Da sauri INdo tace "A'ah Abba wallahi ba halinsu d'aya ba koda can kafin mu saba."

Abba ya kalli Mama itama shid'in take kallo sannan tace.

"Aisha ai shima Sadeeq zai miki abinda marigayi yayi miki kiyi hakuri idan kuma
bakya sonshi shikenan ai ke yanzu babu batun yi miki auran dole za6i gareki a
wannan karan ma. Dama munyi haka ne dan karki shiga damuwa ko da idan kinga Sadeeq
d'in."

Shiru tayi batace komai ba sukayi-sukayi tayi magana amma tayi shiru Umma tace.

"Toh da alama ta yadda Allah ya bada zaman lafiya."

Tashi Sadeeq yayi ya fita Mama da INdo suma suka fita aka bar Umma kasan cewar
itace da girki ranar.

Dakyar ya iya kai kansa gida, lokacin daya shiga Fateema na kwalliya cikin bedroom
taji shigowarsa amma bata ga ya shigo d'akin ba, shi kuwa guri ya samu a falo ya
zauna kan kujera tare da dafe k'irji kanshi na barazanar fashewa ya tarwatse.

Fateema ce ta fito cikin shirin bacci tayi kyau ta kuma fari kai da kaganta kasan
tana cikin kwanciyar hankali, k'arasawa tayi kusa dashi ta d'are kan cinyarsa tana
k'ok'arin d'ago mai kai. Janyo ta yayi jikinsa da k'arfi tare da sanya ta a
k'irjinsa ya matseta da hannuwansa tamkar zai maida ita ciki ita kanta dakyar take
numfashi zuciyar ta cike da mamakin yadda taganshi.

"Wayyo Allah baby zaka karya ni."


Ta fad'a tana k'ok'arin kwatar kanta sabida ba k'aramin azaba takesha a matsar ba.
A hankali ya sassauta mata rik'on dayayi mata cikin sanyin murya Fateema ta kallesa
tace.

"Baby wai meyake damunka, haka kashigo fa ba sallama kuma naga duk jikinka a
sanyaye meya faru..?!"

"Bakomai kinci abinci dai ko?!"

Ya tambaya yana shafar cikinta, kad'a kai tayi tana kallon shi ya lumshe idanuwa
tare da kwantota jikinsa yace.

"Toh why?!"

"Baby kasan dai bana iya ci harsai kana nan, meyasa yanzu kake tambaya na...?!"

"Kinsan ai bana son kina zama da yinwa, kinga gobe ina da lecture 9 to 11 kuma
gashi banajin dad'in jikina ya zanyi ne.."

Fuskar sa ta tallafo sukayi kallon cikin ido ta sakar masa murmushi tana shafar
gashin dake ha6arsa tace.

"Yanzu ai lokaci bek'ure ba goma da rabi saura minti uku kayiwa class captain waya
kace musu bazaka samu damar zuwa ba suyi hakuri zaka samu wani time d'in sai kuyi
musu amfani dashi..."

"Ai kuma baby ban musu lectures bafa tunda aka koma gashi har an fara tambaya na
exam questions, zanje ko abu d'aya ne nayi musu tashi muje kici abinci."

"Inci abinci ko dai muci abinci?!"

Ta tambayesa tana sake lafewa a jikinsa, suna zama yana cewa.

"Kinsan Abba neya k'irani so munci abinci tare dashi."

'Dan hararasa tayi tare da cewa "Ai kasan dai nima nawa yana jiranka dan haka sai
kaci babu wani batun kunci da Abba ko zakayi amai kuwa."

Shi sam yarasa ma mezai yi yinwar ma bajinta yake yi ba shi yasa yace mata haka
amma dan karta shiga damuwa sai yace.

"Toh baby na ya zanyi amma nasan yau babu abinda zan iya tabuk'awa."

Shi dai dakyar ya samu yaci duk tunanin yadda zai 6ullo mata yake yi a cikin
zuciyarsa, sai da ya tabbatar taci ta koshi sannan ta rakashi yayi wanka ta bashi
sleeping gown ta maza yasa sannan suka bi lafiyar gado. Kamar yadda ya sabar mata
koda bazai yi komai ba toh sai sunyi wasa haka yauma har sai da yaga ya kwantar da
kanta kan k'irjinsa zata yi bacci ya bud'e baki dakyar ya k'ira sunanta.

"Zarah..."

Tayi jimmm jin yadda ya k'ira tsohon sunan da yake kiranta dashi tun suna saurayi
da budurwa, can dai ta amsa mai tana shafar k'irjinsa shi kuma yana shafar himilin
gashin kanta domin akwai suma yace.

"For example nine na rasu ba Abubakar ba idan aka ce ki auresa zaki iya..?!"

Ya k'arasa maganar yana d'an d'ago mata kai. Shiru tayi na tsawon lokaci tana
tunanin abinda yasa shi yi mata wannan tambayar marar dad'in ji bare sauraro, sai
da ya sake tambayar ta sannan ta numfasa dakyar tace.

"Haba baby ya zaka min wannan tambayar tunda dai bakai ne ka rasun ba?"

Yace "Eh so nake naji zaki yadda idan aka ce ki auri twinnie d'ina ya zakiyi."

"Gaskiya bazan auresa ba haba ai bashi na aura ba."

"Toh idan aka tursasa kifa ko aka aura miki shi ba tare da kin sani ba ya
zajiyi..?!"

"Ta6 d'i wallahi baby sai ya sakeni uhm'um ni dan Allah ka dena yin irin wannan
tunanin please."

Jikinsa ya sake janyo ta yana shafar bayanta, so yake ya sanar da ita yau basai
taji a bakin wani ba amma ya rasa hanyar fad'ar ya dai daure yace.

"Toh idan hakan ta faru tunda ni bakya sona mutu aka ce na auri Humairah ya
zakiyi?!"

"Bama zata yiwu ba sabida INdo bata sanka har agabana ta fad'a."

Shiru suka yi na tsawon lokaci gashi dare ya tsala ko'ina yayi shiru sai k'arar gen
d'insu kawai akeji. Numfasawa Sadeeq yayi tare da janyota yace.

"Kiyi hakuri baby na yanzu dawowar da kikaga nayi Abba ne ya sanar da ni cewar an
d'aura min aure da ita ni kaina ba..."

Jiyayi ta mik'e zaune a razane daga ita sai bra domin rigar ta zame Fateema ta
bishi da kallo hannunta dafe da k'irji ya kalleta bayan shima ya tashi zaune. Wata
shegiyar harara take wurga mai cikin zafin rai ta fara magana jikinta na rawa.

"Yanzu kana nufin har an d'aura muku aure?"

Sadeeq ya d'aga mata Kai alamar eh yasa hannunsa ya janyo ta a hankali ta fad'a
jikinsa ta saki kuka me ban tausayi ya fara lallashinta shi kansa ji yake tamkar
yaje ya bindige INdo. Babu yadda zatayi ita kuma haka tata k'addarar take daga yin
aure sai kishiya suna cikin more rayuwarsu.

***

A 6angaran INdo kuwa wani uban nishi ta dinga saukewa duk iya k'ok'arin Mama na ta
gaya mata matsalar ta sam tayi shiru tak'i yin magana har gari ya waye bata yiwa
kowa magana ba Mama ta rasa dalili dan ta saki ranta yasa Mama cewa.

"Aisha gobe za'a kaiki gida kije kiyi kwana biyu kafin Sadeeq d'in ya ware yadda
zai yi."

Sai a sannan INdo tayi magana tana dariya tace.

"Toh Mama amma dai ba shine zai maida niba...?!"

"Toh ai Aisha yanzu dai komai yana hannunsa sai abinda yace kiyi mai biyayya kedai
anan zaki samu aljanna."

Ba zato cikin subutar baki tace.

"Ta6 d'ijam.."
Mama ta kalleta cikin mamaki amma sai taga INdon na mutsu-mutsu da baki alamar
magana take a ranta lallai yaran nan da alama zasu basu mugun mamaki sam basuyi
zaton INdo zatak'i Sadeeq ba ganin yadda suke kammani da mijinta ba....

#MZ
#Fan's
#luv-all

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

*A gaskiya ina alfahari daku masoya, comments d'in ku yana sani jin dad'i both
wattpad & WhatsApp. Bazan iya lissafo sunayanku ba sai dai ina yiwa duk wata mai
bibiyar labarin nan fatan alkaira Allah kuma yabar kauna da soyayya love you all*❤

Page *26*

A 6angaran su Sadeeq kuwa dakyar ya iya fita lecture, itama Fateema bata fasa yi
mai breakfast ba sai dai duk babu wanda ya iya ci. Yana tafiya Fateema ta shiga
cikin d'aki taci kuka sannan ta d'auki wayarta ta k'ira Ummanta, tana d'agawa ta
fashe da kuka hankalin Umma yayi matuk'ar tashi tana tambayar lafiya.

"Kiyi shiru kiyi min magana dan sai kin min bayani sannan zansan matsalarki."

Cewar Umman ta cikin lalla6ata dan ta gaya mata. Cikin kukan Fateema tace.

"Umma Sadeeq ne ya k'ara aure jiya..."

Tayi maganar muryarta na hard'ewa hankalin Umman ta ya tashi tace.

"Fateema a ina yayi auran bako labari?"

"Umma yazan yi matar d'an uwansa aka aura mai jiya shima be sani ba, sai da Abban
su ya k'irasa ya gaya mishi."

Ji tayi Umma ta sauk'e ajiyar Zuciya hankalin Fateema ya tashi tana cikin bargo
amma wani irin mugun sanyi takeji yana ratsata, jita yi Umma na cewa.

"Oho Allah sarki, Fateema toh karki damu kinga kema wannan kaddarar batak'i ta
sauka a kanki ba, kiyi hakuri ki zauna ki taya mijinki zama da ita ba'a san abinda
Allah ya shirya ba akan al'amarin. Ina son ki kwantar da hankalinki karki sake ki
nuna masa cewar kina bak'in cikin wannan auran idan kikayi haka nan gaba kezakiji
kunya sabida shirin na Allah ne dan da be d'auki Abubakar ba da hakan baxata faru
ba, ki kankaro mana mutuncin mu ta hanyar k'ar6ar wannan auran cikin nuna farin
ciki koda ba hakan bane a ranki."

Wani irin kuka Fateema ta kuma fashewa dashi wanda da kyar ta iya yin sallama da
Umman tata. Kuma k'udindinewa tayi a cikin bargo tana cigaba dayin abinta har
zazzafan zazza6i ya sake rufar mata.

Sadeeq kuwa yana kammala lecture ya fito daga school d'in, kai tsaye ya wuce
gidansu Fateema ya samu ba kowa sai Umma. Shiga yayi har cikin falonta ya zauna
suka gaisa cikin fara'a ba tare da ta nuna mai komai ba.

Cike da ladabi Sadeeq yayi ma Umma bayanin yadda lamarin ya wakana sannan ya
dad'a da nunawa Umma ta yiwa Fateema nasiha tare da tayashi bata hak'uri, Umma tayi
murmushi tare da cewa.

"Karka damu Sadeeq Allah ne yasan abinda ya shirya har akan ta faru, insha Allahu
kuma zanyi mata nasiha kaima sai kayi hakuri kasan irin wannan lamarin sai mutum
yana kawar dakai dan zakaga ban-banci d'abi'a akan ta baya da kuka yi."

Sadeeq yana sunkuyar dakai yace,

"Insha Allahu Umma na gode Allah ya k'ara girma."

"Amin a gaida mutanan gidan ace muna yi musu Allah ya sanya alkairi."

Batare daya amsa mata ba yayi tafiyarsa baya tunanin ma zai sake zuwa gidan harsai
ya samu labarin cewar INdo bata gidan.

A kwance ya tarar da ita ko gidan bata bud'e ba sai da ya sanya mukulli ya bud'e.
K'arasawa yayi tare da yaye bargon da ta rufa dashi ya ta6a jikinta mai d'auke da
zazzafan zazza6i nan da nan hankalinsa ya tashi ya hau gadon gabaki d'aya ya d'aga
zuwa jikinsa yana k'ok'arin san su had'a ido amma tak'i bari hakan ya faru.

"Baby na kinji jikinki kuwa? Meya sameki?!"

Wani kukan ne ya sake zuwar mata cikin rawar murya tace mai.

"Banajin dad'in jikina kaina ciwo yake."

"Oya tashi muje asibiti Allah yasa ma nayi ajiya."

'Dan janye jikinta tayi ba tare da ta kallesa ba ta koma ta kwanta tana cewa...

"Karka damu basai munje asibiti ba dan yanzu ma haka ciwon mara nakeji."

"Wayyo Allah baby na bana son wannan abun wallahi, nida da yadda za'ayi ma da nasa
an tsayar miki ki denayin sa."

Shiru tayi mai batayi magana ba shi kuwa duk so yake yi ta dawo dai-dai yadda suke
amma ina sai tashi yayi ya koma falo dan bazai juri ganin yadda take sharesa ba, ba
kuma yason ya dinga 6ata mata rai.
Yana zaune a falo yana transfer d'in kud'i a account d'in mutanen daya k'ar6i kaya
yaji wayarsa na ruri, d'auka yayi yaga Mama sai da k'irjinsa ya buga. Addu'a ya
fara yi Allah yasa kar tayi mai zancen INdo domin sam baya k'aunar yaji sa.

"Hello Mama antashi lafiya?!"

"Eh Alhamdulillahi tunda bakaga damar zuwa ba, mekakeyi yanzu?!"

"Kiyi hakuri Mama bak'in zuwa nayi ba yanzun nan na dawo daga lecture, ina gida
nazo?!"

"Eh dama cewa zanyi ka shirya kazo kakai Aisha garinsu ta d'anyi musu kwana biyu
kafin ka samar mata gurin zama."

Had'e rai yayi tamkar a gaban Maman ransa na suya baya son kuma komawa garin nan
duk da cewar sunyi zaman amana dashi amma a yanzu ga Fateema ba lafiya sannan ance
yazo yakai INdo garinsu sabida kawai shi aka sakawa ido komai sai ace shi dama shi
ya mutu ba Abubakar ba da duk ba'ayi mai wad'annan abubuwan ba.

"Kayi shiru Sadeeq kona shirya tunda nina d'akkota sai na mayar da ita."

Yaji Mama na fad'a cikin fad'a-fad'a. Lumshe idanuwa yayi tare da shafar sajan sa
yace.

"A'a Mama kiyi hakuri bari nayi wanka zanzo."

"Toh shikenan kazo kowane lokaci ne sai ka kaita duk ka gama walagigin naka muna
nan muna jiranka."

Tana kammala fad'a ta katse k'iran shi kuma yabi fuskar wayar da kallo, shikam ya
shiga uku wannan wace irin kaddara ce ta hau kansa. Ya kasa gane abinda Abubakar ya
gani a gurinta har yaji yana sonta, ita ba ilimi ba sannan ba Kud'i ba, ba wani
shegen kyau ne da itaba sai shashanci ga6untaka kauyanci da rashin wayewa duk ita
kad'ai shikam a takaitashi da auranta da aka bashi.

Tashi yayi cikin sanyin jiki ya shiga d'aki, fuskar fateema ya kalla sannan yaje
ya shafa fuskar yana kallonta. A hankali ta bud'e sukayi ido hud'u yace.

"Tashi kisha magani kici abinci zansa su Haleema suzo su tayaki zama Mama ta kirani
wai zankai Aisha gidan su yanzu kinji.?!"

K'irjin Fateema ya fara harbawa ganin tun yau sun fara raba abubuwa tsakaninsu, da
kyar ta daure tace.

"Toh sai kun dawo amma kabar su Haleema basai sunzo ba babu abinda zasu yi min."

Magani ya d'akko ya fita kitchen ya d'akko ruwa sannan ya zauna kusa da ita, dakyar
tasha maganin sannan ta kwanta shi kuma ya shiga cikin bathroom yayi wanka gaba
d'aya ma besan abinda zaiyi ba akan INdo.

Fitowa yayi d'aure da towel a k'ugunsa ya k'arasa wajan mirror duk Fateema na
kallonsa a sace ta cikin bargo. Sai daya gama goge ruwan jikinsa sannan ya zauna
kan stool yana shafa mai. Yana gamawa ya nufi wardrobe ya zaro wata shadda
blueblack ya sanya tare da d'akko bak'ar hula zannah ya kafa kan goshi, ya sanya
agogon hannu ya zura takalmi bak'i tare da feshe jikinsa da turare ya d'auki comb
brush ya kwantar da gashin daya zagaye kyakyawan bakinsa.

Duk abinda yake yine yayi amma da Fateema tasan inda zashi sai taji k'irjinta na
harbawa zuciyarta na zafi wani bak'in kishi ya mamaye ciki da wajan zuciyarta bata
san lokacin da hawaye suka zubo mata ba tayi saurin maida fuskarta cikin bargon
ganin zai juyo.

Sadeeq ya k'arasa gurinta bayan ya durk'usa saitin fuskarta ya kura mata ido.

"Babyna karki dinga sanya ranki cikin damuwa, kece mace ta farko dana faraso na
kuma fara aura na fara baiyana mata sirrina na kuma yadda da ita, ina so ki dinga
alfahari da hakan kina cikin zuciyata bazan ta6a yadda wani ya 6ata miki rai ba ko
ya gaya miki ba dad'i in kyalesa.

Ke ko Aisha da aka aura min idan batayi miki biyayya ba sai na sa6a mata wallahi ke
nine nace ina sonki ita kuma mutuwar twinnie d'inane yasa aka bani auranta karki
dinga damuwa kinji ko.?!"

Sai a lokacin Fateemah taji sanyi ko ba komai ya kwantar mata da hankali da


dad'ad'an kalamansa masu zak'in zuma. Kallonsa tayi idanuwanta duk sunyi jah tsabar
kuka sannan ya zuro hannu ta shafi fuskarsa tace.

"Nagode da wannan matsayin daka bani, ka tashi kaje kaga da nisa Allah ya dawo min
dakai lafiya, a gaidasu Mama."

Murmushi yayi mata tare dakai bakinsa kan nata yayi kissing d'inshi sannan ya
mik'e tsaye yana ce mata.

"Amin babyna sai na dawo."

Fita yayi ya shiga mota yabar gidan.

Kai tsaye gidan Mama yayi, a k'ofar gate yayi parking sannan ya fito ta shiga gida
cike da tak'ama dan yau jinsa yake tamkar akan iska. Yana shiga k'annansa suka hau
gaidashi ya amsa musu sannan ya lek'a d'akin Umma ya tarar tana sallar azahar ya
koma ya shiga d'akin Mama.

Cike d'akin yake da k'amshin turaran humra Sadeeq ya bud'e hanci yana shak'a, tsaye
yaga INdo ta gama d'aurin d'ankwali ya kalleta tare da jinjina kai. Idan besan
asalin INdo ba da ace yau shine karo na farko daya fara ganinta toh bazai mata
hausa ba dan babu abinda zai hanashi d'auka cewar batayi degree ba a boko. Sai dai
kashhh shine yasanta yasan ko wacece a fannin dak'ik'anci da rashin son karatu tun
batakai haka ba dan haka yana shiga gurin Mama ya nufa yana mai cire hular kansa.

"Mama na ina wuni?!"

"Lafiya lau Sadeeq na d'auka ma bazaka zo yanzu ba, ya gidan ya Matar taka?"

Sadeeq ya koma bakin gado ya zauna yana cewa.

"Haba Mama na isa ink'i zuwa, lafiya lau take tana gida ma batajin dad'i."

Yayi maganar yana kuma karya k'arin hularsa. INdo kuwa ci kanka batace masa ba Mama
na ganin ikon Allah taga wazai fara yiwa wani magana sai taga kowa yana harkar
gabansa. Kasa yin shiru Mama tayi sai da tace.

"Aisha wai bakiga Sadeeq bane, naga ko gaidashi bakiyi ba!"

Ba kunya INdo tace,

"Mama ai yace idan na sake ganinsa na kusala tom d'ina, har wawuya yace min a
ranar."
Baki bud'e Sadeeq ya kalleta, rabon daya ganta tun rasuwar Abubakar sai jiya da
Abba ya had'asu sai kuma yanzu amma ji sharrin da tayi mai cikin jin haushin ta
yace.

"Karki rainawa mutane hankali yaushe na fad'a.?"

Nan ma ba tsoro bare kunya tace.

"Lokacin rasuwar marigayi sanda nazata bashine ya mutuba Ina murna na rik'eka ka
tureni kace karna sake kulaka, a lokacin ne na tabbatar da cewa Kaine malam Sadeeq,
shi yasa bazan gaida kaiba tunda kace haka."

Tsaki yaja tare da maida hularsa kansa, gaba d'aya ma besan ya fad'a ba yasan dai
lokacin ta bashi haushine. Lallai yarinyar nan akwaita da rik'o toh kar Allah yasa
ta gaidashi sai me (so what).

Mama ce ta kalleta cikin nuna mata martabar miji tace.

"Aisha ya kamata ki ajiye komai daya wuce tsakaninki da Sadeeq, yanzu mijinki ne
dole zaki mai biyayya kamar yadda musulinci ya gindaya. Yanzu ki gaida shi bana son
wani tashin zance."

Babu yadda zata yi domin a haka tana ganin k'ima da darajar Mama, cikin turo baki
tace mai.

"Ina wuni?!"

Dan kar shima Mama tayi mai magana yasa shi amsawa a takaice yace.

"K'alau."

Mama ta jijiga kai tare da rik'e ha6arta, Sadeeq kawai zata jawa kunne domin shine
miji kuma shine sama da INdo duk abinda ya d'orata akai shi zatayi ta kuma k'ara
akan wanda take dashi zama tazo yak'i dad'i suji kunya amma zata bari sai ya dawo
daga kaita tukunna.

Tashi yayi ya fita bayan yace su sameshi a waje. Sosai sukayi sallama da mutanen
gidan suna mata fatan sauka lafiya INdo na amsa musu. Gaba Haleema ta bud'e mata
babu gaddama ta shiga shi kuma Sadeeq yaja motarsa suka wuce INdo sai dariya take
tana jin dad'in yadda duk suke sonta.

Tunda suka fara tafiya yake amsa waya duk ya cika mata kunne, hannu ta zuwa ta
kunna redion motar dan ta riga ta iya Abubakar ya nuna mata sannan ta kunna A.c ta
zuge glass d'in kusa da ita. Sadeeq ya sanya hannu ya kashe redion yana wayar sa
itama ta kuma kunnawa tare da cewa.

"Haba Malam Sadeeq kana wayarka mana ni kuma ina jin redio na bashi kenan ba."

Wata muguwar harara ya watsa mata ta ta6e baki tare da juyawa tana kallon hanya.
Abinda yake k'ona mata rai da turanci yake maganar sai Hausa da yake d'an cillawa.
Wayarta ta d'akko wadda tun Abubakar ne daya sai mata ta fara d'aukar photo tana
selfie style kala-kala ko kulata beyi ba harya gama wayar ya ajiye ta.

Gajiya yayi kunnuwansa sun cika da k'arar camera ya warce wayar daga hannuta tare
da cilla mata ita kan cinya yace.

"Ke bana san kauyan ci fa."

Kallansa tayi hannunta rik'e da ha6arta tana cewa.....


*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

Page *27*

"Malam Sadeeq kenan, ai da kasani ba yanzu ba."

Shareta yayi ya nuna tamkar ma bejita ba ta juya tana kallonsa ta kuma d'aukar
wayarta daya cillo mata. Madubin saitin kujerarta ta bud'e tana gyara fuskarta ya
girgiza kai dan shi dama yasan da wahala yarinyar tayi hankali sabida babu arabi ba
boko yaja tsaki har kusan sau uku sannan INdo ta kallesa tace.

"Babu kyau fa."

Yace "Ni zaki cewa babu kyau? Ko kin fini sanine da zaki cemin babu kyau?!"

"Allah ya baka hakuri, cewa akayi idan kaji wani ko wata sunyi abinda ba kyau ka
tuna masa, toni tuna maka nayi."

"Karki i sake tuna min domin tun kafin kisan hakan nasani, ke karki sake yin magana
har muje inda zan kai kina jina.?!"

Bata sake kula shiba har sukaje danja masu tallar abubuwa suka dinga d'ago musu
taga me alawar madara da sauri ta zaro d'ari biyu ta mik'a masa ji Sadeeq kawai
yayi tana cewa.

"Bani ta dika."

Aikuwa ransa ya kuma mugun 6aci Allah-Allah yake kafin a gama mik'o mata ya figi
motar amma danja batazo kansu ba harsai da aka bata tasa a jaka sannan aka basu
hannu. Leda d'aya ta mik'a masa tace.

"Malam Sadeeq bisimillah."


"Banasha."

Maidawa tayi cikin jaka ta bud'e leda d'aya tana sha har wani kunkuni takeyi irin
na zak'in nan idan ya gauraye kunne. Wayarsa ya d'auka yasa earpiece tare da kiran
layin Fateema, sai da ta kusa yankewa sannan yaji ta d'aga cikin sanyin murya tayi
mai sallama.

"Ohh babyna har yanzu jikin ne?!"

Ya fad'a cike da damuwa, can 6arin Fateema tace.

"A'ah kawai dai bacci nake, kun tafi ne?"

"Eh muna hanya ma yanzu zan dawo insha Allah, amma ki tashi ko tea ne kisha zaki
kuma samun relief."

"Toh Allah ya kiyaye hanya a gaida min ita."

Tana kaiwa nan yaji ta katse, ba haka yaso ba yaso suyi hira ta d'ebe mai kewa amma
tariga ta kashe ya cire earpiece d'in yana cigaba da tuk'insa ba tare daya sake
kallon koda inda take ba.

"Malam Sadeeq dan Allah ka kar6a kasha, wallahi tayi dad'i madara ce zallah."

Yayi shiru ta kuma cewa.

"Inkaji dan Allah sha d'aya kaji."

A fusace ya juya yana kallonta shi har lokacin be manta yanayin ta na baya ba cikin
6acin rai yace.

"Wai dole sai na Shane? Idan dole ne toh sani insha dan Allah."

Ya fad'a tare da d'an kallon gabansa kafin ya juyo yana dank'ara mata harara, d'aya
ta d'akko da sauri ta danna mai ita a baki ya yi saurin furzar da ita a k'asa amma
duk da haka sai da zak'in ya shiga ko'ina na cikin bakinsa ya samu gefen titi ya
tsaya tare da nuna ta da yatsa yace.

"Wallahi tallahi Aisha ki kiyayeni karkija wata rana na 6allaki yasin. Kinga ina
shiga sha'aninki ne? Toh ki kuka da kanki duk rashin kunyarki a tafin hannuna
take...!"

Jan bakinta tayi ta tsuke bata sake cewa komai ba har suka shiga garin Sumaila,
tana ganin barkono dama sund'an tsaya sabida ana bada hannu batare da tayi mai
magana ba kawai yaji ta bud'e k'ofar ta fita tana cewa.

"Bari na siyawa Inna barkono da gyad'a ko kwano d'aya-d'aya ne."

Kafin ya harzuka yayi magana ta k'arasa wajan, Sadeeq ya kifa kansa a steering shi
kam ya shiga uku wannan wace irin yarinya ce tana ganinsu a tsakiyar titi amma ta
6alle murfin motar ta fita. Idan ta dawo sai ya mareta gobe bazata sake yi mai
makamancin haka ba.

K'arasowa tayi wani yaro na biye da ita a baya da kaya ta bud'e gidan baya ya zuba
sannan ta bashi naira hamsin ta shiga motar ta zauna tare da kallonsa tana gyara
mayafi tace.

"Malam muje na dawo, wallahi kuma da arha shi yasa na siyo mata kwano biyu-
biy....."

Bata k'arasa ba taga ya d'ago hannu tayi saurin sunkuyar da kai tare da boyeshi
tana sauke a jiyar zuciya cike da tsoro da mamaki. Fad'a ya fara yi mata kamar ya
samu student d'inshi har ya gama bata d'ago ba ya figi motar taji sun fara tafiya
sannan ta d'ago tana kallonsa.

Kasa yin magana tayi ganin yadda yayi kicin-kicin da fuskarsa dan haka ta share Sa
har sukaje k'ofar gidansu. Mutane kuwa aka fara murnar ga INdo ga INdo, wad'an da
suka sanshi kuma suka dinga gaidashi yana amsawa da kyar tamkar 6eyi rayuwar garin
ba. Kayanta ta kwasa tare da shiga cikin gidan su bata sake fitowa ba, shiru-shiru
taji babu wanda ya lek'o shi kuma jira yake su gaida koda Inna koda Malam Hamza
amma babu kowa daya fito daga gidan haushi da takaici suka sa shi ya tafi ba tare
daya aika ankira wani ba.

A cikin gidan kuwa INdo cewa tayi musu ai ya tafi hakan yasa Inna bataje sun
gaisa ba su kuma murnar zuwan INdon yasa basu fita ba bare su ganshi harya tafi.

Har Sadeeq yaje gida be denajin haushin abinda INdo tayi mai ba, lokacin da yaje
gidan a cike yake da 'yan uwan Fateema hakan yasa shi juyawa yayi hanyar gidan su
ba tare da ya shiga ba dan yasan akwai wad'anda zasu yi mai kallon banza.

Mama na ganinsa hankalinta ya kwanta tace.

"Yauwa Sadeeq har ka dawo?!"

"Eh suna gaida ku."

Ya fad'a yana k'ok'arin zama a kujera, Mama tayi murmushi cikin jin dad'i sannan ta
shiga d'aki ta kawo mai abinci, beyi musu ba yaci dan yasan Fateema ba iya yi
zatayi ba sabida ciwon marar daya barta tana yi. Yana gama ci ya fita yaje can
gidan marigayi ya gano sannan ya wuce gurin abokinsa har sai da aka kira magariba
sannan ya koma gidan.

****

Bayan sati biyu Abba ya gaji da sanya mai ido da safe ya kirasa, yana zuwa sai daya
shiga suka gaisa da Umma da Mama sannan ya shiga gurin abban. Gaisawa suka yi Abba
ya kallesa tare da ajiye magazine d'in hannunsa yace.

"Sadeeq yaushe zaka koma kwaran ne?"

"Abba nan da kwana uku insha Allahu zamu koma."

"Kai dawa?"

Sadeeq yace, "Abba da Fateema mana."

"A'ah Sadeeq ya kamata ka farayi musu adalci tun yanzu, ina son tunda zuwan nan na
k'arshe da Fateema kukayi toh wannan karan sai ku tafi da Aisha bana son ta cigaba
da zama da auranka acan gidan su ina fatan ka fahimce ni.?!"

Wani irin 6acin raine ya ziyarci ran Sadeeq kansa a k'asa yana danna yatsansa cikin
zuciyarsa kuwa abubuwane kala-kala a cikinta. Jin yayi shiru ne yasa Abba kuma yi
mai magana Sadeeq yace.

"Abba ai tafiya ta da Aisha garin nan bazai yiwu ba sabida kaga su ba Hausa sukeji
ba itama kuma ba yarensu takeji ba dama tanajin turanci ne da sauk'i amma gaskiya
tafiya da ita matsala zai jazamin wallahi, nasanta tun kafin Abubakar yasan ta."
"Toh yanzu me kake nufi?!"

"Abba kawai zan samu gida na ajiyeta anan idan yaso sai ta zauna a ciki har mu
dawo."

Abba ya kallesa sosai kafin yace.

"Kana nufin ta dinga zama anan har lokacin da zaka dinga dawowa yayi."

Sadeeq yace. "Eh Abba idan ba hakan ba wallahi bansan yadda zanyi da Aisha ba idan
mukaje can, gashi ta raina ni sam bata ganin girmana tun sanda na koyar dasu a
makaranta."

"Shikenan kafin ka tafi kaje ka d'akkota sai ta tare anan gidan Najib tunda naga ya
kammalasa kuma 'yan haya zai zuba gashi dai-dai itane gidan."

Sadeeq yayi shiru tunani yake yana kuma jin takaici, kawai yana zaman-zamansa an
d'akko mai wani aikin, yanzu duk shekara sai ya bada kud'in gidan hayar da INdo
zata zauna dubu d'ari da talatin. Mtwww yaja tsaki ba tare da yasan ya fito fili ba
sai da yaji Abba yace.

"Sorry ko na shiga hak'inka ne??"

Da sauri Sadeeq ya hau kad'a kai alamar a'a sannan yace.

"Toh Abba kuma ni zanje na d'akkota? Na d'auka kawo ta zasu yi.?!"

"Eh toh kuma hakan dai yafi, amma ina son ka k'ara d'aga tafiyar ka har ta tare
sannan sai kutafi."

Dakyar ya iya amsawa Abba sannan ya tafi. Yau ya kuma yin Nadamar zuwa tsefawa
secondary school domin zuwansa ne yasa Abubakar ya ganta harya aure ta gashi ya
mutu shi anbarsa da alak'ak'ai.

Yana komawa gida ya bawa Fateema labari tace Allah ya sanya alkairi, kallonta kawai
yayi ya shige d'aki.

***

Cikin kwanaki biyu tal Abba yasa Sadeeq aka kwaso kayan INdo na gidan Abubakar
harda wanda duk shine ya siya aka kaisu gidan da INdon zata zauna a matsayin ta na
Matar sadeeq. Su Haleema Rukayya da Amina yasa sukaje suka kwaso kayan sawarta suka
kai can gidan akajera mata sai dai babu dining area gashi INdo tana matuk'ar sansa
dan idan tana kai ji take tamkar tana kusa da sharukhan.

Sadeeq da Umma da Hawwa suka tafi d'akko INdo, hirarsu ce duk ta sashi mance wadda
zasu je su d'akko har suka k'arasa k'ofar gidansu INdo wanda yake cike da mutane
wai ashe su biki suke yi wannan abun ya k'onawa Sadeeq rai sai kace wani sabon aure
mtww.

Sun dad'e a ciki kafin a fito da ita su Uwani sai mata murna akeyi ta baro gidan
dad'i zata koma gidan dad'i INdo taja tsaki ita kad'ai tasan gidan da zata shiga
dan tasan sam basanta yake ba ta kuma riga ta shirya ma zama dashi a kowane irin
yanayi indai vazai hanata abinci da fita yawo ba.

A kusa da Umma ta zauna yayin da Hawwah ta zauna gefensa anata yi musu fatan sauka
lafiya bayan Malam Hamza yazo sun gaisa dashi Sadeeq din ya kuma bashi amanar
'yarsa sukaja mota suka tafi.
Tunda suka kama hanyar komawa yaja bakinsa ya tsuke jin INdo ta zage sai subirbid'a
hira take tamkar ba amarya aka d'akko ba, yaja tsaki ganin sam babu jan aji a
tattare da ita. Suna zuwa a k'ofar gidanta suka sauke ta su Umma suka shigar da ita
ganin amarya yasa mak'otanta suka shiga suma dan su ganta.

Har kusan k'arfe shad'aya na dare Sadeeq be shigo gidan ba, gidan yayi matuk'ar
yin kyau domin yasha tile's bangon da k'asan ta ko'ina sai dai bekai girma da
tsaruwar na marigayi Abubakar ba amma hakan be damu INdo ba domin na iyayanta sam
be kama k'afar su ba. Kallon agogo Hawwah tayi tare dajan tsaki tace.

"Wallahi Yaya Sadeeq d'an wulak'anci ne, yasan fa muna jiransa amma bazai zo ba ga
mijina can sai waya yake yomin."

"Kinga yayya Hawwah kiyi tafiyarki mu zamu jirashi."

Haleema ta fad'a tana gyara kwanciya akan kujera hannunta rik'e da waya wanda hakan
yake nuni da cewar chatting takeyi.

"Ba haka mukayi da Abba ba, cewa yayi karna bar gidan nan sai na tabbatar mai da
shigowar Yaya Sadeeq."

"Toh saiki zauna gyara wani auran ke kuma ki 6allo naki ba."

Waya ta zaro zata k'ira Abba sukajiyo sallamarsa a k'asan makoshinsa. Tashi kowanne
yayi yana sanya mayafinsa ya zauna a kan kujera.

"Toh Yaya Allah ya bada zaman lafiya."

Yayi shiru yana canza channel Hawwah tace.

"Yaya ina muku addu'a kayi shiru."

"Ke malama ku wuce kutafi gida bana son sa ido."

"Amin yayya Hawwah mun gode a gaida gida da abban siyama sai munzo."

Suka jiyo muryar INdo tana fitowa daga bedroom, hatta shi kansa saida ya kalleta ta
gyatsina mai hanci tabi bayansu danyi musu rakiya.

"Amarya kamar karmu barki wallahi."

"Allah sarki Aminatu idan Allah ya kaimu basai ku dawo ba."

"Zamu zo amma da yamma kinga gobe monday akwai makaranta."

Cewar Haleema INdo tace.

"Toh koma dai yaushe ne sai kunzo a gaida Mama."

"Zataji."

Suka fad'a tare da juyawa su shiga mota da driver na jiransu itama ta juya ta shiga
ba tare da ta kulle gidan ba. Zama tayi a falon tana wak'ar Nas ya shareta yana
kallonsa itama bata kulasa ba domin ba so takeyi ba daman.

"Ke jeki kwanta dare yayi."

Yayi maganar yana gyara kwanciya akan kujera. Itama ta gyara zama tare da d'aukar
remote tana murmushi tace.

"Wallahi malam Sadeeq banajin bacci."

Had'e rai yayi domin yana son yin waya da Fateema ya rage mata dare yayi mata
alk'awari gashi wannan yarinyar zata samai ido.

"Ke bakya jin magana ko? Kin tashi kosai ranki ya 6aci.?!"

Tashi tayi cike dajin haushi ta shiga bedroom, kan gadon Abubakar datake so shi aka
sanya mata a d'aki d'ayan kuma dayake matsayin nata aka sashi a d'ayan d'akin da
ake nufin na sadeeq ne. Tana kwance kwai ya fad'o mata ta zura hannu k'ark'ashin
filo wayam babu sweet d'insa da yake ajiyewa ta kalli agogo da yanzu suna tare
kawai ta mik'e ta koma falon tana k'ik'ifta ido.

"Idan Zan iya zama ni d'aya a d'akin Allah ya tsinen..!"

Sadeeq dake manne da waya a kunnensa yaji da fad'a. A hankali yace.

"Babyna wait zan sake kiranki."

Kashewa yayi tare da juyawa ya kalleta sai kuma ya juya ganinta sanye cikin riga da
wando pink and white na bacci sun kuma zauna a jikinta d'as duk da basu kamata ba
yace.

"Toh kina son nazo mu kwanta tare ne."

"Malam Sadeeq ko bakazo badai toh kabarni anan."

"No baki isaba ko kuma ki kwanta anan d'in ni saina shiga ciki."

Zama tayi kan kujerar tare da cewa,.

"Tunda waya kakeyi toh ka k'arasa anan idan ka gama sai ka tafi nasan sannan nayi
bacci bazanji tsoro ba."

Mtwww yaja tsaki ta kwanta suna kallo duk sunyi jigum har wajan 1:45am duk ya gaji
ita kuma sai a lokacin tad'an fara lumshe ido ya zaro wayarsa ya lalibi Fateema
amma abin mamaki switch off ya cillar da wayar gefensa yasan haushi taji be kiraba
yanzu kila tana can tayi mai fassara kala-kala. A takaice duk anan falo suka kwana,
haka har yayi kwanaki biyu a gidanta washe gari Sadeeq da Fateema suka wuce kwara
state cike da farin cikin su ita kuma INdo aka turo mata Aminatu ta taya ta zama..

_M fan's kuyi hakuri gobe zakujini shiru zanyi 'yar tafiya insha Allahu dana dawo
zamu d'ora I need ur prayers please._

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu

*Godiya mai yawa tare da d'inbin farin cikina zuwa ga fan's, na gode da addu'o'inku
garemu munje Lafiya mun dawo lafi na gode sosai da sosai.😍 HAJARAH (MUM ILHAM)
godiya mai tarin yawa a gareki domin kin nuna mana soyayya nida 'yar uwata STYLISH
BCH da kuma 'yata IHSAN, Allah ya saka da alkairi ya bar kauna da soyayya Allah ya
raya Ilham👏UMMUL MEENAL, BILLY S FARI & OLO addu'atw gareku bazata fad'u ba sai dai
ince Allah ya baku abinda kuke nema duniya da lahira domin kuna nuna min sayayya ta
hak'ik'a HAJJA CE na sonku fiye da yadda kuke nunan kauna.💋😍💋*

Page *28*

Tunda suka tafi koda wasa Sadeeq be ta6a gigin k'iran INdo a waya ba, bashi dama
phone number d'inta bare yace zai nemeta. A 6angaranta itama bata ko tunaninsa tana
gidanta hankalinta kwance babu abinda yake damunta. Ranar da su Sadeeq suka cika
sati d'aya da tafiya a ranar INdo ta fara fita, kullum tana gidan mak'ota bata nan
layin bata can sam bata zama cikin kwanaki takwas mutanan unguwar sun santa maza da
mata yara da manya. Yayin da a 6angaran Sadeeq yana son ya kirata tunda yasan tana
da hakki akan sa amma baya kaunar ya kirata tayi mai rashin kunya ko ta gaya mai
maganar da zai kasa bacci dan ya lura akwaita da shuka magana ba kuma ta barinta
indai harka gaya mai toh zata baka amsa hakan yasa ya shareta.

Misalin k'arfe hud'u ta fito daga wanka tana shafa mai tajiyo me tallah a k'ofar
gida, cikin sauri ta janyo doguwar riga a cikin wardrobe ta zura tare da d'aukar
mayafi ta fita. A k'ofar gate d'in ta tsaya dan sake tabbatarwa da kunnuwanta
abinda me tallar yake cewa still taji yana cewa.

"A sai kajin gidan gona matasa..!"

INdo tayi saurin fita tare da kwala mai k'ira ya dawo baya kasan cewar harya wuce
gidan nata. Tsayawa tayi suka fara ciniki zata siya har yace zai siyar mata a yadda
cinikin ya tsaya, guda bakwai ta siya ta shiga gida ta d'akko mai kud'in ta bashi
ya tafi ita kuma ta shiga da 'yan kajinta sai kuka sukeyi iya-iya-iya tana ta murna
taje ta zuba su jikin bathroom d'in tsakar gida dama ba'a shigar sa.

A hankali ta ci gaba da kiwonsu tana bayarwa ana siyo mata abincin su hankalinta a
kwance su Haleema idan suka zo suyi ta mata dariya ita kuma tace da tayi kud'i
saudiya zata tafi idan ta dawo a dinga k'iranta Hajiya INdo kasan cewar sunan ya
bazu cikin gidajen mak'ota k'annan su Sadeeq ne kawai ke kiranta da aunty Humairah
kamar yadda marigayi ke fad'a mata.

Rayuwar INdo ta cigaba da canzawa sana'o'i take yi kala-kala kajinta ma sunata


girma har ta samu sun fara kwai tana tarawa taci takai gidan su Sadeeq sai da Mama
tace ta fara siyarwa sannan ta fara.

Da daddare tana kallon arewa 24 Sumayya tana gabatar da shirin tauraruwa taji yadda
wata mata da ake hira da ita yadda rayuwarta ta faro tun daga tushe har yanzu da
takai wannan matsayin nan da nan INdo tayi sha'awar yin karatu itama tana son ta
iya turanci sai dai tayaya zata iya? Sam kwakwalwarta bata gane turanci ba kuma ta
iya rubutawa sannan ba ta iya maida hankali wajan koya tayaya zata iya zama
tauraruwa kamar yadda taga ana haskilo mata masu aji ana kuma alfahari dasu, tasa a
ranta zata fara koyan turanci kamar yadda marigayi yaso tayi kafin mai rabawa ta
rabasu.

Sannu a hankali tana jin takaicin Sadeeq nak'in nemanta tun ranar da Aminatu ta
guntsa mata cewar ai dan batajin turanci ne yasa Yaya Sadeeq cewa baxai tafi da ita
can ba hakan yasa abin ya kuma ba ta haushi tsanarsa ta kuma hauhawa a cikin
zuciyarta dama ya saba yi musu wulak'anci tun a tsefawa.

M.M Haruna English academic taji anata tallar makarantar a gidan redion express, ta
fara tunanin yadda zata yi ta samu shiga cikin ta.

Tanason zuwa tana tsoron kar da taje ta tarrar da garzazzu wad'anda basa Hausa sai
turancin, wai shin ma meyasa aka maida turanci tamkar saukar alkur'ani da komai
za'a ce in zaka yi sai ka iyasa? Ga larabci yaran annabi amma ba a dagewa da zuwa
islamiyoyi ba'a basu muhimmanci kamar yadda ake baya yaran jajayan farar fatar nan.
idan aka kyaro baka iya bama sai ka zama wani hulugu ka zama abin raini da
wulak'anci a wajan al'umma.

Zata yi turanci itama za kuma taje ta koya badan wulak'ancin Sadeeq kad'ai ba sai
dan wata rana itama ak'irata ayi hira da ita a kuma tambayeta tauraronta tace
Abubakar ne,haka zakila kuma a Dama da ita ita duniya wannan burinta ne ba kuma
zata canza shi ba koda Sadeeq zai saketa.

"Hello mubassheer, kana Ina yanzu.?!"

"Ina majalisa ya akayi ta samu ne..?!"

"Kai d'an rainin wayo ne, kazo dan Allah zamuyi sirri."

"Toh aunty Humaira gani nan zuwa amma fa zaki ban jarkar kunun aya guda biyu."

"Dallah idan baxaka zo ba sai na kira khaleefa wallahi."

"Sorry Matar broth ina zuwa."

Kashewa yayi yana dariya sannan ya d'auki abokinsa guda d'aya suka tafi gidan a
mashin. A falo suka zauna ta kawo musu kunun ayar da zobo da jallop d'in taliya
suka ci sukayi dam sannan mubashsheer ya kalli INdo yana cewa.

"Toh meye sirrin Matar broth, tunda kin bamu munci..!"

Sai da ta hararesa sannan tace mai.

"Dallah kaga ni ba surutu na tambaye ka ba, jujun labo store zaka dan Allah ka siyo
min farm (form) d'in shiga makarantar M.M Haruna Englihi menene ma d'ayan na gaban
ma oho na manta."

"Ah Matar broth wai kina nufin shiga zaki yi..?!"

INdo tace "Eh ya ranka? Zakaje kayi min duk abinda za'ayi na fara zuwa kokuwa
wulak'anci zaka yi min Kai ma..?!"

"Ah Matar broth na isa, kawo kud'in toh sai muje muji ya za'ayi, amma tukunna kin
sanar da broth Sadeeq d'in zaki fara ne dan karya zo yayi min masifa."
"Kai zaka siyo min ko kuwa na sake wani?!"

"Ah na isa kawo kud'in muje muji ya za'ayi."

"Toh nawa zan baka..?!"

"Haba ki kawo ten thousand muje mu fara manage dasu."

"Kana nufin nawa kenan?!"

"Kai Matar broth dubu goma zaki kawo naga kina min wani kallo."

"Ta6 goma fa kace? Wallahi ku tafi na fasa ai ba dole."

Ta fad'a tana shiga cikin d'aki Mubasheer ya dinga yi mata magiyar ta fara bada ten
thousand d'in tace ta yafe bazata ba sai da yace.

"Toh kawo five thousand, dubu biyar wallahi Matar broth kin fiye san Kud'i da yawa,
duk sati dubu biyar broth yake badawa a kawo miki ga kud'in zobo ga kunun aya ga
gullisuwa da kwan kaji dan Allah mekikeyi da kud'i bayan duk akwai abinci a
gidan..?!"

Dubu biyar d'in ta bashi ya kar6a ya k'irga sannan suka tashi zasu tafi INdo tace.

"Dan Allah k'anin miji a rage sa ido, duk lissafin ka yana kaina toh da ba kud'in
zaka ci naman dakaci a cikin abinci ne? Ko zaka ci harda vegetables d'in ne d'an
rainin wayo."

"Magana ta wuce bari muje mu dawo."

Yana fad'a suka fice ita kuma ta shiga d'aki. Ko Ina tas-tas a gidanta bata barin
k'azanta sannan kullum cikin k'anshin turaran tsinke d'akin yake dan haka INdo tana
samun customers a rana sai ta dura jarkokin zobo dana kunun aya guda d'ari biyu
amma baya kaiwa dare Allah yasanya mata nasibi a ciki.

A ranar bataga Mubasheer ba har kwana biyu sai gashi yazo, tsayawa yayi yace ya
gama mata komai zuwa kawai zata farayi domin sai da ya sanar da abban su ya kuma
bada goyan baya sosai. Juma'a na zuwa ta fara zuwa cikin tsoro da fargabar yadda
zata tun kari malamai da d'alibai dan tasan duk sun fita k'ok'ari.

"Matar broth ga class d'inku nan."

Mubasheer ya fad'a yana nunawa INdo ajinsu. Ido ta dinga kwalowa waje hannun ta na
dama dafe da k'irji ta kalli Mubasheer cikin tsoro tace.

"Anya bazan koma gida ba, Mubasheer tsoro nakeji wallahi."

"Kai Matar broth wallahi karkiji tsoro kowa fa da kika gani zuwa yayi a koya mai,
idan kika nuna musu kina jin tsoro zasu raina ki kedai karki fasa yin abinda kike
so ki shiga kawai."

"Toh bari naje idan mun tashi zan yi maka waya kazo ka maidani gida."

"Toh Matar broth Allah ya bada sa'a."

A hankali INdo ta shiga tashin farko ganin yadda hall d'in yake yasa gabanta bugawa
da k'arfi sannan ga d'alibai nan a zazzau ne duk sai ta daburce ta rasa inda zataje
cikin sauri ta juya zata fita sai taga Mubasheer a tsaye yana dariya, cikin
tsananin jin kunya tace.

"Maidani gida bazan shiga ba."

"Hahaha...! Wallahi babu inda zaki, muje na shigar dake haka kurum dan ayi asarar
kud'i sai da aka gama komai zaki wani ce kin fasa."

Yana gaba tana bayansa har ya k'arasar da ita tsakiyar kujerun sannan yayi wa wata
budurwa magana cewar gata nan dan Allah ta fara helping d'inta ta wasu abubuwan.
Karimatu tayi murmushi tare da mik'awa INdo hannu suka gaisa ta zauna a d'ari-d'ari
kamar munafuka sai wulkita idanuwa take a haka Mubasheer ya barta yayi tafiyarsa.

Malami na shiga ta fara sunkuyar da kai, nan aka fara gabatar da lesson kasan cewar
ajin masu koyan turanci ne hakan yasa komai ake yi musu dalla-dalla cikin hikima da
kuma kwarewar malaman ita dai INdo tayi tsit bata ko kwakwaran motsi dan karma
malamin yayi mata tambaya koya saka mata ido. Alhamdulillahi kuma ta tsinto abubuwa
kasan cewar sai anta maimaita musu abu anji kowa ya gane an kuma fahimta sannan
za'a shiga wani abun haka aka dinga yi musu tana kuma zuwa duk juma'a asabar da
lahadi da safe.

****

Wata d'aya da sati biyu su Sadeeq sukayi a kwara state sannan suka juyo suka dawo
kano. Lokacin satin INdo biyu da fara zuwa makaranta, sam bata yi wani murna da
dawowarsa ba sema haushi da takaici dataji. Sai da yayi kwana biyu a gidan Fateema
sannan ya waiwayo yau zaije gidan da INdo take.

K'ofar gidan ta tsaya wajan k'arfe sha biyu na dare, key d'insa na gidan ya zura ya
dan bud'e abu ya gagara sai yahau buga mata tana kwance a kan gado da littafi a
hannunta tana Home work d'in da aka basu, tanaji saidai batasan kowaye ba dan haka
batayi ma niyar tashi zuwa ta gano ba.

Mtwwww yaja tsaki tare da ciro wayarsa ya nemo layin Haleema, mtwww ya kuma jan
wani tsakin jin tana amfani da ita ya sake kiran khaleel cikin sa'a ya d'auka murya
a shak'e Sadeeq tace.

"Dan turo min da number'n Aisha."

Khaleel yace "Yaya bani da ita sai dai ko yah Mubasheer."

"Cene masa ya turo min."

Ya fad'a a dak'ire sabida babu kowa unguwar sai shi kad’ai ga duhu. Yana tsaye yaji
an turo ya kira number'n kamar bazata d'auka ba sai kuma tayi picking tare dayin
shiru dan taji me maganar.

"Ke zoki bud'e min gida kinaji Ina bugawa kik'ak'i zuwa ki bud'e min."

Harzai katse yaji tace. "Waye kai d'in? Wa kuma kake nema..?!"

"Au bakima san waye ba dan rainin hankali Aisha?!"

Tace "Kai kaga k'ila wrong number ne go and check."

Kafin yayi magana ta katse kiran ta cigaba da aikin ta, Sadeeq yabi fuskar wayar da
kallon mamaki ya sake buga gate d'in da karfi cikin jin haushi amma tak'i bud'ewa
cikin 6acin rai ya buga number'n Mama tana bacci Haleema ta d'auka tana dubawa taga
Sadeeq dan haka ta d'an janye wayarta daga kunne da takeyi da saurayinta ta kara
tare da cewa.
"Yaya lafiya? Mama tayi bacci fa."

"Yauwa Haleema kira number'n Aisha kice ta bud'e min gidan Ina waje."

"Okey tom Yaya sai da safe."

Tana kashewa ta kira layin INdo, tana kwance duk tama rasa yadda zatayi Home work
d'inta taga kira ta duba a tunaninta number'n d'azu ce tayi niyar d'agawa tayi mai
rashin mutunci sai kuma taga Mmn dacta da haka akayi mata saving sunan tayi
murmushi tare da karawa a kunne tana shirin gaida ita taji Haleema na cewa.

"Aunty Humairah Yaya fa yana k'ofar gida yace kije ki bud'e mai nidai sai da safe."

"Dama shine? No wonder naji ya fad'a da gadara zoki bud'e min gida, d'an rainin
hankali ai na d'auka harka koma bazaka zo ba."

Hijabi tasa ta d'auki mukulli tayi waje, cire kwad'on (pad lock) d'in tayi ta bud'e
mai ya shigo sannan ta juya ta koma, shi ya bud'e gate din yasa motar sannan ya
rufe gidan ya shiga ciki. Bata falo ya bita bedroom fuskarsa a had'e yana shiga ya
ganta kwance da littattafai a gabanta da biro da alama rubutu takeyi baki bud'e
cikin tsananin mamaki yace...

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

Page *29*

"Aisha wannan kuma books d'in waye kike ta lalatawa haka.?!"

Cikin rashin damuwa tace, "is my own."

"Ooh your own?!"

"Yes..!?"
"Toh zane-zane kikeyi or what.?!"

"Home work nake yi."

Tayi maganar tana sake karkad'a biron hannunta, Sadeeq ya zaro idanuwa yana rik'e
da ha6arsa kafin ya matsa kusa da ita yanan kallon littafin da take yin rubutun
yana jijiga kai ganin note d'in tamkar tafiyar tsutsa wani yayi k'asa wani tsakiya
wani sama ya zauna bakin gadon tare da kallon littattafan gurin ya gansu duk na
turanci. Karo na farko daya fara zama kusa da ita duk da cewar ba kusa da jikinta
ya zauna ba ya d'an bada gap.

'Daukar littafin kusa da ita yazo zai yi INdo tayi saurin janyewa ta 6oye
k'ark'ashin cikinta tana faman harhad'e fuska dan bata son ya kushe mata rubutunta,
ya ta6e baki tare da d'aga kafad’a yana cewa.

"Toh furniture's d'in d'akin kike drawing d'insu ko me kike yi hakan?!"

"A'a ba d'aya malam Sadeeq, makaranta nake zuwa kuma acan ake koya min wannan
karatu."

"Ooh which school ne suka iya d'aukarki a haka Aisha..?!"

Cikin jin haushin sa INdo ta tashi zaune tana kuma 6oye book d'inta tana rurufe
idanuwa tace.

"Dan Allah malam Sadeeq ka kyale ni haka nayi abuna ka takura min, neman ilimi naje
yi sai yanzu Allah yayi zanyi, lokacin da marigayi dacta yana da rai bashi da wani
buri daya wuce yaga nayi karatu amma kai sai afkin yiwa mutane gori toh nima na
shiga school yanzu zan zama tauraruwa wata rana so what.?!"

Sadeeq ya tsaya kallonta, sosai tayi k'iba tayi bulbul da ita tayi fresh, duk da
Cewar sleeping gown ce a jikinta kuma me d'an kauri hakan be hana bayyana yadda
cikar halittar k'irjinta bayyana ba, Sadeeq ya d'auke kansa tare da ta6e bakinsa
yace.

"Kinyiwa kanki gata kuwa Aisha, sai dai nasan zaki sha wahala tunda ba iyawa kika
yi ba tun farko sai yanzu ne kika fara, shin waye ya kaiki school d'in and waye
yake biya miki kud'in?!"

"I am, kasan ance sa kai yafi bauta."

Ta fad'a tana jin tsoran kartaje ya gwasaleta yace ba haka zata ce I am ba, sai
kuma taji yace.

"Good hakan ma yayi kyau, but zan cigaba da biya miki ai ilimin yana da dad'i nan
gaba zakiji dad'insa idan kika yi."

"No kabar abunka zanyi abuna da kaina, ko ka manta sabida rashin Ilimi na yasa kace
ba zaka tafi dani inda kukaje da Fateema ba? Hmm! Allah yaji k'an dacta na, cewa
yayi wallahi babu inda baxai iya shiga da niba dan har gaban Obama zai iya zuwa
dani kuma yace matarsa ce. Ka tashi ka tafi ka kwanta ni bacci nakeji."

Tayi maganar tana share hawayen daya fad'o mata. Kallonta yayi tsab yaga ta tsuke
fuska bayan ta goge kwallar sannan yace.

"Aisha ki lalla6ani, wallahi Zan iya hanaki zuwa school d'in inga ta tsiya dan dama
baki gaya min ba ai kika fara zuwa."
Tace "lallai malam Sadeeq, ai wallahi tallahi sai dai ka sakeni in tafi gida dama
baka sona nima bana Sanka kaga sai kaje kaji da matarka Fateema nima inje inyi
karatuna so what."

"Wato har yanzu baki da kunya ko Aisha? Wallahi zaki sha mamaki na."

Ya fad'a tare da barin d'akin cikin sauri ya koma falo yana jin wani mugun 6acin
rai, ko wane munafikin ne yazo ya gaya mata wannan maganar, wannan yarinyar idan ta
kuma wayewa sai tafi k'arfinsa gara ma ya togeta daga makarantar ya sanyata
islamiya ko zata dinga rissinawa.

***
Washe gari yana farkawa ya fito yayi hanyar bathroom d'in tsakar gida, yana zuwa
yaga kaji gaba d'aya gurin ya zama tamkar dama dansu yayi, cikin tsananin mamaki ya
fara tunanin toh kajin waye ta kar6o haka dan wulak'anci ake 6ata mai gida. A
fusace ya koma ciki ya nufi bedroom d'inta, tana kwance sai shak'ar bacci take tayi
d'ai-d'ai da ita books d'in wasu sun fad'i k'asa wasu kuma ta dannesu ya k'arasa
kusa da ita cike da masifa zai tashe ta yaga abunda yasa shi saurin shigewa toilet
d'inta yana dafe k'irjinsa.

Ya dad'e a tsaye kafin yayi alwala ya fito beko kalleta ba ya fita falo yayi
sallah, yarinyar akwai d'aukar hankali komai nata a wannan stage d'in ya cika yaja
tsaki tunowa da yayi sanda take zuwa da yagaggun kaya ya kwanta akan doguwar kujera
yana sauke numfashi.

Jiyo motsinta yayi sai da ya d'an dad'e har gari ya fara wayewa sannan ya mik'e ya
shiga cikin bedroom d'in nata. Tararwa yayi tana k'ok'arin fitowa suka yi karo da
goshinan su INdo ta dafe gurin tare da fad'in.

"Kai-kai-kai..!"

Shareta yayi domin shima sauran k'iris yayi wai-wai-wai sabida tsabar zugi amma ya
maze.

"Ke meye wancan a bayin waje.?!"

"Ina kwana?"

Itama ta fad'a kafin ta bashi amsar daya tambaye ta, a ciki ya amsa bata damu ba
tace.

"Kaji nane."

"Wai Aisha haka kikeyin duk abinda kika ga dama ne? Yanzu me kikeyi da kaji.?"

"Masu kwai nefa malam, idan suka yi kwai nikuma sai na siyar, ance macen da bata
sana'a aurace toh ni Ina yi kuma da kud'ad'an na shiga makaranta nayi kud'in napep.
Malam tunda ka dawo baka ce INdo sau nawa kikayi rashin lafiya ba amma sai tambaya
ta kakeyi abubuwan k'aruwata."

Shiru yayi domin tafishi gaskiya kuma sam beyi tunanin tambayar tata ba dan haka a
wannan maganar yaji kunya, amma dan ya raina ta sai cewa yayi.

"Toh dama ke kina rashin lafiya ne? Naga tunda ban ta6a jin ance kinyi cuta ba,
kuma da kinyi toh Abba zai gaya min."

Shiru tayi ta shiga kitchen, indomie ta jik'a sannan ta jajjaga kayan miya ta ajiye
tare da komawa cikin d'aki yana zaune a falo yana waya da Fateema ta sharesa dan
sam batajin haushi bare ya d'aga mata hankali. Sai da ta dubi lokaci tasan indomie
d'in ta jik'u sannan ta shiga kitchen ta soya ta dafa tea ta kawo kan center table
ta ajiye da kofu na guda biyu ta zauna tare da cewa.

"Ga abinci malam Sadeeq."

Lokacin sun gama waya yana chatting ya kalleta ya kalli agogon dake kafe a falon
yaga k'arfe bakwai sauran minti uku, yanzu ne za'ayi breakfast sai kace ba yanzu
aka tashi daga bacci ba yace.

"Tun yanzu ake yin karin kumallo.?!"

"Eh ai garin ya waye malam Sadeeq me zamu jira."

"Aci lafiya toh."

Ya fad'a ta kallesa cikin mamaki sannan ta fara had'a tea d'inta, ta iya cin
abincin kuwa kad'an kad'an harta gama ci yana satar kallon ta. Tana gamawa taje ta
fara dafa zo6on ta kasan cewar ranar Monday ce batada school ta wanke ayarta tana
jiran lokacin da almajirinta zai zo ya kai mata markad'e.

Shima Sadeeq bacci yayi yana jiran lokaci yayi ya tafi gidan Fatima yayi wanka dan
zaije lecture. Bata tashesa ba sannan duk batasan zai fita ba domin be sanar mata
ba har tara da kusan kwata sannan ya farka yana duba agogo yaga har lokaci yayi da
sauri ya mik'e ya d'auki mukullin motarsa, beyi mata sallama ba kawai sai tashin
motarsa tajiyo taja tsaki sam malam Sadeeq bashida mutunci a jerin da ta sanya shi
kenan.

***
Yana zuwa gidan Fateema yayi wanka ya shirya ya tafi, around 12:30pm ya dawo, cikin
murna ta tare sa tare da rungumeshi ya d'agota yana cewa.

"Akwai bayani baby na zauna ki gaya min."

Sakinsa tayi ta k'arasa kan TV stand ta d'akko mai wata takadda, bud'ewa yayi ya
karanta tare da zaro idanuwa yana kallonta cikin murna ya kuma rungumeta yana cewa.

"Woww babyna am so much happy wallahi, kin zama malama sai yau Allah yayi."

"Aikuwa baby kaji yadda naji kuwa, anjima zanje gidan Aisha idan zaka tafi please
zanje kaga mun jima bamu had'u ba."

"Toh kinsan itama ta koma school fa."

"Kai baby shine koka gaya min sai yanzu danace zani gidan?

Sadeeq yace "A'afa nima sai jiya naji kuma kinga ai ban zauna ba sai yanzu, kinga
bani abinci naci."

Tashi tayi ta shiga kitchen yayi farin cikin samun aikinta sosai domin yana son
abinda take so, yana kuma son farin cikinta. Egg into egg ta kawo mai tare da kunun
gyad'a ta zuba mai yasha madara ya zauna a hankali ta dinga bashi harya cinye yasha
kunnun sannan suka ci gaba da soyayyar su tamkar babu gobe har mantawa suke yi da
matsayin INdo.

Bayan yaje gidan Mama ya dawo sai ya d'auke ta suka tafi, gidan cike da masu siyan
zo6o da kunun aya wasu na fita wasu na shiga inji yana tayi mamaki ya cika ransu
sai da suka shiga sannan suka tarar da ita a zaune gaban k'atuwar kula duk wanda ya
bata kud'i saita bud'e tabashi ya tafi, Sadeeq ya shiga ciki ransa a mugun 6ace
shin yarinyar nan meta maidashi ne, wato ma ashe harta zama big hajiya besani ba
Allah ya kaisu dare sai ya 6ata mata rai.

Sosai suka yi hira da fateema ta yadda har ta gano lallai itace star a gurin
Sadeeq, anayin magariba ya maida ita gida wajan k'arfe goma yazo gidan INdo lokacin
tana zaune a falo tana kallon film d'in Basaja na farko.

"Ke Aisha daman haka kika mayar min da gida tamkar gidan kallo? Maza da mata su
dinga min strolling a ciki?!"

Tayi shiru ya kuma harzuk'a ta kuma yi mai shiru ganin yana masifa yasa ta cewa.

"Wai malam me yasa ka tsaneni ne? Nifa kamar yadda bakai kace kana sona ba haka
nima bance Ina sonka ba. Yanzu da yake ita Fateema matarka ce ta so ai d'azu tazo
ta nuna min takardar fara teaching d'inta kai da kanka ka kawo ta sai ni da nake
sana'a a cikin gida da kud'ina amma ka dinga min fad'a kana Sa min ido? Toh ka sake
ni dan Allah ka gani idan bazan rayuwa ba."

"Ni zaki cewa na sakeki Aisha? Toh bazan sakeki ba kuma karna sake ganin wani yaro
ko yarinya sun shigo min gida."

Yana kaiwa nan ya kuma barin gidan sai dai be fita da mota ba, anya ta d'aura a
zuciyarta na cewar bazata denaba tunda taga alamar bakin cikin ganin tacigaba
yakeyi. 11:49pm ta d'auki pad lock zata kulle gidan taji sa daga waje jikin gate
din yace.

"Malama karki rufemin gida."

"Gidan hayan."

Ta fad'a tana shiga falo yayi kwafa tare da shigowa ya rufe. Tuni ta shiga d'aki ya
bita dan sake ja mata kunne kawai ya tarar ta cire riga tana niyar saka ta bacci
hankalinsa yayi mugun tashi ya kasa controlling d'in kansa ita kuwa sam batasan
yana tsaye ba saida ta gama saka rigar ta tashi tsaye domin da a zaune take ta ta6e
baki tare da hayewa kan gadon.

Jikinsa na rawa dama Yaya lafiyar kura domin yana da tsananin buk'ata tun yana
saurayi bare yanzu domin fateema harta saba da halinsa.

Cikin rawar jiki ya k'arasa kusa da ita kan gadon ya hau sam bata kulasa ba kawai
taji ya janyo ta jikinsa suka fara fad'a Sadeeq yayi nasarar rungumota jinta a
jikinsa yasa jikinsa ya kuma narkewa ya rasa abinda yake tunzura shi duk da irin
naushin da yake sha a gurinta amma yak'i ya saketa.

"Wai meye hakan ne kake yi min."

"Shhhiiii..."

Yace da ita a dai-dai kunnanta, duk k'arfin INdo amma ta gaza kwatar jikinta Sadeeq
ya sake rungumeta jikinsa sai karkarwa yake yi, cikin k'arfi da yaji sai da Sadeeq
ya samu abinda zuciyarsa take muradi a gurin INdo. Jikinta daya raina yau sun had'u
danasa, bakinta da yake ganin koda million d'ari bazai iya ta6awa ba yau sai da
suka had'u danata tana ta kuka ya rasa yadda zai yi a ganinsa tunda tayi aure ta
riga tasan komai be ta6a tunanin zai jita a yadda yaji yanzu ba (k'ila ya manta
suna cikin amarci Allah ya d'auke mata angon domin Abubakar ba kullum yake yi mata
ba wani sa'in making romance kawai zaiyi da ita) INdo cikin kuka tace.

"Tun farko haka zaka ce ga abinda kake so dani bawai ka hanani yin sana'a taba.
Wallahi malam Sadeeq bana sanka duk da a makaranta ance bakyau a gayawa miji haka
wallahi ni bana sonka Allah kuma saiya saka min."
"Please Aisha b..."

"Karka yi min magana tsakani na dakai babu magana daga yau wallahi bazan sake yi
maka magana ba ko me zakayi min."

Ya kasa rik'ota domin daya kai hannu zata yi mai wata uwar mahangur6a takai mishi
naushi da k'afa da hannu tilas yabar d'akin ya koma falo.

"Innalillahi wa'inna 'ilaihir raji'un why? Why? Sadeeq, Aisha ce fa INdo malam
Hamza tsefawa secondary school ita kayiwa haka.."

Da sauri ya mari fuskarsa ya gani wai ko mafarki yake amma sai yaji zafin marin
sannan kunnuwansa na jiyo masa kukanta. Rintsa idanuwa yayi tare da toshe kunnansa
yana faman girgiza kai dan yadda yaji wata bahaguwar kaunarta na tafasa cikin
zuciyarsa yayi saurin tashi tsaye ya shiga d'akin da take kwance ya durkusa saitin
kanta gwaiwarsa a k'asa ya......

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

_Alhamdulillah³ naji sauk'i godiya me tarin yawa ga masoya, naji dad'in addu'@r ku
gareni gashi Allah ya amsa nagode Allah yabar kauna da soyayya._🤲🤝

Dan Allah duk wanda yayi min magana jiya zai ga ban amsa ba wallahi wayar ce
tayi wiping kuyi min afuwa dan Allah, na gode❤

*Today is my daughter’s birthday🎂🔥🎂, Fateema Omar Farooq Pz. Wishing you long life,
Allah ya raya min ita ya shirya min ita ya tsare min ita da duk 'ya'yan musulmai
baki d'aya love you so much my daughter*🎂🔥🎂

Page *30*

Hannu ya kai zai ta6a ta amma sai ya kasa, kallon bayan ta yake yi kawai
zuciyarsa na tsananin harbawa.Tashi yayi ya koma gefen gadon ya d'an zauna a
hankali ya kira sunanta cikin sanyin murya a kuma dai-dai kunnanta yace.
"Aisha bari muyi magana kota minti d'aya ce please."

Motsi INdo ba tayi ba bare yasa ran zata juyo ko ta tashi zaune, yana jin yadda
take sauke ajiyar zuciyar ta amma ji yake tamkar tashi ake bubbugawa sabida
tsananin yadda yake ji. Hannu ya kai ya rik'o kafad'unta ta baya amma ko motsi bata
yi ba ta dak'ire mai daga kwancen sai ya samu kanshi da kwanciya a bayan ta ya
rungumeta a jikinsa tsam amma still bata motsa ba, ya d'ora kansa a wuyanta yana
shafar kitson kanta zanan hannu, nan ma ko gezau INdo bata yi ba.

Duk wani hanyar lallashi da Sadeeq ya sani yabi INdo dasu amma taki motsi duk da
cewar tana numfashi hasalima idanunta biyu amma ya gagara ko mirgino da fuskarta
gurinshi sabida yadda tayi mai taurin kai ta kafe a guri d'aya tamkar mutum mutumi.

"Aisha me yasa bakya jin maganata ne? Shin baki son matsayina a gurinki bane kike
yi min haka? Nace ki tashi dan Allah zamu yi magana kinji ko..?!"

Wayyo Allah..! ko pillow'n kanta be motsa ba bare ta mik'e, Sadeeq yayi ya kad'a ya
raya, yayi magiyar yayi lallamin tare da lallashi amma tayi gardama. Ya manta INdo
amma yanzu ya tuna ko wacece, ya tuna lokacin da tace ta dena zuwa makaranta kuma
hakan aka yi ta dena zuwa sai da taji labarin ana bada kyauta sannan ta fara zuwa,
ya tuna lokacin da tazo dan samun kyautar atamfa bata yanke farce ba ya hanata tace
ta dena zuwa k'arshe ma ta yi hijira daga kauyan sani zuwa kauyen saye bata dawo ba
sai da marigayi yaje ya dawo da ita. Wannan suna d'aya daga cikin taurin kanta daya
sani dan haka yanzu ya zai yi mata gashi zuciyar sa na buk'atar kasancewa tare da
ita, shin me zai yi mata ta huce gashi tace bazata sake mai magana ba, meya kai shi
haike mata bayan duk basu shirya yin hakan ba daga shi har ita.

"Ya ilahi...!"

Ya fad'a cikin zuciyar sa. Har kusan k'arfe biyu na dare yana kusa da ita, haka ya
gaji ya mik'e ya shiga toilet wanka yayi sannan yayi alwala yaje falo yana fita ta
sakko daga kan gadon ta rufe d'akin tamkar dama jira take yi. Yana shimfid'a
sallaya yaji ta rufe ya kalli k'ofar cike da mamaki kafin ya tayar da sallah. A
ranar Sadeeq be runtsa ba ya dinga sak'e-sak'e da neman hanyar dazai sassauto da
zuciyar INdo, har yayi asuba a gurin sannan ya samu 6arawon ya sace sa bayan ya
gama samun mafita.

INdo kuwa tana kulle k'ofar ta hau kan gado sai kuka take yi, tasan yayi mata ne
dan mugunta amma tayi alk'awarin ba zai sake ta6a ta ba bare har yayi gigin yi mata
wani abun. wata sabuwar tsanarsa ta kuma shiga cikin zuciyarta.

Sai da asuba sannan tayi wanka tayi sallah duk a nan cikin d'akin sannan ta koma ta
hau gado dan ta san yana nan kuma idan ya ganta zai iya yi mata magana abinda ta
tsana yanzu kenan ko kallen ta bata son yayi.

Misalin k'arfe bakwai na safe ya nufi d'akin ya bubuga mata amma tak'i bud'ewa haka
ya hakura yabar gidan kasan cewar yana da lecture da k'arfe takwas. Tana jiyo shi
ya fita ya rufe gate tayi saurin hantsilowa daga kan gadon taje ta gark'ame gidan
da padlock sannan ta koma falo ta zauna sai zabga tsaki take tana harara-harare
tamkar ance mata yana gurin ranar bak'in ciki ya hanata yin zo6o da kunun aya sai
gurin kaji da taje ta kwashe kwan da suka yi.

***

Shi kuwa Sadeeq yana zuwa gidan Fateema yasa key ya bud'e, shiga yayi a kwance ya
tarar da ita tana ta bacci ya lalla6a ya kwanta a bayanta tare da shiga cikin
bargonta ya rungume ta tsam a jikinsa yana cizon lip's d'in sa tare da goga
goshinsa a bayan ta.
Yadda taji ya nanik'eta ne yasa ta rik'o hannunsa da ya mak'alota dashi ta d'ora
akan k'irjin ta shi kuma ya matse ta jikinsa sai rawa yake yi. Gabaki d'aya ransa
INdo ce daya rufe ido zai tuno abinda ya faru tsakaninsa da ita, haka ma daya bud'e
idon zai dinga ganinta gashi ya tabbatar da yana da mugun tabo a gurinta. Yanzu ya
zai yi wajan ganin ya wanke kansa a gurinta? sam beyi tunanin cewar hakan zata ta6a
faruwa a tsakaninsa da ita ba sabida tsananin yadda yake ganinta tun zamanin tana
INdon ta ba yanzu ba da ta koma aunty Humarah ko aunty Aisha ba.

Da kyar ya iya shiryawa yaje yayi lecture ya dawo, directly ya wuce gidan INdo,
cikin tsananin mamaki ya tsaya yana kallon gate d'in gidan ganinsa a gark'ame. Mota
ya koma ya wuce gidan su yana tunanin can ta tafi amma abin mamaki sai yaji su Mama
suna tamyarsa ita amma ya maze tare da cewa.

"Tana nan Lafiya lau."

Ya d'an jima a gidan ya mik'e ya fita, Haleema ya k'ira a waya tana d'agawa yace.

"Haleema d'an k'ira Aisha a waya naji ina ta k'iran ta not reachable please yanzun
nan amma."

"Toh Yaya bari naji."

Wayar INdo Haleema ta k'ira, tana d'agawa tace.

"Aunty Humaira ina kika shiga ne keda wayar ki?"

INdo ta yatsina fuska tamkar a gaban ta take cikin takaitawa tace.

"Ina gida.."

"Okey tom shikenan."

Haleema ta k'ira Sadeeq yana d'agawa tace.

"Yaya tana gida wai."

"Okay thanks."

Suka kashe wayar, Sadeeq ya dinga mamaki wato ma ashe tana jin motarsa amma tak'i
bud'e mai lallai yarinyar nan ta mugun raina sa gashi ya kuma siyowa kansa wani
sabon rainin. Juyawa yayi ya koma gidan Fateema yak'i kuma bari ta gano yanayin sa.

Haka Sadeeq ya dinga sintiri a ranar daga gidan Fateema zuwa gidan INdo amma abin
mamaki har kusan magariba bata bud'e gidan ba, sannan ya kirata a waya yafi sau
ashirin amma bata d'aga ba ya san ba k'aramin 6ata mata rai yayi ba.

Har ya kammala kwanaki biyun sa a gidan Fateema INdo bata bud'e gidan ba haka
kuma duk wanda yaje bata bud'ewa. Sadeeq kuma ya rasa yadda zai yi tsoransa d'aya
karta mutu a gidan besan mezai ce ba. 10:35pm yana zaune a falon Fateema ya shiga
cikin tunani yaji Fateema na shafar sajan sa ya kalleta yana murmushi tare da
lumshe ido tamkar ya sha kwaya don sunyi wani iri tace.

"Baby ya kamata ka tashi kaje gidan Aisha dare nayi maka fa."

"Ai bata nan taje garin su."

Ya samu kanshi da fad'ar haka yana kallonta, Fateema tana da kyau sosai domin tafi
INdo haske da idanuwa ga gashi amma cikar hallitta gaba da baya INdo tafi Fateema.
Ya lumshe idanuwa tare da janyo ta jikinsa yana shafar bayan ta, sai dai cikin
ransa so yake yaga INdo kota halin k'a-k'ane amma ya rasa hanya.

Friday morning INdo ta shirya tsab ta tattara littattafanta tasa mayafi ta fita,
bud'e gidan tayi sannan ta rufeshi daga waje ta tari napep ta wuce makarantar M.M
HARUNA. Submitting d'in books na Home work d'in da aka basu aka yi dan malamin ya
duba yana zuwa kan na INdo yaga ba kanta hakan yasa ya kira sunanta da ya gani a
jikin littafin yace idan an tashi taje ta samesa a office.

Hakan kuwa aka yi ta sami M.m harunan a office d'insa ya nuna mata guri ta zauna
yace.

"Aisha Hamza daga wace school kika taho nan..?"

INdo tace "Gaskiya malam ban gama makaranta bani, ni yanzu ne dai nake son yi
sabida gaskiya kaga mijin da aka bani d'an rashin mutunci ne kuma a jami'a yake
koyarwa, nidai malam dan Allah kuyi iya k'ok'arin ku wajan ganin na iya nima shida
matarsa duk malamai ne shi yana min gori kar nan gaba itama tazo ta fara yi min.."

M.M HARUNA yace "Toh karki damu Aisha tunda dai har kinsa a cikin ranki zaki koya
toh nasan ba zaki sha wahala ba, yanzu zaki fara tun daga kan alphabets kije ki
kwafe su cikin note book d'inki gobe ki kawo min ki kuma dinga k'ok'artawa wajan
yin magana da turanci koda kuwa za'a yi miki dariya dan ni daga yauma ki dena min
hausa da yawa understand.?!"

"Toh malam yes."

Ta fad'a tana rufe fuska yayi dariya shima tare da cewa "Good." Littafi ya d'akko
sabo ya rubuta mata from A-Z yace taje tayi irinsu duka. Allah sarki da yake tana
so ba taji wani girman kaiba ta kar6a tana komawa gida a kwance ta tarar da Sadeeq
har ya shigo gidan da yake babu abinsa padlock daga waje, ta wuce cikin d'akin ta
yayi saurin tashi ya bita a baya ya tsaya a wajan wardrobe ko kallansa ba tayi ba
bare ta gaida shi yace.

"Aisha fitsara.., wato ni kika hana shigowa gidan ko? I think nawa ne, koda yake
kin ce gidan hayane amma wayake biyan kud'in gidan.?!"

Ko kallansa ba tayi ba ta zare hijjab d'inta ta ninke tasa a wardrobe taje zata
shiga toilet Sadeeq ya fizgota nan ma tak'i yin magana ganin haka yasa shi fita
yabar gidan, yana tafiya ta kuma kullewa taje tayo fitsari ta shiga kitchen ta dafa
abinda zata ci ta koma falo taci ta k'oshi sannan ta fara assignment d'in ta tana
gamawa tayi bacci bata sake bud'e gidan ba sai washe gari da zataje makaranta.
kullum haka take yi bata bari su had'u dashi kwata-kwata.

Ranar litinin Fateema ta fara zuwa gurin aiki, damuwa da shiga tashin hankali
suka taru suka yiwa Sadeeq yawa ya rasa yadda zai yi da INdo, sam ta dena bari ya
kwana a gidanta sabida da anyi magariba zata 6ame gidan har Fateema ta gano suna da
Matsala a tsakaninsa da Aishan sai dai bata nuna mai san jin abinda ke faruwa kasan
cewar bata son shiga cikin abinda duk be shafeta ba.

****

"Abba wannan karan ina son tafiya da Aisha sai dai tak'i yadda ma muyi maganar da
ita."

"Sadeeq kenan yanzu kai da iyalinka ka kasa shawo Kansu waye toh kake son yaje ya
shawo maka kanta? Duk tsaya ai kaine kafi mu kusanci da ita ya kamata kasan yadda
zaka yi ta yadda har Ku tafi tare."

Shiru Sadeeq yayi ya rasa ya zai yi gashi ranar Thursday yake son komawa, ga
Fateema tunda ta fara zuwa makarantar nan yasan itama ba yadda zata yi ta bishi ba
kasan cewar ya mata alk'awarin idan har takardar aikinta yafito toh zai barta tayi,
gashi bazai iya tafiya shi kad'ai ba tunda ya riga ya saba kasan cewa da mace.

"Sadeeq ya kayi shiru? Idan ita Aishan tak'i binka ba saika tafi da wadda kuka saba
tafiya tare ba."

"Abba ai Fateema ta fara aiki dan tun yanzu ma ta fara nuna k'in bina wallahi."

"Toh ya zaka yi da rashin iya yaren su da ita Aishan bata iya ba? Kar taje tana
baka matsala fah tun da a baya haka kace."

Kan Sadeeq a k'asa yana goga yatsansa a k'asan carpet d'in d'akin, shi kansa yasan
ba zai iya tafiya kwara state ba sai da matarsa a kusa dashi gashi abban da zai
temaka mai shima yace yaje su sasanta da d'aya a cikin su.

"Shikenan Abba zanje na kuma tambayar su, sai da safe Allah ya k'ara girma."

Abba ya kallesa tare da cewa "Amin Sadeeq a gaida min dasu baki d'aya.

Fita yayi ya wuce gidan Fateema ranar ma anan ya kwana. Washe gari ta kasance
Wednesday bayan Fateema ta tafi gurin aiki misalin k'arfe goma Sadeeq ya shirya
cikin wani rantsatsan yadi mai matuk'ar taushi sky blue ya d'ora hula yasa turare
sannan ya fita. Gidan INdo ya wuce yayi niyar yau kota halin k'ak'ane sai ya shiga
gidan ya kuma nuna mata kuskuranta na rainin da tayi masa.

Cikin sa'a ma yana zuwa ya tarar da gidan a bud'e nan da nan zuciyarsa ta sanyaya,
a k'ofar gidan yayi parking sannan ya shiga gida bakinsa d'auke da sallama. Takalma
ya gani a k'ofar d'akin hakan ya tabbatar masa da cewar bak'i tayi, ya shiga ciki
da mamaki sai yaga su Nafeesa, Sagiru da Shehu sai wani wanda besan ko waye ba amma
da alama tare suke.

"Yaya Sadeeq ina kwana?!"

Yaji Nafeesa ta fad'a bayan ta durkusa k'asa, murmushi yayi tare da k'arasawa ciki
yana amsa mata su kuma Su Sagiru ya basu hannu suka yi musabuha.

"Yasu Inna da malam Lafiya dai ko?"

"Lafiya lau, sunce suna gaida kai."

"Ina amsawa yaushe zaku koma..?!"

Sagiru yana shafa k'eya kasan cewar yanzu duk sun girma yace.

"Nan da anjima zamu wuce."

"Okey tom Allah ya kaimu."

Yana fad'a ya wuce d'akin INdo a tunaninsa zata biyo shi irin abin nan na tsakanin
mata da miji da idan ya dawo zata bishi taji abinda yake da buk'ata ko kuma a sake
yin wata special Oyo yon amma yaji shiru sai ma dariyar ta da yake jiyowa ya dafe
goshi tare da rintsa idanuwa daga bisani ya mik'e yabar gidan. Tunda ya fita be
sake dawowa ba sai da akayi magriba sannan ya shiga gidan lokacin bata rufe gidan
ba suna zaune da 'yar mak'otansu Mansura suna kallo suna hira.

Ganin ya dawo ne yasa Mansura tayiwa INdo sallama ta tafi shi kuma ya zauna a falo
yana kallonta. Sanye take cikin atamfa me ratsin green, white, brown, da purple
d'inkin riga da zani sun cika ta sunyi mata d'as tayi kyau sosai ya kalleta amma
ita hankalinta na kan TV, sadeeq ya d'auki remote ya kashe TV d'in tare da kallonta
sai yaga tana kokarin mik'ewa ta shiga d'aki yayi saurin rik'ota ta fara fisge-
fizge zata kwace ya jingina ta jikin bango bayan ya rik'e mata hannuwa.

Murya tamkar ta marayan daya kwana biyu be samu abin kaiwa baki ba Sadeeq yace.

"Aisha what's wrong with you ne ah? Dani zaki yi gaba? Kin manta matsayi na a
wajanki ne? Ko baki san wannan abin da kikeyi min ba kina cikin fushin ubangiji ba?
Please Aisha ki bari mu fahimci juna I beg of you please..."

Still shiru tayi Sadeeq yakai fuskarsa saitin k'irjinta yana goga fuskarsa yaji
tayi magana.

"Wai malam Sadeeq ya haka ne?!"

"Aure ne haka if you don't know."

INdo ta dinga mai-maita if you don't know cikin zuciyar amma ta kasa gane me if
d'in take nufi dan tasan don't know da you dan haka tayi tunanin ko wata maganar ya
gasa mata dan haka ranta ya kuma 6aci ta zabga mai harara yakai bakinsa ta kauda
kai amma duk da haka sai daya laso idon rashin kunyar da harshensa yace.

"Aisha you don't know me shi yasa kike min duk abinda kikaga dama ko.?!"

INdo ta ta6e baki tare da yatsina fuska ta daddage tace.

"Ta6 I know you're noun, ko banda malam sadeeq kana da wani sunan..?!"

"I know you're noun." Ya maimaita a fili yana kallon gefen fuskarta still yana
rik'e da ita a jikin bango ya rasa gane me take nufi hakan yasa shi lek'a fuskarta
yace.

"Mene kuma noun a cikin maganar da kika min Aisha.?"

Ta murgud'a baki tare da cewa.

"Sakar min hannu malam Sadeeq, kace ban sanka shine na nuna maka nikuwa na sanka,
noun is a name of person, animal, place or tins (things) ko ka d'auka yanzu ma
banajin abinda kake fad'a? Never past tense kenan wallahi (Da kenan)."

Sadeeq ya cuno baki, so yake yayi dariya amma baya son yayi taji haushi dan so yake
ya lalla6a yayi mata wayo ya samu ta bishi dan haka ya dinga gumtse dariyarsa ita
kuma tana k'ok'arin kwatar jikinta yace.

"Very Good Aisha you're trying, but kin san menene? Ki shirya kayanki gobe mu tafi
kwara state a can wallahi zaki iya komai domin su basa Hausa sosai kafin kiga
bahaushe sai kin dad'e, muje ki shirya kayan ki sai na taya kima."

Ya fad'a tare da janyo ta jikinsa ya rungume ta. Cikin sauri INdo ta fisge tare da
cewa....
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*THANKS ALL FAN'S, baki, hannu bazasu iya rubuta yawanku ba domin kunada yawa wlh.
Na gode all grps da sukayi ma ihsan wishes. Allah yabar so da kauna.*

_My wattpad so sorry please wallahi nayi nayi yaki yin update kuyi hakuri wallahi
tun safe yak'i yi nasara dalili😪_

Page *31*

"Wallahi ni dai baza ni ba, haba-haba da bakin kafa kace wai ba zaka je dani ba
sabida ni banajin turanci, toh wallahi yasin yanzu dakaji na faraji ba zan bika ba
Allah kuwa."

"Idan nace kuma sai kinje fa ya zaki yi?!"

"Ai karka ma fad'a dan ba binka zanyi ba, kaje ku tafi da Fateema."

"Aisha...!"

Ya fad'a cikin gentle mood wanda yasa INdo saurin kallonsa cikin ido hudu, hannunta
ya janyo yana kallon fuskarta a fili ya fara magana besan ma a filin yake yi ba.

"Aisha My heart is filled with instant joy, you give me everlasting warmth. Aisha
your eye's, your nose, your pretty cheeks your mouth, your chin, the whole of you
all are sweet and so you are. Please Aisha ki bini wallahi babu abinda zan miki
kinji na rantse."

Kallonsa kawai INdo tayi sam duk ta kasa gane abinda yake cewa hasalima dabarbarta
ta yayi kwakwalwarta ta fara hasashe kafin tace.

"Dare nayi malam Sadeeq kaje ka kwanta nima kwanciya zanyi na gaji."

"Toh zaki bini mu tafi d'in..?!"

"A'ah wallahi bance ba."

"Wai me yasa kike da taurin Kai ne Aisha.?!"


"Malam Sadeeq wane kai ne me laushi?!"

Mtwwww yaja tsaki tare da sakin mata hannu yaje ya d'auki mukulli ya tafi rufe
gidan sannan ya dawo, yana dubawa ya tarar ta rufe d'akin ta ya san ko magana yayi
ba bud'e mai zata yi ba kawai ya kwanta a falo. Washe gari yana yin sallah yabar
gidan bayan ya ajiye mata 10k ya tafi gidan Fateema.

Yana zuwa ya tarar harta gama had'a mai kayansa ita kuma tana k'ok'arin shirin zuwa
gurin aiki. Sai da ta temaka masa ya samu relief sannan suka shirya tare suka fito
ta samu napep shi kuma ya Shiga mota yayi gidan su dan yi musu sallama. Suna gamawa
ya juya ya d'auki hanya bayan yasawa ransa cewar zai gwada musu shi d'in namijin
duniya ne sai sun nemesa musamman INdo da bata ganinsa da gashi aka.

**** ****

Bayan watannin uku.

12:30pm tana tsaye a mak'ale jikin bishiyar darbejiya sai makaka ruwan sama ake
yi, ta jik'e tayi sharkaf da ita, ganin tamkar ruwa da iskar yana k'ok'arin jijjige
bishiyar yasa ta ci gaba da tafiya sai faman tangad'i take tamkar ana tura ta, sam
ba tayi tunanin ruwan zai yi yawan haka ba kafin ta k'arasa gida data fito daga
school. Hakan ne ya bata damar tahau napep tayi gidan Asma'u tsautsayi kuma yasa ta
fito tace ita gida zata tafi.

Horn d'in mota taji amma bata juya ba sabida ko ganin hanya bata yi sabida k'arfin
ruwan. Kuma yi mata horn yayi da nufin idan tana son temako idan kuma yayi mata sau
uku toh zai rabu da ita ya k'ara gaba k'ila ba bil'adam bace.

Tana jin ya kuma yi ta fara lalu6en inda taji mutar har Allah ya temake ta ta6ota,
a hankali taje wajan k'ofar ta bud'e a she ta saitinsa ce sai ji tayi ya ce.

"Ke daga ina kike haka..? Ki zagaya ba ta nan zaki shigo min ba."

"I am not ke sir..., I am Aishat Hamza by name so please don't call me ke again..!"

Ta fad'a tare da d'an bud'e ido ta kalli motar, da sauri ta zagaya ta d'ayan gefen
ta shiga ganin Sadeeq ne jikinta sharkaf ya kalleta baki bud'e ta zauna sai ya
kauda kai tare da mik'a mata wani d'an kyalle ta kar6a tana goge fuska dashi kafin
shi kuma yaja motarsa suka fara tafiya a hankali kasan cewar ruwa ake yi sosai
tamkar da bakin kwarya.

"Ke wai daga ina kike haka cikin wannan ruwa?"

"Please sir I told you am not ke, kace min Aisha and daga school nake.."

"K'arya ne ya aka yi banga students ko d'aya ba sai ke kad'ai zaki tsaya yi min
wani turancin banza."

"Hmmm oga Sadeeq you don't know justice is the best policy ko?!"

"Kut..!" Ya fad'a ba tare da ya san ya fito fili ba sabida tsananin mamakin ta da


d'aurewar kai jin abinda take ce mai. Juyawa yayi yana kallonta tana goge fuska ya
cije lips d'insa na k'asa har suka k'arasa bakin gate d'in gidan ta, tayi niyar
fita taji motar a kulle sai ta kallesa tace.

"Malam Sadeeq we are here fa, please ka bud'e min zan fita thanks for the help."

"Karki fito ki zauna a ciki na gaya miki."


Yafad'a tare da zarar mukullinsa na gidan ya fita da kanshi. Kallo tabishi dashi
sai tayi murmushi lokacin ta tuno da Abubakar sam baya d'aure mata fuska tun
lokacin da ya d'akkota daga Saye, yakan yi mata duk abinda zai satayi dariya ko
tayi farin ciki amman wannan gadai kaman nin sak amma zuciyar ta banbanta.

Dawowa yayi cikin motar shima duk ya jiki, shigar dasu yayi har parking lot da
yake k'arami ne dai-dai mota d'aya INdo ta bud'e ta shige d'aki kasan cewar babu
nisa befi taku hudu ba. Shima yana gama parking ya shiga falo bata nan ya wuce
bedroom d'inta, tsaye ya ganta d'aure da zani ta juya baya wanda da alama da taji
motsinsa ne tayi saurin yi.

A hankali ya taka yaje har kusa da ita ya tsaya, matsawa yaga tayi gaba shima ya
matsa har takai k'arshe sannan yace.

"Go on.."

"Aisha you're beyond my control ko meye dalili ne?!"

"Because we don't love each other."

"You dai but me...."

Yayi shiru yana kallon keyarta don har lokacin bata juyo ba sabida wani dalili nata
da bata son ya gani. Ji tayi ya rungumeta ta tayi saurin rintse idanuwa jin yadda
tsigar jikinta ta tashi yarrr yana k'ok'arin d'ora hannun a saman cikinta tayi
saurin rik'e mai hannu.

"Please don't touch me."

"Akan wane dalili? Shin Aisha an hanaki yin yaren Hausa ne?"

Tayi shiru tana kauce mai da sauri ya finciko ta suka fad'a kan gado har zanin da
tayi d'aurin k'irji dashi yana zamewa tayi saurin tashi a firgice shi kuma yasa
hannu ya dawo da ita duk da cewar kayan jikinsa a jik'e suke.

"Innalillahi wa'inna ilaihir raji'un malam Sadeeq ka tak'aita ni k'il...!"

Da sauri ya mik'e zaune jin abinda ta fad'a, itama ra mik'e cikin kid'ima ta sauke
zanin k'asa ya zamana bra ce kawai tayi saura daga cibinta zuwa sama, hannunta a
saman cikinta daya d'an fito wanda ba kowa yake gani ba idan ba kwance pzani tayi
ba ko kuma tasa t.sheet yaga tana shafar cikin bakinta a cune tana shirin yin kuka
yace.

"Aisha what's going on.? Ciki gare..Ki..ne...!"

Bata lokacin da ta d'aga mai kai ba sabida Asma'u tace mata kar tayi abinda zai sa
cikin ya samu matsala yau gashi Sadeeq zai nakasa mata shi. A zabure ya dawo k'asa
idanuwa waje INdo na hawaye ta narkamai harara mai tattare da tsananin bak'in ciki
ya kalleta k'irjin nan fam ya kuma yin kyau cikin in'ina yace.

"How come's daga yi d'aya...?!"

"Ka kaini asibiti nidai, idan ba bakayi ba yau ai gashi ka dauje ni."

Ya akai haka daga one day wanda yasha matuk'ar wahala ace mai tana da ciki ga
Fateema da suka dad'e tare ko 6atan wata bata ta6a yiba amma INdo nada Ciki.., ya
kuma kallonta sai hawaye take yi bayan ta gyara d'aurin zaninta gashi har lokacin
ruwa ake tsugawa Sadeeq ya koma kan gadon tare da zama a bayanta a hankali ya
rungume ta tare da rintsa idanuwansa yana jin wani feelings har cikin k'ahon
zuciyarsa.

"Aisha Allah ne ya baki Abubukar a lokacin da zaku fara sabuwar rayuwa sai ya
d'auke sa ba tare da kowa yasan manufar yin hakan ba, an had'a mu aure ba tare da
muna so ba sai dai ko wannen mu ya d'auki hakan a matsayin kaddara. Aishi kiyi
hakuri ki gafarce ni wallahi ko wanne tafiyar dani nayi tane cikin damuwa da tashin
hankali amma ke babu abinda ya dameki why."

"Nidai ka kaini asibiti kawai dan Allah."

"A cikin ruwan nan? Dama gashi kinje kin kaimin shi ruwa ya jibgeshi k'ilama kinja
mata/masa mura."

Sake rik'ota yayi sosai a jikinsa yana yawo da hands d'insa tayi d'if, ganin haka
yasa Sadeeq matsawa ya kwantar da ita kan gadon ya kura mata kyawawan idanunsa yana
shafar cikin ta a hankali saitin kunnanta yace.

"How many months."

INdo ta kawar da kai tace "Ai bakaso ka dawo ka tarar dani a raye ba malam Sadeeq,
sabida tunda ka tafi ko please call me baka ta6a gigin yi min ba. A gabana kasha
yiwa Fateema waya sabida ita *Son ranka ce* ni kuma *Za6in iyayanka* hakan yasa
baka san komai daya danganceni ba. Duk surutuna wallahi danaga kana yin haka ka
watsar dani yasa nak'i nunawa kowa ina da ciki sai Asma'u da Mama sune kawai suka
sani, sai gashi Allah ya raya ni da abinda yake cikina cikin k'oshin lafiya. Baya
sani wani laulayi yadda neke komai a baya haka nake yi har yanzu.

Malam Sadeeq baka sona sabida kasan cewa ta 'yar kauye, matalauciya, marar Ilimi.
Karka manta Allah dayayo ka cikin wadata bawai yafi sonka bane, Allah dayayo ka
hazik'i fasihi mai d'in bin basira bawai dan yafi sonka bane ko kuma dabarar ka da
iyawarka ba kawai hakan ma jarabawa ce sai gashi kana min gori akan hakan. Shin ka
manta twinnie broth d'inka duk ya fika wannan felek'an amma da Allah ya tashi sai
ya bashini, ya zamto a duniya ni yake so har ya koma ga mahaliccinsa. Shine mutum
na farko daya fara tsamoni daga k'angin wahala da toshewar kwakwalwa Allah ya
gafarta mai haka kuma har cikin zuciya ta yana nan I will never forget
him..never..never...."

"Kiyi hakuri Aisha."

Yayi maganar jikinsa a sanyaye, INdo ta share hawayen fuskarta tana cizon lips,
ruwan da akeyi ne ya haddasa wani sanyi me ratsa cikin tsokar mutum hakan yasa INdo
takure guri d'aya, Sadeeq na ganin haka ya xura kansa cikin wuyanta idanunta a
lumshe yace.

"Aishi kinyi hakuri kin yafe min? Namiki alk'awarin maye miki wanda yafi Twinnie
d'ina, bazaka sake yin kuka dani ba har nima lokacin da tawa zata kasance. Ina son
ki bani dama na shiga cikin rayuwarki nima na d'an yi miki koda rabin abinda
Marigayi yayi miki ne, ina rok'onki alfarma ko yaya ne ki bari muyi rayuwa tare."
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

_Na baku page d'in nan kyauta danjin dad'in ku, *Home of novel, Tsakar Munay,
Zauren Sadeeya, Khadija candy, Rano online, Feedohm novella, Dandalin Billy bilya,
Basma elr Lele grp,* Tnxs n I really appreciate ur love's care's of d comment's_😍👍

Page *32*

'Dan zame jikin ta tayi daga nasa ta kallesa, "shin da gaske ni yake so ko kuma
cikin dake jikina? Anya malam Sadeeq kana sona kuwa? Amma zamu gani idan gaske ne."

"Kin yi shiru."

Dariya ce ta su6uce mata ganin yadda yake kallonta tamkar wani mara lafiya, ganin
tana dariya yasa shi jin wani farin ciki har cikin ransa ya kuma janyo ta cikin
jikinsa yana shafarta, ba zai mata komai ba dan karma tayi tunanin dan hakan yake
sonta yanzu gara ya daure ya hakura ana d'auke ruwa kawai ya gudu gurin Fateema
tunda Allah ya kasa ya bashi biyu.

"Kana ganin yanzu babu abinda ya samu cikina?!"

"Insha Allahu karki damu, ko kina jin wani ciwon ne?"

"A'ah bana jin komai ni sai yunwa."

"Okay sorry bari ruwan naga ya fara d'an tsagaitawa sai na samo miki wani abun
kici. Bafa ki bani amsa ta ba Aisha baki ce kin yadda zaki zauna dani ba."

Dariya da kuma yi tunowa da maganar Asma'u da tace tayi hakuri wata rana sai
labari, shi gani zai yi kamar an shiga rayuwarsa ne shida Fateema amma tunda had'in
Allah ne wata rana sadeeq zai kulata sai so ta koda bekai na Fateema ba tunda har
Allah ya kuma had'a su a bed gashi harda rabo.

"Aisha me kikema dariya ne? Ko gemun dana tara kikewa dariya.?"

"Kai a'ah wallahi ni ina ruwana da wani gemu."

"Toh kina so kenan in barshi yamin kyau?!"

"Lalalah bance ba yadda kagani kai dai, kuma tunda ka barshi ai kowa yasan so kake
yi taya za ai nace beyi maka ba ni INdo."
Tayi maganar tana rik'e ha6arta cikin nuna k'ask'anci dan ta san bata kai wannan
matsayin ba da har zata bashi umarni yabi ba. Yatsansa yasa a goshin ta wajan
billenta yana shafawa ta lumshe idanuwa tana tuno Abubakar sabida duk sanda zai
ganshi sai ya ta6a mata shi, sai dai idan ta d'aura d'an kwali ta cukaro shi ya
rufe shine kawai ba zai ta6a ba.

"INdo malam Hamza...! Wai me yasa ake ce miki haka ne, a memakwan Aishat Hamza."

Ya fad'a cikin wani irin style wanda yasa ta kalli cikin idanunsa shi kuma ya kanne
mata nasa tayi murmushi tare da cewa.

"Haka mutane suke kiran baban mu, toh lokacin da aka sani a makaranta dama kowa
INdo yake cemin banda Inna ita sai dai tace min 'yar nan, shi kuma baba yace min
uwata shine da aka kaini sai aka tambaye ni sunana baban mu yak'i fad'a ni kuma
karna fad'i sunansa sai nace INdo Malam Hamza shine kawai sunan ya zama haka."

"Ummm! Good, toh yanzu kuma fa a school? Ko har yanzu kina nan a INdo malam
Hamzan?"

"No..no..noooo, Aishat Hamza tun lokacin da Mubasheer yaje yamin registration ya


saka min haka shikenan nima na cigaba da sawa."

Kallonta yayi yaji wani mugun tausayinta sai dai shi kansa yasan ya makaro, tun a
baya ya kamata yaji tausayinta amma beji ba ganin batada nutsuwa a memakon ya
tallafa mata sai ya k'ita sam baya k'arfafa mata gwiwa akan sha'aninta amma ya zai
yi da sharrin zuciya dana shed'an, yasan dai marigayi shine ya kwashe ladan gashi
har yau da baya duniya ta kasa manta shi. Yana fatan shima wata rana tayi mai irin
wannan abun ko yana da rai ko kuma lokacin yabi d'an uwansa.

Uban ruwan daya jibgeta ne gashi kuma ya rungemata a jikinsa ta takure yasa wani
daddad'an bacci ya sace ta ba tare da tasani ba. Shima sai da ya janyo ta yaji
jikinta ya saki hakan yasa shi leken fuskarta kawai sai yaga ashe har tayi ya
bacci, ya juya yadda zai dinga kallon fuskarta ya kura mata ido.

Ya dad'e yana kallon kyawunta mai kwantar da zuciya kafin yayi murmushi tunowa da
yayi sanda ta d'auke mai naira d'arinsa daya je siyayya. A hankalli yaka sanya
hannunsa saman cikinta yana shafawa zuciyarsa na tsananin harba mai cikin wani
masifaffan son kasancewa tare da ita ya kai lips d'insa kan nata ya sumbace shi
sannan ya mik'a a hankali ya sanya mata pillow a inda ya tashi tare da rufa mata
lallausan bargo ya mik'e da sauri kasan cewar an tsayar da ruwan har an fara
k'iraye-kirayan sallar juma'a.

Cikin sand'a ya fitar da motarsa sannan ya kulle mata gidan ya tafi gidan Fateema
da zafi-zafinsa. A k'ofar gida yayi parking motar ya tura gate d'in a kulle,
wayarsa ya janyo ya kirata ringing d'aya ta d'aya cikin murna da zumud'i tace.

"Allah yasa dai baby haka zaka cemin ka iso cikin Kano..?!"

Muryasa cikin murmushi yace.

"Fito ki gani ina gate."

Zaro idanuwa Fateema tayi tamkar tana gabansa cikin sanyayya murya tace.

"Baby kadawo kana waje? Please I'm so sorry kaga yanzun nan muka tashi yara sabida
ruwa, dan Allah baby kajira ni in k'araso."

"Okey toh kiyi sauri kinga karna rasa sallahn juma'a."


"Toh godiya nake baby na sai na k'araso."

Sallama tayi da sauran malamai matan da suka fito tare, cikin sauri ta tari Napep
kafin wani sakannin har ya kawo ta. Cikin mota ta tarar dashi ya ziro k'afarsa waje
hannunsa rik'e da wayar marigayi yana kallon pic's d'insa dana INdo wanda yayi mata
tun tana INdo malam Hamza ranar da taso cin atamfa Allah beyi ba, dana d'aurin aure
harda wad'anda suka yi a Munjibur park da wad'anda yake mata a cikin gida sai dai
duk babu hotan banza a ciki Fateema na k'arasawa wajan Motar yayi saurin zura wayan
a cikin aljihunsa.

"Oyo-yo baby nah, taho mushiga ciki."

Ta fad'a tana kallonsa cikin murmushi tare dayin gaba ta bud'e k'ofar gate d'in shi
kuma ya biyo bayan ta. A parking lot ta tsaya yana shigowa suka rungume junansu
cikin nuna kewa kafin yace.

"Bari nayi alwala naje nayi sallah kafin na dawo ki samar min wani abincin kiyi da
d'an yawa za'a kaiwa Aisha na biya naga ashe batajin dad'i."

Kallansa tayi tana dariya tace.

"Wai wannan uban k'asumbar daka tara gashi hardasu gemu duk na meye."

Shafar faskar yayi yana tafiya yana cewa.

"Baby wannan gemun na komai ne wallahi, hmmm danma Allah ya temake ku a iya tara
gemu na tsaya, bari dai naje na dawo please ki d'ora girkin."

Dai-dai lokacin suka shiga cikin Falo ya shiga toilet ita kuma tayi bedroom d'insa
dan k'ara masa k'amshi duk da cewar kullum tana k'amsasa shi. Yana yin alwalan ya
tafi masallaci, ana idarwa ya wuce gidan su suka gaisa dasu Mama tana tayin
murmushi a tunaninta be fara ganin cikin INdon ba tasan zai yi murna d'an k'aniya
da ana bashi yana nuna baya sonta.

****
Yana dawowa ya tarar ta gama dama already tana da miya wadda tayi jiya tasha
kifi sai k'amshi takeyi. Rungume ta yayi cikin tsananin so da buk'atuwa domin da
k’yar yayi sallah banda ta juma'a ce da bazai yi ba sai ya fara samun nutsuwa.
Sannan baya son komawa gidan INdo da wannan matsalar dan kar tayi tunanin hakan ne
yasa shi cewa su shirya yanzu yana sonta, ya fison ya fara nuna mata yanzu ita d'in
yake so kafin ya fara nuna mata ainihin waye shi.

Bedroom suka koma hakan ya tayarwa da Fateema hankali dan tasan a wannan yanayin
ita yak'e muradi gashi ita kuma tana period ya zata yi mai? Ganin yadda yake mata
zafi-zafi yasa ta rik'o hannunsa tare da kwato shi saman k'irjinta murya a karye
tace masa

"Sorry baby.."

"For what.?!"

Ya tambaye ta yana matsar ta da gashin kanta, nuna mai tayi hakan ya tayar mai da
hankali duk iya k'ok'arinta na ganin ya samu nutsuwa abin ya faskar sai da kawai ya
nuna mata yayi normal sabida baya son damuwarta yasan da zata iya d'auke blood d'in
da yanzu tayi.

"Baby Ina abincin Aishan, kawo naje nakai mata zan biya can gurin Anas akwai abinda
zan k'ar6o a gurinsa."
Kallonsa tayi tasan k'ila yaje gurin Aisha, amma a k'a'ida yau itace dashi sai dai
baxata so ta ganshi cikin matsala ba, tayi murmushin yak'e tana shafar gashin da ya
lullu6e k'ewayan bakinsa tace.

"Yana falo na zuba."

Tashi yayi ya mayar da kayansa ta rakosa ya d'auki basket d'in k'irjinta na bugawa
dan tana zargin akwai abinda zai had'asa da INdo amma tasan basa shiri zai iya
sharewa ya jira har lokacin da zata samu tsarki.

"Bye-bye baby ina dawowa zanci abinci nayi bacci dan agajiye nake munyi kwanan
mota."

"Toh sai ka dawo ayi mata sannu, kona zo muje tare?!"

Kallonta yayi na 'yan dak'ik'a kafin yayi murmushi yace.

"Yanzu kika dawo daga gurin aiki, sannan kice zaki fita bayan mijinki ya dawo daga
tafiya me nisa. No ki zauna ki tanadar min dadd'ar hirar da zaki min idan na dawo."

Fateema tayi dariya tare da d'aga mai hannu ya fita tana kallonsa kishinsa fal
cikin k'ahon ziciyarta.

Yana fita ya shiga mota yayi gidan INdo, yana zuwa a bud'e yaga gidan yayi parking
a gefen gidan ya d'auki kayan abinci ya Shiga. Babu kowa har ya shiga cikin bedroom
d'inta bayan ya ajiya abincin a falo. Tararwa yayi ta idar da sallah, ya tsaya a
bayanta yau INdo ce take sallah harda su addu'a, lallai Allah buwayi mai sauyin
lamari kamar yadda ya sauya salon alak'arsu daga malamin ta zuwa mijin twinnie
d'insa daga nan ya sauya zuwa mijinta.

"Humairah."

Taji ya fad'a k'irjinta yayi tsananin bugawa tayi saurin waigawa tana kallonsa ido
waje. Murmushi ya sakar mata tayi saurin d'auke kai dacta ya fad'a mata jin muryar
data fara kiranta da sunan. Anya ba munafuntar ta akayi ba Sadeeq ya mutu aka raina
wayonta aka ce Abubakar ne, anya shima ba yaudararta yake yi ba aka had'a baki
dashi zasu raina mata hankali.

Bata gama dai-dai tuwa ba taji ya zauna a kusa da ita har suna gogar juna ya lek'a
fuskarta tare da cewa.

"Tunanin me kikeyi haka? Ni ko Abubakar."

Ta zame hijjab d'inta ba tare da ta kallesa ba. Shin me yayi mata a cikin rayuwarta
da zata wani dinga tunaninsa, wanda yayi matan ya koma ga Allah ko kuma dan yayi
mata ciki shine zai sa ta dunga tuna sa kila haka yake nufi.

"Okey yanzu bazaki kulani bama.?"

"Welcome back malam Sadeeq."

"Sai da na rok'a, ai ba haka kikewa M twinnie ba oya hug me."

"Kitchen zani mafa ko indomie na dafa, nasan dai kai bazakaci ba."

"I said kiyi min Oyo-yo, kamar yadda kika min ranar danaje d'akkoki kika yi tunanin
marigayi ne, oya am waiting."

Tura baki tayi tana mamakinsa ganin irin yadda dacta yake mata abubuwa tace.
"Ni a'a, ka kyaleni naje wallahi inajin yunwa."

"Na kawo miki abinci, amma sai kin min oyo-yo sannan zan baki."

A hankali ta juya ganin ya takura mata ta rungumesa bayan ta rintsa idanuwa. Jin
k'irjinta a nasa ya sashi jin wani shock ya sanya hannunsa ya mak'alota gabaki
d'ayanta jikinsa ya hau rawa tana jin haka ta kwace kanta ya samu da kyar yajata
suka fita falo.

Da kanshi yaje ya d’akko plate a kitchen ya zuba mata, tunda taji k'amshin kifi
take jin tamkar ta cinye abin miyar ya zuba musu tare sai kallonsa take yi ganin
yanzu yana mata wasu abubuwan da marigayi yake mata hakan kuma ya sa ta d'an sakar
masa tun yana bata a yangance taji ko abinda ke cikin nata besan ana bata abinci ba
yasa ta cewa.

"Kawo ni na dinga baka gaskiya."

A tunaninsa ko ta fara sonsa yayi murmushi tare da sakar mata spoon da pork d'in,
idan ta bashi sau d'aya sai tayi kusan spoon biyar sannan zata kuma bashi, ya dinga
bin fuskarta da kallo yana jin wani abu tamkar magnet yana fisgarsa. Sai da suka
k'oshi sannan ta kwashe kwanukan takai wajan wanke-wanke yana binta da kallo duk da
cewar doguwar riga ce a jikinta sai dai komai na jikinta rawa yake yi Sadeeq ya
jingina da kujera shi kam bazai iya kwana a haka ba, tunda yasawa ransa idan ya
dawo zai samu nutsuwa koda a gurin Fateema ne toh gashi tana off yayi 3mothns a
wahale bazai iya kwana haka ba.

"Sir Sadeeq na gode sosai, a cewa Fateema itama na gode ga kwanukanta."

INdo ta fad'a tana k'ok'arin ajiye kwandon akan center table. Shi kuwa tamkar me
bacci haka yayi nan kuwa yana kallonta ta k'asan ido yaga tana kallonsa jin yayi
shiru yasa ta shiga d'aki ta zauna a bakin gado tare da d'akko jakar makarantar ta
ta fito da books d'in wanda duk iya kunshesun da tayi a jiki saida ruwa ya ta6a su
ta bubbud'e su akan gado tana turo baki ganin duk sun sha ruwa.

Ta bayanta taji ya rik'o ta, sharesa tayi ta cigaba da hura book d'in hannunta da
baki ya sa hannu ya k'ar6a ya ajiye akan gadon ita kuma ya jata suka kwanta akan
gado INdo tace.

"Ana k'iran sallar la'asar."

"Uhmm naji Humaira but I need your help please."

"Tofa name.?!"

"I need you, dan Allah humaira karki min wata fassarar karki hanani ina cikin
matsala humaira wallahi I love you... I love you Aisha karkiyi tunanin kodan wannan
abun ne."

Jikin INdo yahau rawa ta fashe da kuka tana jin yadda yake mata amma ta kasa hanasa
domin tana jin hirar matan ajinsu akan mazajen su. Shi kuma jin bata yi masa irin
na farko ba yasa shi cikin karyar da kai da nuna tsantsar nadama yasa har ya cinma
muradinsa akan ta sannan shima yahau yin nasa hawayen.

_"Twinnie kasan nifa ni bazai yuwu nazo gidana naga matata ba sannan na kyaleta ba
no Zuciya ta baza ta bari bama tunda nasan mallakina ce."_

Ya tuno irin hirarrakin su da Abubakar cikin shak'kk'iyar murya Sadeeq yace wa


INdo.
"Skukran-laki Aisha Humaira. Do you love me? Please humaira love me as I love koda
na iya yau ne kawai."

"Malam S.."

Ya rufe mata baki da nasa cikin son katse ta da sunan da yaji zata kirasa sannan ya
cire yace.

"Don't call me malam again. please change my name in dai har kin yadda zaki soni
kamar yadda kike son twinnie d'ina."

Hannunsa zagaye da wuyan ta suna had'a numfashi INdo tace.....

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

Page *33*

"Toh mezan ce maka? Kaga kaima Fateema ka fara aura, kuma ita kake so kafin ni. Toh
nima ina sonka amma nafison marigayi dacta nima kaga ma an raba kar wani yaji
haushin wani."

Fuskarta yakai dai-dai tata ya had'e hancinsu guri d'aya yana rik'e da hannunta
yace.

"No Humaira wannan ba magana bane har yanzu ke yarinya ce. Idan nace zan dinga nuna
miki soyayyar Fateema a fili zaki sha wahala tunda kinga ina nuna mata itama zata
fallasa nata. While ke kuma idan kika ce zaki fifita soyayyar m twinnie a gurina
babu abinda zanji sabida yadda muke dashi kuma baya raye bare ya dinga rama miki
kamar yadda zamu yi nida Fateema a gabanki. So kidena kawo wannan abun a ranki
yanzu ni zaki saka a cikin zuciyarki ba wani ba."
INdo ta juya baya tare da cewa.

"I love him tayaya zank'i fad'a kawai dan ya mutu? Dama haka soyayya da amana take
idan ka mutu a shafe babin rayuwarka? No gaskiya nayi mai alk'awarin bazan manta da
shiba har k'arshen rayuwa ta."

Rintsa idanuwa Sadeeq yayi, sam


Baiyi tunanin zaiji kishi haka ba amma yaji ransa na sosuwa jin yadda take cewa
tana son wani mamaci ba shiba. No wonder mutane suke tsoron auran matar mamaci
sabida koyaya zaka yi mata abu sai ta fad'esa ta nuna maka yafika, shi kam ya shiga
uku gashi wani sanyayyan sonta sai sake shigarsa yake. Ba shakka indai haka
Abubakar yaji a baya dole ya rikice yace yana sonta a duk yadda take, dole ya kira
ta zuciyarsa sabida yadda a yanzu ta kuma shiga cikin tunanin Sadeeq d'in.

"Juyo toh kiji."

Yayi maganar yana kallon bayanta, a hankali ta juyo sai dai idanunta a kulle suke
gam yace.

"Zaki bini idan zan koma kwara state? Karki ce min a'a kinga ina son hakan so nake
na shirya yadda zanyi tun daga yanzu."

"Kai karatuna fa?!"

"Karki tashi hankalinki kina dani zan dinga yi miki wannan makarantar duk k'aryar
banza ce. Ki bini kigani zaki sha mamaki in a few days."

(Kunji wayo... Wai makaranta ce karyar banza dan kawai yana son yi mata wayo
maxa..maza mutanan mu).

"Amma kuma fa malam Sadeeq..."

Yayi saurin katseta bayan ya janyo ta jikinsa yana zagaye hands d'inshi a k'irjinta
yace.

Shhhii “ba anan zaki dinga kirana malam ba sai munje teburin d'aukar darasi but
wannan gurin kam ki dinga kirana da wani sunan special da zai zama kene kike
k'irana dashi”

“Kamar irin su honey, sweetie, heartbeat, July juice, mango, touch light, tomato,
vest....."

"Ke.. Ke..! Uhm..uhm duk wannan sunan fa, na waye ne.?!"

"Toh ai lissafo maka nakeyi sai ka za6a a ciki."

"Shine harda su July juice, vest, tomato? You ko.."

Ya fad'a tare da ja mata hanci tayi dariya har hak'oranta suka fito murya k'asa-
k'asa tace.

"Ashe kaima wata ran kanada kirki..?!"

"Eh dama kece bakya lura but yanzu ai kin fara gani, tashi muje muyi wanka gashi
bamu yi sallah ba."

"Toh amma ka fara yi."

"A'a tare xamuyi tunda komai tare muke yi."


"Innalillahi nidai gaskiya ka fara zuwa ka yi."

"Yauwa kin tuna min ma, baki gaya min ba zaki bini muje? Kinga a lokacin nake son
dana koma na sake bud'e wani gurin kema ya kasan ce idan muje kina da naki d'akin,
bana son business a nan sabida sa ido da nan kawai zan dawo gabaki d'aya."

Shiru INdo tayi dan a gaskiya bata son zuwa garin tunda yanzu ta fara iya
turancinta, itada ba kwarewa ta gama yi ba kawai ya jata su tafi sai sun je shima
ya sauya mata tana tsoron Allah tana tsoron butulcin d'an Adam.

"Tunda ba gobe zan tafi ba zan kyaleki kiyi shawara kinji?!"

"Toh."

Ta fad'a ya mik'e ya shiga toilet ya tarar musu ruwa ya dawo, da kyar ta bari suka
je wanka suka yi tare duk da dakyar ta tsaya.

Sai da suka d'auro alwala sannan suka fito yana rik'e da ita duk asan samunsa na
ganin ta aminta dashi ta saki jiki ta kuma yadda da shid'in me sonta ne da gaskiya.
Riga tasa ta atamfa da skirt sannan ta shimfid'a musu sallaya ta bishi da kallo
ganinsa a zaune bashi da niyar sa kaya tace.

"Sallan fa, kona yi tawa?!"

Ido ya lumshe tare da hura iskar bakinsa yace "wane kayan zansa.?!"

"Lallai ni ina na sani, ai kasan fa ko hularka babu a cikin gidan nan. Nidai bari
nayi tawa sai ka tafi gidan Fateema kayi acan."

Tana fad'a ta fara k'ok'arin tayar da sallah ya mik'e tsaye tare da tsayawa a
gabanta yace.

"A'a bari nasa riga ta ai doguwa ce ta rufe min gwiwa."

"Nashiga uku haka zaka yi babu wando ji kafafuwa a waje a haka zaka yi sallan? Oh
ni INdo..."

"Eh aini an hallarta min yin hakan kune dai aka haramta muku yin sallah idan baku
lullu6e jikinku duka ba, Allahu akubar²."

Taji kawai ya tayar. A ranta kawai ta barsa dan tasan sallar malam Sadeeq bata
kar6u ba. Suna idarwa sai ga su Haleema tayi sauri zata mik'e ta fita Sadeeq ya
rik'ota suka yiwa juna kallon ciki ido.

"Ina zaki?"

"Su Haleema nefa ba kaji muryar su ba."

"Naji amma ai baki tsaya kinyi addu'a ba kamar d'azu, zo kiyi addu'a sai ki fita
gurin nasu."

Komawa tayi ta zauna su kuma sai rangad'a sallama suke yi jin shiru yasa Aminatu
lek'awa d'akin.

"Au ashe sallah suke yi Yaya ma nanan."

Guri suka samu a falon suka zauna suna jiran fitowar su. Matsawa yayi kusa da ita
tana addu'a saitin kunnanta yace.
"Kiyi mana addu'a, amma dan Allah karki rok’ar min mutuwa da gaggawa."

Bata juyo ba tayi murmushi jin abinda ya fad'a. Shi kuwa tsoran irin addu'o'in da
takeyi mai a baya ne yasa shi fad'ar haka yanzu tunda sun fara shryawa . Kuma
mik'ewa tayi ya janyota tare da waigawa yana kallon k'ofa sannan ya sumbaci saman
lip d'inta ta fita.

"Aunty Humaira ya gida??"

Ta zauna tana kallon Haleema sabida itace me kallonta tunda ta fito, INdo tace.

"Ke wai meye ne? Sai wani kallon tuhuma kike min."

"Kai aunty Humaira, missing d'inki nayi fa kinsan kwana hud'un nan duk a cikin
hostel nayi su, bama haduwa sai naji kamar shekara nayi ban ganki ba."

"Oho ni kuwa banyi wani missing d'inki ba sabida kullum idan baki zoba bacci na
nakeyi."

"Aisha.."

Sadeeq ya kira ta ta mik'e taje d'akin. Tsaye ta gansa yana gyaran hular kansa ta
d'an tsaya nesa dashi ya janyo ta yace.

"Zan fita anjima zan zo muyi sallama."

Tace "Toh sai kazo."

"Is this all abinda zaki ce min?!"

INdo ta d'an kallesa kafin tace.

"Toh kayi shaving wannan gemun yayi ma yawa."

"Sunnah ce fa cutie amma tunda bakya so zan cire."

"Toh sai ka dawo."

"Kin gaji ne? Na tafi na baki guri ko?"

"Ah kawai kaga dai su Haleematu na nan."

"Okey bari naje na dawo, give me good bye hug."

Ya fad'a yana bud'e mata hannuwa, ya zata yi dole taje ta rungumesa ya matseta a
jikinsa kafin ya sake ta suka fito tare, 'yan k'annan nasa suka gaidashi sannan ya
fita ita kuma ta zauna gurin su suka sha hira har Aminatu ta dafa musu Indomie suka
ci.

Sadeeq kuwa gidan Fateema ya koma, tare suka yi sallan isha sam be nuna mata cewar
gidan INdo yaje ba nuna mata yayi yana kai abinci gurin Anas ya wuce. Suna idar da
sallahn isha'i yace mata.

"Baby na bari naje can gidan nayi mata saida safe, daga can zan tsaya nayi aski ki
dafa min tea kafin na dawo."

Fateema da shagwa6a tasan yana son shagwa6a tana jikinsa a tsaye tace.
"Gaskiya Baby karka yi aski ni dai ka barshi ina son shi yayi ma kyau."

Idanuwa Sadeeq ya zaro jin ita kuma abinda tace, INdo tace bata so ita kuma tace ya
barshi tana so ya shiga uku.

"Menene naga ka zaro idanuwa haka? Shikenan jeka aske tunda baka son ka barmin kuma
ina so."

"Ah baby na isa, tunda kina so ai dole na barshi uwar gida sarautar gida. Bari toh
naje na dawo."

Fateema tayi murmushin jin dad'i ganin yana yi mata duk abinda take so. Sai da ta
raka shi har gate ya juyo yana kallonta bayan yayi kalar tausayi yace.

"No bye bye kiss ko? Shikenan nayi fushi."

Da gudu ta rik'osa ganin zai fice tana dariya ta kamo wuyansa ya sunkuyo da kansa
tayi kissing d'inshi tare da cewa.

"Sai ka dawo karka dad'e."

"Okey as you wish baby."

Sannan ya fita yana tunanin yadda zai yi musu. Su Haleema kuwa Sai wajan k'arfe
takwas na dare sannan suka tafi gida ya rage sai INdo kawai tayi sallahn isha'i ta
cigaba da gyaran littattafanta.

Jam-luck tasa hakan yasa yana sanya mukulli k'ofar ta bud'e. Shiga yayi tana jin
motsinsa tayi saurin kwanciya tayi baccin k'arya. Kallonta yayi ganin yadda ta
kwanta akan books d'in gashi ta kudindine fuska cikin bargo, ya k'arasa kan gadon
tare da sanya hannu ya cire mata shi daga fuskar ta.

"Oh harma bacci kika yi bayan nace miki zan dawo ko?!"

Yayi maganar cikin kunnanta, INdo tayi mik'a alamar wai ya tashe ta sannan ta fara
mistsike idanuwa murya a shak'e tace.

"Au ka dawo?!"

"A'a ina can."

Ya bata amsa yana kallon fuskarta ta wani maze tamkar daga baccin gaske ta tashi.

"Shikenan sai da safe in tafi..?!"

"Eh sai da safe amma 8:00am zan tafi makaranta fa."

"Ba nace kin dena zuwa ba?!"

"Kai malam Sadeeq weekend fa nake zuwa ita kuma Fateema yau da gobe bata da aiki
kuma dama acan kake toh kaga ai ba abin hanani zuwa, ni dai gaskiya zani Ina son
school d'in gashi malamin shima yana son yaga na iya wallahi yana da k'irk'i yana
sona."

"Yana sonki kuma?!"

Cewar Sadeeq a mamakance, cikin rashin fahimtar fassarar dayayi ma maganar INdo
tace.
"Eh wallahi har extra lesson yake min."

"What...!"

"Kai malam Sadeeq dafa ace bankai kaina wannan makarantar ba da nasan wallahi har
yanzu baxakai marmarin so naba. Toh meyasa yanzu na shiga kake kuma k'ok'arin
rabani da ita bayan akan rashin iyawa t...."

Be bare ta k'arasa magana ba taji bakinsa cikin nata. Irin deep nd passionate
kissing d'in nan ya dinga tura mata har jikinta ya kasa d'aukarta ta shiga biye mai
ba tare da tasan ta iya hakan ba. Cikin rashin sani suka sake kasan cewa da juna
musamman Sadeeq da sai da ya jima sannan ya gano da tabbacin abinda ya sake faruwa.

"Na barki... Na barki Humaira kiyi karatunki zan cigaba da baki nawa gudun mawar
insha Allahu. I love you with all my heart and soul Aisha please say you love me
dan Allah...."

Shiru INdo tayi ta kasa fad'a ji take yi tamkar idan ta fad'a tayi k'arya dan
bataji wani love dinsa ba dazai iya sawa ta gaya masa.

"In tafi bakya sona ko?!"

"A'ah ni bance ba, amma ka tafi dare nayi Fateema na jiranka."

"Aisha bakya sona ko? Shikenan."

"Toh ina sonka, aini bance bana sonka ba."

Agogo ya duba yaga sha biyu saura minti goma, da kyar ya tashi ya sa kaya INdo na
kwance idanunta a rufe yaje ya sumbaceta sannan ya tafi ya kullo mata gidan da
mukulli.

Yana zuwa ta dinga kallonsa wanda yasa shi tsarguwa yayi murmushi tare da
d'aukar ta suka wuce bedroom. Romance d'inta ya dinga yi har sai da ya nuna mata
shima fa yana buk'ata yasan hakan ne kawai zai wankesa da zargin da ya hango a
cikin idanunta, ganin ya fita birkicewa ne kuma ya tayar mata da hankali ta koma
bashi hakuri tana lallashinsa sannan yace.

"Toh baby ya zanyi bari kawai naje nayi wanka amma kwanakin da kikeyi sunyi yawa
har 7days."

Tana nan kwance yaje yayi wanka ta had'a masa tea yasha sannan suka kwanta bacci
bayan sun nanik'i juna kamar za'a sace d'aya.

Sai da yayi kwana biyu a gidan Fateema sannan ranar lahadi da daddare ya koma gidan
INdo wanda a lokacin sai da tayi rok'on zuwan period amma ina sabida cikin jikinta
gashi a gurinta kawai yake hucewa tunda ya dawo har ta fara jin haushinsa amma baya
damuwa bare ya nuna ya gane nufinta.

Abu d'aya yake mata ya d'auke hankalinta shine zai ce tazo suyi lesson wannan abun
kawai yake sawa yaga ta sakar mai jiki har itama takan faranta masa ta hanyar
kwanciya a jikinsa.

Sadeeq kuwa ta k'arfi da yaji ya zama mak'arya ci a gurin INdo sabida tace bata son
gemun Fateema kuma tana so dole yace wa INdo inda ake mai askin ne suka yi gobara
yanzu gyara gurin suke yi sai sun gama, gashi shi baya son zuwa ko'ina idan ba
gurin ba. Ita kuma Fateema ya rasa yadda zai sanar mata da cikin INdo domin zata yi
mamakin tayaya hakan ta faru shida baya nan har tsawon 3months.
***
Ranar Sunday misalin k'arfe 4:30pm Sadeeq da Fateema suna toilet sai rigima suke
yi ya rik'e mata hannuwa yana cewa.

"Bake kika hanani yin shaving d'in ba dan haka yanzu babu abinda zai sa kice sai
nayi tunda kina so."

"Nidai to yanzu ka rage please, Allah yanzu ta sake yin yawa."

Ganin ta kafe ne yasa shi k'ar6a yayi ya rage iya yadda yake barinsa sannan suka yi
wanka suka fito. Shiryawa sukai ko wannce cikin shigar daya fiso sannan suka fito
zuwa gidan INdo dan can gidan su Mama zai kaisu ana kawo kayan sa ranar Haleematu.

"Wait anan inje insa ta fito karku shiga ku shantake."

Tashi yayi yashiga gidan ita kuma ta zaro phone d'inta ta kunna data kafin su fito.
Yana shiga zaune ya tarar da ita tayi shirinta tsab mayafinta a kan cinyarta yayi
sallama ta amsa tare da kai idanunta kansa, har ya k'arasa bata dena kallonsa ba ya
mik'a mata hannu ta bashi nata ya d'ago ta tayi murmushi tare da cewa.

"Ko kaifa da kayi wani kamar tsoho.."

"Okey ko shi yasa ma kallon tsufan da kike min yasa kikak'i kar6ar tayin
soyayyata?!"

"A'a nidai ban fad'a ba."

Yana rik'e da hannunta ya durkusa yasa gwiwarsa d'aya a k'asa d'ayar kuma ya ajiye
ta kamar dai yadda turawa sukeyi yana faman kashe mata narkakkon eye's d'insa yace.

"Humaira kina sona?!"

Ta kallesa ta tuna ajinsa da matsayinsa da kud'insa da martabarsa tun tana cikin


duhun kai amma yazo yana rok'on ta so shi duk da har yanzu bata kai matarsa ilimi
ba amma itama ta waye dan duk wanda ya kalleta sai yayi tunanin ko ta kammala
degree ko tana kanyi. Murmushin jin dad'i tayi sannan tace.

"Ina sonka amma sai kayi k'ok'arin wajan Musanya Zuciya ta daga kan doctor domin
har yanzu yana cikin Zuciya ta bazan munafince kaba."

"Aisha...! Are you in your right sence?I'm your husband but kullum sai kin min
zancen marigayi why? Please we should help ourselves in one way or the other. Yanzu
dai am asking you kina sona??"

"Eh ina sonka.. I love you."

Yana jin ta fad'a ya mik'e tsaye tare da yi mata alama da ta zo su wuce. Har ya
d'an tafi yaji ta rik'osa ya kalleta fuskarta a narke ya tsaya yana zaro ido yace.

"Menene kuma?!"

INdo tace "kayi hakuri nafa ce ina sonka."

Rik'ota yayi yana murmushi sannan ya kar6i mayafin ya yafa mata suka fito ya kulle
falon still yaga tana kallonsa yaje ya rungume yana cewa.

"Is okay cutie na yadda but sai kin fara nuna min from now on kinji ko?!"

"Toh.."
Ta fad'a tare da gyara swagger bag d'in hannunta. Itace ta fara fita shi kuma ya
tsaya rufe gidan. Zaune taga Fateema tana danna waya a gaba ta yatsina fuska ganin
sai dai fa ta shiga baya sannan taje ta zauna suna yiwa juna kallon yake har ya
shiga shima ya zauna ya tayar da motar suka tafi.

Suna zuwa tare suka shiga lokacin har an kawo kayan anata gani.

'Dakin Mama suka shiga nan suka ga su Hawwah aikuwa suka had'u suna ta hirar su.
Har aka yi magrib suna tare sai da INdo ta cire mayafi ta shiga toilet tayo alwala
tana fitowa taga suna kallonta alamar dai sunyi gulmarta Hawwa tayi dariya tare da
cewa.

"Su aunty Humaira kuma ashe-ashe...."

INdo ta ta6a baki cikin rashin fahimta tace.

"Ashe-ashe me?!"

"Wallahi matar broth wannan ciki ne, haba shi yasa sai wani shining kike yi sannan
kin kuma yin kubul-kubul ga shi kuma ya fita."

"Toh ai ba haramun bane ko kin manta a gidan miji nake. Allah sister Hawwah keda
Hali dubu (Haleema) kun saka min ido ya isheku haka."

Tunda suka fara magana Fateema take kallon cikin INdo, tabbas wannan ciki ne ba
te6a ba. K'irjinta ne ya dinga bugawa yana mata wani rad'ad'i har tana jin tamkar
zai fasa mata zuciya. Lallai no wonder taji Sadeeq yanzu baya mata zance yana son
yaga ta haihu ashe tuni yaje ya kunsawa INdo.

Babu wanda beyi magana ba a cikin d'akin face Fateema domin idan tace zata tanka
babu shakka hawaye zata yi har a samu wasu suce bak'in ciki takeyi mata, sai kawai
tayi shiru dama a kwance take hakan yasa ta lumshe idanuwa har aka kira sallan
isha'i sannan ta fita basu sake sanya ta a ido ba har Sadeeq yazo d'aukar su...

*Page d'in naki ne aunty Mammn Mu'aleem. Ina fatan zai sanyaya miki rai kamar yadda
naji dad'in kulawarki.*🤩

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na
*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

Page *35*

Shirin zuwa Sumaila kauyen sani suke farin ciki ya cika zuciyar INdo har ta kasa
6oyewa, kallonta yayi bayan ta rufo d'akinta ta juyo gashi cikinta ya fito yace.

"Cutie koma d'aki gaskiya mun fasa zuwa."

K'irjin INdo ya shiga bugawa hankalinta duk yayi mugun tashi ta kallesa dan san
tabbatar da maganarsa. Gani tayi yana dariya hakan yasa ta yin kansa zata dokesa
yayi saurin guduwa cikin shagwa6ar da ta farayi wadda yanzu take neman zame mata
jiki tace.

"Ka tayar min da hankali Allah ya dawo damu lafiya sai na rama."

Fitowa suka yi suka shiga mota Sadeeq ya d'auki hanya, wannan karan cikin hira suka
ta kai da ka gansu kasan masoyane sa6anin lokacin da aka ce ya kaita garinsu ya
dinga kumbura tamkar wanda aka sanyawa yeast. Cikin kwanciyar hankali suka shiga
garin sumaila, suna zuwa kan kwanar da zasu shiga kauyen sani adeeq ya kalleta yana
murmushi yace.

"Cutie ga barkono da gyad'a bazaki siya bane?!"

Juyawa tayi tana kallon gurin kafin tace.

"Eh wallahi kuwa, dan Allah kaje ka siyo min kwano d'aya-d'aya."

"Ke wasa nake miki ni."

Ya fad'a yana tafiya, kallonsa tayi shima ya kalleta tare da d'aga mata girarsa.
Hannunsa yasa ya janyo nata yana matsawa ta lumshe idanuwa tana shafar cikinta da
d'ayan hannunta.

A k'ofar gidan su yayi parking, gidan yana nan yadda yake tun lokacin da Abubakar
ya gyara musu katangar su ya maida ita ta bulo sa6anin da datake na k'asa. INdo ta
kallesa tare da Kama hannunsa tace.

"Wait for me, naje na sanar ma Inna zaka shigo ku gaisa."

"Hmm lalle wariyar launin fata, meyasa ni bazan shiga direct ba sai an wani yi min
iso? Ban yadda ba tare zamu shiga kema ai idan mukaje gidan Mama wani sa'inma kina
rigani shiga."

"Hehehehe lallaima, toh ai ni macace zan iya shiga direct, kaifa sabida su
Mubasheer na zuwa su shiga kai tsaye kasa duk muke kulle gidajen sai an buga munji
ko waye sannan mu bud'e."

"Toh ai ni har yanzu saurayi ne, su kuma su Inna sun tsufa toh meye a ciki."

"Kai My super glue, wallahi Inna ta ba tsohowa bace rayuwa ce kawai ta maida su
haka amma ka bari na kammala karatuna sannan cinikin zo6o ya kankama zaka sha
mamakin Inna da baba wallahi. Kuma kasan dai ai abban ku dasu Mama sun girmi su
Innata."

"Kaiii cutie..?!"

"Yanzu dai bazaka barni in shiga ba."

Tayi maganar tana turo baki,janta yayi kasan cewar tinted glass ne yasa ba'a
ganinsu. Sadeeq ya shafo cikinta tare da cewa.

"Yau dai ina zata ga k'ok'arina, but dan Allah cutie karki bari ta ankara harsai
nazo mun gaisa na fito, wallahi kuma sai naji inajin kunya."

"Kunya kuma? Hahahah ta6 ai aikin gama ya riga ya gama, yanzu wannan abun taya yaya
za'aiyi ya 6oyu? Dama hijabi ne ko duguwar riga shine zan iya d'anyin dabara amma
ai yanzu kuwa ka makaro hakan nan zan shiga Inna ta gani kuma ka shiga ku gaisa da
ita."

Sadeeq ya turo bakinsa tare da dafe kuncinsa yana kallonta yace.

"Toh ya zanyi? Dole na shigo tunda an banike."

Tana dariya ta bud'e k'ofar yaran unguwar da suka zo gurin suka dinga kallon INdo
wasu na cewa itace wasu kuma suna cewa ai k'anwar Inna ce dan ga kama nan. Gidan ta
shige tana dariya jin abinda suke fad'a, tana zuwa tsab ta ajiye cewa itace 'yar
fari ta d'ane Inna dake sharce gurin da tayi wanke-wanke.

"Oh ni Maryamu waike yaushe ne zaki san kin girma 'yar nan.?!"

Inna ta fad'a tana janye jikinta daga na INdo. Dariya kawai ita kuma takeyi tare da
kallon Innar tana cewa.

"Kai Inna Oyo-yo fa mukayi, nayi missing d'inku wallahi Inna dake da baba tunda aka
kaini baku jeba sai su d'an rainin hankalinnan Sagiru..."

"Ga INdo... Ga INdo, yeeeeee sannunku da zuwa."

Nafeesah ta fad'a tana rungume INdo, murmushi tayi cikin nunawa wayewa da kuma
zaman birni tare da nuna zaman teburin class ta kamo hannunta tace.

"Su Feenah 'yan mata daga ina haka..?!"

Ta fad'a tana jan hannunta suka nufi cikin d'akin Inna.

"Kinga Feenah d'auki tabarmar baba ki shimd'a anan sabida Malam Sadeeq zai shigo su
gaisa da Inna."

Sabuwar tabarmar malam Hamza aka shimfid'a sannan INdo ta ciro d'ari biyar ta bawa
Nafeesah cikin k'asa-k'asa da murya tace.

"Mazaki siyo min lemon roba da ruwa zanba shi yasha."

Kar6ar kud'in Nafeesah tayi sannan ta fita da saurinta, sai da ta kuma tsayawa
wajan Sadeeq yana tsokanarta kafin ta wuce zuwa shagon da zata iya samowa mijin
yayarta ta lemo da ruwan jarka.

"Sannun ku da zuwa, ke d'aya kika zo ko hardashi me gidan naki?!"


"Inna tare muke dashi zai shigo ku gaisa ma, wai ina baba?!"

"Malam yana can gurin sana'arsa, bari wani ya shigo sai yaje ya kirasa ku gaisa."

INdo dake bakin gadon Inna na k'arfe tace "toh.". 'Dan kuma gyara d'akin tayi
sannan ta share shi ta ciro turare a handbag d'inta ta fesawa d'akin da kan
tabarmar da Sadeeq zai sauna sannan tace.

"Inna bari nace ya shigo ko? Karya ga an barshi a mota shi d'aya."

"Toh kice ya shigo barina saka mayafi na nima."

Fita tayi suka yi karo da k'awarta Uwani da Sahura da alama sunji labarin zuwanta.

"Ahhhh kaga su hajiya INdo amaryar Malam Sadeeq oh harda su abinga."

Sahura ta fad'a tana d'aga mayafin jikin INdo, kaf d'insu sunyi wani bululumu dasu
Uwani ma harda tsohon ciki kai idan ka gansu bazaka ce k'awayanta bane sabida
tsabar yadda kalar wayewar ta bambanta.

"Kai sahura kina nan da gulmarki, ku shiga ciki ina zuwa."

Ta fad'a tare da dukan bayan Uwani ganin yadda ta rik'e ha6arta tana kallonta.
Cikin gidan suka shiga ita kuma ta shiga motar Sadeeq wanda ke jingine jikin kujera
ya sanya hularsa a fuska yana kuma zagaye kwantaccen quarter million d'in fuskarsa.

Jin an bud'e k'ofar motar ne yasa shi cire hularsa ya kalleta, zama tayi tana
kallonsa da murmushi a fuskarta yace.

"Uhmmm wato anzo gida harma kin manta tare muka zo ko?"

Hannunsa ta kamo cikin nata cikin kalar jimami tace.

"Ni na isa, tunda na shiga mafa koda Inna bamu gaisa ba kuma babu kowa duk basa nan
amma ni banajin zan iya mantaka a yanzu domin ka zama ni na zama kai kadena sawa
ranka cewar duk inda zan shiga wai Zan manta dakai no, idan nayi haka toh Zan iya
mantawa da kaina nima."

Sadeeq ya lumshe idanuwa tare da jan hannunta murya a shak'e cikin wani irin salo
yace.

"Kina nufin kenan munyi *MUSAYAR ZUCIYA* dani dake a yanzu? Ba kamar da ba yadda
kike nuna min cewar zuciyarki ta M twinnie ce shi kad'ai yanzu zaki iya mallaka min
ita...?!"

"Sosai ma kuwa na baka ita ina fatan ka rik'eta amana. Anan aka d'aura mana aure
dan haka anan na kuma baka amanar kaina da duk abinda ya shafeni."

"Na kar6a cutie Allah kuma ya bani ikon rik'ewa gam-gam, a baya ma *Illar Zuciya*
ce tasa nake ganin kamar anyi min ba dai-dai ba amma a yanzu..."

Yakai bakinsa kan hannunta ya sumbace shi yana kashe mata idanuwa tayi saurin kawar
da kai tana dariya. Nafeesa ta hango hakan yasa INdo fitowa da sauri. Amsar aikenta
tayi ta shiga ciki Nafeesah kuma ta tsaya a gurinsa suka dinga hira har su Shehu
suka dawo suma suka gaida shi. Cikin gida kuma INdo ta gama jerawa Sadeeq abin
tarba dan inna ta gama dafa wake da shinkafa Allah sarki harda yanka mai lawashin
albasa kuma duk INdo bata hana ba domin ta haka ne zata iya kuma tabbatar da kaunar
da yake cewa yana mata dan marigayi baya kyan-kyamin duk abinda zata bashi bare
yanzu tasan kanta tasan me takeyi ta kuma san waye mijinta.
"Lallai INdo wai duk malam Sadeeq d'in kikewa wannan tanadin?!"

Uwani ta tambaya tana ta6e baki, gani take kamar INdo ta zurma da yawa duk miji
akewa wannan hidimar.

"Toh Uwani bakin ciki kikeyi ko me? Ina zan samu kifi ma dan yana son wake da
shinkafa da kifi ko dafaffen kwai."

"Ta6 lallai INdo Hamza, toh k'ila dai yana baki kema ba irin muba da sai dai komai
kayiwa kanka."

"Kwaji dashi gulmammu, Inna bari naje nace ya shigo."

Tana fad'a ta kuma fita tace ya shigo. Jerawa suka yi shida Nafeesah yana kallon
INdo daga baya. Gaskiya ikon Allah baya k'arewa a duniya ko kana menene sai ya nuna
ikonsa akanka yau shine da INdo harda kunshin cikinsa a jikinta "Allah
astagfurullah."

Ya fad'a cikin ransa tare da shiga gidan yana sallama, su Sahura da Uwani suka amsa
bakinsu a washe yayin da Inna ke tsaye kanta a k'asa sam bata iya kallonsu tun
zamanin Abubakar. Cikin d'aki Nafeesah ta shigar dashi ya zauna yana sosa keya yana
shafa wuya.

Daga bak'in k'ofa Inna ta tsugunna suka gaisa da Sadeeq sannan su Uwani ma suka
sake gaidashi duk da cewar sun gaidashi a cikin mota INdo ta kallesu tare da makewa
Sahura hannu ganin yadda take leken sadeeq tana wangale baki.

"Kedallah can malama kina da miji kina kallon mijin wasu haba."

"Kai INdo bana san herri."

Tashi Inna tayi ta shiga rumfar malam Hamza bayan ta tura Nafeesah tace ta kirasa.
Kallonsu tayi tace.

"Zan shiga daga ciki, karku ce na barku anan."

"Lallai ma INdo toh ba abinci zaici ba? Toh ki zauna muyi shira mana kafin ya
gama."

Uwani ta fad'a tana hararta cikin jin haushin yadda take wani nan-nan da malam
Sadeeq sai kace su basuda mijin.

"Toh kuje ku gama muna nan hajiya INdo."

"Toh hajiya Sahura."

Itama ta fad'a tare da shiga cikin d'akin. Kallonta yayi ta zauna kusa dashi tare
da d'akko Coca-Cola ta bud'e mai cikin halin damuwa tace.

"Kayi hakuri kasha a haka da bakin jarkar, nan gidan bamu da kofuna kaji my super
glue ka daure."

"INdo Aisha ta zaria med'an kallabi..!"

Ya fad'a tare da matsawa kusa da ita. Lek'awa yayi k'ofa aikuwa karaf suka had'a
ido dasu Sahura da Uwani suna lek'owa yayi dariya tare da Kai bakinsa saitin kunnen
INdo yace.
"Gaskiya d'aliban nan nawa gulmammu ne, sai lek'en mu suke kamar a gidan zoo."

Itama dariya tayi cikin hillata da shagalta yaci wake da shinkafar nan dan sai da
suka cinye ta cikin kwanon silbar da Inna ta kawo musu. Suma su Sahura da suka kasa
suka tsare aka zuba musu sukaci lokacin malam Hamza ya shigo fuskarsa kunshe da
fara'a Sadeeq yayi saurin tura kwanon gaban INdo da ragowar lemonsa da ledar yajin
ya maze sai wani danne-dannen waya yake shi a dole beci da yawa ba.

INdo kuwa banda dariya babu abinda takeyi mai amma still ya maze su Uwani na jiyo
ta sai mamakin abinda yasa ta dariyar suke yi.

"Sadeequ ashe kunzo? Sannunku da zuwa. Ah kaga uwata an zama manya."

Sadeeq ya fara motsi yana gyarawa malam Hamza guri dan ya shigo. Gaida shi suka yi
sannan yayi ta sanyawa Sadeeq da marigayi albarka ganin yadda INdo ta canza tamkar
ba 'yarsu ba.

Tare da malam Hamza Sadeeq suka fita ita kuma INdo ta koma tsakar gida gurin su
sahura Inna ma taje ta zauna. Suna zaune Rukayya ta shigo murna ba'a magana sabida
ganin INdo da ciki, nan fa suka shiga hira baji ba gani amma duk da haka zuciyar
INdo bata manta da Sadeeq a mota ba. Nafeesah ya d'auka suka shiga cikin garin har
sai bayan sallan la'asar sannan ya dawo dan su tafi.

"Gaskiya Inna zan baki kud'i a hannunki a samu dan Allah a gyara band'akin nan,
habba wallahi za'a iya d'aukar larura tunda aka haifeni a haka yake. Ga dubu sha
biyar nan ita kad'aice a hannuna nasan k'ila malam Sadeeq zai bawa baba ma wasu
amma idan be bayar bama dan Allah Inna a fara da wannan kud'in ko buhu d'aya ne na
siminti a siyo a malale k'asan band'akin can kosu Sagiru ne da Shehu sai suyi ai
sun iya."

Kwallah Inna ta share tare da yin godiya sam bata ta6a tsammanin akwai ranar da
'ya'yanta zasu yi mata wani abunba ganin itama ba tayi wa nata komai sabida rashi
gashi ance sai kanayi za'ayi maka.

"Inna ya kike kuka? Karki bari na tafi haka dan bazan yafewa kaina ba bayan na
barki cikin kuka."

Murmushi Inna tayi tare da cewa.

"Allah nakewa godiya 'yar nan domin ban ta6a zata zanga irin wannan ranar ba
musamman akanki, sai gashi Allah ya shirya minke ya kuma azurtaki gashi har kina
tallafa mana da abinda kike dashi, Allah yayi muku albarka dukanku."

"Amin Inna ta, karki damu dana gama karatu na kware insha Allah zanyi kud'i duk
gidan nan sai an gyarasa."

"Toh Allah ya yassare miki."

"Feenah dan Allah idan ya koma kwara state zan cewa Sagiru ya kawoki mu zauna tare
ko bakya so?!"

"Ke! Ina so mana ai wallahi kin more gidan miji INdo."

Mtwww "Ban hanaki cemin INdo ba gatsal? Ki kirani yayya Aisha ko Yaya INdo karki
sake cemin wani INdo mara kunya."

Kallonta Nafeesa tayi tana ta6a baki kafin ta kad'a kai tabar d'akin. Har zaure
Inna ta raka ta tana yi musu fatan alkhairi bayan Sadeeq yazo sunyi sallama. Dubu
d'aya ta kar6a gurin Sadeeq ta bawa su Sahura su raba d'ari biyar-biyar suka dinga
godiya suna k'ara jinjina arzikin da INdo ta samu sannan ta shiga mota suka tafi
cike da farin ciki.

***
Kwanaki biyar yayi bayan sunje kauyan Sani sannan suka d'aga suka tafi kwara
state da Fateema bayan yayi yayi da INdo ta bishi tak'i sabida karatunta. Yana
tafiya da kwana biyu tasa Sagiru ya kawo Nafeesa duk ranar school d'inta zasu je
tare ta zauna a barandar ajinsu INdo idan sun tashi su koma gida ta koya mata
abinda ta iya itama hakan ya k'ara bud'e brain d'inta ga cikinta yana ta girma
cikin kwanciyar hankali.

Duk wata Sadeeq suke dawowa kuma INdo bata nuna damuwarta duk da bata son tafiyarsa
amma bata son nuna mai dan karya kansile mata karatunta, gashi dama ya sanyata a
makarantar dare ta islamiya ta matan aure anan unguwarsu hakan yasa ta kuma zama
busy tana kuma wayewa ta fannoni da yawa a cikin rayuwarta.

Cikinta har ya shiga 10months bata haihu ba sai dai yayi girma har bata iya zuwa
ko'ina. Ranar wata laraba cikin dare ta farka lokacin Sadeeq na mak'ale da ita duk
da girman cikin jikinta hakan baya hanashi nanik'arta. Kallonsa tayi tana faman
rintsa ido cikin wani irin mugun rik'o yaji ta rik'e mai hannu hakan yasa shi
saurin farkawa.

"Cutie what happen?" Shiru sai cizon lips d'inta takeyi tana matse idanuwa ya mik'e
tsaye ya sakko yace.

"Cutie kodai haihuwa ce? Bari nazo muje asibiti."

A gigice ya sanya jallabiya ya zari mukulli yayi parking lot. Motar ya fitar da ita
shiru garin babu kowa ya kuma komawa gidan da kyar ya kimtsata ya fito da ita mota
lokacin mak'ocinsa ya leko sabida yaji k'arar mota. Ganin halin da ake ciki ne yasa
shi taso matarsa ta bisu zuwa asibitin.

Duk ya rud'e ya bugawa Fateema ya gaya mata itama hankalinta ya tashi gashi babu
abin hawa bare tabisu gata mace. Ganin abun yayi yawa ne yasa suka kira Sadeeq d'in
ciki INdo tana ta kuka ya rik'e hannunta zuciyarsa na bugawa da k'arfi da k'arfi
tace.

"Dama a makaranta malama tace idan mace zata haihu k'afarta d'aya a duniya d'aya
kuma a k'abari. Malam Sadeeq kayi hakuri nasan nima yau dacta zan..."

Sadeeq yayi saurin rufe mata baki yana kad'a kai, da k'arfi ta fizge kanta ta juyar
da kai tana ci gaba da magana.

"Sai na fad'a d'in ka bari in gaya maka mana, dacta zanbi nima yau amma dan Allah
tunda ance namiji zan haifa dan Allah koda na tafi malam Sadeeq ka sawa d'an suna
Abubakar Sadeeq kar kuma a 6oye mai suna dan Allah."

Jikin sadeeq ya dinga rawa gumi gaba d'aya ya gama jik'asa, tana gama yin magana
kawai nurse d'in dake gurin tasa hannun zureren jariri ya santalo kan hannun nurse
d'in INdo na kwance tayi shiru yayin da Sadeeq ya bud'e baki yana kallon fuskarta
gumi na d'iga akan hannunta na jikin fuskarsa....

*Fatan alkairi gareku masoya, a koda yaushe Ina alfahari daku cikin labarin MUSAYAR
ZUCIYA. Hajja ce take muku fatan alkairi tare da d'in bin godiya marar adadi*💘
*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

Happiest bday ASMY B ALIYU🎉you are truly one of the most amazing writers I
knw..Forever and a lifetimes to come tawan...🎊

Page *34*

Tana fita napep ta tare ya kaita gidan su. Tana shiga ta fashe da kuka tare da
fad'awa kan kujerar d'aya daga cikin falon.

"Ke lafiya kuwa kamar wadda aka yiwa mutuwa?"

Cewar yayan ta Shamsu yana kallonta, Fateema bata yi shiru ba tana ta kuka Shamsu
ya tashi ya dinga mata fad'a yace idan baza tayi magana ba ta tashi ta koma inda ta
fito. Mama ma kallonta take yi tana jiran jin abinda zata fad'a ranta cike da
addu'ar Allah yasa ba tsakaninta bane da mijin.

"Ke wallahi karki bari na tashi tsaye dan sai na fasa miki baki, aikin banza kawai
kiyi magana shine zaki tsaya yiwa mutane kuka."

"Mama Sadeeq ya munafurce ni, Mama be ta6a gaya min matarsa Aisha nada ciki ba sai
yau da muka gani gashi har ya fito. Wallahi bazan koma gidan saba yaje can su
k'arata munafiki kawai, dama ance duk wacce ta d'auki namiji uba toh lallai zata
mutu ma..."

Mtwww "Shut-up Fateema, bakida hankali ne? Toh sakinki kike so yayi?!"

"Nidai kam bazan koma ba yaje can su k'arata."

"Toh idan ya sakeki sai kizo na aureki nine kawai idan na aureki za'a haramta min
k'ara aure bare har matar ta rigaki haihuwa."

"Yaya Shamsu ka aureni kuma?!"

"Eh toh kince maza ba 'yan goyo bane, kinga ni uwa d'aya uba d'aya muke ki goyani
na goyaki babu mejin haushin wani, amma ko barin Sadeeq kikayi toh wani mijin zaki
aura kuma shima wata ran zai miki wani abun sannan ba lallai ki kuma samun saurayi
ba sai da kema ki shiga gidan wata."

"Umma...."

"Karki min magana Fateema, dai-dai gwargwado kina da ilimin addini shin na zamani
ne ya rinjayi da addininki ko kuwa wani saban iskancinne haka? Karki manta wannan
auran nasu had'in Allah ne duk wanda yace zai ja da ikonsa akan lamarin toh bazai
kwana cikin jin dad'i ba. Fateema karki manta nima da yanzu bani bace mahaifiyarku,
amma kinga da yake Allah yayi ta hanyata zai samu haihuwa sai ya d'auke matarsa ta
farko da kyar mahaifinku ya yadda ya aureni da yace ya gama aure amma a satin da na
tare a satin na samu cikin yayan ku ki gaya min da mahaifinku yayi butulci ya kafe
akan bazai sake aure ba ta wace hanya zai sameku tunda Allah yayi yana da rabonku a
duniya?!"

Fateema ta kuma fashewa da kuka tare da mik'ewa zaune tace.

"Toh Umma kiyi hakuri wallahi sharrin shaid'anne, amma kuma me yasa koda wasa be
gaya min ba ya yi min shiru sai yau naji na kuma gani?!"

"Hmm Fateema kenan, toh ko tunda kuka yi auran Sadeeq be ta6a kusantarki bane har
sai da aka yi musu aure da ita Aishan?!"

"Kai Umma.."

Fateema ta fad'a da alama nauyi tambayar tayi mata, kallon Yaya Shamsu tayi k'asa-
k'asa kawai suka had'a idanuwa ya zabga mata harara tare da cewa.

"Ke..! Kallon me kike yi min haka? Ko kin d'auka bansan meye auran ba sai ke kika
sani.??"

Da sauri ta zaro udanuwa hannunta a baki tana girgizawa tare da kallon Umma Fateema
taga Umman ma ita take kallo, lallai Yaya bashi da kunya ma wallahi a gaban
Ummansu. Koda yake itace ta kallesa dole yayi mata bayani.

"Fateema karki yadda ki nunawa mijinki bak'in cikinki akan cikin matarsa, ina son
ki nuna masa kinfishi son cikin ma. Sannan karki bari abban ku ya dawo ya ganki a
cikin gidan nan wallahi kinsan ranki ne zai 6aci abanza, gara kije kiyi zaman
aurenki har Allah ya baki kema wata rana idan kina da rabo."

"Toh Umma, amma dan Allah ki tayani da addu'a dan wallahi ina jin zuciyata nayin
zafi da nauyi."

"Kidena sawa a ranki insha Allahu zaki ji bakya ji shaid'an ne kawai yake son shiga
cikin lamarinki, ki yawaita azkar zakiji dad'in ranki."

Wayarta ce dake cikin jaka taji tana ta ringing amma tak'i d'agawa dan tasan baxai
wuce Sadeeq ba ita kuma bata shirya abinda zata ce masa ba. Tashi tayi suka yi
sallama Yaya Shamsu yace bari ya kaita gidan da kansa, suna tafiya yana k'ara bata
shawarwari wani maganar ma har mamakinsa takeyi lallai yayan nata aure kawai yake
jira amma babu abinda be sani ba.

***

Shi kuwa Sadeeq k'arfe tara yaje d'aukar su amma aka ce Fateema bata nan, duk an
duba bata gidan ya kira ta yafi sau goma amma ba'a d'agawa hakan yasa yace INdo ta
fito su tafi. Gidan Fateeman suka fara biyawa amma akulle hakan yasa Sadeeq tafiya
yakai INdo gida tunda ranar a gidan Fateema yake.
"Malam Sadeeq d'an tsaya a can gurin me balangun can na kan kwana ka siya min."

Kallonta yayi sai yaga ita kalle-kalle takeyi abinta cikin mamakin daya mak'ale mai
a wuya yace.

"Cutie ballangu kuma."

"Eh dan Allah kace su sa yaji daban."

"Ikon Allah shi kike son ci kenan."

"Eh, akwai fura da nono da ake damawa a gurin, ana sa kwakwa da ayaba da madara
please dan Allah itama ka siyo min."

Dai-dai lokacin suka tsaya a gurin ya kalleta tare da cewa.

"Toh ke ya akayi kika son nan gurin harda abubuwan da ake siyarwa.?!"

Juyawa tayi ta kallesa suka kalli junansu tayi murmushi tare da cewa.

"Bafa zuwa nake yi ba da kai na, a'a ina dai bawa khaleefa yana siyo min nima
rannan ne Abba ya aiko min dashi. Naci naji dad'i shine nake bayarwa yana siyo
min."

"Okey yanzu naji batu na d'auka kinyi tunanin nan ma kauyan Sani ne, kowa zai iya
fita san ransa."

Baki ta turo tana yatsina fuska ya fita, leda biyu yayo musu sannan ya dawo motar
yana kallonta yaga still a shagwa6e fuskarta take ya shareta domin so yake su
k'arasa gida zaifi jin dad'in lalla6a ta.

A bakin gate ya tsaya ta fito suka shiga gidan, tun a parking space ya rik'ota tana
turesa yayi niyar d'aukarta sai dai yana ganin bazai iya ba sabida cikinta gashi ba
laifi INdo kamar (Ummi Aisha take ba ruwa na lol).

"Goya ni toh."

Sadeeq ya zaro idanuwa jin abinda ta fad'a, yana kamo hannunta suna tafiya yace.

"Ina tunanin yadda zan iya d'aukarki ke kina cewa na goyaki kin manta abinda yake
cikin ki ko."

"Toh gaskiya tunda kayi niyya malam Sadeeq to ka goya ni."

"A'ah cutie ni ba niyya nayi ba, cewa nayi Ina tunanin yadda zan d'aukeki kekuma ma
goyo zaki ce."

A bakin k'ofar d'akin ta tsaya ya ajiye leda d'aya kusa da k'ofar yaje ya tayar da
gen ya d'auka ta shiga ciki amma sai ya ganta tayi kalar tausayi ta kuma turo baki
yayi dariya.

"Mata problem. Nan kiyi can tayi Allah ya sa in iya muku."

'Daukarta yayi suka shiga ya dinga k'ak'aro nishi tana dariya, yana ajiyeta ya
zauna ya d'aura kansa akan cinyarta.

"Masha Allah sati d'ayan da nayi a garin nan yasa kin kuma yin k'iba, nan gaba sai
kin kasa tashi cutie Aisha."
"Ni kadena cemin nayi k'iba."

"Na dena ina balagun naki?ko bazan ci ba?!"

INdo tace. "Kaje kuci kaida Fateema nima kaga mu biyu zamu ci wannan."

"Nak'i wayon wannan zanci."

Tashi yayi yaje ya shigo da ledar ya kuma zuwa ya d'akko plate da zo6o tare da
kofina ya ajiye, anan falon ya rage kayan jikinta ta zauna daga under wear sai have
vest kasan cewar yanzu bata sanya bra tana d'an takura mata ciwon k'irji.

Kallonta yake tamkar zai shige cikin jikinta farat d'aya, remote ta d'auka tare da
kunna TV ta juyo zata ci naman taga sai kallonta yake cikin mamaki tace.

"Wai ya haka ne?!"

Sadeeq ya shafa k'eya tare da komawa kusa da ita ya zauna ya sanya hannu ya
rik'ota tare da kwanciya a bayanta murya sassanya yace.

"Aisha banyi tunanin zaki dawo haka ba, lokacin da kuna j.s one ko k'irg..."

Bata bari ya k'arasa ba tayi saurin rufe mai baki da hannunta. Dariya ya dinga yi
ta d'auki naman tafara ci sannan ta sakar mai baki yace.

"Zanci."

'Daukowa tayi ya rik'e mata hannu, fuskarta ya kama sannan ya sanya bakinsa a
hankali cikin nata sai faman zaro ido takeyi. Gani tayi ya ciro na cikin bakin nata
yana k'arasa taunawa ta bishi da kallon mamaki, yanzu kam ta tabbatar da cewa
Sadeeq yana sonta, a shirye yake tsab da ya shiga cikin rayuwarta yayi mata duk
abinda take so. Jiyayi kawai ta rungumesa tsam a jikinta a hankali kuma yaji tana
zubar da hawaye ya d'agota yace.

"Sorry na 6ata miki rai ko? Bazan sake ba, bana son ganin hawayenki musamman ace
nine silar zubar su."

Sabo ta d'akko tasa mai a bakin yayi murmushi ya fara taunawa idanunsa akanta, tana
ganin ya fara taunawa itama ta rintsa ido tare da kai nata bakin cikin nasa kamar
yadda taga yayi mata ya tura mata shi a bakinta da kanshi sa6anin shi da ya ciro
nata da harshensa.

"Ashe ba haushi kikaji ba d'azu?!"

Ya fad'a yana lasar lips d'inshi. Juyawa tayi tana murmushi ta fara dangwala yaji
tana sawa a baki. Mik'ewa yayi yana gyaran rigarsa yace.

"Na tafi na tabbata duk inda taje yanzu ta dawo, idan na isa zan kiraki."

"Toh a gaida ita."

"Ba rakiya?"

Dariya tayi ta mik'e suka fita tare, kamar karsu rabu haka sukeji amma babu yadda
zasu yi dole ya fita ita kuma ta rufe gidan ta koma ciki zuciyarta fal Sadeeq
domin ya tafine ya barta da abinda bazata ta6a manta shi bakoda da second d'aya ne.

****
A falo ya zauna tare da d'aukar laptop d'insa daya bari jikin charge. Fateema na
jinsa ta d'an Lek'o har lokacin tunanin abinda zata cemai takeyi, ganin tana
k'arasa 6ata lokaci yasa tayi shahada kawai ta shiga falon tana sanye cikin kayan
bacci me wando k'arami wanda ko cinyarta be gama rufewa ba.

Kusa da k'afarsa taje ta zauna, shafar k'afar ta farayi wanda take cike da
kwantaccen bak'in gashi. Sak'e mak'alo k'afar tayi sannan ya saki mai kuka a
hankali hawayen na sauka a k'afarsa, har cikin zuciyarsa yake jin kukan amma ya
shareta yana aikinsa, ganin haka yasa ta fara magana.

"Baby kayi hakuri dan Allah, wallahi raina ne ya 6aci akan abinda ka 6oye min kaida
Aisha."

Jin abinda ta fad'a ne yasa shi cewa,

"Me kuma muka yi? Duk abinda muka yi Fateema ya dace idan har na kiraki ki amsa min
amma kikak'i toh ina kikaje ma tukunna..?"

"Kayi hakuri baby, yanzu duk matsayin da nake a gurinka na matarka ace ka kasa gaya
min cewar Aisha ciki gareta? Ko kana ganin kamar zan cutar da itane? Wallahi kaji
dalilin da yasa kawai da na gani yau kawai sai na tafi gida, can kuma ina zuwa Yaya
Shamsu ya dinga min fad'a, baby kayi hakuri da 6ata maka rai danayi dan Allah."

Zuciyarsa ce tayi sanyi jin itace ma take basa hakuri, ture laptop d'in yayi
tare da janyo ta jikin sa. Gashin kanta da bata mai kitso ya dinga shafawa sannan
ya numfasa yace.

"Kamata yayi tunda nine na kaiku duk abinda zai faru ki tsaya naxo na d'auke ku,
amma ba komai nasan sharrin iblis ne. Sannan kuma ke ya kamata nayiwa wannan
k'orafin cewar baki sanar min da cewar Aisha nada ciki ba sabida ku na bari tare
har tsawon 3months amma baki gayan ba sai da na dawo na gani why baby?!"

Fateema ta d'ago tare da kwantar da kai cikin maganar tace.

"Wallahi ban ta6a lura ba kuma dai gaskiya bana wannan tunanin ganin nima har yanzu
babu. Sai d'azu da na ji Hawwa na fad'a kuma na gani a zahiri."

Sadeeq ya sake kamota tare da cewa.

"Kinga kenan duk babu me laifi, Fateema bana son ki tashi hankalinki domin ina
sonki a duk yadda kike. Kema Allah ba mantawa yayi dake ba domin da yawan aikin ne
toh da yaci ace kema yanzu kin kusa ma saukewa amma fa Allah me meyi, yanzu three
months da tafiya ta ita kuma cikinta wata hudu kinga kenan bayin kaina bane. Ina
son dan Allah karki tayar da hankalinki rashin haihuwarki bazai rage soyayyarki ba
a cikin Zuciya taba *I love you* Fateema Allah shine shedata."

" *I love you too* baby nima ka taya ni da addu'a na samu kafin na mutu."

Shhhiiii yayi mata bayan ya d'ora yatsansa akan lips d'inta. Shiru tayi sannan ya
janyo ledar da ya shigo da ita taje ta d'akko cup's ta zuba musu furar suna manne
da juna suna cin abin su idansa akan agoga yana son ya kira INdo kamar yadda yayi
mata alk'awari.

Daya rasa yadda zai yi kawai sai ya tura mata text message.

"Affuwan cutie na ba credit da yawa a ciki gashi masu shops sun rufe, zamu had'u
gobe I love nd miss you (#DeepKiss)."
Yana ganin sak'on ya tafi ya gogesa tas daga cikin wayar (tamkar miss Xoxo da take
da cutar clearing masseges).

INdo na kwance ta gama duba littafin ta taji shigowar sako, a hankali d'aya bayan
d'aya (word by word) ta karance sakon kafin ta tattarashi ciki kwakwalwarta ta sake
nanata sakon gaba d'ayan sa sannan tayi murmushi ta kashe wayar ta kwanta, wani
sabon yanayi na soyayyarsa yana shigarta haka ta dinga murmushi ita kad'ai a kan
gado har bacci ya d'auketa.

Yayin da shi kuma yake can suna soyewa da Fateema wadda itama fatan ta da burinta
da addu'arta a daren be wuce itama Allah ya azurtata da ganin gudan jininta ba.

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

Page *36*

Gurin d'ayar nurse d'in ta k'arasa ta bawa baby boy d'in kafin ta dawo gurin ta
kalli Sadeeq dake shafar kan INdo yana hura mata iskar bakinsa ganin bata bud'e ido
ba.

"Angon k'arni leave us please kafin a gama shirya ta."

Da kyar Sadeeq ya iya yin magana ba tare da ya kalli nurse d'in ba yace.

"Ki fara duba ta tukunna naga tayi haka bata k'ifta idanuwa sosai."

"Ah karka damu wannan ba wani abu bane ba, kawai wahalar haihuwa ce kad'an bamu
guri tunda kaima ka bamu gudun mawa."

Tashi Sadeeq yayi yana kallon INdo wadda idanunta ke a rufe sannan ya fita. Maman
Sayyid mak'ociyar su da suka zo tare ta kallesa tana zaune ta mik'e duk da cewar
tajiyo kukan jariri tace.
"Malam Sadeeq yayi ita d'in?!"

"Sun ce zasu gyara sune but ni banga ita Aishan tana wani abu ba da zai nuna min
cewar komai normal ba."

"Insha Allah komai lafiya lau karka damu shi yasa banso ka shiga cikin ba naso ace
kawai sai dai a kiraka ace kazo ka gansu."

Numfashi yaja tare da yi mata godiya sannan ya wuce masallacin dake cikin asibitin
kasan cewar anata kiran sallan asuba. Kafin ya dawo daga massalacin an gama kintsa
su duk da basu zo da kayan haihuwa ba, nurse d'in da ta k'arbi haihuwar tana siyar
da kayan babies ta sanyawa yaron ita kuma INdo ta bata sabon zani wanda shima itake
siyarwa ta d'aura tare da bata maternity pad da pant.

Resting room aka maida su Maman Sayyid na zaune kusa da ita tana mata barka INdo
kuwa ji take wani girim-girim ganin cewar wai yau itace ta haihu ga d'ama har tana
bashi yana shi.

Sadeeq kuwa sai da ya gama sharara addu'a sannan ya fito daga massallacin har gari
ya d'an fara yin haske. Yana shiga reception yaga Fateema tana kalle-kalle tana
juyowa kuwa ta ganshi dai-dai lokacin nurse ta fito ta nuna mai d'akin da aka
kaisu.

"Baby ina kwana? Ya su Aishan?!"

Ta fad'a tana kallonsa kai da ka ganta kasan itama tunda ya sanar mata suna asibiti
bata samu wani ishasshen bacci ba. Hannunta ya kama ganin babu mutane suka shiga
cikin d'akin da su INdo ke kwance Maman sayyid na ganin su ta mik'e daga bakin
gadon tana musu murna.

Rufe idanuwa INdo tayi dan wata irin kunya takeji azo aga ta haihu. Yaron Fateema
ta k'ar6a tana kallonsa yana ta bacci yasa yatsansa babba a cikin bakinsa, ta
k'arasa wajan Sadeeq dake zaune a wajan INdo ya rik'o hannunta yana murmushi ganin
yadda tak'i bud'e ido.

Jaririn ya kar6a yayi mai hud'u ba sannan ya ciro wayarsa, su Mama ya kira ya sanar
dasu yayin da Fateema ta kuma kar6an yaron ta zauna kusa da Maman sayyid. Yaron
jawur dashi me kyau k'irjinta ya dinga bugawa tana dannewa sabida jinsa take inama
daga nata cikin ya fito sai dai baza ka gane hakan ba sabida tayi nasarar fin
k'arfin zuciyarta.

"Wai cutie wa kikejin kunya a gurin nan da kika k'i bud'e idanuwanki.?!"

Kad'a kai tayi still idanta a kulle yayi murmushi tare da mik'ewa ya fita. Gurin
doctor yaje dan yana son a basu sallama su tafi gida dan kar a cika asibitin.

"Mu wuce gidan Mama Fateema."

Ya fad'a bayan ya dawo d'akin. Da sauri INdo ta juyo tana yin kamar zata yi kuka
tace.

"Gidan Mama kuma? Ni dai wannan karan baza ni gidan Mama ba can gida za'a maida
ni."

"Aisha wane gidan za'a maidake bayan haihuwar fari ce.?!"

Sadeeq ya tambayeta bayan ya mik'ar da ita zaune.


"Sani, ni dai can zan tafi gaskiya."

"Au lallai gidan namu ne bazaki zauna ba?!"

Shiru tayi tana tutturo baki su Fateema suka yi dariya kafin tace.

"Gaskiya ranka ya dad'e a al'adance haka ake yi, a kaita gida har tayi arba'in ko
sittin sannan sunyi kwari ita da baby sai a dawo dasu."

"Haka ne kam."

Maman sayyid ta sake gasgata zancen, Sadeeq ya shafa kai lallai akwai kwarbai kenan
duk da ba zama yake yi ba ai zai so ya zauna dasu ko na d'an wani lokaci ne tayaya
zai bari su wani tafi kauyan Sani.

Account number d'in nurse d'in ya k'ar6a dan zai tura mata kud'in kayanta sannan ya
siya magungunan me jego suka wuce can gidan INdon kasan cewar tak'i yadda ya kaita
gidan Mama wannan karan da hankalinta dan haka bazata yadda taje gidan sirikai
wankan jego ba.

Suna komawa kuwa 'yan uwa suka fara zuwa dole tasa Sadeeq kwasar yanashi-yanashi na
gidan ya tafi dasu gidan Fateema.

"Allah sarki, dama rabon wannan yaron ne Allah ya d'auke Habu. Gashi daga tafiyarsa
har Allah ya bada arzik'in yaro zuk'e-k'e tubarkallah."

Cewar k'anwar abban su Sadeeq da tazo ganin d'ah. Hakama duk mutane suka fad'a duk
wanda yaji labarin haihuwar wanda hakan sai da yasa INdo yin kuka sabida surutun
mutane da tada mata da baya.

Haka aka dinga zarya zuwa gidan INdo da nufin idan anyi suna za'a maida ita sani
bayan Mama ta nunawa Sadeeq amfanin komawar tata tunda tafi son can. Ba k'aramin
k'ok'ari Sadeeq yayi ba wajan ganin ya fita kunyar mejego da baby harma da mutane,
Fateema ma be barta haka ba sai da yayi mata na fitar suna sannan itama da su
Ummanta sunyi rawar gani sunyi musu kayan barka tamkar ba kishiya ce ta haihu ba.

"Cutie me jego, naga alamar haihuwar nan wata wawuyar kunya ta sanya miki why?"

INdo ta tura mai baki ya sanya hannunsa yajasa tayi 'yar k'ara tare da d'an dukan
hannunsa. Rungumeta yayi kafin yace.

"Toh me ake buk'ata na gobe wanda ba'ayi ba.?!"

"Ba komai hakan ma mun gode."

"Toh gobe dai nasan ganinki zai min wahala sabida mata dan ba shigowa zanyi ba,
idan ma kuna son wani abun ki kira Mubasheer ko khaleefa sai ki sanar musu."

INdo ta kallesa, wani irin tausayinsa takeji sabida ganin hidimar da yayi tundaga
kan abincin sunan da za'aci zuwa kayan rabo na sunan da ragunan da za'a yanka ga
kayan barka dayayi musu yace.

"Allah yasa ayi taro lafiya cutie, please karki fushi da kowa kinga duk wanda kika
gani zuwa yayi dominki domina domin marigayi infact dai kowa yazo ne dan tayamu
farin cikin samun k'aruwa. Na tafi sai gobe zuwa dare zan samu mu had'u."

Kai ta d'aga sannan ya juya zai tafi, da sauri tasa hannu ta rik'osa sabida wani
sassanyan sonsa daya kuma shigarta a d'an tsayuwar da suka yi. Rungumesa tayi shima
yasa hannu ya rik'ota yana shafar bayanta murya na rawa yaji tace.
" *I love you* Sadeeq forever, I'm also wishing you all the best in your life. You
are always by me, to share simple joys and each Nd every need and now with out your
loving presence I'm very lonely indeed I love with all my life my husband..."

A yadda yaji tana fitar da words d'in ba k'aramin tsumashi suka yi ba, a hankali ta
dinga jerosu dan ba k'aramin k'ok'ari tayi ba. K'ok'arinta da kuma son ganin tayi
abu yake k'ara sonya shi cikin k'aunarta, ya d'ago da fuskarta cikin lumshe ido ya
zura bakinsa cikin nata. Kissing juna sukeyi cikin wani irin shauk'i har Sadeeq
yaji yana neman fita a hayyacinsa sannan ya kyaleta da kyar ya shafi fuskarta
sannan ya bar d'akin da sauri sabida yasan mutane na nan sun sawa d'akin ido suga
mintuna nawa zaiyi a ciki.

'Yan saye duk sunje da 'yan uwan Inna daga dawakin tofa su Uwani, Sahura, Rukayya,
su Maryam haka 'yan kauyan sanin nan suka yo mota guda suka zo duk da ance su bari
zata dawo amma wasu suka ce ai daman basu san gidanta taba dan haka sai sunje.

Washe gari suna yaro yaci sunan Abubakar dan haka ko ajikin kalandu da key holders
da sauran abubuwan da akayi aka sanya mai Abubakar A (Ayman) wanda Fateema ce ta
za6i lak'anin yace wa INdo yana son ta bari a sanya mai tunda dama shima uban
sunansa ne dan ayi mata kara.

'Yan kauyan nan an samu shinkafa dasu zo6o lemukan jarka da sauransu suka dinga
lodawa cikin jakunkunan su, gidan ya cika mak'il da al'umma su Xoxo sai nan-nan ake
da little Sadeeq (ayman) duk nacin yayya Nabee ta hanata d'aukarsa sai dai ta
kallesa a hannunta. 'Yan grps da fad'ar yawansu bazai musaltuba suma sai salfie
suke da mejego dan a samu na sawa a status da dp, su Sis Mom s/fulani, princess
meenat, Olo, aunty jidda musa, mmn ansar, ummi k.d, mmn sadeeq³ aunty baraka, yayya
Ummi s/fulani aunty Fatee, sis Ummi A shitu, Heedah, Muhmeelat, redbutterfly, B s
fari, meela adeel, ummul m, mrs splined (ko? Sunan ne na 'yan gayu Allah yasa na
iya rubutawa dai-dai lol) su Sum-Q, Kaumi shaddad, matar shehi, my Halymah, (yasin
da yawa kuyi hakuri dan idan nace zan jeroku ta6...) Duka masoyan INdo da Fateema
duk sunje kuma sunci sunsha alhamdulillahi taro yayi sweet mejego an yi fitar suna
ta kece raini.

Yamma nayi 'yan sumaila suka kama hanyar komawa bayan sun jajjada ma INdo cewar ta
taho musu da naman sunan su.

K'arfe tara na dare Sadeeq yazo k'ofar gidan yana fitowa daga mota mutane dake
wajan suka dinga mai barka fuskarsa cike da farin ciki.

"Yaya Sadeeq kenan kwana biyu."

Yaji an fad'a cikin nok'e murya, kallonta yayi bayan ya zare glass d'in idansa.
Sanye take cikin wani fitinannan material anyi mata d'inkin riga da skirt sun
d'ameta sosai, gashi kwan lantarkin k'ofar gidan ya haske su ya zabga mata harara
cikin tsuke fuska yace.

"Chuchu wai banace ki dena yin irin wad'annan banzayen d'in kunan ba? Wallahi Zan
je na samu uncle Ahmad d'in wata k'ila baya lura da yadda kuke rayuwarku."

"Kai Yaya Sadeeq yanzu nan meye na rashin dai-dai a cikin rayuwata..?!"

Tayi maganar tana d'aga mayafin jikinta, tsaki yaja tare da kara wayarsa a kunne
taji yana cewa.

"Cutie lalla6o kizo waje ina mota."

Mayar da wayar yayi cikin aljihu tare da komawa cikin mota chuchu ta matsa jikin
murfin ya kalleta tare da cewa.

"Matsa ki bani guri."

"Kai Yaya Sadeeq dan Allah, wai kana nufin kace har yau baka gane inda Zuciya ta
take ba akan ka? Please Yaya Sadeeq tun kafin na mallaki hankalin kaina nake sonka
amma sai wani shareni kake yi ko banyi maka ba Yaya Sadeeq?!"

"Ke! Zaki matsa ki bani guri anan ko sai nayi ball dake."

Turo baki tayi tana sake matsawa kusa dashi, cikin nuna izgilanci tace.

"Hmmm Yaya Sadeeq duk matanka nasan tarihinsu kuma duk cikinsu babu wacce takaini
komai ba kamar wannan aunty Aishan me jego, ita da ko wayewar ma anan gurinka tayi
'yar kauye da..."

Kwaf... Taji ya kwad'e mata baki da phone d'in daya d'akko, dai-dai kuma lokacin
INdo ta fito tayo gurin motar Sadeeq yace.

"Chuchu bar gurin nan kafin raina ya kuma 6aci, k'atuwar banza sakarya kawai."

Kuka tasa ganin harda jini ya fito INdo taga ta tafi tana kuka ta shiga motar shima
ya kulle suka kalli juna tace.

"Me kuma ya sanya chuchu kuka my super glue? Allah yasa dai ba wani abun kayi mata
ba tana da kirki."

"Cutie rabu da ita rashin kunya takemin. Kinga bama wannan ba ya taro hope kunyi
komai cikin jin dad'i da wal-wala..?!"

Hancinsa INdo taja tana murmushi jin dad'i sannan tace.

"Kana sona mijina Allah ya shi albarka ya k'ara bud'a maka hanyoyin samu, mu kuma
Allah ya bamu ikon yi maka biyayya kamar yadda kake iya k'ok'arin ka wajan ganin ka
faranta mana."

"Amin Ummi ayman ina jin dad'in yabon nan da yake fitowa daga bakinki. Ina d'ana
baki taho min dashi ba, kinsan yaufa tun asuba rabona dashi."

Dariya tayi sannan ta zuge jakar hannunta ta fito da kud'ad'an ciki wanda duk na
barka ne. Mik'a mai tayi be kar6a ba ya kallesu tare da cewa.

"Uhmm k'arin bayani tukunna cutie ai bakya mik'on Kud'i haka ba bayani ba."

"Toh ka kar6a mana ai zan maka bayani, kud'in da mutane suka bani ne na barka. Ka
kar6a kayi amfani dasu kaga akwai k'ananu nima sai nayi wani abun ko idan za'a
nema."

Dariyar shima yayi zuciyarsa fara kal, chuchu na can gefe a tsaye tana gunguni
sauran 'yan uwa na mata sannu amma idanunta suna kan motar Sadeeq haushi kamar zata
had'iye motar.

"Cutie wannan ai naki ne, ni babu abinda zan kar6a Allah yayi miki albarka ya
albarkaci yaron da kika Haifa min Ina alfahari dake Ina sonki har cikin k'ahon
Zuciya ta."

Kowa dad'i yake ji sun dad'e a cikin motar kafin ya duba agogo ya kalleta cikin
yanayi nasan nuna rashin son abinda zai fad'a yace.
"Zan tafi, gobe insha Allah ance za'ayi suyar nama acan gida kinga kar a 6atawa
masu gidan idan an kammala za'a kawo jibi idan Allah ya kaimu za'a kaiku sumaila
sai kuma kinyi arba'in."

"Ko baka son na tafi ne..?!"

Yayi murmushin yake domin harga Allah baya son suna rabuwa amma ya zai yi ko ta
zauna fitina zai dinga jawa kansa gashi kuma zai koma kwara Fateema baza ta bishi
ba wannan karan sabida zasuyi wani taro a makarantar da take aiki dole ya barta
taje. Hannunta ya kamo tare da cewa.

"Cutie karki damu kije ki dawo hmmmm zaki shaaaa."

Da sauri ta bud'e motar suna dariya bata bari ya k'arasa, lek'ansa tayi sunata
dariya yace.

"Idan kin shiga kicewa Fateema ta fito mu tafi."

Baki ta turo ya shafa kansa ganin harta mai fassara ya kashe mata ido d'aya sannan
ta tafi, tasan komai shi kenan yanzu shida Fateema zasu cigaba da zama sai taji
wani iri a cikin zuciyarta da kyar ta iya fad'an sakon sannan Fateema ta fita,
chuchu na ganin haka ta kalli su Haleema tace.

"Kuzo muje wajan Yaya Sadeeq ya rage mana hanya duk da munyi fad'a."

Tashi suka yi da sauri suka k'arasa wajan motar yana kokarin tadawa suka rok'esa,
sai da ya fara dank'arawa Chuchun harara kafin yace.

"Ku shiga amma wallahi badan halinku ba ku dukan sakarkaru kawai."

Shiga suka yi ya ya dinga jan Fateema da hira dan ya denajin muryoyinsu musamman ta
Chuchun da take kamar ta gyare kyar-kyar-kyar. Yana zuwa suka fita chuchu ta
kallesa shi kuma yak'i bari su had'a idanuwa sabida mugun haushinta yake ji sabida
yadda yaji zata ta6a mai mutuncin matarsa uwar d'ansa.

****

Washe gari bayan anyi suyar nama an kasa kowa an bashi. INdo ta kimtsa musu kaya
itada ayman da Nafeesah da daddare Sadeeq yazo gidan ya kuma siyo mata wasu
abubuwan da zata buk'ata na ayman sannan ya tafi.

Washe gari da kanshi ya shirya zuwa kaisu sumaila tun a hanya suka fara jin kewar
junan su sai dai yayi mata alk'awarin zuwa duk sanda ya dawo kano.

Yana kaisu ya juyo dan INdo har kuka tamai wanda da kyar ya lalla6a ta sannan ya
tafi bayan ya bata kud'i tak'i kar6a sabida akwai na barkar data samu a hannunta...

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICTEED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*Shafin yau naki ne m sweet heart SOFIYYA GALADANCI, I love you Allah ya nuna mana
ranar Auranki da rai da lafiya nasan ke ko...?🤨kawai dai Allah ya k'ara miki
baseera dear Bari nayi tsit*❤💘

Page *38*

Alama yayi mata da hannu ta saki labulen da aka nannad'e aka d'ora akan k'ofar
d'akin. Murmushi tayi tare da zaro idanuwa tana girgiza kai alamar a'a, ganin haka
yasa shi matsawa yana kallon k'ofar ganin babu me kallonsa yayi saurin sauke
labulen INdo tace.

"Kai.. Kai... Kai! ba ruwa na nidai Inna ce fa ta d'aga shi wai sabida akwai zafi."

Hannu yasa ya janyo ta kusa dashi yana kallon fuskarta, ya kaleta ya kalli Ayman a
hankali ya kai bakinsa saman goshinta ya sumbace ta INdo tasa hannu ta bayansa ta
rungume shi itama sannan ta kallesa tace.

"Ka zauna ka tsaya."

Hannunsa cikin nata suka zauna yana kuma rik'e da Ayman.

Kwantar da Ayman yayi a gefe kasan cewar yana cikin towel sannan ya juya yana
kallon INdo wanda ke kallon k'irjinsa dan wani iri taji da yadda yake mata wani
irin kallo.

"Sannu da zuwa, ya gurin su Mama?"

"Kin yi kyau cutie na, kinyi kamar ba me jego ba dan babu wani alamun da zai nuna
hakan meye sirrin?"

"Inna ce."

Ta bashi amsa tana wasa da yatsun hannunsa yayi murmushi tare da matso da ita kusa
dashi yana mak'alota jikinsa.

"Ko kawai ma idan zan wuce mu tafi tare tunda kun gama wanka ai kin fara sallah ma
ko cutie?"

INdo ta zaro idanuwa tana kallansa yayi murmushi yana d'aga mata girarsa kafin yaji
tace.
"Ta6... In bikafa kace? So kakeyi insha zagi kenan a cikin garin nan, kasan mu
bazan koma gidan ka ba dole sai an yi garar barka sannan za'a maida ni."

Kallonta yayi cikin rashin fahimtar maganarta ta sannan ta d'an zame ta janyo kayan
abincin ta tsiyaya mai lemo ya kar6a har yana cewa.

"Cutie ban gane abinda kike nufi bane wace irin garar suna? Kuma wazai kai? Wa za'a
bawa.?!"

"Kayan abinci ne ake kawowa gidan su me jego,su anan sun maida hakan kamar ibada
dan haka idan miji be yi ba sai abin ya zama gori har jikokin mutum."

"Ikon Allah, Allah guda d'aya amma garuruwa daban-daban ni ban ta6a ji ba koda wasa
wallahi. Toh idan kuma mijin bashida halin yi fa sai ayi ya ya cutie?"

INdo tana gyara k'afar Ayman ba tare da ta kallesa ba tace.

"Idan miji beyi miki ba shikenan sai a rabu dashi baza a mayar da ita ba. Idan aka
ga ya takura da zaryar zuwa gidan su kuma sai ad'auke ta a kaita inda bazai sake
ganinta ba har sai ya kawo kayan."

Sosai mamaki ya cika masa zuciya, lallai akwai d'inbin gyara a cikin kauyan nan
amma banda haka ya za'ayi a hana miji matarsa akan abinda ba alkurani bane ya
wajabta shi ba. Lallai yadda ya k'agu ta koma su tafi kwara state tare dole yaje a
harhad'o a kawo,yarinyar tayi tsada da yawa daga wannan sai ace maka wannan.

"In zuba maka yanzu ko sai kayi sallan azahar naga an kusa kirawo wa."

"Bari sai nayi sallah cutie, dawo nan in dinga jin duminki a jikina."

Matsawa tayi ya rungumeta, yana yawo a jikinta da hannunsa ita kuma ta lumshe ido
tana sauraransa. Sallamar su Uwani suka jiyo Sadeeq yayi saurin zame hannunsa daga
jikinta yana yatsina fuska yace..

"Su waye?"

"Inajin su Maryam ne naji muryar su da Uwani da Sahura."

"Kai nashiga uku ni Sadeeq, wai hardasu nake aure ne da kullum na shigo garin nan
sai sunzo sun samin ido? Ko 'yan uwanku ne cutie?"

"A'ah k'awaye nane amma kuma su haka suke duk inda sukaji labarin wani abun tofa
sai ka gansu sabida dama ba wani tambayar miji fita suke yi ba."

"Ai munafukai ne wallahi."

Ya fad'a a kufule kafin ya matsa sun shigo cikin d'akin bakunansu a washe.

Zama suka yi daga bakin k'ofar amma hakan be hana warin ranar jikinsu da kaurin
icen girki shiga cikin hancin Sadeeq ba ya tuna da tuni itama INdon haka take amma
Allah ya d'aukaka ta.

Da kyar ya amsa musu a ciki-ciki sabida yadda suke kallansu suna rik'e ha6a sabida
sunga sun manne jikin juna.

"Cutie zanyi alwala."

"Okey toh bari akawo ruwa k'ofar gida, ko zaka yi anan ciki."
"A'ah Inna na nan da dai bata nan sai nayi."

Tashi yayi suka d'an ra6e ya wuce sannan INdo ta fito suma suka bita a baya, tunda
tazo gida suke bibiyarta ganinta suke tamkar Matar wani shugaban me rik'e da wani
muk'amin.

Ruwa ta zuba tasa mayafi takai mai wajan mota sannan ta koma ciki.

Hira suka farayi dasu har aka idar da sallah Sadeeq ya dawo daga massalaci dan har
tsayawa yayi suka d'anyi hira da principal d'in tsefawa makarantar su INdo daya
bari.

Nafeesah ce ta kuma fita ta shigo dashi sannan INdo ta bishi su kuma su Uwani suka
ci gaba da hira da Inna duk da bata cika sanya musu baki ba.

"Cutie Ina baby na kika kaishi?"

"Inna ta goyashi ko na kar6osa?!"

"Ah no kyalesa kar ace nayi rashin kunya."

Waina ta zuba masa da miya sannan ta matsa kusa dashi, had'e hannuwa yayi a
k'ijinsa tare da bud'e baki alamar ta bashi da kanta.

Murmushi tayi tana girgiza kai ta fara bashi kunnuwansa har motsawa suke yi sabida
yadda miyar tayi mai dad'i idan ta bashi sau d'aya itama sai ya tura mata wanda ta
kuma d’ebowa yasa mata a baki haka suka dinga yi har suka kusa cinyewa yace ya
k'oshi.

"Cutie gaskiya ranar Sunday zaki koma zanyi duk iya yadda zanyi na tabbatar da an
kawo kayan nan, sannan direct za'a wuce dake can gidan marigayi acan zaki ci gaba
da zama an raba gado Abba yace idan kin koma zaizo yayi miki bayani kinji.?!"

Kifta idanuwa ta shiga yi alamar hawaye take son karsu fito ya janyo ta tare da
kamo fuskarta yana san saka kwayar idanunsa cikin nata.

"Karki zubar min da hawaye kinga nima ina tattala nawa, keda ma ba'ayi miki da yawa
ba tunda an baki me kamadashi iri d'aya sak sannan kina cikin zuciya ta kamar rai.
Ni kuwa tare muka taso mu kwana tare muyi fad'a mu shirya ba tare da kowa ya sani
ba, shine ni nine shi amma yau babu shi."

"Ka d'auka kaima a ranka nice shi tunda dama silarsa ce ta sa muka zama abu d'aya
dakai, na zame maka shi kaima karka sake yin kuka mun riga munyi *MUSAYAR ZUCIYA*
ni da kai fatana a yanzu shine na zama tauraruwa kamar yadda yake so yaga na zama
kayi min addu'a malama Hannatu tace addu'ar miji akan matarsa tana saurin kar6owa."

Bakinsa da yake ta motsi tun d'azu shi ya zura cikin nata cikin wani mugun
tausayinta da wata azababbar kaunarta da soyayyarta da ta taso mai. Kissing d'in ta
yake cikin wani irin salo wanda yasa INdo ta kasa gane kansa, ya shagala kawai suka
ji muryar malam Hamza a tsakar gida amma Sadeeq ji yayi tamkar a tsakiyar d'akin
yayi sabida tsabar tsoro.

"Na tafi cutie kar nayi abun kunya a gidannan a d'akin baba dan naga kema ba hanani
zaki ba."

Dariya INdo take yi sosai wanda tasa Sadeeq kallonta yana hararata dan har rik'e
ciki takeyi ya matsa can bakin k'ofa-k'ofa tare da maida hularsa yana jiran
shigowar malam Hamza d'akin dan yaji Inna tana cewa suna ciki.
"Matsoraci kawai Abu Ayman, uhm...uhm..uhm.."

INdo ta fad'a cikin dariya ya juya yana mata gwalo shima. muryar malam Hamzan yaji
a bakin k'ofar Sadeeq yayi saurin d'aga labulen ita kuma INdo ta fara matsar da
kayan da suka ci abinci kamar masu gaskiya.

"Baba sannu da shigowa, gashi duk mun tsare maka d'akin."

Sadeeq ya fad'a yana gyara zama tare da turo hula gaba yana kuma mai da ita baya
alamar kunya ya keji.

Malam Hamza yayi dariya tare da k'arasawa cikin d'akin ya zauna a bakin gadon sa
yana cewa ba komai Gaidashi Sadeeq yayi cike da girmamawa har suka d'an fara hira
ita kuma INdo ta kwashe kayan ta fita dasu can su Uwani aka ci ragowar ana
jinjinawa INdo ganin duk da kud'inta tayi wannan shagalin.

Malam Hamza da Sadeeq sun jima suna hira kafin malam Hamza ya fita INdo ta shiga
tare da d'ora mai ayman akan k'afarsa kasan cewar ta kar6o masa shi dan tasan yana
son ganinsa.

"Cutie ni kikawa dariyar mugunta ko? Hmmm zan rama ai zaki zo inda nake."

"Toh ai kaine da abin dariya wallahi."

"Za dai mu had'e you will see."

Kallon ayman yayi tare da cewa.

"Cutie wannan da wa yake kama sam na kasa ganewa?!"

"Ban sani ba nima kasan ance ba'a gane kamanin jarirai harsai sun fara girma."

"Ki dinga karanta mai ayatul kursiyu kina tofa mai a mad'igarsa ai kin iya ta ko?"

Tana kallonsa yatsan hannunta k'arami a cikin bakinta tace.

"Eh na iya mana."

"Matso nan toh kiyi min inji ko dai-dai ne."

Cikin jin wani iri dan kar ta kakare ta matsa jikinsa ya rik'ota, a hankali ta fara
karanto mai inda yaji zata 6ata wani gurin sai ya gyara mata harta gama sannan
yace.

"Yauwa ki dinga yi mai Allah ya kare mana shi daga sharrin shaid'anu."

"Amin abu Ayman."

"Zan wuce sai kinzo cutie ki yo shiri sosai dan wannan karan hmmmm."

Dariya ta kuma yi sannan ya zaro kud'i 10k ya bata ko zata yi wani abun idan zata
dawo sannan ya mik'e itama ta tashi suka rungumi juna kamar basa son rabuwa cikin
yanayi na ba haka aka so ba Sadeeq ya bata Ayman sannan ya fita suka yi sallama da
Inna su Uwani sai subirbid'a mai addu'ar sauka lafiya suke yi dan har lokacin suna
gidan.

A zaure Sadeeq yaga malam Hamza kan wata guntuwar tabarma yana gyaran redio suka yi
sallama bayan ya ajiye mai 5k yana ta godiya.

Yana shiga mota INdo tazo nan ma suka yi sallama ji yake tamkar ya tafi da ita amma
ba yadda zai yi dole ta fita yaja motar ya tafi cike da kewarta ji yake ma tamkar
basu had'u ba kamar yanzu ne ma yake kan hanyar zuwa ya gansu....

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

Page *39*

Tunda Sadeeq ya koma gida be sanar da kowa zancen da suka yi da INdo ba kasan cewar
baya son duk wani abinda zaija ayi mata gori akai ba. Gidan k'anwarsa Hawwa yaje
suka yi magana hakan yasa duk abinda ya siyo ita yake kaiwa ga shirin gidan da ake
yi mata wanda zata koma.

Cikin kwana biyu ya gama had'awa washe gari ana sauran kwana biyu INdo ta dawo yasa
aka kai hawwa gidan su INdon takai kayan. Sosai aka dinga murna ana yiwa INdo
barkar cewar mijinta ya fitar da ita kunya da kayan da babu wacce aka ta6a yiwa
kowacce mace irinsa a kauyan. Shiri tayi sosai ciki da waje Rukayya ta kawo mata
kayan INdo ta sake yin wani sassanyan kyau sam bata bari a sauya mata ak'idar da
take da ita dan yanzu a kauyan akwai 'yan matan da suke kwaikwayar shigarta da
kwalliyarta har yafa mayafi ma.

***

"Gaskiya Fateema kina da hakuri, ki duba ki gani a cikin shekara d'aya da auranku
kishiyarki tayi zaman gidaje gashi yanzu mijinku d'aya amma zata koma wannan uban
gidan na alfarma ke kina wannan duk da cewar shima yana da kyau amma nata yafi
girma da kuma kyau ya kamata kema kiyi bori wallahi asan yadda za'ayi dake."

Cewar wata malama da suke k'awance da Fateema tun zuwanta school d'in. Numfasawa
Fateema tayi tana jin k'irjinta na bugawa zuciyarta na zafi dan ta tabbatar da
zancen aunty Hafsat gaskiya ne, gashi uwa uba ita bata haihuwa duk da bata fitar da
rai da rahamar ubangiji ba a kan samun ciki.

"Amma ni ina ganin ba wani abun d'aga hankali bane Hafsat ganin dama tun farko a
cikinsa ta fara zama, karki manta gidan mijinta ne na farko kafin tazo mu had'e.
Kuma a k'ishin-k'ishin d'in da naji cewar an bashi gidan kinga dan ya mayar da ita
baxan d'aga hankalina ba tunda itace ta fara zama a cikinsa."

"Lallai Fateema toh ai nan gaba na san zaki gane abinda nakeso ki fahimta."

Murmushi tayi kawai bata son nuna hassada akan lamarin tunda taga wanda ya narka
kud'in yayi abunsa Allah be barsa yaji dad'in da ya tanadarwa rayuwarsa a cikin
gidan ba. Idan ta tashi hankalinta akan abun itama Allah sai ya d'auke ta aga ta
tsiya tunda kamar yadda Ummanta ta fad'a auran Sadeeq da Aisha Had'in Allah ne.

Shiga yayi gidan ya tarar tayi tagumi sam ba taji shigowarsa ba sai tsayuwar sa
taji Sadeeq ya zauna a gefenta yana kallonta. Murmushi tayi mai sai dai iyakarsa
le6anta kasan cewar ita kanta taga yadda yake rawar k'afar dawowar matarsa dan
yakan iya gaya mata zata dawo kusan sau biyar arana duk shigowa sai ya gaya mata
hakan yake bata mamaki har take tunanin ko yanzu ya dena sonta ne, duk da cewar be
sauya mata ba yana nuna mata soyayya fiye da tunanin me tunani.

"Baby tunanin me kike yi haka?"

"Babu komai baby kawai ina tunanin rayuwa ne."

"Hmmm da alama dai zaman kad'aicin nan ne yasa ki shiga tunani, toh na dawo kuma
bazan fita ba yau ina tare dake soyayya zamu yi."

Yayi maganar yana rik'ota yana shak'ar k'amshinta, ita ma tayi k'ok'arin Kawar da
abinda yake damun cikin ranta.

"Kai baka gajiya da aiki ne baby?"

"Ehmm kinsan ai ked'aya ce yanzu, kuma duka duka yaushe na dawo ai kinga nayi
k'ok'ari baby."

Dariya tayi tana shafa kanshi ya lumshe idanuwa. Wato mata biyu Lafiya ne daga nan
kayi nan babu fargaba bare tashin hankali dole maza suyiwa Allah godiya daya basu
wannan damar. Sai gaf da magriba ya samu ya fita bayan sallan isha'i suka yi waya
da INdo sannan ya shiga gidan ba tare da Fateema ta gane sunyi ba. washe gari ya
tafi Sumaila kauyan Sani yaje ya d'akko matarsa.

Yana zuwa ya buga mata waya ba'a d'auka ba sai gani yayi Sagiru ya fito, gaisawa
suka yi sannan ya sanar masa cewar tana wanka Sadeeq yace ba komai sannan Sagiru ya
koma gidan. Tana fitowa ta buga mai ya katse ya kirata da kanshi dan shine yafi
can-cantar yin hakan ba itaba.

"Cutie meye nayin wanka, da kin bari idan mun koma gida sai muyi tare."

"Hahaha..lallai a haka kake son na bar Sani zuwa cikin gari ko? Ban yadda ba gashi
na fito kaya kurum zansa sai mutafi."

"Shikenan ai tunda abun 'yar haka ne, ki turo a kawo min yaro na mu fara gaisawa
nayi missing d'insa."

"Okey shi zaka fara gani ba niba ma ko?shi kenan bari a kawo shi sai ku tafi ni
saina zauna a gidan."

"Wayyo cutie ki rufamin asiri I can die idan kika k'i bina Zuciya ta zata iya shiga
rud'ani zan iya rasa nutsuwa ta. Cutie kin zamo wani jego a cikin rayuwata Ina
sonki dan zan iya cewa nafi m twinnie kaunarki Ina jin zuciyata na bugawa a duk
lokacin dana tuna cewar bani na fara nuna miki soyayya ba but ki yadda cewar ni
d'in ina wahala a cikin raina da rayuwata idan bake a kusa dani, please kiyi sauri
ki fito mu tafi dan Allah."

"Gani nan fitowa barima a fara fito da kayan namu."

Tana fad'a ta ajiye wayan sannan ta lek'a tsakar gida ta kira su shehu suka fitar
da kayansu. Tsab INdo ta shirya Nafeesah ta shirya Ayman sannan ta fitar dashi, sai
da suka gama shiryawa ta fita kallansa tayi ta glass d'in motar tare da cewa.

"One minute."

Mak'ota suka shisshiga suka dinga yi musu sallama har sai da suka zagaye unguwar
sannan suka koma Sadeeq ya gaida Inna sannan INdo suka yi sallama da kowa na gidan
suka shiga mota Sadeeq yaja zuciyarsa shar daya juya yagan su sai yaji wani farin
ciki yana kuma ratsashi.

"Cutie me d'ah, wai ke dan Allah bakya mamakin hakan?"

"Bana yi, kai da ace fa marigayi be d'akko ni daga Saye ba da inajin yanzu 'ya'yana
biyu ko uku da wani saurayi na salele."

"Toh naji abar maganar waye wani salele ba ko dad'in ji. Cutie nayi missing d'inki
amma ke da alama kamar bakiyi nawa ba."

"Abu Ayman kenan, karka fad'i haka domin zaka zalince ni. Kawai ba yadda zanyi ne
ko na nuna babu yadda zanyi tunda ko a gidan ka na zauna dole baka nan amma nayi
missing dinka dan ma akwai Ayman ina kallonsa Zuciya ta na ganin kamar kaine shi
yasa kaga banyi ramar rashinka ba."

Dariya yayi hannunsa na ta6o k'afar Ayman, haka suka dinga hirar yadda suka yi
rashin juna har suka k'arasa k'ofar gidan marigayi wanda zata ci gaba da rayuwa a
cikinsa.

K'irjinta ne ya dinga bugawa Sadeeq yaje ya bud'e gate ya shigar da motar duk yana
ganin yadda ta sauya jikinta yayi sanyi hannunta dafe da k'irjinta idanunta a rufe.
Hannunsa INdo taji a wuyanta hakan ya sake tayar mata da hankali kawai sai ta sakar
masa kuka mai sauti.

Ayman ya k'ar6a kafin yayi wani abun su Haleema sun fito suna musu oyo-yo kasan
cewar suna ciki sune 'yan taryar su.

"Cutie ya haka? Kuka? Ohh ya subahanallahi danasan zaki kuka da wallahi baxan yadda
na kawoki gidannan ba, cutie bakya sona ko? Please dan Allah kiyi shiru bazan iya
barin ki fita daga motar nan ba alharin kina kuka dan kinga mun shiga nan gidan ba.
Ki dinga sawa a ranki nine Abubakar Sadeeq gaba d'aya ki tuna cewar kina da irinsa
kamar yadda nima nake ganinki a matsayinsa please."

Share mata fuska yayi sannan yasa hannu a baya ya d'akko jakarta ya zare powder da
kanshi ya shafa mata ya gyara mata fuskar ya sakar mata murmushi tare da cewa.

"Kinfi ma kyau yanzu da nayi miki kwalliyar kin ganki kuwa Son Sadeeq k'in wanda ya
rasa zuk'i..."

Dariya yaga tayi sannan yayi unlock d'in motar su Haleema suka bud'e tana kar6ar
Ayman tana cewa.

"Wai toh me kuke yi a motar kuka dad'e aunty Humaira."

"Toh gulmammiya ina ruwanki bana son saka idofa."


"Sorry broth sannun da hanya."

Shareta yayi yana hararta INdo dasu Aminatu suka shiga ciki shima yabiyo bayansu.
Kujerun d'ayan falon na ciki wanda ba'a shiga su aka dawo mata dashi falon farko
kasan cewar da nata aka kai mata can gidan Sadeeq dining room d'inta yana nan
tad'al-tad'al tayi fuskarta nason yin hawaye amma murmushi kwance a fuskarta
lokacin da take tuno yadda suka yi rayuwa da marigayi,Sadeeq ya shiga tare da kama
hannunta ya nufi bedroom su Haleematu suka zare idanuwa hannu rik'e da ha6a sannan
suka ta6e baki.

Suna shiga ya jata jikinsa suka tsaya wajan madubi yana kallonta. Hannu ya d'ora
saman k'irjinta yana wasa dashi bakinsa saitin kunnanta yace.

"What happen to my cutie angel ne? Aisha I love you but naga ke har yanzu akwai
marigayi a cikin zuciyarki kin kasa sanyani a ranki why.?”

Numfashinta na sama-sama sabida yadda taji yana mata murya a sark'e tana narke mai
sabida yadda k'afarta take neman kasa d'aukarta tace.

"Wa yace maka baka cikin raina? Shin duk yadda nake cewa kana cikin raina kazama ni
nazama Kai duk a tatsuniya kake d'aukar su?"

Juyo da ita yayi yana kallonta yace.

"Na kasa ganewa but prove me now."

A hankali ta sanya hannu a wuyansa ta sargafo shi tare da had'e hancinsu guri guda
cikin salo ta zuro bakinta cikin nasa Sadeeq yayi saurin kar6ar sakon tare da
rik'ota shima. Kukan Ayman ne ya sanya suka tsaya da abinda suke yi jin kamar
hanyar d'akin aka yo dashi, sadeeq na matsawa sai ga Sajida da Ayman tana cewa.

"Aunty Humaira wai kuka yakeyi inji yayya Haleema."

Kar6arsa tayi sannan ta fita Sadeeq ya zauna a bakin gado yana cewa.

"Wallahi munafincin Haleematu ne dama naga take-taken su nasan ganin gulma."

INdo tayi dariya tana k'ok'arin ba Ayman.... Sadeeq ya mik'e yana cewa.

"Bari naje na maida su gida bana son kinibibin yaran nan."

"A'a dan Allah ka rabu dasu kana ganinfa ko gaisawa bamu yi ba."

"Yanzu cutie kin fison su zauna akan ni na zauna?!"

"A'ah ba haka nake nufi ba, amma kaga ba dad'i ka kyalesu basu yi niyar tafiya ba
toh ka kyakesu dan Allah."

"Shikenan toh bari naje d'ayan gidan ai Fateema na nan."

Yana fad'a ya fita INdo ta bishi da kallo, ai dole yace haka tunda ta dawo gurin
sa. Tashi tayi ta koma falo wajan su haleema suka fara murnar dawowa da hirar
yaushe gamo.

Sai da akayi magariba sannan su Haleematu suka tafi ita kuma ta cigaba da gyara
kayanta. Har kusan tara na dare Sadeeq be shigo gidan ba hakan ya 6atawa INdo rai
ganin ko dai ya dawo da itane dan ya fara wulak'anta ta. Shirin bacci suka yi itada
Ayman gashi ko gen ba'a kunna musu ba kuma bata damu ba domin a can gidan su ko
wearing na nefa basu dashi, tana gamawa tayi kwanciyar ta zuciyarta na k'una ta
janyo pillow ta rungume tare da rufe idanuwa.

Sai wajan 10:15pm ya shigo hannunsa rik'e da ledoji, kayan ya ajiye a falo sannan
ya fita ya tayar da injin taja tsaki tamkar yana gurin ta kuma rufe idanuwa dan ba
k'aramin haushinsa takeji ba na watsar da su d'in da yayi.

"Cutie..! Cutie..!"

Yaji shiru sai ya shiga cikin d'akin, kwance ya gansu da alama sunyi bacci ya
lalla6a ya k'arasa kusa da ita yana son juyo da ita yaji tayi tauri hakan ya
tabbatar masa da cewar idanunta biyu.

"Haba cutie ba Oyo-yo shine zaki zo ki wani kwanta tashi muje falo."

"Sorry bacci nake ji ka koma inda kafi so."

"What..?!"

Banza tayi mai ya kuma komawa wajan fuskarta yana matsa hannunta yace.

"Amma ki bari sai munzo kwanciya sai muyi wannan wasan but yanzu dai taho muje
falo."

"Nace kayi tafiyar ka wajan matarka, nasan dama can itace za6in zuciyar ka bani ba
da aka lik'a maka, toh kaje katafi gurin Fateema daka fi so na bar mata kai. Banda
mutuwa ma me fallasa ai da hakan bata faruba bare kamin wulak'anci harda cewa toh
kaima ka tafi wajan Fateema shine sai yanzu goma da wani abun zaka ce ka dawo in
tashi."

Ta k'arasa maganar cikin kuka tare da tura fuskarta k'ark'ashin pillon da kanta
yake kai. Ba k'aramin tashin hankali Sadeeq ya shiga ba jin abinda take fad'a, ya
janyo ta yana lallashi kan ta sanar mai da abinda yayi mata amma tak'i, har zai
rabu da ita yaji bazai iya ba sabida zuciyar da take tsananin sonta tak'i jin
haushinta sai ma k'ara k'ask'antar da kansa da yayi yana cewa.

"Kinga ba wai da gangan kika ga nayi dare haka ba no, ana yin sallahn magrib muka
tafi gidan wani malami nida Abba bamu dawo ba sai bayan sallahn isha'i naje nakaisa
gida sannan nayo muku siyayya naje ko dad'ewa banyi ba a gidan Fateema nayo nan
amma shine zaki min wulak'anci ko? Shikenan tunda har kin fara yi min mumunan
zato."

Yana fad'a ya fara k'ok'arin sauka a gadon sai kuma yaji ta rik'osa, itama bazata
iya fushi dashi ba ya lek'a fuskarta ta kallesa sannan ya tashi tare da d'agata
suka nufi falo.

"Cutie ki dena min saurin fushi bana so yana sani cikin damuwa da tashin hankali
kinji?!"

"Toh amma nima ka dena barmin gidan ka dad'e baka dawo ba tunda kana garin."

"Insha Allahu."

Ya fad'a, kitchen taje ta d'akko plate da cups ta dawo. Gashasshiyr kaza ce da aka
sanya mata kwai tasha kayan lambu ga yajin tafarnuwa suka zauna suka ciyar da juna
ranar sunyi kwanan farin ciki marar bayyanawa bare rubutawa.

Satin INdo uku da dawowa da kyar da nuna jajircewar shine mijin ba ita ba ta yadda
zata bisa zuwa kwara state sabida ta kafe ita karatunta zata koma amma yak'i har
kuka tayi suka yi fad'an kwana biyu amma yaki sakkowa dole ta hakura ta bisa suka
tafi aka bar Fateema...

Nd Page finale is loading🤨


#love you
#my fan's

*HAJJA CE*👈
[7/31, 5:13 PM] Aisha Galadima: *⚗⚗ MUSAYAR ZUCIYA...⚗⚗*
♥♥

A true life story

Na

*K.A.S Precious Hajja ce*👈

*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡


(Home of expert & perfect writer's)

*DEDICATED TO:* Sanah Isma'il Matazu.

*TUKWAICI GA:-* Dota Fateema (Marok'i).

*DAN JIN DAD'INKI:-* Billy S Fari.

*VOTE me on wattpad @Hajjac*

*End*

Page *40*

Tun a cikin mota suke yin fad'a k'asa-k'asa yadda ba kowa ne zai gane ba bare aji.
INdo mita kawai take masa sabida tsabar ta gaji da zama bata ta6a yin tafiya irin
me nisan haka ba gashi tun a cikin motar ta fara ganin ban-bancin kano da inda za
suje domin duk cikin motar yare ne basufi su shida bane hausawa kuma suma ba wai
zaune suke a guri d'aya ba kowa yana kan kujerarsa. Wani yare dake kusa dasu yana
ta kallon Ayman ya zuro hannunsa yana shafar kanshi tare da tambayar INdo ya sunan
d'an cikin yarbanci k'irjin INdo ya dinga bugawa jin bata gane abinda yake nufi ba,
sai kallon mutumin take shi kuma yana faman kuma tambayarta. Kallon Sadeeq tayi
kawai taga yayi tamkar baya jinsu yana karanta jarida tasa hannu ta zunguro shi ya
kalleta sannan ta kawar da kai tare da cewa.

"Ana maka magana fah."

Kallonta yayi yana k'umshe dariyar sa kafin ya kalli bayeraben sai taji ya gaya
masa sunan Ayman bayeraben ya jinjina kai bakinsa a washe ya cewa Sadeeq yaron yana
da kyau Sadeeq yayi dariya duk babu abinda INdo taji a cikin maganar gashi sai
dariya bayeranen yake hakan ya sake k'ona mata rai domin abinda take gudu ne yake
shirin faruwa wato a dinga magana bata son me ake cewa ba. Sun tsaya anyi sallah
anci abinci an rage mara sannan suka kuma d'aukar hanya ran INdo ba k'aramin 6aci
yayi ba har suka k'arasa garin cikin tsakiyar dare. Duk da tayi bacci a mota amma
ji take tamkar bata ta6a yin bacci a rayuwarta ba, ko wanka bata yi ba dakyar ya
samu tayi sallan magrib da isha'i tabi lafiyar gado.

Da kyar Sadeeq ya samu ta farka k'arfe takwas tayi sallah dan tunda ta kwanta ba
tayi juyi ba, ko kukan Ayman bataji sai dai shi ya farka ya ciro.. sannan ya samai
abincinsa a baki idan ya saki kuma sai ya mayar mata sam bata sani ba sai da tazo
suna gaisawa yake bata labari suka dinga dariya. Fita Sadeeq yayi ita kuma ta shiga
taga yadda gidan yake bayan ta goya Ayman. Be jima ba ya dawo hannunsa rik'e da
leda yaje kitchen ya juye musu abincin daya siyo musu suka tafi falo.

"Wannan kuma bak'in abun menene haka."

"Amala ce da miyar ayayo da dad'i kuma cutie ci kiji."

Zama tayi suka faraci tana sawa abaki ta dinga yatsina fuska daga k'arshe ta matsa
ta had'iye ta cikin bakinta da kyar. Sadeeq ya kalleta cikin mamaki yace.

"Cutie ya haka? Ba kya ci ne?"

"Gaskiya bana ci wallahi wannan abu a samo min wani."

Shima jiyayyi sam ba zai iya ci ba duk kuwa da son amala da yake yi. Kallonsa tayi
tana goge hannu cikin shagwa6e fuska tace.

"Kuma ni yunwa nakeji wallahi kamar inci babu, ko cinyeka nayi ji nake bazan k'oshi
bama gashi da Ayman ya farka zaice zai sha kuma babu komai a ciki wallahi duk ya
tsotse."

"Kai cutie wai ba komai a ciki, toh duk meye wannan abun a ciki?!"

Yayi magana yana kallonta da mamaki, ta kuma narkewa cikin nuna jin yunwa sosai
tace.

"Shikenan tunda baka yadda ba, ni dai ka samo min abinci."

Tashi yayi da sauri tun yanzu yaga ban-banci tsakanin su da Fateema domin duk
abinda ya siyo ko bata ta6a ciba toh zata ci amma ita common amala tace wai ba
dad'i. Tunani ya dinga yi yana neman abinda zai siyo mata gasu da shegen tsadar
abubuwa daya rasa yadda zai yi kawai sai yaje gurin wata k'awarsa cinyere da take
dafamai abu idan bezo da Fateema ba yasa ta dafa mai indomie da ruwan tea ya kar6a
ya kai ma INdo, harda su murmushi tayi mai sabida ganin abinda zata iya ci. Kad'an
yaci kasan cewar bata damesa ba ita kuwa taci sosai kad'an ta bari tasha tea sannan
walwalarta ta dawo taje kuma ta dinga narke mai tana takura mai.

Satinsu d'aya da zuwa garin babu inda INdo take zuwa ko lek'e batayi ba, aranar
kuma ya fara fita gurin aikinsa yana tafiya ita kuma tana gyaran gidan sai ga wasu
'yan mata kowacce da 'yar bingilar riga da mini skirt suka shigo.

"Madam excuse us,can we come in please?"

INdo ta bisu da kallo ita kuwa me ya had'a ta da arna da har suke neman shigo mata
gida? Ganin tayi shiru ne yasa d'aya daga cikin su tace.

"We are friends of your husband,can you let us in..Mrs sadeeq?!”

"Me..? For what reason??"

"Don't get wrong Mrs sadeeq,we are friends of sadeeq ,we just came by to see his
newly born baby”
Shi kuma ya rasa da suwa zai yi k'awance sai da mata dan rainin hankali, toh baxata
bada d'an su ganshi ba bama su da kunya basu santa ba kawai zasu wani zo k'ilama
k'arya suke salon su sace mata d'ah ne.

"Madam please..."

"Eyyah m sorry he is sleeping.."

Ta fad'a tana d'ari-d'ari kar su gano cewar 'yar koyo ce a cikin yaren turancin.
Suka ce zasu dawo anjima ko gobe, suna fita ta kulle gidan bata bud'e ba sai da ya
dawo ya buga mata waya taje ta bud'e.

"Ya aka yine cutie wallahi yanzu kin fiye rigima kamar ma k'aruwa take yi. Sam
kamar baki haihuba yanzu kuma meye ya faru ko yaro nane ya ta6oki ne..?!"

Yana rik'e da hannunta suka shiga falon ta kuma had'e rai ya juyo da ita suna
kallon juna yace.

"Gaya min menene ko kina nufin dad'ewa nayi ban dawo ba?!"

Zaunar dashi tayi taje ta kawo ruwa yasha kad'an sabida baya tare da k'ishi dan kar
tayi zargin wani abun ne yasa shi yasha. Zama tayi Ayman na kan kujera yana bacci
ta kwantar da kanta a cinyarsa yana jan hancinta tace.

"Bayan ka fitane wasu mata arnaye gunduma-gunduma suka shigo su hudu ko wacce da
wani banzan skirt, wai dan son maidani wata sakarai suke ce min sunzo ganin Ayman
ne wai ka gaya musu kanada d'ah."

"Ohh su Juliet ne da blessing sauran ne dai ban gane ko suwaye ba. Toh kin basu sun
ganshi ko?"

"Kut in basu kuma..?! Wai kaima ka d'auka har yanzu bani da hankali ne? Kawai ban
san su ba baka yi min bayanin su ba zan d'auki d'ana na basu, lallai da hankalina
wallahi yanzu ba dah bane."

Kallonta yake shi yanzu baya ganin wani aibunta komai tayi sai yaji zuciyarsa ta
aminta da abun koda kuwa yana son yi mata gyara. Hannunta ya rik'o ya sumbata
sannan ya fara shafar fuskarta yace.

"Cutie su Juliet mak'otan mune wannan benan na jikin mu shine gidan su, please ki
bari kuyi mutunci musulunci be hana ba suna da kirki basuda matsala suna ganin
girmana sosai."

"Lallai in rasa da wad'an da zanyi k'awance sai da arna wallahi ba ruwa na bazan yi
ba sam."

Shafa kanta yayi lallai ashe akwai gwarmai domin idan yazo da Fateema suna zuwa
kuma bata kyarar su hakan yasa suka saba ita kuma ko me ta d'auki Christians oho
mata. Share zancen yayi ya d'agata tare da janta suka shiga kitchen dan yaga alamar
har lokacin haushin bak'in basu barta ba.

"Cutien Sadeeq da Ayman a dafa min wannan abun."

Yafad'a yana ciro wani magani a cikin aljihunsa, tana tsaye tasa shi ya d'akko
tukunya tace ya tari ruwa a sink ta kunna gas ya zuba maganin yana dariya k'asa-
k'asa dan dama yasan INdon sa tun a tsefawa 'yar rigima ce dan haka yanzu in tayi
abin bazai damesa ba sosai kuma tafishi gaskiya tunda bata sansu ba tayi hankali da
ta hanasu dan za'a iya zuwa a damfareta hakan kuma da tayi ta nuna mai ba da kowa
zata dinga yadda ba kamar yadda wasu suke ganin hakan cinyewa ne sai kuma an cucesu
suzo suna kuka. Har ya dahu suna kitchen d'in tana ta6ara.

"Muje falo naga wasu littattafan turanci, tunda maganin ya dahu kafin ya huce na
karanta maka kaji."

Hannunsa ta fara jah yayi saurin rik'ota tare da girgiza mata kai ta had'e rai.
Maganin ya d'auka ya kai bathroom ya juye cikin bahon wankan Ayman sannan ya mayar
da tukunyar kitchen ya kalleta ta zauna kan kujera sai cuno baki take yi ya zauna
kusa da ita yana rik'o hannunta murya a sark'e yana narke mata idanuwa yace.

"Cutie rigima, zo muje ai naki ne shiga ciki zaki yi."

INdo ta zaro idanuwa fuskarta a d'aure tana mai wani irin bahagwan kallo, ganin
yadda take kallansa a hagunce yasa shi shafar fuskarta yace.

"Whats wrong?"

"Shin bakajin nutsuwa dani ne ko kuwa dai wani abun kakeji a tattare dani? Ko kuma
me kake nufi malam Sadeeq da zaka kawon abu wai in shiga ciki...?!"

Hannu yasa ya rik'e kansa tare da rintsa ido jin yadda ta mayar mai da abunsa.
'Dagowa yayi idanunsa jawur sabida yadda ransa ya sosu dajin abinda tace ba tare da
yayi magana ba ya d'auki phone ya kira Fateema bayan ya had'iye 6acin ransa.

"Hello baby na ya aiki? Yasu my sweet Ayman?!"

"Lafiya lau baby ya skull kin dawo ko?"

INdo ta mik'e zata bar gurin yayi saurin rik'ota ta fara k'ok'arin kwatar kanta dan
wani haushinsa takeji. Ji tayi ya cigaba da yin wayarsa hankali kwance kafin taji
yace.

"Ammm baby ko kina son na taho miki da wannan ganyen maganin naga wannan zuwan ma
na kawo shi kina so?!"

"Woww babyna ina so mana dan Allah kaje ka siyo karya k'are please my awesome
husband."

"Okey tom zan kawo miki insha Allahu bye zan kiraki anjima."

"Thank you baby a gaida min da Ayman my son."

"Insha Allahu."

Kashewa yayi yana kallon INdo wadda still fuskarta a had'e take. Janyo ta yayi ta
fad'o jikinsa tana turesa ya matseta tare da zura kansa saitin wuyanta yace.

"Banyi tunanin cewar akwai abinda zan saki kiyi amma ki tsaya tuhumata ba, Aisha ko
wuta na rura nace kishiga hakan ya nuna min bazaki shiga ba sabida bakya sona da
kina sona duk abinda zan ce kiyi bazaki tsaya wani tunani ko gaddama ba sai gashi
kinyi na gani shi kenan na gode Allah yaso ina da wadda ta yadda dani 100%."

INdo najin haka ta saka kuka shi kuma ya tureta ya juya kan kujerar yayi kwanciyar
sa duk da yanajin kukan har cikin k'ahon zuciyarsa. Tashi tayi a hankali tana kukan
ta shiga bathroom, shiga tayi cikin ruwan tana ciki tana jan majina yayi murmushi
ya kuma k'i bin bayanta, bata fito ba har sai dashi kansa yaga dacewar lokacin
tafito yayi amma tak'i fitowa.
Zaune ya ganta a ciki ta saka fuskarta tsakankanin jinyoyinta sai gunjin kuka
takeyi, k'arasawa yayi ya tsugunna a gabanta tare da saka hannu ya fara k'ok'arin
d'ago fuskar ta amma tak'i ta kafe. Taurin kai na INdo sai addu'a ya mik'e tare ya
d'agota cikin nuna k'arfi sannan ya fito da ita suka shiga bedroom yana rungume da
ita suka zauna a bakin gado.

A gabanta ya zauna tare da rik'o hannunta kanta a k'asa idanuwanta a rufe sai faman
sauke ajiyar zuciya takeyi. Kallon fuskarta yakeyi cikin tsananin sonta da kaunarta
yace.

"Cutie nine fah ya kamata nayi kuka sabida kin kasa yadda dani, cutie i love
you..ban san yadda zanyi na misalta miki ba duk abinda kikaga nayi dan ina sonki
ne. Cutie koda kikaga na dage sai kin biyoni nan karkiyi tunanin cewar ko bana son
kiyi karatune a'a ina son zuwa dake ne sabida ko bayan rai na kiyi alfaharin kema
naje dake inda nake zuwa shi yasa kika ga na dage sai kin bini amma duk abinda nayi
miki na rashin dad'i cikin sani ko rashinsa kiyi hakuri ki yafemin."

Hawaye suka kuma zubo mata ya tashi ya zauna kusa da ita tare da janyo ta jikinsa
yana buga bayanta cikin muryar kuka take magana.

"Ni ka dena bani hakuri bayan baka min komai ba, nice zan baka hakuri sabida nice
nake 6ata maka rai amma dan Allah abu Ayman kayi hakuri ka dinga yafemin koda a
cikin zuciyar kane nasan ina 6ata maka rai dan All..."

A hankali yasa hannunsa ya toshe mata baki yana kad'a mata kai alamar tayi shiru,
da sauri ta rungumesa suka k'ank'ame junansu cikin shauk'i. Basu fito ba sai da
kowa yasan ya farantawa d'an uwansa sannan suka yi wanka suka ci gaba da soyayyarsu
yana kuma koya mata karatunta cike da kwarewa yadda kuma zata gane ta fahimta duk
da cewar tana d'an dad'ewa kafin ya zauna a kwakwalwarta danma understanding takeyi
ba wai hadda ba.

Bayan sati uku

Lokacin sun cika wata d'aya da zuwa cikin ikon Allah kuma ya samu INdo ta fara
sakarwa su blessing fuska sai dai yawanci sunfi yin wasa da Ayman kasan cewar
turancin INdo ba nisa yayi ba kamar su da yazama shine yarensu na biyu da suke ji
bayan inyamuranci. Itama takan d'an lek'a gidan su amma ba sosai ba dan su kan yi
yarensu wanda yafi bawa INdo haushi sabida ko "zo" bata iya ba su kuma sunfi yinsa.

Sosai suka sake kulla babin soyayya dan zaman su anan su biyu ya kuma kulla sabuwar
alak'a dan har basa son wani yayi nisa sukanji har zazza6i amma da an had'u sai a
warke zuciyar su ta riga ta zama d'aya, duk abinda d'aya yakeji wala na dad'i ko
rashinsa sai duk sunji yanayin a jikinsu, ciwon kai idan d'aya yayi sai d'ayan ma
yayi koda kuwa fad'uwar gaba ce wannan yanayin yana basu mamaki da al'ajabi, sun
kuma sake tabbatar da cewa sunyi *MUSAYAR ZUCIYA* ya kar6i tata itama ta k'ar6i
tashi suna kula da junansu sannan ta rage yi masa taurin kai musamman da yake
karanto mata tarihin annabawa duk dare idan sunje bacci.

Ayman yana ta wayo suna kula dashi sosai sannan koda second d'aya Sadeeq be ta6a
manta Fateema ba yakan buga mata waya a rana kusan sau biyar yayi missing d'inta
sosai domin ko wacce mace tana da nata matsayin a zuciyar miji musamman da ya kasan
ce ita ya fara furtawa kalmar So ya kuma fara auranta ya fara saninta a matsayin
matarsa. Yana jin dad'in zama da matansa su duka musamman yanzu da soyayyarsa ta
kuma zama a cikin zuciyar INdo, yafi ta sonta amma yakan daure domin karya d'ora
mata girman kai karta dinga d'aukar kanta a wani abun tunda yanzu ne yake d'orata
akan sabuwar rayuwa dan yanzu ne take kuma sanin komai na rayuwa duk abinda ya
d'orata akai zai ga shi takeyi bata ta6a k'etare duk wani abu da ya karanto mata ya
fassara mata.
Watansu biyu suka shirya komawa lokacin INdo ta kuma wayewa tayi kyau tayi k'iba ta
zama tamkar wata k'aramar hajiya tayi dam kwanciyar hankali ya fito a jikinta da
yanayinta dama yadda take gudanar da abubuwanta dan takanji zata iya gogawa da ko
wacce irin mace a fad'in duniyar nan duk da cewar iliminta bema kai na Fateema ba
amma yadda zata gudanar da wani abun sai mutum ya rantse ko tana kanyin master's
ne.

*****
Kwance take a jikinsa tana kuka domin ba k'aramin rashinsa tayi ba wata biyu ba
wasa bane a gurin miji da mata musamman idan basu tare. Gashinta yake shafawa yana
kuma rik'e da hannunta yana matsawa Sadeeq yace.

"Baby dan Allah kiyi shiru kinga dai ba zuwa nake garin can ina yawo in dawo ba,
kinsan abinda nakeyi kinfi kowa sani tun kafin kowa ya sani hatta Abba kin fishi
sanin me nake zuwa inyi dan haka bana son kukan nan please yana sani cikin shakku
da kokwanto."

"Toh baby amma dai ka dena dad'ewa dan Allah. Ko kuma ka tattaro ka dawo nan kano
shikenan kana tare damu koda yaushe."

"No... Fateema bana son zaman garin nan ga sa'ido sai dai ke idan kin yadda ki
ajiye aikin ki idan zan tafi sai na tafi dake na ajiyeki a can kinga na huta kina
can bani da fargaba ita kuma Aisha tana nan kun hutar dani ma."

"Nayi shiru baby nigara ku dinga tafiya da ita can babu kowa d'an uwa dangi duk
babu sai sababbin da zaka yi na hakura zan dinga jiranka har lokacin da zaka dawo."

"Ummm kaji me wayo, wato ke k'ink'i bina sabida aikin ki. Amma ni kina son na dawo
nan da zama shi kenan kullum a ce mijinku yana guri d'aya baya zuwa konan da can
toh na gano ki kuma nak'i wayon."

Ya fad'a yana mata cakulkuli a cikinta suna ta dariya dan baya son yaji ta sako mai
zancen rashin haihuwarta sabida shi be ta6ajin haushin hakan ba ko yaji sonta ya
ragu a'a kullum yana jin sonta musamman da take mai biyayya da nuna soyayya.

Haka Sadeeq ya cigaba da rayuwa da matansa cikin kwanciyar hankali duk da wani
sa'in yakan fuskanci matsala ta kowane 6angare amma yakan warware ta cikin hikima
ta yadda ya san halin kowacce a cikin su. 'Daukar su yayi su duka sukaje aka yi
musu hoto ya bud'a su ko wane gida yasa d'aya guda d'aya babu kuma wadda ta nuna
mai bata so.

****
"Hello, Rasheedat. Okey ai zan shigo nan da 11:00 tuna sai 11:30 ko.? Okay sai na
shigo."

Kwance yake akan kujera INdo na k'ok'arin zuba masa fruits salad duk tana jin
abinda yake fad'a ranta yayi mugun 6aci zuciyar ta na zafi kishi ya turniketa sai
faman had'e gira takeyi. Tashi tayi jikinta har rawa yake yi taje takai mai fruit
salad d'in ya d'ago ya kalleta ganin yanayinta yasa shi riko hannunta ta fizge ya
kuma rikowa ta kuma k'ok'arin fizgewa ya janyo ta kusa dashi ta zauna kirjinta sai
dokawa yake yi Sadeeq yace.

"Toh yau kuma me Sadeeq sarkin 'yan masu laifi yayiwa cutien sa cikin 'yan
sakanni.?!"

"Ba komai kyale ni zan shiga d'aki."

"Toh ki fara bani na gama sha sai kije kiyi aikin ki."
INdo ta kuma yin kicin-kicin a kufule tace.

"Ka kira Rasheedat ta baka mana amma ba ni ba."

"Rasheedat kuma cutie? Kin santa ne ko kuma dan kinji muna waya ne zuciyar ki ta
fara halin nata."

Turo baki tayi tana harare-hararen gefe ta kasa cewa komai, Sadeeq ya janyo ta
jikinsa yasa hannu a tsakiyar k'irjinta yaji yadda yake bugawa cikin tashin hankali
ya mik'e zauna dan da a kwance yake yana rik'e da ita.

"Subahanallahi cutie kishi ne haka? Rasheedat ba budurwata bace d'alibata ce yau


zanyi musu lecture shine take tambaya na shin zanje nace eh su shirya shikenan fa."

Sadeeq yana jin sanda ta sauke wata muguwar ajiyar zuciya sannan ta kallesa ya
sakar mata murmushi tace.

"Toh banda basu da kunya meye na bugo maka, su ba students bane baxasu jira har
kaje ba zasu wani bugo maka waya. Ina monitor da bazai bugo ba sai ita tana mace
banzar kawai."

"Ta6 cutie har ina cewa zan k'ara aure sai kema na barki anan ki cigaba da
karatunki Fateema tayi aikinta ita kuma amaryar na barta acan kwara gidana na
Ilorin kunga an huta da zirga-zirgar fitar ku."

Share sa tayi ta d'ibi fruit d'in a cokali ta sanya mai a baki, yana dariya ya
kar6a har ta gama bashi sannan ya janyo ta k'irjinsa yace.

"Cutie I love you zan iya mutuwa a duk sanda kika juya min baya, ki kula damu dani
da yaro na dama wad'anda zaki haifamin nan gaba please cutie."

Sumbatarsa tayi a goshi sannan ta kwantar da kanta a saman k'irjinsa tana shafar
kansa tace.

"Nima ina sonka my super glue, your my Biggest comport..my breath... My heartbeat..
Kai my everything but ka dena min zancen zaka k'ara aure, a cikin shekara d'aya
kayi mata biyu sannan kace kana shekara ta biyu zaka yi ta uku ai sai ka jamana
surutu. Dan Allah ka barmu mu biyu ka dena tunanin wata idan ba haka ba zanyi
kuka."

"Yi muga irin kukan da zaki yi idan zan k'ara au..."

Tayi saurin toshe mai baki da nata kafin ta cire ta kalli cikin idanunsa daya bud'e
su a hankali duk sun zama na rigima tace.

"Haka zanyi uhm..uhm..uhm..ahhh..wayyoooo...!"

Suka kyalkyale da dariya Sadeeq ya rungumeta akan kujerar yanajin k'aunarta har
cikin ransa. Sun dad'e suna faranta ran juna duk sun manta da rigimar su ta baya
Sadeeq ya kawar da rayuwarta ta baya a cikin ransa yana ganin tamkar dama a hakanta
ya santa. Watan Ayman takwas kenan har gidan Fateema ake kaisa ya d'an jima kafin a
dawo dashi tana son yaron har cikin ranta domin tana masifar son mahaifinsa.

*****

K'arfe takwas ya shiga gida, zaune ya ganta tana gyarawa Ayman kwanciya a falo,
dariya yayi har yana rik'e ciki ganin yau kuma da salon da za'a siyeshi can ta
tsuke cikin riga da wando nan kuma tayi mai shigarta daya santa a real INdon ta
zamanin tana kauyan sani.
"Kai malam Sadeeq he wani kallona kakeyi he kace baka sanni ba."

Wayyo dariya Sadeeq ya tsugunna agurin ya dinga yi dan gani yake tazo mai da wani
sabon salon soyayya. Ta dashare mai baki tare da k'arasawa wajan sa tasa hannu ta
rik'osa da nufin ya tashi aikuwa ya janyo ta itama ta fad'a kansa suka dinga dariya
cikin shauk'i.

"Cutie I love you so much."

"I love you too Abu Ayman."

"Allah yajik'an M tiwwine yasa rahama ta baibayesa yasa yana cikin farin ciki kamar
yadda muke a yanzu."

"Amin ya Allah."

Ta fad'a tana wasa da ma6ullayen rigarsa nan suka dinga hirar baya suna dariya.
Shirye-shiryen bikin Haleematu suka farayi Sadeeq yayi k'ok'ari sosai dan da su
biyu suke had'uwa suyi komai shi yayi kayan d'akin hawwa Abubakar kuma yayi na falo
amma yanzu baya nan daga shi sai Abba suka dinga yin komai. Duk matan sa kuma sun
zage anyi komai dasu cikin farin ciki dajin dad'i, suna nan kuma har yanzu a tare
mijin su yana sansu iya gwargwado yana bawa kowacce hakkinta.

ALHAMDULILLAH.

Allah na gode maka daka nuna min farkon labarin nan da kuma k'arshensa, Allah kaine
abin godiya kuma abin alfahari alhamdulillah. Allah kajik'an marigayi kasa aljanna
ce makomarsa da aiyukan alkairinsa. Duk wad'anda suka rigamu gidan gaskiya a cikin
musulmai Allah ka yafe musu mu kuma kasa mu cika da kyakkyawan aiki.

Dole na godewa masoya masu kaunar Hajja ce da kuma rubutunta, hakika wannan novel
d'in ya sadani da mutane masu d'in bin yawa wad'anda baki baxai iya fad'ar yawansu
ba, haka kuma hannu bazai iya k'ididdige yawanku ba sai dai nace Allah yabar
soyayya da kauna tsakaninmu yasa sakon ciki ya amfanar daku. Nasan na 6atawa wasu
rai toh dan Allah kuyi hakuri, nasan na farantawa wasu rai toh kuma kun faranta
min, nasan na nishad'antar da wasu nima kun sani nishad'i kusani reader's kune
jigon saka duk wata writer cikin farin ciki haka kuma kune kuke saka writer cikin
damuwa domin idan bakwa karantawa bazataji dad'in yin rubutun ba duk kuwa dason yin
rubutunta nidai na gode muku masoya na fili dana 6oye na kusa dana nesa bazan iya
lissafoku ba domin hakan ya janyo min fitina harma wasu daga cikin wad'anda nake
alfahari dasu suka gujeni sabida ban yi musu dedication ba amma still suma idan sun
karanta karshen page dinnan suyi hakuri ni 'yar Adam ce me laifuka kala-kala a
doran k'asa suyi hakuri but bazan manta dasu ba a cikin zuciya ta ba.

*K'ANWATA STYLISH.*:-Dake aka shirya za'ayi rubutun nan kika gudu kika barni, but
ba komai nasan dama ke lazy writer ce (smile) nayi na gama kuma na gode miki da
sake zakulo min muhimman abubuwan cikin labarin Allah ya barki da mijinki Lafiya
keda k'anwarki Abler.

*MISS XOXO:-* Bazan iya kammala rubutu na ba ban sakoki ba koda kuwa wasu zasuji
haushina, kin taka muhimmiyar rawa a cikin rubutuna ta yadda nake hanaki bacci nake
hanaki jin dad'i har sai kin bada taki gudun mawar hakan kuma yasa labarin ya tafi
cikin tsari da jin dad'in karanta shi, Allah yayi miki albarka ya nuna min lokacin
auranki autarees Ina alfahari dake ked'in masoyayyar Hajja ce wanda babu algus.

Ina alfahari da duk me bin labarina grps d'in da nake ciki da wanda bana ciki Ina
alfahari daku. 'Yan wattpad ina alfahari daku Ina sanku har cikin kalbina kud'in na
daban ne. My co-writer's da suka bi labarin nan ku sani naji dad'i sosai duk da
wasu na sansu wasu kuma ban sani ba amma sun karanta Ina fatan duk wacce taga gyara
ko kuskure zata yi min domin Ina son hakan Allah ya k'ara baseera da kwarin ido.
Olo my one &only Ina alfahari dake ked'in aminiya ce ta kwarai.Tare da aunty na
Maijidda musa da yayata barrister Fateen Bch.

*HAJJA CE NOVELS GRP*❤👍😍

*HASKE WRITER'S:-* kungiya ta Ina alfahari daku Allah ya k'ara baseera ya k'ara
had'e kawunan mu amin.

*HAJJA CE*👈

*HAJJA CE*👈

You might also like